Sashe 147
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta tashi da gudu ta nufi ɗaki tana kuka, saman gado ta zauna tana kunna wayarta, saƙon da ya shigo mata be bata mamaki ba saboda momi ta faɗa mata komai tun kamin Asim yayi mata wannan saƙon.
_Apple ɗin da kika ci Mahaifiyarki ce ta ba ni tace na kaiwa tsohuwar mamata, bayan kuma ta san na mutuwa ne, mahaifiyata ta ci ta mutu dan haka na yi ɗaukar fansa da ke_
_Ba ka yi kuskure ba Asim, Mahaifiyarta ta cancanci fiye da abunda ka yi mata, ni kuma na yi kuskuren yarda da kai, amman har gobe ina son ka_
Shine amsar da ta mayar masa, ta share hawayenta ta kwanta saman gado tana kallon window. Yayinda Hajiya Sadiya take tsaye a falo tana ta buge-bugen waya akan a taimaka mata kar ƴarta ta mutu, idan ta kira wannan tana kuka ta kira wannan duk ta bi ta haukace sai kuka take kamar zata tashi gidan. jin kamar ƴarta na tari yasa ta bar falon a guje ta nufi ɗakin tana kiran sunanta, amman ina Nably ta yi nisa har bata iya magana, duk ta ɓata gadon da aman jini kamar wacce ta amaye hanjin cikinta. Hannayenta biyu tasa tallafo kanta tana shafata.
“Nabila karki ta fi ki bar ni ke kaɗai kika rage min, na shiga uku na saka kai na a halaka, wannan baƙar ƙungiya bata min rana ba”
Kallonta kawai Nabila ke yi a wahalce tana numfashi da ker, hawaye na bin fuskarta har ta amsa kiran mahallicinta.
Wani uban ihu Hajiya Sadiya ta saki ta fita a ɗakin a guje, tana kaiwa harabar gidan ta zame ta faɗi ƙasa ba sumammiya.
UZAIR POV.
Wasa-wasa yau kusan talatin da ɗaya ana abu ɗaya babu sauƙi, sau biyu ana fita da shu waje amman babu abunda yake canjawa kuma ko ina aka je abu ɗaya ake faɗa cewar ba zai sake tafiya ba.
Tun ranar da ya aika Tahir be gane kan maganarshi ba, sai yawo yake ta masa da hankali, kullum da kalar abinda zai faɗa masa, kuma duk tsowon lokaci Yasmin bata taɓa taka asibitin da sunan ta zo ganin Uzair ba, abunda ya bawa kowa mamaki ciki har da Abbah. Ranar wata Lahadi duka ƴan'uwa suka saka ta gaba ana mata faɗa da tambayar dalilin ƙin zuwa ganin mijinta, amman ta kasa furta musu komai sai kuka take, a dole tasa suka ƙyaleta suka saka mata ido.
Ana sauran kwana biyu Abbah ya sake fitar da shi india, Tahir ya zo dubasa daman duk bayan kwana biyu yake zuwa ya gansa.
Yau ya fi bashi tausayi fiye da ko yaushe, ya rame sosai kamar ba abokinsa ba, wai yau Uzair ne kwance a nan baya iya komai, lallai duniya abun tsoro ce. Hawayen da ya gani a idon Uzair ya tashi hankalinsa sosai hakan yasa yau ya yanke shawara faɗa masa gaskiya, da kuma ba shi shawarar abunda yake tunanin zai zame masa mafita.
Ajiyar zuciya Tahir ya sauke yana kallon Uzair ya ce.
“Na yi ta maka wasa da hankali akan maganar Malamin nan, magana ta gaskiya Uzair mutumen baya raye, lokacin da naje gidansa na samu ranar ake sadakan bakwai nasa, na ɓoye maka ne saboda karka tashi hankalinka”
Wasu zafafan hawaye ne suka zubowa Uzair, ya haɗe yawun bakinsa cike da tausayin kansa ya ce.
“Tawa ta ƙare kenan! Haka ƙarshe na zai zo ni kuma? Ina ma ace mutuwa na yi na huta...”
Tahir ya dafa ƙafaɗarsa ya matsa kaɗan.
“ina tunanin abunda ya fi, ka samu Namra da iyayenta ka yi musu bayanin komai, kuma na nemu yafiyarsu, wata ƙila abunda ka aikata ne haƙƙi yake biye da kai, idan kuma har ba haka bane, to Amira ce ta yi maka asiri, idan zaka fallasa komai ka fallasa tare da Amira idan tana gurin, hakan zaisa guiwarta ta yi sanyi ta je ta kare abunda ta yi maka”
“Zan aikata Tahir indai har wannan zai sa na samu lafiyata, amman ya za'ayi Amira ta zo nan? Da wane ido zan kalli Abbah na ce ina son magana da Namra?”
“Zan kawo maka Amira, Namra kuma ka faɗawa Abbah kana son ganinta tare da Abbah”
Ya jinjina kai, shi dai ya shirya yin komai akan lafiyarsa, dan bai jin zai jure zama a irin wannan rayuwar. Bayan Tahir ya fita Mahaifiyarsa ta dawo ɗakin daman yanzu ita ce take jinyarsa ita da wani ƙanensa da kuma ƙanwarsa.
“Umma ina son ganin Abbah da Namra”
Ta kalleshi cike da mamaki.
“Ta maka me? Yarinyar da tun da ka kamu da rashin lafiyarnan bata taɓa cewa tana gaisheka ba balle ta zo duba ka ita zaka nemi gani yanzu?”
“Zan yi wata magana da ita mai muhimmanci, dan Allah ki taimaka min itace kawai mafitar wannan ciwon da nake yi, da ta zo zan samu sauƙi”
“Ban gane ba? Kamar ya itace mafitar ciwonka? Kana magana kamar wanda baya cikin hayyacinsa, Uzairu cuta fa ba mutuwa ba ce”
“Ki taimaka min ki kawo min ita mu yi magana zan faɗa muku komai,ciki har da dalilin daya sa Yasmin ta ƙi ta tako asibitin nan”
Da farko Umma ta ɗauka zafi ciwo ne yasa shi wannan maganar, daga baya kuma sai ta fahimci yana cikin hankalin kansa, sai dai maganganun da yake sun ɗaure mata kai.
Tahir na barin gidan ya nufi gidansu Amira, kamin ya isa sai da ya kira yayanta ya faɗa masa shi baya gida amman Amira tana gida. Harabar gidan ya shiga da motarsa, sannan mai gadin ya shiga ciki yace ana sallama da Amira, bayan ƴan mintuna ya dawo yace wai ance wanene?
“Kace Tahir ne abokin Big Bro”
Sai mai gadin ya koma, ya dawo ya ce wai ance ya shigo ciki. Ba musu ya doshi babbar ƙofar Falon. Da sallama ya shiga Ammy ta amsa masa tare da Amira sannan ya zauna, suka gaisa ya faɗa musu abunda yake tafe da shi. Ba Amira ba har Ammy ta yi mamakin jin Uzair na son ganinta to me zai ce mata? Bayan duk abunda yayi mata, daman tun da suka samu labarin bashi da lafiya Ammy da Abban Amira suke cewa wai amanar Amira ce ta kama shi.
“Yana nemana kamar ya ? Me zai ce mun?”
“Nima ban sani ba, amman yace maganar tana da muhimmanci, sosai”
Ammy ta ce
“To ba zata ita kaɗai ba, tare zamu je, kuma sai Abbah ta ya dawo duk abunda ya ce shi zamu yi”
Tahir ya miƙe tsaye yana faɗin
“Kamin na zo nan sai da na yi magana da Big bro, idan har wani abu ne mai cutar da ke ba zai bari na shigo nan na faɗa miki ba”
“Koma dai minene sai mahaifinta ya dawo”
“To hakan yayi, ni zan wuce”
“A gaida gida”
Ammy ta faɗa sannan ta bishi da kallo har ya fice. Gaɓa ɗaya jikin Amira yayi sanyi, zuciyarta sai yaye-yaye take mata, ta rasa dalilin da zai sa Uzair ya so ganinta, to ko yana zargin tana da hannu a ciwonsa ne? Ko kuma wani abun ne kuma ya faru? Maganar Abbah ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi.
“Bari na kira Abbah ki na faɗa masa”
Kai kawai ta iya ɗagawa ta cigaba da tunanin da take.
NAMRA POV.
Bayan an gama bikin Maryam da Hindatu, Abbah ya shiga fafutukar nemawa Namra Admissions a wata makarantar koyarda ilmin computer. Kasancewar duka jami'o'i a yanzu sun gama ɗaukar ɗalibai, gashi kuma bata da komai a yanzu saboda ƙonewar da takardunta suka yi a motarta lokacin da Asim ya taɓa haɗari, ba ƙaramin kuɗi Abbah ya kashe ba wajen fito mata da tsofin takardun da suke makarantar primary da kuma Secondary school. Jami'ah kuma sai next year zata fara, tun da ta riga ta lalata karatunta tun a wacan lokacin.
Sai dai wannan karon kan Alhamdulillah komai ya zo da sauƙi, kasancewar Abbah ya saki ƙuɗi cikin ƙanƙanen lokaci aka yi komai. Aiko murna gurin Anty Amaeya da Namra ba a magana kamar su haɗe Abbah, dan jindaɗi.
Monday mai zuwa Namra zata fara zuwa makaranta, ranar Assabar da Safe Abbah ya kawo mata sabon direba da zai riƙa kai ta makaranta, Namra ta yi murna sosai dan bata tsammaci haka daga gurin Abbah ba.
“Abbah ka yi min abubuwan da ban yi tsammani ba, ka nuna min sosai, Allah ya ba ni ikon saka maka”
Duk suka amsa da Amin har Anty Amarya dake ƙara jin son Abbah har cikin ɓargon ranta. Namra ta ɗauki ɗankwalin abayarta ta yafa ta fita dan ganin sabon direban nata. Tsaye tayi cak a baki ƙofa tana furta
“Lamido”
“Yes Ma'am”
Ya amsa a natse, yayi fari yayi kyau sosai ƙananna kayan da ke jikinsa sun ƙarɓe sa sosai. Ta nunashi da yatsa sai ta kasa magana. Murmushi yayi ya gabatar da kansa.
“My Name is Aliyu Adamu Lamido your new driver”
“How.... How....”
Maganar ta laƙe ta ƙi fitowa sai ta sake nuna shi da yatsa.
“You...”
Murmushi ya sake yi yana kallon yadda ta canja ta yi kyau kamar ba ita ba, baƙin nan nata sai sheƙi yake ga dogon hancin nan da farraren idonta da suka ƙara fitowa.
‘Black beauty akwai kyau’
A zuciyarsa yayi maganar a fili kuma murmushi yake mata mai ɗaukar hankali. Juyawa ta yi ta koma cikin falon, cike da ruɗani ta kalli Abbah ta ce.
“Abbah da gaske shine sabon direba na?”
“Eh ko be miki ba ne?”
“Me direban yayi”
Anty Amarya ta tambaya. Zaunawa Namra ta yi tana faɗin.
“Anty Lamido ne fa”
“Wane Lamido kin san shi ne?”
“A gidansu na sauka Kaduna, shi ya ɗinga ɗawainiya da ni har kuka zo kuka ɗauke ni, Lamido na gidansu Neina fa”
“Au shine? Ya akayi ya zo nan ne?”
“Nima ban sani ba, abun ya ɗaure min kai ne, Abbah ina ka haɗu da shi?”
“A can ƙamfani ya same ni, wai yana son a ɗauke shi direba idan zai samu, kuma baya son na kamfani na gida yake so, kin san daman ni kuma ina neman direban da zai riƙa kai ki scul yana maido ki, shiyasa na ɗauke shi”
Namra ta girgiza kai.
_Apple ɗin da kika ci Mahaifiyarki ce ta ba ni tace na kaiwa tsohuwar mamata, bayan kuma ta san na mutuwa ne, mahaifiyata ta ci ta mutu dan haka na yi ɗaukar fansa da ke_
_Ba ka yi kuskure ba Asim, Mahaifiyarta ta cancanci fiye da abunda ka yi mata, ni kuma na yi kuskuren yarda da kai, amman har gobe ina son ka_
Shine amsar da ta mayar masa, ta share hawayenta ta kwanta saman gado tana kallon window. Yayinda Hajiya Sadiya take tsaye a falo tana ta buge-bugen waya akan a taimaka mata kar ƴarta ta mutu, idan ta kira wannan tana kuka ta kira wannan duk ta bi ta haukace sai kuka take kamar zata tashi gidan. jin kamar ƴarta na tari yasa ta bar falon a guje ta nufi ɗakin tana kiran sunanta, amman ina Nably ta yi nisa har bata iya magana, duk ta ɓata gadon da aman jini kamar wacce ta amaye hanjin cikinta. Hannayenta biyu tasa tallafo kanta tana shafata.
“Nabila karki ta fi ki bar ni ke kaɗai kika rage min, na shiga uku na saka kai na a halaka, wannan baƙar ƙungiya bata min rana ba”
Kallonta kawai Nabila ke yi a wahalce tana numfashi da ker, hawaye na bin fuskarta har ta amsa kiran mahallicinta.
Wani uban ihu Hajiya Sadiya ta saki ta fita a ɗakin a guje, tana kaiwa harabar gidan ta zame ta faɗi ƙasa ba sumammiya.
UZAIR POV.
Wasa-wasa yau kusan talatin da ɗaya ana abu ɗaya babu sauƙi, sau biyu ana fita da shu waje amman babu abunda yake canjawa kuma ko ina aka je abu ɗaya ake faɗa cewar ba zai sake tafiya ba.
Tun ranar da ya aika Tahir be gane kan maganarshi ba, sai yawo yake ta masa da hankali, kullum da kalar abinda zai faɗa masa, kuma duk tsowon lokaci Yasmin bata taɓa taka asibitin da sunan ta zo ganin Uzair ba, abunda ya bawa kowa mamaki ciki har da Abbah. Ranar wata Lahadi duka ƴan'uwa suka saka ta gaba ana mata faɗa da tambayar dalilin ƙin zuwa ganin mijinta, amman ta kasa furta musu komai sai kuka take, a dole tasa suka ƙyaleta suka saka mata ido.
Ana sauran kwana biyu Abbah ya sake fitar da shi india, Tahir ya zo dubasa daman duk bayan kwana biyu yake zuwa ya gansa.
Yau ya fi bashi tausayi fiye da ko yaushe, ya rame sosai kamar ba abokinsa ba, wai yau Uzair ne kwance a nan baya iya komai, lallai duniya abun tsoro ce. Hawayen da ya gani a idon Uzair ya tashi hankalinsa sosai hakan yasa yau ya yanke shawara faɗa masa gaskiya, da kuma ba shi shawarar abunda yake tunanin zai zame masa mafita.
Ajiyar zuciya Tahir ya sauke yana kallon Uzair ya ce.
“Na yi ta maka wasa da hankali akan maganar Malamin nan, magana ta gaskiya Uzair mutumen baya raye, lokacin da naje gidansa na samu ranar ake sadakan bakwai nasa, na ɓoye maka ne saboda karka tashi hankalinka”
Wasu zafafan hawaye ne suka zubowa Uzair, ya haɗe yawun bakinsa cike da tausayin kansa ya ce.
“Tawa ta ƙare kenan! Haka ƙarshe na zai zo ni kuma? Ina ma ace mutuwa na yi na huta...”
Tahir ya dafa ƙafaɗarsa ya matsa kaɗan.
“ina tunanin abunda ya fi, ka samu Namra da iyayenta ka yi musu bayanin komai, kuma na nemu yafiyarsu, wata ƙila abunda ka aikata ne haƙƙi yake biye da kai, idan kuma har ba haka bane, to Amira ce ta yi maka asiri, idan zaka fallasa komai ka fallasa tare da Amira idan tana gurin, hakan zaisa guiwarta ta yi sanyi ta je ta kare abunda ta yi maka”
“Zan aikata Tahir indai har wannan zai sa na samu lafiyata, amman ya za'ayi Amira ta zo nan? Da wane ido zan kalli Abbah na ce ina son magana da Namra?”
“Zan kawo maka Amira, Namra kuma ka faɗawa Abbah kana son ganinta tare da Abbah”
Ya jinjina kai, shi dai ya shirya yin komai akan lafiyarsa, dan bai jin zai jure zama a irin wannan rayuwar. Bayan Tahir ya fita Mahaifiyarsa ta dawo ɗakin daman yanzu ita ce take jinyarsa ita da wani ƙanensa da kuma ƙanwarsa.
“Umma ina son ganin Abbah da Namra”
Ta kalleshi cike da mamaki.
“Ta maka me? Yarinyar da tun da ka kamu da rashin lafiyarnan bata taɓa cewa tana gaisheka ba balle ta zo duba ka ita zaka nemi gani yanzu?”
“Zan yi wata magana da ita mai muhimmanci, dan Allah ki taimaka min itace kawai mafitar wannan ciwon da nake yi, da ta zo zan samu sauƙi”
“Ban gane ba? Kamar ya itace mafitar ciwonka? Kana magana kamar wanda baya cikin hayyacinsa, Uzairu cuta fa ba mutuwa ba ce”
“Ki taimaka min ki kawo min ita mu yi magana zan faɗa muku komai,ciki har da dalilin daya sa Yasmin ta ƙi ta tako asibitin nan”
Da farko Umma ta ɗauka zafi ciwo ne yasa shi wannan maganar, daga baya kuma sai ta fahimci yana cikin hankalin kansa, sai dai maganganun da yake sun ɗaure mata kai.
Tahir na barin gidan ya nufi gidansu Amira, kamin ya isa sai da ya kira yayanta ya faɗa masa shi baya gida amman Amira tana gida. Harabar gidan ya shiga da motarsa, sannan mai gadin ya shiga ciki yace ana sallama da Amira, bayan ƴan mintuna ya dawo yace wai ance wanene?
“Kace Tahir ne abokin Big Bro”
Sai mai gadin ya koma, ya dawo ya ce wai ance ya shigo ciki. Ba musu ya doshi babbar ƙofar Falon. Da sallama ya shiga Ammy ta amsa masa tare da Amira sannan ya zauna, suka gaisa ya faɗa musu abunda yake tafe da shi. Ba Amira ba har Ammy ta yi mamakin jin Uzair na son ganinta to me zai ce mata? Bayan duk abunda yayi mata, daman tun da suka samu labarin bashi da lafiya Ammy da Abban Amira suke cewa wai amanar Amira ce ta kama shi.
“Yana nemana kamar ya ? Me zai ce mun?”
“Nima ban sani ba, amman yace maganar tana da muhimmanci, sosai”
Ammy ta ce
“To ba zata ita kaɗai ba, tare zamu je, kuma sai Abbah ta ya dawo duk abunda ya ce shi zamu yi”
Tahir ya miƙe tsaye yana faɗin
“Kamin na zo nan sai da na yi magana da Big bro, idan har wani abu ne mai cutar da ke ba zai bari na shigo nan na faɗa miki ba”
“Koma dai minene sai mahaifinta ya dawo”
“To hakan yayi, ni zan wuce”
“A gaida gida”
Ammy ta faɗa sannan ta bishi da kallo har ya fice. Gaɓa ɗaya jikin Amira yayi sanyi, zuciyarta sai yaye-yaye take mata, ta rasa dalilin da zai sa Uzair ya so ganinta, to ko yana zargin tana da hannu a ciwonsa ne? Ko kuma wani abun ne kuma ya faru? Maganar Abbah ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi.
“Bari na kira Abbah ki na faɗa masa”
Kai kawai ta iya ɗagawa ta cigaba da tunanin da take.
NAMRA POV.
Bayan an gama bikin Maryam da Hindatu, Abbah ya shiga fafutukar nemawa Namra Admissions a wata makarantar koyarda ilmin computer. Kasancewar duka jami'o'i a yanzu sun gama ɗaukar ɗalibai, gashi kuma bata da komai a yanzu saboda ƙonewar da takardunta suka yi a motarta lokacin da Asim ya taɓa haɗari, ba ƙaramin kuɗi Abbah ya kashe ba wajen fito mata da tsofin takardun da suke makarantar primary da kuma Secondary school. Jami'ah kuma sai next year zata fara, tun da ta riga ta lalata karatunta tun a wacan lokacin.
Sai dai wannan karon kan Alhamdulillah komai ya zo da sauƙi, kasancewar Abbah ya saki ƙuɗi cikin ƙanƙanen lokaci aka yi komai. Aiko murna gurin Anty Amaeya da Namra ba a magana kamar su haɗe Abbah, dan jindaɗi.
Monday mai zuwa Namra zata fara zuwa makaranta, ranar Assabar da Safe Abbah ya kawo mata sabon direba da zai riƙa kai ta makaranta, Namra ta yi murna sosai dan bata tsammaci haka daga gurin Abbah ba.
“Abbah ka yi min abubuwan da ban yi tsammani ba, ka nuna min sosai, Allah ya ba ni ikon saka maka”
Duk suka amsa da Amin har Anty Amarya dake ƙara jin son Abbah har cikin ɓargon ranta. Namra ta ɗauki ɗankwalin abayarta ta yafa ta fita dan ganin sabon direban nata. Tsaye tayi cak a baki ƙofa tana furta
“Lamido”
“Yes Ma'am”
Ya amsa a natse, yayi fari yayi kyau sosai ƙananna kayan da ke jikinsa sun ƙarɓe sa sosai. Ta nunashi da yatsa sai ta kasa magana. Murmushi yayi ya gabatar da kansa.
“My Name is Aliyu Adamu Lamido your new driver”
“How.... How....”
Maganar ta laƙe ta ƙi fitowa sai ta sake nuna shi da yatsa.
“You...”
Murmushi ya sake yi yana kallon yadda ta canja ta yi kyau kamar ba ita ba, baƙin nan nata sai sheƙi yake ga dogon hancin nan da farraren idonta da suka ƙara fitowa.
‘Black beauty akwai kyau’
A zuciyarsa yayi maganar a fili kuma murmushi yake mata mai ɗaukar hankali. Juyawa ta yi ta koma cikin falon, cike da ruɗani ta kalli Abbah ta ce.
“Abbah da gaske shine sabon direba na?”
“Eh ko be miki ba ne?”
“Me direban yayi”
Anty Amarya ta tambaya. Zaunawa Namra ta yi tana faɗin.
“Anty Lamido ne fa”
“Wane Lamido kin san shi ne?”
“A gidansu na sauka Kaduna, shi ya ɗinga ɗawainiya da ni har kuka zo kuka ɗauke ni, Lamido na gidansu Neina fa”
“Au shine? Ya akayi ya zo nan ne?”
“Nima ban sani ba, abun ya ɗaure min kai ne, Abbah ina ka haɗu da shi?”
“A can ƙamfani ya same ni, wai yana son a ɗauke shi direba idan zai samu, kuma baya son na kamfani na gida yake so, kin san daman ni kuma ina neman direban da zai riƙa kai ki scul yana maido ki, shiyasa na ɗauke shi”
Namra ta girgiza kai.