Sashe 29
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Bana son karatun nan a yanzu kwata-kwata ya fita rai na, na fi son sana'ar da zata riƙa kawo min ƙuɗi sosai ta yadda zan riƙa kyautatawa matana”
“Wace sana'ah zaka yi?”
“Wai da naso na kama wani shago dake nan Uguru Plaza na zuba atamfa haka da lace da shaddodi na gwada na gani, na ma yi maganar shagon dan akwai wani abokina daya ce babansa yana ba da rancen kuɗi ko nawa kake so kayi sana'ah kuna raba riba, toh shine nake son na masa magana”
Ɗagowa tayi ta kalleshi, damuwa ƙarara a fuskarta.
“Kamar nawa zaka kashe?”
“Zai kai 1.5 million, har kuɗin hayar shagon, indai ana son a saka kaya masu kyau”
“Tau me zai hana na siyar da motana sai na...”
Bata ƙarasa ba yaja wani dogon tsaki, ya tureta daga jikinsa ya tashi ya nufi ɗakin. Da sauri ta rufa masa baya tana karantar yadda ransa ya ɓace nan take.
“Kuɗin ba zasu iya ba ne?”
Ta tambaya lokacin data kunna kai cikin ɗakin. Sai ya juyo kamar a fusace yace
“Ban taɓa sanin baki da wayo da hankali ba Namra sai yau, da badan na sanki ba da sai nace shaye-shaye kike yi, taya zaki ce a siyar da motarki saboda na kama sana'ah? So kike zargin da mutane suke min ya tabbata gaskiya ko? Daman ance na auri ki ne dan dukiyarki, dan Allah dan Annabi ki taimaka wajen shanye raɗa da riƙe amanarki”
Sai yanzu hankalinta ya kwanta, data ji dalilin fushi nasa. Murmushi tayi tasa hannyenta ta laƙamo wuyansa tana kallon hawayen da suka cika masa ido.
“Bana nufi komai sai alheri, kai kan ka yanzu ai abun kunya ne kaje wani guri neman rance bayan ni ina da hanyar samo maka wannan kuɗin. Zai zame kama abun magana ace kana angonka kaje wani guri rancen kuɗin da zaka yi sana'ah, kuma ni Wallahi ba zan faɗawa kowa ba.
Nasan motar zata yi 2.5 ko ma 2 million, kaga idan ka kama sana'ah sauran sai mu siye abinci da sauran kayan gida, ni kai na ina buƙatar ƙuɗi a yanzu”
Kai ya girgiza mata ya cire hannayenta daga wuyansa.
“A'a kima daina wannan maganar dan Allah, kin san ko kuɗin da kika bani na haɗa lefe sai da nayi baƙinciki karɓar su? Nayi nadama sosai da zuciyata ta yaudareni na karɓi kuɗin”
“Amman ai baka da wata mafita Asim, idan ban baka kuɗin ba a ina zaka samo? Wannan ma ai dole ka karɓa”
“Da baki bani ba, da dole zan nemo mafita a duk inda take, ko wane hali zan iya shiga dan na samo kuɗin aurenki”
“Wannan ma ni zan taimaka maka da yardar Allah, kawai ka amince da buƙatata dan Allah, ba ma acan za'a siyar ba, kawai zan yi ma Anty waya nace zaka zo ka karɓa min motana, idan an zo nan sai a siyar Asiri rufe”
Kai ya girgiza mata, irin shi fa sam ba zai karɓa ba, ya nufi ƙofa yana wani huci kamar gaske.
Da kallo ta bishi tana murmushi har ya fice, zuciyarta cike da shauƙin son Asim, tana jin lallai tayi dacen miji.
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa22_13.html
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 23*
NOT EDITED ⚠️
Haka ta cika gidan da ihu sai kuka take duk ta bi ta rikice, zuciyarta na nasaltama Asim ya tafi ya bar. Yarinyar da suke tare ne taje da gudu ta faɗawa Mahaifiyarta, sai gata ta zo da gudu cikin gidan tare da Babbar ƴarta.
Dafa Namra tayi tana girgiza ta.
“Haba ke kuwa sai kace ba musulma ba? Cewa akayi ya mutu ne?”
Cikin kukan Namra ta amsa mata.
“Ban sani ba, sun ce yana asibitin Funtua”
“Yanzu ba kuka ya kamace ki ba, tashi ki wanke fuskarki Mardiya ta raka ki, kuje Asibitin”
Da sauri ta tashi ta shiga ta wanke fuskarta ta ɗauko Hijabinta ta saka, keys ɗin gidan ma sai da Mardiya ta karɓa ta rufe mata gidan, sannan ta koma gida ta shirya sannan ta suka kama hanya Mahaifiyarsu na mata Allah ya tsare.
Keke Napep suka hau ta kai du tasha, sannan suka shiga motar Funtua.
Tun cikin Motar Namra take kuka, har suka isa Funtua, kowa sai tambayar yake lafiya, Mardiya ce kawai take iya amsawa, Namra kan ji take kamar ta yi tsalle ɗaya ta ganta gaban Asim, sam zuciyarta ta kasa aminta da be mutu ba.
Suna isa cikin asibitin suka tambaya, sai a nuna musu emergency ward. Hankali a tashe ta shiga gurin, sai rabon ido take, akwai mutane da yawa a gurin ga kuma ɗakunan bata san wanda zata shiga ba.
Daga gefe ta tsaya ta kira wayar Asim, ringing biyu aka ɗauka.
“Ga mu cikin Asibitin yana ina?”
“Yana ciki suna duba shi, bari na fito yanzu”
Ba a ɗauki dogon lokaci ba, sai gashi ya iso gurin sanye da uniform ɗin road safety. Sai ya miƙa mata wayar hannunsa yana faɗin
“Hajiya ki kwantar da hankalin ki be mutu ba, sai dai ɗan abunda ba za'a rasa ba, ba shi kaɗai yayi haɗarin ba tare da wata babbar mota da kuma ƙananan motaci uku, duk babu wanda be ji ciwo ba, motar ma da yake ciki duk ta ƙone”
Wani sabon kuka ne ya dawo ma Namra.
“Dan Allah da gaske yana da rai?”
“Ko da muka kawo shi nan yana da rai, mutun biyu ne kawai suka rasa rai ciki, amman shi yana da rai”
“Na gode...”
“Ba komai, amman ki kwantar da hankalin ki babu abunda zai faru”
Hawayen idonta ta share, ta fidda wayarta ta saka number Anty Amarya ta kira ta, sai da kiran ya katse bata ɗauka ba, sai ta sake kiranta, sai a uku ta ɗaga.
“Assalamu Alaikum, Namra kin kira ina sallah”
“Anty Asim yayi haɗarin mota yanzu haka muna asibiti”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Da sauki dai ko?”
“Eh sun ce be mutu ba, amman har yanzu likitoci suna kansa”
“Wace Asibitin?”
“Specialist dake Funtua”
“Toh ki kwantar da hankalin ki kin ji? Kin san abunda Allah ya ƙaddara ma bawa baya wuce shi ko? Ki daina kuka ke ma malama ce Namra, ki fawwalawa Allah komai”
“Toh Anty”
“Kin kira mahaifiyarsa?”
“A'a”
“Toh ki kira ta yanzu ki faɗa mata, Allah ya bashi lafiya, gobe zamu zo inshallahu”
“Tau Anty”
Daga haka ta kashe wayar. Ta ɗauki tasa wayar ta kira number Mahaifiyarsa. Ringing ɗaya ta ɗauka tana faɗin.
“Yanzu nake cewa a sawo min kati na kira ka, na ji ko ka isa lafiya”
“Mama ba shi bane Namra ce, yayi haɗari ne a hanyarsa ta dawowa, yanzu haka muna asibitin Funtua”
“Wayyo ni Allah na shiga uku, ya mutu ne? In ya mutu ki faɗa min Namratu”
“Be mutu ba yana da rai”
“Ba shi waya muyi magana”
“Likitoci suna duba shi yanzu, ba zai yiyu ki yi magana da shi ba”
“Kice min kawai ya mutu, wayyo Allah ni Halimatu, na shiga uku na lalace”
Kuka take sosai cikin wayar, Namra na amsa mata da nata kukan. Daga bisani ta kashe wayar, ta risina a gurin tana kuka.
“Haba Namra, ki gode Allah mana da ba mutuwa yayi ba, ki tashi muje muyi Sallah”
Cewar Mardiya tana goge ma Namra hawayenta. Tashi tayi suka nufi wani ɓangare na asibitin suka siye pure water suka yi alwala Mardiya ta shinfiɗa ɗankwalinta tayi Sallah, sannan Namra ta yi.
Ta daɗe tana yi ma Asim addu'ah kamin ta tashi su koma cikin emergency ɗin. Sai kusan goman dare likitoci suka fito da shi tare da wasu mutane maza da mata kusan mutum shida.
Wani ɗakin aka kai shi, irin ɗakin da ake aje majinyata, aka ware masa gado ɗaya, suka saka masa jini. Kusa da shi ta zauna tana kallon fuskarsa. Idonsa a rufe, gefen kansa an saka masa bandeji, an ɗaure ƙafarsa ɗaya, da cinyar hannunsa.
Wani irin tausayinsa take ji, ji take kamar ta cire ciwon ta maida a kanta. Sam bata ji maganar da likitan yake mata ba har sai da Nurse ɗin dake tare da shi ta taɓa ta.
“Kece Matarsa?”
Kai ta ɗaga mata, dan bata jin zata iya magana a yanzu, saboda bakinta kumshe yake da kuka.
“Ki zo likita yana son ganinki”
Tashi tayi tabi bayan Nurse ɗin dan likitan tuni ya tafi duba wasu masara lafiyar.
A kusa da wani marar lafiya likitan yake tsaye yana masa tambayoyi, sai da ya ƙare dashi sannan ya kalle ta ya miƙa mata wata takarda take cikin file ɗin dake hannunsa.
“Ki siyo masa wanɗannan magungunan yanzu, kuma ki siyo masa ɗan ƙaramin wando da riga a saka masa, kin ga yanzu zane kawai aka rufa masa”
Hannu biyu tasa ta karɓa, sai ta koma gurin da Asim yake, Mardiya na zaune a kujerar dake kusa da shi. Namra ta dafa ta.
“Zan je na siyo magani yanzu na dawo”
“Amman kin san guri?”
“Zan tambaya”
“Toh Allah ya tsare”
“Amin”
Haka ta sa kai ta fice ba dan tasan inda zata ba, bata ma jin kuɗin da yake jakarta zai isa ta siye duka maganin. Da tambaya ta isa pharmacy dake cikin asibitin, suka duba magungunan suka ce mata babu irinsu a cikin asibitin sai ta fita waje.
Bata bar gurin ba sai da ya kwatanta mata inda zata samu, can unguwar dake kusa da asibitin. A harabar Asibitin ta hau Napep ta faɗa nasa inda zai kaita. Be direta ko ina ba sai bakin pharmacy ɗin. Sai ta ciro naira ɗari ta miƙa masa. Ta taka da ƙafa ta shiga pharmacy ɗin, sai da aka gama da wasu mutanen sannan ta miƙa musu takarɗar maganin.
Dubawa mutumen yayi ya rubuta kuɗin ko wanne a jikin rubutun.
“Duka dubu shida da dari takwas da naira arba'in”
Gabanta ya faɗi, kwata-kwata kuɗin da yake jakarta be wuce dubu ɗaya da wani abu ba. Wayarta ta ciro ta miƙa masa.
“Dan Allah ka riƙe wayar idan na kawo maka ƙuɗin gobe sai ka bani wayana, mijina ba lafiya kuma bani da kuɗin yanzu, amman nasan gobe Mamana zata zo”
Ba musu ya karɓi wayar, ya miƙawa ɗayan
“Duba mana wannan ba fake ba ce?”
“Wace sana'ah zaka yi?”
“Wai da naso na kama wani shago dake nan Uguru Plaza na zuba atamfa haka da lace da shaddodi na gwada na gani, na ma yi maganar shagon dan akwai wani abokina daya ce babansa yana ba da rancen kuɗi ko nawa kake so kayi sana'ah kuna raba riba, toh shine nake son na masa magana”
Ɗagowa tayi ta kalleshi, damuwa ƙarara a fuskarta.
“Kamar nawa zaka kashe?”
“Zai kai 1.5 million, har kuɗin hayar shagon, indai ana son a saka kaya masu kyau”
“Tau me zai hana na siyar da motana sai na...”
Bata ƙarasa ba yaja wani dogon tsaki, ya tureta daga jikinsa ya tashi ya nufi ɗakin. Da sauri ta rufa masa baya tana karantar yadda ransa ya ɓace nan take.
“Kuɗin ba zasu iya ba ne?”
Ta tambaya lokacin data kunna kai cikin ɗakin. Sai ya juyo kamar a fusace yace
“Ban taɓa sanin baki da wayo da hankali ba Namra sai yau, da badan na sanki ba da sai nace shaye-shaye kike yi, taya zaki ce a siyar da motarki saboda na kama sana'ah? So kike zargin da mutane suke min ya tabbata gaskiya ko? Daman ance na auri ki ne dan dukiyarki, dan Allah dan Annabi ki taimaka wajen shanye raɗa da riƙe amanarki”
Sai yanzu hankalinta ya kwanta, data ji dalilin fushi nasa. Murmushi tayi tasa hannyenta ta laƙamo wuyansa tana kallon hawayen da suka cika masa ido.
“Bana nufi komai sai alheri, kai kan ka yanzu ai abun kunya ne kaje wani guri neman rance bayan ni ina da hanyar samo maka wannan kuɗin. Zai zame kama abun magana ace kana angonka kaje wani guri rancen kuɗin da zaka yi sana'ah, kuma ni Wallahi ba zan faɗawa kowa ba.
Nasan motar zata yi 2.5 ko ma 2 million, kaga idan ka kama sana'ah sauran sai mu siye abinci da sauran kayan gida, ni kai na ina buƙatar ƙuɗi a yanzu”
Kai ya girgiza mata ya cire hannayenta daga wuyansa.
“A'a kima daina wannan maganar dan Allah, kin san ko kuɗin da kika bani na haɗa lefe sai da nayi baƙinciki karɓar su? Nayi nadama sosai da zuciyata ta yaudareni na karɓi kuɗin”
“Amman ai baka da wata mafita Asim, idan ban baka kuɗin ba a ina zaka samo? Wannan ma ai dole ka karɓa”
“Da baki bani ba, da dole zan nemo mafita a duk inda take, ko wane hali zan iya shiga dan na samo kuɗin aurenki”
“Wannan ma ni zan taimaka maka da yardar Allah, kawai ka amince da buƙatata dan Allah, ba ma acan za'a siyar ba, kawai zan yi ma Anty waya nace zaka zo ka karɓa min motana, idan an zo nan sai a siyar Asiri rufe”
Kai ya girgiza mata, irin shi fa sam ba zai karɓa ba, ya nufi ƙofa yana wani huci kamar gaske.
Da kallo ta bishi tana murmushi har ya fice, zuciyarta cike da shauƙin son Asim, tana jin lallai tayi dacen miji.
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa22_13.html
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 23*
NOT EDITED ⚠️
Haka ta cika gidan da ihu sai kuka take duk ta bi ta rikice, zuciyarta na nasaltama Asim ya tafi ya bar. Yarinyar da suke tare ne taje da gudu ta faɗawa Mahaifiyarta, sai gata ta zo da gudu cikin gidan tare da Babbar ƴarta.
Dafa Namra tayi tana girgiza ta.
“Haba ke kuwa sai kace ba musulma ba? Cewa akayi ya mutu ne?”
Cikin kukan Namra ta amsa mata.
“Ban sani ba, sun ce yana asibitin Funtua”
“Yanzu ba kuka ya kamace ki ba, tashi ki wanke fuskarki Mardiya ta raka ki, kuje Asibitin”
Da sauri ta tashi ta shiga ta wanke fuskarta ta ɗauko Hijabinta ta saka, keys ɗin gidan ma sai da Mardiya ta karɓa ta rufe mata gidan, sannan ta koma gida ta shirya sannan ta suka kama hanya Mahaifiyarsu na mata Allah ya tsare.
Keke Napep suka hau ta kai du tasha, sannan suka shiga motar Funtua.
Tun cikin Motar Namra take kuka, har suka isa Funtua, kowa sai tambayar yake lafiya, Mardiya ce kawai take iya amsawa, Namra kan ji take kamar ta yi tsalle ɗaya ta ganta gaban Asim, sam zuciyarta ta kasa aminta da be mutu ba.
Suna isa cikin asibitin suka tambaya, sai a nuna musu emergency ward. Hankali a tashe ta shiga gurin, sai rabon ido take, akwai mutane da yawa a gurin ga kuma ɗakunan bata san wanda zata shiga ba.
Daga gefe ta tsaya ta kira wayar Asim, ringing biyu aka ɗauka.
“Ga mu cikin Asibitin yana ina?”
“Yana ciki suna duba shi, bari na fito yanzu”
Ba a ɗauki dogon lokaci ba, sai gashi ya iso gurin sanye da uniform ɗin road safety. Sai ya miƙa mata wayar hannunsa yana faɗin
“Hajiya ki kwantar da hankalin ki be mutu ba, sai dai ɗan abunda ba za'a rasa ba, ba shi kaɗai yayi haɗarin ba tare da wata babbar mota da kuma ƙananan motaci uku, duk babu wanda be ji ciwo ba, motar ma da yake ciki duk ta ƙone”
Wani sabon kuka ne ya dawo ma Namra.
“Dan Allah da gaske yana da rai?”
“Ko da muka kawo shi nan yana da rai, mutun biyu ne kawai suka rasa rai ciki, amman shi yana da rai”
“Na gode...”
“Ba komai, amman ki kwantar da hankalin ki babu abunda zai faru”
Hawayen idonta ta share, ta fidda wayarta ta saka number Anty Amarya ta kira ta, sai da kiran ya katse bata ɗauka ba, sai ta sake kiranta, sai a uku ta ɗaga.
“Assalamu Alaikum, Namra kin kira ina sallah”
“Anty Asim yayi haɗarin mota yanzu haka muna asibiti”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Da sauki dai ko?”
“Eh sun ce be mutu ba, amman har yanzu likitoci suna kansa”
“Wace Asibitin?”
“Specialist dake Funtua”
“Toh ki kwantar da hankalin ki kin ji? Kin san abunda Allah ya ƙaddara ma bawa baya wuce shi ko? Ki daina kuka ke ma malama ce Namra, ki fawwalawa Allah komai”
“Toh Anty”
“Kin kira mahaifiyarsa?”
“A'a”
“Toh ki kira ta yanzu ki faɗa mata, Allah ya bashi lafiya, gobe zamu zo inshallahu”
“Tau Anty”
Daga haka ta kashe wayar. Ta ɗauki tasa wayar ta kira number Mahaifiyarsa. Ringing ɗaya ta ɗauka tana faɗin.
“Yanzu nake cewa a sawo min kati na kira ka, na ji ko ka isa lafiya”
“Mama ba shi bane Namra ce, yayi haɗari ne a hanyarsa ta dawowa, yanzu haka muna asibitin Funtua”
“Wayyo ni Allah na shiga uku, ya mutu ne? In ya mutu ki faɗa min Namratu”
“Be mutu ba yana da rai”
“Ba shi waya muyi magana”
“Likitoci suna duba shi yanzu, ba zai yiyu ki yi magana da shi ba”
“Kice min kawai ya mutu, wayyo Allah ni Halimatu, na shiga uku na lalace”
Kuka take sosai cikin wayar, Namra na amsa mata da nata kukan. Daga bisani ta kashe wayar, ta risina a gurin tana kuka.
“Haba Namra, ki gode Allah mana da ba mutuwa yayi ba, ki tashi muje muyi Sallah”
Cewar Mardiya tana goge ma Namra hawayenta. Tashi tayi suka nufi wani ɓangare na asibitin suka siye pure water suka yi alwala Mardiya ta shinfiɗa ɗankwalinta tayi Sallah, sannan Namra ta yi.
Ta daɗe tana yi ma Asim addu'ah kamin ta tashi su koma cikin emergency ɗin. Sai kusan goman dare likitoci suka fito da shi tare da wasu mutane maza da mata kusan mutum shida.
Wani ɗakin aka kai shi, irin ɗakin da ake aje majinyata, aka ware masa gado ɗaya, suka saka masa jini. Kusa da shi ta zauna tana kallon fuskarsa. Idonsa a rufe, gefen kansa an saka masa bandeji, an ɗaure ƙafarsa ɗaya, da cinyar hannunsa.
Wani irin tausayinsa take ji, ji take kamar ta cire ciwon ta maida a kanta. Sam bata ji maganar da likitan yake mata ba har sai da Nurse ɗin dake tare da shi ta taɓa ta.
“Kece Matarsa?”
Kai ta ɗaga mata, dan bata jin zata iya magana a yanzu, saboda bakinta kumshe yake da kuka.
“Ki zo likita yana son ganinki”
Tashi tayi tabi bayan Nurse ɗin dan likitan tuni ya tafi duba wasu masara lafiyar.
A kusa da wani marar lafiya likitan yake tsaye yana masa tambayoyi, sai da ya ƙare dashi sannan ya kalle ta ya miƙa mata wata takarda take cikin file ɗin dake hannunsa.
“Ki siyo masa wanɗannan magungunan yanzu, kuma ki siyo masa ɗan ƙaramin wando da riga a saka masa, kin ga yanzu zane kawai aka rufa masa”
Hannu biyu tasa ta karɓa, sai ta koma gurin da Asim yake, Mardiya na zaune a kujerar dake kusa da shi. Namra ta dafa ta.
“Zan je na siyo magani yanzu na dawo”
“Amman kin san guri?”
“Zan tambaya”
“Toh Allah ya tsare”
“Amin”
Haka ta sa kai ta fice ba dan tasan inda zata ba, bata ma jin kuɗin da yake jakarta zai isa ta siye duka maganin. Da tambaya ta isa pharmacy dake cikin asibitin, suka duba magungunan suka ce mata babu irinsu a cikin asibitin sai ta fita waje.
Bata bar gurin ba sai da ya kwatanta mata inda zata samu, can unguwar dake kusa da asibitin. A harabar Asibitin ta hau Napep ta faɗa nasa inda zai kaita. Be direta ko ina ba sai bakin pharmacy ɗin. Sai ta ciro naira ɗari ta miƙa masa. Ta taka da ƙafa ta shiga pharmacy ɗin, sai da aka gama da wasu mutanen sannan ta miƙa musu takarɗar maganin.
Dubawa mutumen yayi ya rubuta kuɗin ko wanne a jikin rubutun.
“Duka dubu shida da dari takwas da naira arba'in”
Gabanta ya faɗi, kwata-kwata kuɗin da yake jakarta be wuce dubu ɗaya da wani abu ba. Wayarta ta ciro ta miƙa masa.
“Dan Allah ka riƙe wayar idan na kawo maka ƙuɗin gobe sai ka bani wayana, mijina ba lafiya kuma bani da kuɗin yanzu, amman nasan gobe Mamana zata zo”
Ba musu ya karɓi wayar, ya miƙawa ɗayan
“Duba mana wannan ba fake ba ce?”