Sashe 66
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hawaye ya fara bin fuskarsa.
“Kai yi min abunda wani be taɓa min ba, ko a mafarki ban za ci zaka aikata min ba, Asim ka yi taɓon da har na koma ga mahallacin na ba zai gogu ba, baka tambaye ni waye ba, baka bincike alaƙa ta da shi ba, sai kawai ka zarge ni, ka ɗaga hannunka ka mareni”
Ya fara mata kuka kamar gaske.
“Na san ban kyauta ba, kuma na cancanci ko wane irin hukumci, amman ki dubi girman Allah ki yafe min, dan Allah karki faɗawa kowa abun da ya faru tsakaninmu, Wallahi idan har ki ka bar zan iya shiga ko wane irin hali, haƙiƙa ni butulu ne kuma ajizi, Namra ki dubi girman ƙaunar dake tsakanin mu ki yafe min, ni har ganin nake kamar shiga tsakani ne”
“Ban faɗawa kowa ba, kuma ba zan faɗa ba, kuma na yafe maka”
“Na gode Allah yayi miki albarka, dan yaushe zaki dawo? Ko nasa Mama ta zo taje da ke?”
“Ba sai ta zo ba, zan dawo cikin satin nan”
“Yaushe?”
“Nan da kwana uku”
“Kwana uku yayi nisa Namra, da a'ce da hali sai ki dawo gobe ko jibi”
“Sai jibin dai”
“Na gode sosai Allah yayi miki albarka, duk suna lafiya ko?”
“Kowa ƙalau”
“Ina gaida kowa dan Allah”
“Za su ji”
“Na gode sai na ƙara kira”
Ta sauke wayar tana cigaba da hawaye.
“Na yafe maka, amman ba zan manta ba, zan zauna da kai saboda zama da kai ya zame min dole, son ka be amfana min komai ba Asim sai baƙinciki da damuwa”
Ta share hawayenta tana jin wani irin ƙuna da zuciyarta ke mata. Ɗan abincin da take ci sai ya fita ranta, ta tattara kayan abinci ta ɗauki tray ta nufi kitchen da shi, bayan ta aje ta dawo falonta zauna tana miƙawa Anty wayarta.
“Har kun gama”
“Eh wai tambaya yake yaushe zan dawo”
“Dika yaushe kika zo? Me kika ce masa”
“Nace masa sai Next week amman ya ce sai dai na dawo gobe, daker ya haƙura na kai jibi”
“Haba Anty Namra dika yaushe kika zo ma?”
Maryam ta faɗa. Anty tace
“Zan yi magana da shi ya bar ki kiyi ko wata ɗaya”
“A'a Anty kin san ba shida lafiya sosai ma, kuma bana son satin da Abbah ya bani ya cika ban koma ba”
Ɗaya bayan ɗaya Anty ta bisu da kallo, a tunaninta ko a cikinsu ne wani ya faɗa mata Abbah yace karta wuce sati ɗaya.
Maryam ce ta fara tsarguwa da kallon Anty ta yi magana.
“Wallahi ba ni na faɗa ba”
Aisha
“Ni ma dai”
Hindatu.
“Balle kuma ni”
“Waya faɗa? Ko muna da aljanu ne a gidan?”
Namra tayi murmushi, irin murmushin nan na ƙarfin hali ka danne baƙincikin ka.
“Ba suka faɗa ba, Abbah ne ya faɗa min da kan sa”
“Yaushe?”
“Jiya da naje gaishe shi, yau ma ya nanata min”
Anty tayi shiru bata sake cewa komai ba. Sai dai bata jidaɗin da Abbah ya faɗama Namra haka ba.
“Akwai abubuwan da kike buƙata ne? Dan a siya da wuri kar lokaci ya ƙure, ko kuma kuɗi zan baki kije can ki siya?”
“Kuɗin zai fi, dan ɗaukar kaya a nan ma ai aiki ne”
“Amman Namra ba zai yarda ku dawo nan ba?”
“Kwana ki ma yayi min maganar haka, amman nace ya haƙura har yaji sauƙi sosai sannan mu dawo”
“Gaskiya kam zama a nan zai fi, kim ga nan zai fi muku kuma kin ga nan ko ba komai kina kusa da mu”
Sallamar Doc Faruk ne yasa suka katse firar da suke suka amsa sallamar suna masa sannu da zuwa.
A kujerar da Namra take zaune ya zauna, kasancewar ta zaman mutum uku ce, sai ya soma gaiswa da Anty cikin far'ah, tun da shi ba baƙon gidan ba ne.
Maryam da Hindatu da Aisha sai duk suka tashi suka bashi guri, Anty ma tana gama gaisawa da shi, ta shige ɗakinta dan tasan abunda ya kawo shi, daman ita ta kira shi, ganin hakan kamar zai fi sauƙi tun da likitan gida ne.
“Daman akan maganar planning ne Anty tana tsoro kar ayi mai side effects, so ni abunda naƙe ganin ya fi shine ki yi na roba, saboda idan an saka mishi kin ga sai lokacin yayi sannan za'a cire, ba kamar allura bane da a za'a riƙa yi duk months, kuma kin ga shan ƙwayoyin zai iya ƙara miki matsala ma a mahaifa, za a iya tsuke miki bakin mahaifa”
“Amman robar idan an saka ba shi da wata illa ne?”
“Eh to kin san komai karɓa karɓa ne, amman gaskiya baya da matsaloli kamar sauran, kuma kin ga shi a duk lokacin da aka tashi cire miki za'a iya cirewa”
“Amman yanzu ina katsina da zama idan na saka ta nan za'a iya cire min a can?”
“Za'a iya cire miki mana, amman idan son samu ne inda aka saka miki a cire miki ita, saboda aikin wani ba shine aikin wani ba, kuma idan ma son samu ne likitan daya saka miki ita ya zama dik lokaci shine ya ke duba ki”
“Amman kana ganin ba zai haifar minnda matsala nan gaba ba?”
“Gaskiya bana jin zai haifar miki da matsala, indai ba abunda Allah ya kawo ba, sai dai kinsan komai yana da side effects sai dai wani ya fi wani”
“Okay, ba matsala when za'a saka?”
“Ko yaushe kika tashi, a hannun hagu ake sakawa kuma idan an saka miki ba zaki yi aikin da hannun ba tsawon 24h, amman za mu buƙaci sa hannun mijinki kamin mu saka miki”
“Mijina baya tare da ni yana Katsina, kuma idan da hali ina son a saka min gobe”
“Consider it done, zan yi replacement ɗin mijinki a gurin sa hannu ko da wannan zan yi alfahari”
Tayi kamar bata ji shi, sai ta tashi ta nufi ɗakin Anty tana faɗin
“Zan shiga ciki”
“Around nine za ku shigo”
Ya faɗa sannan shi ma.yasa kai ya fice.
“Mun yi magana da shi zai saka min roba ta hannu”
Ta faɗa tana ƙoƙarin zama kusa da Anty.
“Ta shekara nawa? Ita bata da matsala kamar sauran ko?”
“Eh haka ya ce, gobe da safe za mu shiga”
“Allah ya kai mu, ya baki lafiya”
“Amin”
Kwantawa tayi saman gado, Anty ta tashi ta fita.
Washen garin ranar da yace musu suka tafi aka saka mata, duk wani shirin a ranar Anty tayi mata shi, saboda komawar da zata yi gobe.
Hajiya Barau tayi mamakin komawarta da wuri haka, a take ta raya a zuciyarta ƙila Abbah ne yace be yarda ta daɗe masa a gida ba, ita tama yi mamakin da ya barta har ta zauna, goma na arziki ta haɗa mata, tun daga kan kayan sawa zuwa kuɗi da kayan mata.
Ranar da zata koma taje yi ma Abbah sallama, ranar ta sha kuka kamar ranar da za'a kaita ɗakinta, Anty ma tayi kuka sosai har hakan ya saka sauran ƴaƴan na ta kuka.
Direban gidan aka sa ya kaita har katsina dan Anty bata son ta shiga motar haya. Sai da ta biya gidan Gwaggo tayi mata sallama sannan suka kama hanyar katsina.
RASHIDA POV.
Washe garin ranar data dawo Malamin ya kira yana labarta mata bayanin da ƙasa ta bada akanta.
“Ba zaki taɓa komawa gidan Mijin ki ba, matuƙar wannan matar tana cikin gidan, sannan idan baki tashi tsaye ba, to har ƴaƴanki mijinki zai wulaƙanta su akan ta, kuma kin yi kuskuren ba mu suna, Ummu Kalsoom take ba Ummulkhairi ba”
“Na ɗauka ai duka ɗaya ne”
“Ba ɗaya bane, sannan mun ga wani baƙin hudu a tare da ke, kuma bayani ya nuna a halin yanzu tana sama da ke sai kin tashi tsaye”
“Malam wane irin baƙin abu ne wannan?”
Duk ta tsorta.
“Bayani be fito mana fili ba, amman lailai akwai baƙin abu yana biye da ke, kuma akwai abu a jikinki wanda kike ɓoyewa dangin ki”
“To Malam a taimaka ayi mana aiki, ta fita gidan kamin na cika idda kuma ayi min abunda zai jawo hankalin mijina gare ni”
“Dika za'ayi aikin ma nasa a aiwatar da shi yau”
“Amman ƙasa ta bada bayanin zan koma gidan Hilal?”
“Ƙasa ta bada bayani kan mijinki, matakin da muka ɗauka yanzu idan be yi ba, sai mu yi na biyu idan be yi ba, sai na uku wanda shi kam dole ne a samu nasara”
“Wane mataki ne?”
“Dika zaki jisu, amman na biyu da na uku abubuwa masu matuƙar wahala”
“To Malam na gode, amman dan Allah a taimaka a bincika min baƙin duhun nan”
“Zamu bincika”
Ya kashe wayar, ita kuma ta sauke ajiyar zuciya tana dafa kai. Baƙin abun nan ya tsaya mata a rai, sai faman tunani take wane baƙin abu ne? Ko dai Ƙalsoom ce ko kuma ciwon da take ɓoyewa ne? Bata samu amsar tambayarta ba har ta gaji da tunanin ta tashi ta shirya ta nufi makarantar su Ezzah. A hanyarta ta tafiya ne Alh Bashi ya kirata wai yana nemanta kwana biyu yayi kewarta, tsaki taja ta faka gefe tana magana da shi.
“Hala baka san aurena ya mutu ba?”
»“Na sani mana, sai dai ban san dalilin mutuwar auren na ki ba”
“Kishiyata ce ta fi ƙarfina ta mallake min miji da ƴaƴa”
Daga can cikin wayar yayi dariya ya ce
“Ke yanzu kamar ki har wata mace ta isa ta fi ƙarfin ki, anya mijin ki ya san mace kowa?”
“Hmmm ƙaddarace ta gitta irin wace zata gitta ka saki Asmee nan gaba”
“A'a aure na da Asmee ai na zobe ne, idan kin ga na rabu da ita to na mutu, indai ina raye ba zan rabu da ita ba, idan kin ga na rabu da ita to na rabu da uwata ne”
‘Hmmm saboda ta maka mugun magani ba, ai wallahi tayi ma kan ta ƙiyamul laili’
Rashida ta faɗa a ranta, a fili kuma sai ta ce
“Kasan da ita kake zama da ni”
“Wannan ai daban, ni dai ki zo ina son ganin ki”
“Ko na zo babu abunda zan maka, dan ni period na ke”
“Kai yi min abunda wani be taɓa min ba, ko a mafarki ban za ci zaka aikata min ba, Asim ka yi taɓon da har na koma ga mahallacin na ba zai gogu ba, baka tambaye ni waye ba, baka bincike alaƙa ta da shi ba, sai kawai ka zarge ni, ka ɗaga hannunka ka mareni”
Ya fara mata kuka kamar gaske.
“Na san ban kyauta ba, kuma na cancanci ko wane irin hukumci, amman ki dubi girman Allah ki yafe min, dan Allah karki faɗawa kowa abun da ya faru tsakaninmu, Wallahi idan har ki ka bar zan iya shiga ko wane irin hali, haƙiƙa ni butulu ne kuma ajizi, Namra ki dubi girman ƙaunar dake tsakanin mu ki yafe min, ni har ganin nake kamar shiga tsakani ne”
“Ban faɗawa kowa ba, kuma ba zan faɗa ba, kuma na yafe maka”
“Na gode Allah yayi miki albarka, dan yaushe zaki dawo? Ko nasa Mama ta zo taje da ke?”
“Ba sai ta zo ba, zan dawo cikin satin nan”
“Yaushe?”
“Nan da kwana uku”
“Kwana uku yayi nisa Namra, da a'ce da hali sai ki dawo gobe ko jibi”
“Sai jibin dai”
“Na gode sosai Allah yayi miki albarka, duk suna lafiya ko?”
“Kowa ƙalau”
“Ina gaida kowa dan Allah”
“Za su ji”
“Na gode sai na ƙara kira”
Ta sauke wayar tana cigaba da hawaye.
“Na yafe maka, amman ba zan manta ba, zan zauna da kai saboda zama da kai ya zame min dole, son ka be amfana min komai ba Asim sai baƙinciki da damuwa”
Ta share hawayenta tana jin wani irin ƙuna da zuciyarta ke mata. Ɗan abincin da take ci sai ya fita ranta, ta tattara kayan abinci ta ɗauki tray ta nufi kitchen da shi, bayan ta aje ta dawo falonta zauna tana miƙawa Anty wayarta.
“Har kun gama”
“Eh wai tambaya yake yaushe zan dawo”
“Dika yaushe kika zo? Me kika ce masa”
“Nace masa sai Next week amman ya ce sai dai na dawo gobe, daker ya haƙura na kai jibi”
“Haba Anty Namra dika yaushe kika zo ma?”
Maryam ta faɗa. Anty tace
“Zan yi magana da shi ya bar ki kiyi ko wata ɗaya”
“A'a Anty kin san ba shida lafiya sosai ma, kuma bana son satin da Abbah ya bani ya cika ban koma ba”
Ɗaya bayan ɗaya Anty ta bisu da kallo, a tunaninta ko a cikinsu ne wani ya faɗa mata Abbah yace karta wuce sati ɗaya.
Maryam ce ta fara tsarguwa da kallon Anty ta yi magana.
“Wallahi ba ni na faɗa ba”
Aisha
“Ni ma dai”
Hindatu.
“Balle kuma ni”
“Waya faɗa? Ko muna da aljanu ne a gidan?”
Namra tayi murmushi, irin murmushin nan na ƙarfin hali ka danne baƙincikin ka.
“Ba suka faɗa ba, Abbah ne ya faɗa min da kan sa”
“Yaushe?”
“Jiya da naje gaishe shi, yau ma ya nanata min”
Anty tayi shiru bata sake cewa komai ba. Sai dai bata jidaɗin da Abbah ya faɗama Namra haka ba.
“Akwai abubuwan da kike buƙata ne? Dan a siya da wuri kar lokaci ya ƙure, ko kuma kuɗi zan baki kije can ki siya?”
“Kuɗin zai fi, dan ɗaukar kaya a nan ma ai aiki ne”
“Amman Namra ba zai yarda ku dawo nan ba?”
“Kwana ki ma yayi min maganar haka, amman nace ya haƙura har yaji sauƙi sosai sannan mu dawo”
“Gaskiya kam zama a nan zai fi, kim ga nan zai fi muku kuma kin ga nan ko ba komai kina kusa da mu”
Sallamar Doc Faruk ne yasa suka katse firar da suke suka amsa sallamar suna masa sannu da zuwa.
A kujerar da Namra take zaune ya zauna, kasancewar ta zaman mutum uku ce, sai ya soma gaiswa da Anty cikin far'ah, tun da shi ba baƙon gidan ba ne.
Maryam da Hindatu da Aisha sai duk suka tashi suka bashi guri, Anty ma tana gama gaisawa da shi, ta shige ɗakinta dan tasan abunda ya kawo shi, daman ita ta kira shi, ganin hakan kamar zai fi sauƙi tun da likitan gida ne.
“Daman akan maganar planning ne Anty tana tsoro kar ayi mai side effects, so ni abunda naƙe ganin ya fi shine ki yi na roba, saboda idan an saka mishi kin ga sai lokacin yayi sannan za'a cire, ba kamar allura bane da a za'a riƙa yi duk months, kuma kin ga shan ƙwayoyin zai iya ƙara miki matsala ma a mahaifa, za a iya tsuke miki bakin mahaifa”
“Amman robar idan an saka ba shi da wata illa ne?”
“Eh to kin san komai karɓa karɓa ne, amman gaskiya baya da matsaloli kamar sauran, kuma kin ga shi a duk lokacin da aka tashi cire miki za'a iya cirewa”
“Amman yanzu ina katsina da zama idan na saka ta nan za'a iya cire min a can?”
“Za'a iya cire miki mana, amman idan son samu ne inda aka saka miki a cire miki ita, saboda aikin wani ba shine aikin wani ba, kuma idan ma son samu ne likitan daya saka miki ita ya zama dik lokaci shine ya ke duba ki”
“Amman kana ganin ba zai haifar minnda matsala nan gaba ba?”
“Gaskiya bana jin zai haifar miki da matsala, indai ba abunda Allah ya kawo ba, sai dai kinsan komai yana da side effects sai dai wani ya fi wani”
“Okay, ba matsala when za'a saka?”
“Ko yaushe kika tashi, a hannun hagu ake sakawa kuma idan an saka miki ba zaki yi aikin da hannun ba tsawon 24h, amman za mu buƙaci sa hannun mijinki kamin mu saka miki”
“Mijina baya tare da ni yana Katsina, kuma idan da hali ina son a saka min gobe”
“Consider it done, zan yi replacement ɗin mijinki a gurin sa hannu ko da wannan zan yi alfahari”
Tayi kamar bata ji shi, sai ta tashi ta nufi ɗakin Anty tana faɗin
“Zan shiga ciki”
“Around nine za ku shigo”
Ya faɗa sannan shi ma.yasa kai ya fice.
“Mun yi magana da shi zai saka min roba ta hannu”
Ta faɗa tana ƙoƙarin zama kusa da Anty.
“Ta shekara nawa? Ita bata da matsala kamar sauran ko?”
“Eh haka ya ce, gobe da safe za mu shiga”
“Allah ya kai mu, ya baki lafiya”
“Amin”
Kwantawa tayi saman gado, Anty ta tashi ta fita.
Washen garin ranar da yace musu suka tafi aka saka mata, duk wani shirin a ranar Anty tayi mata shi, saboda komawar da zata yi gobe.
Hajiya Barau tayi mamakin komawarta da wuri haka, a take ta raya a zuciyarta ƙila Abbah ne yace be yarda ta daɗe masa a gida ba, ita tama yi mamakin da ya barta har ta zauna, goma na arziki ta haɗa mata, tun daga kan kayan sawa zuwa kuɗi da kayan mata.
Ranar da zata koma taje yi ma Abbah sallama, ranar ta sha kuka kamar ranar da za'a kaita ɗakinta, Anty ma tayi kuka sosai har hakan ya saka sauran ƴaƴan na ta kuka.
Direban gidan aka sa ya kaita har katsina dan Anty bata son ta shiga motar haya. Sai da ta biya gidan Gwaggo tayi mata sallama sannan suka kama hanyar katsina.
RASHIDA POV.
Washe garin ranar data dawo Malamin ya kira yana labarta mata bayanin da ƙasa ta bada akanta.
“Ba zaki taɓa komawa gidan Mijin ki ba, matuƙar wannan matar tana cikin gidan, sannan idan baki tashi tsaye ba, to har ƴaƴanki mijinki zai wulaƙanta su akan ta, kuma kin yi kuskuren ba mu suna, Ummu Kalsoom take ba Ummulkhairi ba”
“Na ɗauka ai duka ɗaya ne”
“Ba ɗaya bane, sannan mun ga wani baƙin hudu a tare da ke, kuma bayani ya nuna a halin yanzu tana sama da ke sai kin tashi tsaye”
“Malam wane irin baƙin abu ne wannan?”
Duk ta tsorta.
“Bayani be fito mana fili ba, amman lailai akwai baƙin abu yana biye da ke, kuma akwai abu a jikinki wanda kike ɓoyewa dangin ki”
“To Malam a taimaka ayi mana aiki, ta fita gidan kamin na cika idda kuma ayi min abunda zai jawo hankalin mijina gare ni”
“Dika za'ayi aikin ma nasa a aiwatar da shi yau”
“Amman ƙasa ta bada bayanin zan koma gidan Hilal?”
“Ƙasa ta bada bayani kan mijinki, matakin da muka ɗauka yanzu idan be yi ba, sai mu yi na biyu idan be yi ba, sai na uku wanda shi kam dole ne a samu nasara”
“Wane mataki ne?”
“Dika zaki jisu, amman na biyu da na uku abubuwa masu matuƙar wahala”
“To Malam na gode, amman dan Allah a taimaka a bincika min baƙin duhun nan”
“Zamu bincika”
Ya kashe wayar, ita kuma ta sauke ajiyar zuciya tana dafa kai. Baƙin abun nan ya tsaya mata a rai, sai faman tunani take wane baƙin abu ne? Ko dai Ƙalsoom ce ko kuma ciwon da take ɓoyewa ne? Bata samu amsar tambayarta ba har ta gaji da tunanin ta tashi ta shirya ta nufi makarantar su Ezzah. A hanyarta ta tafiya ne Alh Bashi ya kirata wai yana nemanta kwana biyu yayi kewarta, tsaki taja ta faka gefe tana magana da shi.
“Hala baka san aurena ya mutu ba?”
»“Na sani mana, sai dai ban san dalilin mutuwar auren na ki ba”
“Kishiyata ce ta fi ƙarfina ta mallake min miji da ƴaƴa”
Daga can cikin wayar yayi dariya ya ce
“Ke yanzu kamar ki har wata mace ta isa ta fi ƙarfin ki, anya mijin ki ya san mace kowa?”
“Hmmm ƙaddarace ta gitta irin wace zata gitta ka saki Asmee nan gaba”
“A'a aure na da Asmee ai na zobe ne, idan kin ga na rabu da ita to na mutu, indai ina raye ba zan rabu da ita ba, idan kin ga na rabu da ita to na rabu da uwata ne”
‘Hmmm saboda ta maka mugun magani ba, ai wallahi tayi ma kan ta ƙiyamul laili’
Rashida ta faɗa a ranta, a fili kuma sai ta ce
“Kasan da ita kake zama da ni”
“Wannan ai daban, ni dai ki zo ina son ganin ki”
“Ko na zo babu abunda zan maka, dan ni period na ke”