Sashe 105
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A cikin gidan akayi masa salla, duk da yake gidan mai faɗi ne kuma ƙaramin yaro ne amman hakan be hana mutane da dama halartar zina'izar ba, wasu saboda Hilal wasu kuma saboda Hajiya wasu na ɓangaren Rashida ne wasu kuma dan gulma ne, saboda labari ya ishesu ɗan da kishiyar uwarsa tasa masa guba ya rasu, so that su samu damar bada labarin ai da su ma akayi salla yaron. Har da masu ɗaukar hoton gawar suna ɗorawa status duk da kasancewar wasu ƴan'uwane amman hakan be hana su yaɗa abunda suke ganin ya zame musu wajibi ba. Kan kace kwasi.har labarin mutuwar Rafiq ya cika social media, kowa sai faɗin albarkacin bakinsa ya ke, alhalin wasu basu sam komai akai ba.
Bayan sun tafi kai Rafiq ne maƙota mata suka shio cikin gidan, suka zazzauna tare da Rashida dake ta kuka kamar ranta zai fita suka bata haƙuri wasu kuma a ransu suke tsine mata suna faɗin wai kuna munafurci ne, daman wasu ganin fuskarta ya kawo su cikin har da Asmee Aminiyar Rashida.
Bayan sun dawo daga kai shi ne, mutane suka soma yi ma yi ma Kalsoom da Hilal gaisuwa. Tashi Kalsoom tayi ta shige ɗakinta ta bar su Hajiya falo dan duk sai ta tsargu da zaman Hajiya a falon.
Aikaws Hajiya tayi aka kira mata Hilal sai ta koma can ƙarshen falon ita da shi ta faɗa masa wai a maida zaman makokin a gidanta zai fi, shi dai to kawai ya amsa mata, dan ransa baya masa daɗi.
“To ita wannan yarinyar fa?”
“Hajiya a nan zata zauna ai kinsan Musulumcin ya yarda mace ta yi idda a gidan mijinta”
“Ikon Allah anya Hilal kana cikin hankalin kan ka? Wai wace hujja kake da ita ne na yarinyar nan ba ita ta aikata ba?”
Ajiyar zuciya ya sauke, dan har ga Allah be da abunda zai nunawa Hajiya a matsayin dalilinsa na ba ita ta aikata ba, shi dai a rantsuwar da tayi masa ya gamsu, kuma jikinsa na bashi ba ita ce ta aikata ba, wata ƙila dan yana sonta ne.
Ganin be ce komai ba yasa ta ce
“Zamu wuce can, idan ka gama lelenta sai ka kaita gidan su”
Juyawa ta yi ta koma gurin mutanen da suke zaune falon, shi kuma ya nufi ɗakin Kalsoom jiki a sanyaye.
ASIM POV.
Har yanzu bashi da damuwa akan abunda yayi ma Namra, shi yana nan yana jiran ta kira shi ko kuma ta aiko masa da saƙon ban haƙuri. Yana yawan waya da Nabila Nably da kuma Mardiya, a ɗan kwana ɗayan nan har ya saba da Nably kusan kullum sai sun yi waya sau biyar ko fiye da haka. Ya tura mata hotunsa ita ta turo masa, sai yaba kyawunta yake yana faɗin nan gaba kaɗan zai zo Abuja dan ta kawai.
Yau ya tashi da nishaɗin ɗaya kwana da shi tun jiya da dare da Hajiya Sadiya ta labarta masa zuwan baƙonsa. Yasan saɓon Allah ne zai aikata amman zuciyarsa a wanke take saboda burin samun kuɗin da Hajiya ta faɗa masa zai samu idan har ya sake jiki da mutumen. Suna breakfast ta ke ƙara nanata masa yadda zai masa da kuma irin shigar da zaiyi, already ta siya amsa turaruka masu kyau da tsada da zai saka.
A gida ya wuni duk da kasancewar ta yi nata bakin amman a ɗakinsa dan ta faɗa masa iɗan har tana da baƙi bata da buƙatar ya shigo gurinta idan ba wani babban dalili ba. A gida yyai Salla magariba bayan yayi isha'i ya shiga yayi wanka ya cuɗa jikinsa sosai kamar zai cire fatan, sannan ya fito jikinsa sai ƙamshin sabulan wankan yake kamar wanda ya saka turare, saboda tsadarsu, wasu ma ayau ya fara amfani da su.
Gaban madubi ya zo ya xauna kamar wani mace yana kallon jikinsa, tare da gyara gashin kansa. Mayuka masu kyau da saka laushin jiki ya shafa sannan ya bi jikin nasa da humra na maza sannan ya shafa wasu turarukan masu tafiya da imanin mutum ya shafe duka jikinsa. Sannan ya ɗauki wani baƙin jean ya saka da farar riga mai kyau, sannan ya ɗauki facing cap baƙa ya saka ya ɗauki wani turaren ya feshe jikinsa, da shi ya ɗauki lipstick ya shafa a bakinsa ka ɗan, sai kuma ya ɗauki baƙin madubin ido ya saka. Tsayawa yayi gaban madubi yana duba kansa da kansa, shi kansa yasan ya yi kyau mashallah, hakan yasa shi murmushi tare da ɗaukar kansa hoto.
Shigowar Hajiya Sadiya ne yasa ƴa ɗan natsu ya rage murmushin da yake.
“Wow...... Gaskiya Asim kana da kyau, kaga kan ka kuwa”
Ta taɓa masa gemu tana murmushin jindaɗin ganin yadda yayi kyau, har ya ɗauki hankalinta.
“Lallai za a je da kai Asim, wannan ƙamshi haka hhmnn ka iya business, to sai ka fito ga mota can ya aiko da dareba a ɗauke ka”
“To Hajiya”
Ya faɗa kamar a kumyace, sai kuma ya samu kansa da faɗuwar gaba. Ita kanta ta lura da yanayinsa na alamar tsoro ko kuma fargaba da ke cikinsa.
“Ka kwantar da hankalinka ka sake jiki ka ci arziki babu abunda zai faru, jeka mota na jiran ka”
“Okay”
Ya faɗa kana ya ɗauki agogon hannunsa ya saka, bayan ya ƙara fesa turare, ya nufu ƙofar fita. Ita kuma ta bishi da kallo tana murmushin jindaɗi.
ABDOOL POV.
Da wuri yyi breakfast gurin Ummi saboda tafiyar data zame masa ta dole, dan tun cikin dare Mai Martaba ya kira shi ya faɗa masa ya tura tawarga da za su je tare tun da rana, shi kuma zai bi jirgin safe ya sauka kaduna, dan da ƙarshe biyu za a ɗaura aure, so zai sauka da wuri dan ya samu ya huta ta kuma kimtsa cikin lokaci.
Duk cin abincin da yake idon Amira na kansa, irin kallon take masa na rasa yadda zan yi da kai. Sai dai bata bari ya ganta ko kuma Ummi ta ganta duk kallon da take ƙasa ƙasa take masa shi wanda ba kasafai mutum zai kula ba.
“Dude za ma zaka je da ni”
Amal ta faɗa tana ƴar dariya tare da kallon Ummi.
“Yaje dake ya aje ki ina? Shi da zai je ɗaurin aure kuma”
“To yau Assabar ba aiki”
“Ba shi na ke magana ba, yau zai je yau zai dawo”
Ummi ta amsa tana cin wainar ƙwai. Daman duk weekend sune suke rigan karyawa, sauran ƴan matan gidan duk sai dai su yi ta kwanan gajiya.
Agogon hannunsa ya kalla sai yayi saurin miƙewa tsaye yana dire kofin tea ya ce
“Ummi ayi mana addu'ah”
“To Allah ya tsare ya kiyaye hanya”
“Amin ya rabb, dude sai na dawo ko?”
“To Allah ya tsare”
Ta ɗaga masa hannu. Har ya juya sai Amira ta kira shi.
“Ya Abdool”
Yana juyowa ta miƙa masa tissue paper dan ya goge bakinsa. Hannu ya kai ya karɓa yana murmushi.
“Thank you. Sai na dawo”
“Allah ya tsare”
Ta faɗa tana murmushi kamin ta biyo sawunsa tare da Ummi suka raka shumi har gurin mota. Sai da ya bar gidan sannan suka koma ciki.
Goma da rabi na safe ya sauka kaduna, daga airport motocin Mai Martaba suka tarbosa, dukansu dagarawa ne cikin jajayen kaya sai bashi girma suke suna masa kirara, abunda ya tsana a rayuwarsa, shiyasa ya fi ƙaunar ya zo da a cikin motar Army's.
Yana shiga motar suka kama hanyar masaukin Mai Martaba da ke kaduna, dan acan zai huta sannan ya shirya su ɗauki hanyar Zaria. Jaridar dake cikin motar ya ɗauka yana duba, sababin labarai ne a cikin. Akwai labaruka kala-kala na abubuwan da suke faruwa a nigeria da kuma na ban aljabi.
Kerrrrr motar dake gabansu ta taka burki, sai direban dake jan Abdool ya tsayar da motar da suke ciki. Abdool be damu daya tambaye dalilin tsayawar motar ba, shi dai hankalinsa gaba ɗaya ya tattara ya koma kan jaridar.
Ɗaya ɗaga cikin dogaran da suke motar gaba ne ya zo ya ƙwanƙwasa ma direban dake tuƙa Abdool da kuma dogarin da ke front seat. Zuƙe gilashin motar dogarin yayi yana sauraren abunda ɗayan dogarin yake ce masa.
“Subhanallahi”
Kalmar da diriban motar yayi ne ya ɗago da hankali Abdool a izuwa gare shi.
“Ran Yareema ya daɗe, wani mai Napep ne aka kaɗe”
Dogarin dake front seat ya faɗa 6ana ɗaga ma Abdool hannu irin girmamawa nan.
“Garin yaya?”
Dogarin dake tsaye jikin motar ne ya amsawa Abdool.
“Allah ya taimaki Yarima Kutse yayi mana, yyai aron hannu ne mu kuma zo da gudu. Amman za'a wuce da kai gida ne mu sai mu ji da da shi”
Uffan Abdool be ce ba, sai kawai ya aje jaridar dake hannunsa ya buɗe motar zai fita, da saurin sauran dogaran duk suka yo kansa, na gaban yayi sauri buɗe gambun motar wa Abdool yana mai girmamashi.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *65 NOT EDITED⚠️*
*ASIM, AMIRA, MARDIYA, UZAIR, RASHIDA. Duk suna muku barka da sallah 😂*
Da ƙarfi take cije bakinta, tana mulmula saman tabarma dake ɗakin, sai faman rumtse ido take tana buɗewa, ita kaɗai tasan irin zugin da take ji.
Hawaye ne ya fara mata zuba, lokacin da ta ji abu mai ɗumi ya fara bin ƙafafunta, bata buƙatar a faɗa mata abunda yake shirin faruwa da ita, tasan abunda yake cikinta yake ƙoƙarin rabuwa da ita, sai dai ita kam har ga Allah bata shirya rabuwa da shi ba, dan tana jin kamar shi kaɗai ne mafita a gareta, ko ba komai bata son ta mutu bata bar abunda za a kalla a riƙa tuna ta ba. Babu banbanci tsakanin wacan ciwon da ta ji da kuma wannan, sai ma jin da take kamar wannan ya fi tsananta masa.
“Innalillahi wa'inna ilaihi”
Shi ta samu ta furta da ƙarfi tana ƙoƙarin fita hayyacinta. Kana ganin yadda take yaƙi da numfashinta, kasan tana da buƙatar ratuwarta, wata ƙila saboda wasu dalilai na ta na karan kanta, ko kuma saboda cika wasu kuɗirinrika da suke gabanta.
Lokaci zuwa lokaci numfashinta yake barin jikinta, sai ta yi hanzarin dawowa da shi tana sauke ajiyar zuciya da ƙarfi.
Uwani ce ta shigo ɗakin da sauri tana tambayar.
“Lafiya Namra?”
Bayan sun tafi kai Rafiq ne maƙota mata suka shio cikin gidan, suka zazzauna tare da Rashida dake ta kuka kamar ranta zai fita suka bata haƙuri wasu kuma a ransu suke tsine mata suna faɗin wai kuna munafurci ne, daman wasu ganin fuskarta ya kawo su cikin har da Asmee Aminiyar Rashida.
Bayan sun dawo daga kai shi ne, mutane suka soma yi ma yi ma Kalsoom da Hilal gaisuwa. Tashi Kalsoom tayi ta shige ɗakinta ta bar su Hajiya falo dan duk sai ta tsargu da zaman Hajiya a falon.
Aikaws Hajiya tayi aka kira mata Hilal sai ta koma can ƙarshen falon ita da shi ta faɗa masa wai a maida zaman makokin a gidanta zai fi, shi dai to kawai ya amsa mata, dan ransa baya masa daɗi.
“To ita wannan yarinyar fa?”
“Hajiya a nan zata zauna ai kinsan Musulumcin ya yarda mace ta yi idda a gidan mijinta”
“Ikon Allah anya Hilal kana cikin hankalin kan ka? Wai wace hujja kake da ita ne na yarinyar nan ba ita ta aikata ba?”
Ajiyar zuciya ya sauke, dan har ga Allah be da abunda zai nunawa Hajiya a matsayin dalilinsa na ba ita ta aikata ba, shi dai a rantsuwar da tayi masa ya gamsu, kuma jikinsa na bashi ba ita ce ta aikata ba, wata ƙila dan yana sonta ne.
Ganin be ce komai ba yasa ta ce
“Zamu wuce can, idan ka gama lelenta sai ka kaita gidan su”
Juyawa ta yi ta koma gurin mutanen da suke zaune falon, shi kuma ya nufi ɗakin Kalsoom jiki a sanyaye.
ASIM POV.
Har yanzu bashi da damuwa akan abunda yayi ma Namra, shi yana nan yana jiran ta kira shi ko kuma ta aiko masa da saƙon ban haƙuri. Yana yawan waya da Nabila Nably da kuma Mardiya, a ɗan kwana ɗayan nan har ya saba da Nably kusan kullum sai sun yi waya sau biyar ko fiye da haka. Ya tura mata hotunsa ita ta turo masa, sai yaba kyawunta yake yana faɗin nan gaba kaɗan zai zo Abuja dan ta kawai.
Yau ya tashi da nishaɗin ɗaya kwana da shi tun jiya da dare da Hajiya Sadiya ta labarta masa zuwan baƙonsa. Yasan saɓon Allah ne zai aikata amman zuciyarsa a wanke take saboda burin samun kuɗin da Hajiya ta faɗa masa zai samu idan har ya sake jiki da mutumen. Suna breakfast ta ke ƙara nanata masa yadda zai masa da kuma irin shigar da zaiyi, already ta siya amsa turaruka masu kyau da tsada da zai saka.
A gida ya wuni duk da kasancewar ta yi nata bakin amman a ɗakinsa dan ta faɗa masa iɗan har tana da baƙi bata da buƙatar ya shigo gurinta idan ba wani babban dalili ba. A gida yyai Salla magariba bayan yayi isha'i ya shiga yayi wanka ya cuɗa jikinsa sosai kamar zai cire fatan, sannan ya fito jikinsa sai ƙamshin sabulan wankan yake kamar wanda ya saka turare, saboda tsadarsu, wasu ma ayau ya fara amfani da su.
Gaban madubi ya zo ya xauna kamar wani mace yana kallon jikinsa, tare da gyara gashin kansa. Mayuka masu kyau da saka laushin jiki ya shafa sannan ya bi jikin nasa da humra na maza sannan ya shafa wasu turarukan masu tafiya da imanin mutum ya shafe duka jikinsa. Sannan ya ɗauki wani baƙin jean ya saka da farar riga mai kyau, sannan ya ɗauki facing cap baƙa ya saka ya ɗauki wani turaren ya feshe jikinsa, da shi ya ɗauki lipstick ya shafa a bakinsa ka ɗan, sai kuma ya ɗauki baƙin madubin ido ya saka. Tsayawa yayi gaban madubi yana duba kansa da kansa, shi kansa yasan ya yi kyau mashallah, hakan yasa shi murmushi tare da ɗaukar kansa hoto.
Shigowar Hajiya Sadiya ne yasa ƴa ɗan natsu ya rage murmushin da yake.
“Wow...... Gaskiya Asim kana da kyau, kaga kan ka kuwa”
Ta taɓa masa gemu tana murmushin jindaɗin ganin yadda yayi kyau, har ya ɗauki hankalinta.
“Lallai za a je da kai Asim, wannan ƙamshi haka hhmnn ka iya business, to sai ka fito ga mota can ya aiko da dareba a ɗauke ka”
“To Hajiya”
Ya faɗa kamar a kumyace, sai kuma ya samu kansa da faɗuwar gaba. Ita kanta ta lura da yanayinsa na alamar tsoro ko kuma fargaba da ke cikinsa.
“Ka kwantar da hankalinka ka sake jiki ka ci arziki babu abunda zai faru, jeka mota na jiran ka”
“Okay”
Ya faɗa kana ya ɗauki agogon hannunsa ya saka, bayan ya ƙara fesa turare, ya nufu ƙofar fita. Ita kuma ta bishi da kallo tana murmushin jindaɗi.
ABDOOL POV.
Da wuri yyi breakfast gurin Ummi saboda tafiyar data zame masa ta dole, dan tun cikin dare Mai Martaba ya kira shi ya faɗa masa ya tura tawarga da za su je tare tun da rana, shi kuma zai bi jirgin safe ya sauka kaduna, dan da ƙarshe biyu za a ɗaura aure, so zai sauka da wuri dan ya samu ya huta ta kuma kimtsa cikin lokaci.
Duk cin abincin da yake idon Amira na kansa, irin kallon take masa na rasa yadda zan yi da kai. Sai dai bata bari ya ganta ko kuma Ummi ta ganta duk kallon da take ƙasa ƙasa take masa shi wanda ba kasafai mutum zai kula ba.
“Dude za ma zaka je da ni”
Amal ta faɗa tana ƴar dariya tare da kallon Ummi.
“Yaje dake ya aje ki ina? Shi da zai je ɗaurin aure kuma”
“To yau Assabar ba aiki”
“Ba shi na ke magana ba, yau zai je yau zai dawo”
Ummi ta amsa tana cin wainar ƙwai. Daman duk weekend sune suke rigan karyawa, sauran ƴan matan gidan duk sai dai su yi ta kwanan gajiya.
Agogon hannunsa ya kalla sai yayi saurin miƙewa tsaye yana dire kofin tea ya ce
“Ummi ayi mana addu'ah”
“To Allah ya tsare ya kiyaye hanya”
“Amin ya rabb, dude sai na dawo ko?”
“To Allah ya tsare”
Ta ɗaga masa hannu. Har ya juya sai Amira ta kira shi.
“Ya Abdool”
Yana juyowa ta miƙa masa tissue paper dan ya goge bakinsa. Hannu ya kai ya karɓa yana murmushi.
“Thank you. Sai na dawo”
“Allah ya tsare”
Ta faɗa tana murmushi kamin ta biyo sawunsa tare da Ummi suka raka shumi har gurin mota. Sai da ya bar gidan sannan suka koma ciki.
Goma da rabi na safe ya sauka kaduna, daga airport motocin Mai Martaba suka tarbosa, dukansu dagarawa ne cikin jajayen kaya sai bashi girma suke suna masa kirara, abunda ya tsana a rayuwarsa, shiyasa ya fi ƙaunar ya zo da a cikin motar Army's.
Yana shiga motar suka kama hanyar masaukin Mai Martaba da ke kaduna, dan acan zai huta sannan ya shirya su ɗauki hanyar Zaria. Jaridar dake cikin motar ya ɗauka yana duba, sababin labarai ne a cikin. Akwai labaruka kala-kala na abubuwan da suke faruwa a nigeria da kuma na ban aljabi.
Kerrrrr motar dake gabansu ta taka burki, sai direban dake jan Abdool ya tsayar da motar da suke ciki. Abdool be damu daya tambaye dalilin tsayawar motar ba, shi dai hankalinsa gaba ɗaya ya tattara ya koma kan jaridar.
Ɗaya ɗaga cikin dogaran da suke motar gaba ne ya zo ya ƙwanƙwasa ma direban dake tuƙa Abdool da kuma dogarin da ke front seat. Zuƙe gilashin motar dogarin yayi yana sauraren abunda ɗayan dogarin yake ce masa.
“Subhanallahi”
Kalmar da diriban motar yayi ne ya ɗago da hankali Abdool a izuwa gare shi.
“Ran Yareema ya daɗe, wani mai Napep ne aka kaɗe”
Dogarin dake front seat ya faɗa 6ana ɗaga ma Abdool hannu irin girmamawa nan.
“Garin yaya?”
Dogarin dake tsaye jikin motar ne ya amsawa Abdool.
“Allah ya taimaki Yarima Kutse yayi mana, yyai aron hannu ne mu kuma zo da gudu. Amman za'a wuce da kai gida ne mu sai mu ji da da shi”
Uffan Abdool be ce ba, sai kawai ya aje jaridar dake hannunsa ya buɗe motar zai fita, da saurin sauran dogaran duk suka yo kansa, na gaban yayi sauri buɗe gambun motar wa Abdool yana mai girmamashi.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *65 NOT EDITED⚠️*
*ASIM, AMIRA, MARDIYA, UZAIR, RASHIDA. Duk suna muku barka da sallah 😂*
Da ƙarfi take cije bakinta, tana mulmula saman tabarma dake ɗakin, sai faman rumtse ido take tana buɗewa, ita kaɗai tasan irin zugin da take ji.
Hawaye ne ya fara mata zuba, lokacin da ta ji abu mai ɗumi ya fara bin ƙafafunta, bata buƙatar a faɗa mata abunda yake shirin faruwa da ita, tasan abunda yake cikinta yake ƙoƙarin rabuwa da ita, sai dai ita kam har ga Allah bata shirya rabuwa da shi ba, dan tana jin kamar shi kaɗai ne mafita a gareta, ko ba komai bata son ta mutu bata bar abunda za a kalla a riƙa tuna ta ba. Babu banbanci tsakanin wacan ciwon da ta ji da kuma wannan, sai ma jin da take kamar wannan ya fi tsananta masa.
“Innalillahi wa'inna ilaihi”
Shi ta samu ta furta da ƙarfi tana ƙoƙarin fita hayyacinta. Kana ganin yadda take yaƙi da numfashinta, kasan tana da buƙatar ratuwarta, wata ƙila saboda wasu dalilai na ta na karan kanta, ko kuma saboda cika wasu kuɗirinrika da suke gabanta.
Lokaci zuwa lokaci numfashinta yake barin jikinta, sai ta yi hanzarin dawowa da shi tana sauke ajiyar zuciya da ƙarfi.
Uwani ce ta shigo ɗakin da sauri tana tambayar.
“Lafiya Namra?”