Sashe 16
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Toh ai ba'a ɗaura mana aure ba, amman dai idan na aure ta zaki ga soyayyah ba ni ba har ke sai tayi feeding ɗin ki”
“May God forbid ,kuma Allah ya tsine mata albarka”
Ta tashi ta nufi ɗakinta da kuka, shi kuma ya bita da murmushi yana jin son matar tasa har cikin ranshi.
UZAIR POV.
A mota ɗaya suke zaune shi da Najeeb, suna jiran fitowar Amira.
Sai ta ɓata musu lokaci, sannan ta fito sanye da abaya, tazo tayi musu tsaye tana hararar Uzair.
“Me ya kawo ka gidan mu?”
“Shiga mota zamu yi magana”
Ba musu ta buɗe motar ta shiga gidan baya ta zauna. Sai da ya gabatar mata da Najeeb sannan ya faɗa mata abunda ya kawo su.
“Lallai Uzair ban zaci zaka iya zuwa da wata buƙatar a gare ba, kira nawa nayi maka amman baka ji ba, yanzu ka haɗa ni da ƙawata har ta fara zargina”
Najeeb yayi murmushi mai sauti.
“Wannan ita kaɗaice mafita a gareki a gare mu kuma gaba ɗaya, kin ga idan mun aikata haka har ke asirinki zai rufu, amman idan asirinki ya tonu zaki fi kowa shiga cikin matsala”
Shiru tayi tana tunani.
“Amman nawa zaka biya ni?”
Uzair yayi murmushi.
“Zan baki 100k yanzu idan aiki ya yi zan baki 300k har abunda ya yi sama, amman ki tabbatar ta saka rigar”
“Taya zan iya tabbatar wa tun da ba tsare ta zan yi ba?”
“Ko ya ya zakiyi a kin sani tun da ke mace ce kuma Aminiyarta, idan ta kama sai ki kwana a gidan, yanzu dai kije ki karɓo mana rigar da dare zamu zo mu karɓa”
Cewar Najeeb.
“Naji amman ni ba zanje gurin wani Malami ba, kuje ku yanke min kai”
Duk dariya sukayi, sai Uzair yace
“Mun ji amman dai ki tabbatar rigar data taɓa sakawa ce, zan miki transfer 100k an jima”
Uzair be yarda ya faɗa mata abun ze iya dawawa idan be kamata ba, sai kawai ya ƙaleta har ta buɗe motar tayi ta fita.
Su kuma suka yi kwana suka wuce, daman baki gate suka tsaya basu shiga ciki ba.
Cikin gidan ta koma, a tsakar gida ta samu Ammy da Yayanta a tsaye suna magana, sai ta wuce ciki ta ɗauko handbag ɗinta sannan ta cewa Ammy zata je ta duba Namra.
“Kice ina gaishe ta dan Allah”
Cewar Ammy, sai ta fice tana faɗin
“Toh zan faɗa mata”
Waje ta fito ta tari mai napep ta shiga. Lokacin data shiga falon Anty Amarya ce kawai a zaune, su Maryam da Hindatu duk sun tafi makaranta, Mama Zainab kuma tun jiya da yamma suka kama hanya.
Har ƙasa ta risina ta gaishe da Anty Amarya sannan ta tambayi Namra, Anty Amarya tace mata tana ɗakinki sai ta tashi sun-sun ta nufi ɗakin.
Namra na kwance saman gadonta tana hawaye.
Kusa da ita ta zauna ta kai hannu ta riƙa hannunta.
“Haba Namra yanzu kina ganin kukan naki maganin ne?”
Tasowa Namra tayi ta rumgume Amira.
“Amira kowa fushi yake da ni, ina jin tsoro Amira”
“Tsoron me?”
“Ina tsoron kar ace sun taɓa min mutunci”
Amira ta fara hawaye.
“Nima ina wannan tunani Namra, kuma idan har haka ta tabbata kika yi ciki kin gama wulaƙanta a rayuwarki ta duniya”
Ƙara fashewa Namra tayi da kuka.
“Wallahi duk na gano wanda yayi min wannan abu sai na kashe ki, sai na masa wulakacin mafi ƙasƙanci a duniya”
Gaban Amira ya faɗi, ji take kamar da ita Namra take.
“Mafita ɗaya ce Namra, ki gwada shan magani da haila zata zo miki, kin ga ko da kina da cikin sai ya zube, tun ba daɗe ba”
Namra ta ɗago ta kalleta
“Amman ba ni da tabbaci”
“Shiyasa nace ki sha ɗin, kin ga idan ma anyi ko ba'ayi ba ke dai kin san babu ciki a tare da ke”
“Ina zan samu maganin?”
“Zan nemo miki, zan bincika na siyo miki”
“Na gode sosai Amira Allah ya bar zumunci, amman har yanzu baki da labarin Asim”
“Wallahi har yanzu, amman ki kwantar da hankalinki na san zai dawo komai daren daɗewa”
“Allah yasa”
“Amin, ni bari na tashi na tafi, daman gurin ɗinki zanje sai nace bari na biyo na duba ki, daga nan na ari rigarki ta atamfa”
“Gashi can je ki duba wanda kike so”
“Na jikin ki zaki ara min, dan bana son ɗinki mai hayaniya”
Ba tare da tunanin komai ba, Namra ta tashi ta cire rigar ta miƙa mata tare da zane sai ta saka wata gown.
“Ai dama kin bar Zanen tun da ba shida wani style, rigar kawai nake so”
Mayarda zanen Namra tayi ta aje, ta ɗauko mata jaka ta saka rigar, sannan ta tashi tana faɗin.
“Bari na je kar Ammy ta ga na daɗe tace na gaishe ki”
“Ina amsawa yaushe zako dawo?”
“Da na siyo maganin zan zo na kawo miki, amman ki kwantar da hankalin ki kinji?”
Kai kawai Namra ta ɗaga mata.Sai Amira tayi mata sallama ta fice.
Bayan fitar Amira Anty Amarya ta shigo ɗakin. Ɗaga bakin ƙofa ta tsaya tace
“Uzair ya janye zancen Auren shi dake yace shi ya haƙura, Abbah ki yace shi ba zai sake miki zaɓi ba ki kawo Asim ɗin zai ɗaura miki aure da shi”
Anty Amarya na kaiwa nan ta juya ta fice. A maimakon ta ji farinciki, sai kawai ta ji wani kalar abu ya baibaye ta, shi ba farinciki ba kuma ba baƙinciki ba. Sai kawai ta rushe da kuka.
Amira na fita gidan ta kira Uzair ta faɗa nasa yadda sukayi da Namra, ya jidaɗin abunda Amira tayi tun da yana ganin ta nan zasu samu mafita. Da dare yazo ya karɓi rigar, yace mata jibi ze kawo mata tare da maganin.
RASHIDA POV.
Tun da safe tayi shirin office, wace ke fita takwas ko takwas da rabi yau tun shida ta bar masa gidan, tun jiya da dare kuma ta ƙi sake masa sai fushi take dashi.
Kai tsaye gidan su ta nufa, Mahaifiyarta tayi mamakin ganin ta tun da sanyin safiya, ga fuska duk hawaye.
“Ke lafiya?”
Sai kawai ta faɗa jikinta tana kuka. Sai duk ta rikita mahaifiyarta a zatonta ma ko sun yi faɗa da Hilal ne ko kuma wani ne ya mutu. Sai da tayi kukanta mai isarta sannan ta faɗa mata abunda ya faru.
“Mom wai Hilal aure ze ƙara”
“Amman shine kika zo kika ta da mun hankali na ɗauka ko wani abun ne ma? Toh dan ze yi aure hana shi zakiyi ko me? Ke kaɗai aka ce masa ya aura?”
“Mom kishiya fa ze min ko baki gane ba”
“Na gane mana, ba'a aure ke aka aureki? Tun yaushe yake miki zancen ƙarin aure?”
“Mom wannan karon da gaske yake”
“Toh idan da gaske yake sai me? Hana shi auren zaki yi? Ke idan mai hankali ce ai da kanki ma kyace masa yaje yayi aure, duk irin haƙurin da yake da ke, idan ma yayi auren ai sai ki samu me riƙa miki yaranki”
Ɗaukar gyalenta tayi ta yafa ta ɗauki jakarta
“Ai daman nasan ba zaki goya min baya ba”
“Oh so kike na goya miki baya ki yima mijinki rashin mutunci ko? Shine kika wani ɗauko gyale kika zo gida ko kunya baki ji, kuma Wallahi bari jiki na faɗa miki kar ki biye son zuciyarki kije ki kawa kanki, kar naji wata matsala ta shiga tsakanin ki da mijinki akan auren nan”
Ficewa tayi tana hawaye tana faɗin
“Ba zan sake zuwa gidan nan ba”
Mom taja tsaki ta tashi ta nufi bathroom.
NAMRA POV.
Haka Anty Amarya ta kwashe kusan kwana huɗu babu ruwanta da Namra, ita kuma tana cikin ɗaki ta kasa fitowa kullum sai kuka take da ƙaratun Ƙur'ane, abun duniya duk ya isheta ji take kamar ta kashe kanta ta huta.
Bayan sauko Sallah Jumma'ah Namra ta tashi ta shiga banɗaki tayi alkwala ta fito ta gabatar da Sallah Azahar, bayan ta ƙare ta ɗauko Ƙur'ane tana karantawa.
Ta tsagaita karatun ne lokacin data ji sallamar Amira, sai da bata tsaya ba sai da ta kai ƙarshen aya, sannan tayi addu'ah ta rufe Ƙur'ane, ta juyo ta kalli Amira.
“Amira”
“Na'am”
A kasale Amira ta amsa mata, dan jikinta ya gama mutuwa tun ɗazu, gashi ko ɗazu sai da Uzair ya jaddada mata baya son a samu matsala.
Sai da Namra ta kai Ƙur'ane mazauninsa ta aje sannan tazo ta zauna kusa da Amira.
“Amira tun ranar ban ganki ba, gashi bana da waya balle na kira ki”
“Wallahi ban samu zama bane kinsan ga makaranta, wai miyasa kika daina zuwa ne mutane sai tambayarki suke”
“Amira kunyar shiga makaranta nake yanzu, a gida ma na kasa sakewa balle makaranta”
“Amman da kin daure ai tun da gani, zai riƙa cire miki kewa, kin ga yanzu fa kina ajin ƙarshe idan kika ce ba zakije ba duk wacan karatun naki zai tafi a banza fa”
Namra ta sauke ajiyar zuciya.
“Ni dai ba wannan ba, kin kawo min magani?”
“Na kawo miki gashi a jaka na, amman ban zan baki ba har sai kin min alƙawarin zaki saka atamfar nan mu fita tare da ke, dan zaman nan ke kaɗai shi ke ƙara miki tunani”
Ta ƙarasa ta ciro rigara daga jaka.
“Ba zan iya ba Amira bana iya fita ko ina yanzu”
“Ni dai ko cikin gida ne”
“Naji yanzu ina maganin?”
“Gashi nan”
Ta ciro ta miƙa mata.
“Gashi amman yace idan kina son yayi sauri zo miki toh ki sha huɗu, kuma yace idan kin sha ki ɗan yawata”
A take Namra ta karɓa ta ɓare huɗu ta shiga bathroom ta sha. Tana fitowa Amira ta miƙa mata rigar.
“Tun jiya na wanke miki ita, ɗinkin nan yaɓa fitar dake ke, je ki saka sai mu fita ko garden ne mu zagaya”
“May God forbid ,kuma Allah ya tsine mata albarka”
Ta tashi ta nufi ɗakinta da kuka, shi kuma ya bita da murmushi yana jin son matar tasa har cikin ranshi.
UZAIR POV.
A mota ɗaya suke zaune shi da Najeeb, suna jiran fitowar Amira.
Sai ta ɓata musu lokaci, sannan ta fito sanye da abaya, tazo tayi musu tsaye tana hararar Uzair.
“Me ya kawo ka gidan mu?”
“Shiga mota zamu yi magana”
Ba musu ta buɗe motar ta shiga gidan baya ta zauna. Sai da ya gabatar mata da Najeeb sannan ya faɗa mata abunda ya kawo su.
“Lallai Uzair ban zaci zaka iya zuwa da wata buƙatar a gare ba, kira nawa nayi maka amman baka ji ba, yanzu ka haɗa ni da ƙawata har ta fara zargina”
Najeeb yayi murmushi mai sauti.
“Wannan ita kaɗaice mafita a gareki a gare mu kuma gaba ɗaya, kin ga idan mun aikata haka har ke asirinki zai rufu, amman idan asirinki ya tonu zaki fi kowa shiga cikin matsala”
Shiru tayi tana tunani.
“Amman nawa zaka biya ni?”
Uzair yayi murmushi.
“Zan baki 100k yanzu idan aiki ya yi zan baki 300k har abunda ya yi sama, amman ki tabbatar ta saka rigar”
“Taya zan iya tabbatar wa tun da ba tsare ta zan yi ba?”
“Ko ya ya zakiyi a kin sani tun da ke mace ce kuma Aminiyarta, idan ta kama sai ki kwana a gidan, yanzu dai kije ki karɓo mana rigar da dare zamu zo mu karɓa”
Cewar Najeeb.
“Naji amman ni ba zanje gurin wani Malami ba, kuje ku yanke min kai”
Duk dariya sukayi, sai Uzair yace
“Mun ji amman dai ki tabbatar rigar data taɓa sakawa ce, zan miki transfer 100k an jima”
Uzair be yarda ya faɗa mata abun ze iya dawawa idan be kamata ba, sai kawai ya ƙaleta har ta buɗe motar tayi ta fita.
Su kuma suka yi kwana suka wuce, daman baki gate suka tsaya basu shiga ciki ba.
Cikin gidan ta koma, a tsakar gida ta samu Ammy da Yayanta a tsaye suna magana, sai ta wuce ciki ta ɗauko handbag ɗinta sannan ta cewa Ammy zata je ta duba Namra.
“Kice ina gaishe ta dan Allah”
Cewar Ammy, sai ta fice tana faɗin
“Toh zan faɗa mata”
Waje ta fito ta tari mai napep ta shiga. Lokacin data shiga falon Anty Amarya ce kawai a zaune, su Maryam da Hindatu duk sun tafi makaranta, Mama Zainab kuma tun jiya da yamma suka kama hanya.
Har ƙasa ta risina ta gaishe da Anty Amarya sannan ta tambayi Namra, Anty Amarya tace mata tana ɗakinki sai ta tashi sun-sun ta nufi ɗakin.
Namra na kwance saman gadonta tana hawaye.
Kusa da ita ta zauna ta kai hannu ta riƙa hannunta.
“Haba Namra yanzu kina ganin kukan naki maganin ne?”
Tasowa Namra tayi ta rumgume Amira.
“Amira kowa fushi yake da ni, ina jin tsoro Amira”
“Tsoron me?”
“Ina tsoron kar ace sun taɓa min mutunci”
Amira ta fara hawaye.
“Nima ina wannan tunani Namra, kuma idan har haka ta tabbata kika yi ciki kin gama wulaƙanta a rayuwarki ta duniya”
Ƙara fashewa Namra tayi da kuka.
“Wallahi duk na gano wanda yayi min wannan abu sai na kashe ki, sai na masa wulakacin mafi ƙasƙanci a duniya”
Gaban Amira ya faɗi, ji take kamar da ita Namra take.
“Mafita ɗaya ce Namra, ki gwada shan magani da haila zata zo miki, kin ga ko da kina da cikin sai ya zube, tun ba daɗe ba”
Namra ta ɗago ta kalleta
“Amman ba ni da tabbaci”
“Shiyasa nace ki sha ɗin, kin ga idan ma anyi ko ba'ayi ba ke dai kin san babu ciki a tare da ke”
“Ina zan samu maganin?”
“Zan nemo miki, zan bincika na siyo miki”
“Na gode sosai Amira Allah ya bar zumunci, amman har yanzu baki da labarin Asim”
“Wallahi har yanzu, amman ki kwantar da hankalinki na san zai dawo komai daren daɗewa”
“Allah yasa”
“Amin, ni bari na tashi na tafi, daman gurin ɗinki zanje sai nace bari na biyo na duba ki, daga nan na ari rigarki ta atamfa”
“Gashi can je ki duba wanda kike so”
“Na jikin ki zaki ara min, dan bana son ɗinki mai hayaniya”
Ba tare da tunanin komai ba, Namra ta tashi ta cire rigar ta miƙa mata tare da zane sai ta saka wata gown.
“Ai dama kin bar Zanen tun da ba shida wani style, rigar kawai nake so”
Mayarda zanen Namra tayi ta aje, ta ɗauko mata jaka ta saka rigar, sannan ta tashi tana faɗin.
“Bari na je kar Ammy ta ga na daɗe tace na gaishe ki”
“Ina amsawa yaushe zako dawo?”
“Da na siyo maganin zan zo na kawo miki, amman ki kwantar da hankalin ki kinji?”
Kai kawai Namra ta ɗaga mata.Sai Amira tayi mata sallama ta fice.
Bayan fitar Amira Anty Amarya ta shigo ɗakin. Ɗaga bakin ƙofa ta tsaya tace
“Uzair ya janye zancen Auren shi dake yace shi ya haƙura, Abbah ki yace shi ba zai sake miki zaɓi ba ki kawo Asim ɗin zai ɗaura miki aure da shi”
Anty Amarya na kaiwa nan ta juya ta fice. A maimakon ta ji farinciki, sai kawai ta ji wani kalar abu ya baibaye ta, shi ba farinciki ba kuma ba baƙinciki ba. Sai kawai ta rushe da kuka.
Amira na fita gidan ta kira Uzair ta faɗa nasa yadda sukayi da Namra, ya jidaɗin abunda Amira tayi tun da yana ganin ta nan zasu samu mafita. Da dare yazo ya karɓi rigar, yace mata jibi ze kawo mata tare da maganin.
RASHIDA POV.
Tun da safe tayi shirin office, wace ke fita takwas ko takwas da rabi yau tun shida ta bar masa gidan, tun jiya da dare kuma ta ƙi sake masa sai fushi take dashi.
Kai tsaye gidan su ta nufa, Mahaifiyarta tayi mamakin ganin ta tun da sanyin safiya, ga fuska duk hawaye.
“Ke lafiya?”
Sai kawai ta faɗa jikinta tana kuka. Sai duk ta rikita mahaifiyarta a zatonta ma ko sun yi faɗa da Hilal ne ko kuma wani ne ya mutu. Sai da tayi kukanta mai isarta sannan ta faɗa mata abunda ya faru.
“Mom wai Hilal aure ze ƙara”
“Amman shine kika zo kika ta da mun hankali na ɗauka ko wani abun ne ma? Toh dan ze yi aure hana shi zakiyi ko me? Ke kaɗai aka ce masa ya aura?”
“Mom kishiya fa ze min ko baki gane ba”
“Na gane mana, ba'a aure ke aka aureki? Tun yaushe yake miki zancen ƙarin aure?”
“Mom wannan karon da gaske yake”
“Toh idan da gaske yake sai me? Hana shi auren zaki yi? Ke idan mai hankali ce ai da kanki ma kyace masa yaje yayi aure, duk irin haƙurin da yake da ke, idan ma yayi auren ai sai ki samu me riƙa miki yaranki”
Ɗaukar gyalenta tayi ta yafa ta ɗauki jakarta
“Ai daman nasan ba zaki goya min baya ba”
“Oh so kike na goya miki baya ki yima mijinki rashin mutunci ko? Shine kika wani ɗauko gyale kika zo gida ko kunya baki ji, kuma Wallahi bari jiki na faɗa miki kar ki biye son zuciyarki kije ki kawa kanki, kar naji wata matsala ta shiga tsakanin ki da mijinki akan auren nan”
Ficewa tayi tana hawaye tana faɗin
“Ba zan sake zuwa gidan nan ba”
Mom taja tsaki ta tashi ta nufi bathroom.
NAMRA POV.
Haka Anty Amarya ta kwashe kusan kwana huɗu babu ruwanta da Namra, ita kuma tana cikin ɗaki ta kasa fitowa kullum sai kuka take da ƙaratun Ƙur'ane, abun duniya duk ya isheta ji take kamar ta kashe kanta ta huta.
Bayan sauko Sallah Jumma'ah Namra ta tashi ta shiga banɗaki tayi alkwala ta fito ta gabatar da Sallah Azahar, bayan ta ƙare ta ɗauko Ƙur'ane tana karantawa.
Ta tsagaita karatun ne lokacin data ji sallamar Amira, sai da bata tsaya ba sai da ta kai ƙarshen aya, sannan tayi addu'ah ta rufe Ƙur'ane, ta juyo ta kalli Amira.
“Amira”
“Na'am”
A kasale Amira ta amsa mata, dan jikinta ya gama mutuwa tun ɗazu, gashi ko ɗazu sai da Uzair ya jaddada mata baya son a samu matsala.
Sai da Namra ta kai Ƙur'ane mazauninsa ta aje sannan tazo ta zauna kusa da Amira.
“Amira tun ranar ban ganki ba, gashi bana da waya balle na kira ki”
“Wallahi ban samu zama bane kinsan ga makaranta, wai miyasa kika daina zuwa ne mutane sai tambayarki suke”
“Amira kunyar shiga makaranta nake yanzu, a gida ma na kasa sakewa balle makaranta”
“Amman da kin daure ai tun da gani, zai riƙa cire miki kewa, kin ga yanzu fa kina ajin ƙarshe idan kika ce ba zakije ba duk wacan karatun naki zai tafi a banza fa”
Namra ta sauke ajiyar zuciya.
“Ni dai ba wannan ba, kin kawo min magani?”
“Na kawo miki gashi a jaka na, amman ban zan baki ba har sai kin min alƙawarin zaki saka atamfar nan mu fita tare da ke, dan zaman nan ke kaɗai shi ke ƙara miki tunani”
Ta ƙarasa ta ciro rigara daga jaka.
“Ba zan iya ba Amira bana iya fita ko ina yanzu”
“Ni dai ko cikin gida ne”
“Naji yanzu ina maganin?”
“Gashi nan”
Ta ciro ta miƙa mata.
“Gashi amman yace idan kina son yayi sauri zo miki toh ki sha huɗu, kuma yace idan kin sha ki ɗan yawata”
A take Namra ta karɓa ta ɓare huɗu ta shiga bathroom ta sha. Tana fitowa Amira ta miƙa mata rigar.
“Tun jiya na wanke miki ita, ɗinkin nan yaɓa fitar dake ke, je ki saka sai mu fita ko garden ne mu zagaya”