Sashe 129
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta ƙamƙame ƙafafun Anty amarya, tana wani irin kuka mai yaɓa zuciya. Yanzu kam Neina da Lamido sun fahimcin wacece Anty amarya. Anty ƙasa magana ta yi saboda majina data cika mata hanci. Can Namra ta ɗago kai ta kama hannayen Anty Kaamar wace ta ruɗe.
“Anty da gaske kece?”
Ta kalli Lamido da Uwani.
“Kuna ganin abinda nake gani, ko dai mafarki nake?”
Lamido ya ɗaga mai cike da ɗaurewar kai, Uwani kuma tace
“Muna gani Namra”
Anty Amarya tasa hannu biyu ta riƙo Namra ta tashe ta tsaye.
“Nice Namra, ba mafarki kike ba, Mahaifinki ma yana nan waje, tare muka zo da shi lokacin komawarki gida yayi”
“Anty waya faɗa muku nan? Na kasa yarda ba mafarki nake ba, kaina nake jin yana juyawa”
Ta miƙe tsaye ta nufi ƙofae waje. A gurin ta samu Abbah tsaye ya maida hannayensa baya kansa ƙasa kamar mai nazari.
“Abbah....”
Ta furta tana kallonsa da kyau da kyau. Ɗan murmurshi yayi kaɗan irin murmushin da be kai zuci ba. Sai kawai Namra ta faɗa jikinsa ta rumgumeshi numfashinta na rawa, kuka yazo mata a lokaci ɗaya.
Sai da tayi kukanta mai isarta taji ta samu natsuwa sannan ta sauko gurin ƙafafunsa ta riƙe.
“Dan Allah Abbah ka yafe min, ban kyauta maka ba, kwata-kwata abunda na aikata be dace ba, Abbah Asim ya sake ni, tsoron abunda zaka min ya hanani komawa gida, dan Allah ka yafe min Abbah”
Kanta ya shafa fuskarsa ba yabo ɓa fallasa.
“Idan ban yafe miki ba, ba zan zo nan ba Namra, nasan yanzu kin riga da kin gane kuskurenki, tashi tsaye kar ki tara mana mutane”
Fitar Namra yaba Anty Amarya gaisawa da ƴan gidan, wato su Neina har take faɗa musu ai tare da Abbah ta suke yana waje.
“Haba kije kice ya shigo mana ya zai tsaya daga waje”
Sannan Anty Amarya ta nufi ƙofa da jimmar faɗa masa sunce ya shigo. Sam sam sam Lamido be jidaɗin ganin iyayen Namra ba, duk wani farinciki da son da yake ta shirya da iyayenta sai yaji baya sonsa, musmaman yadda zuciyarsa take raya masa Yarima ne silar hakan,ko ba komai yasan Namra zata fi son Abdool sama da shi, shi ko yana da ƙudurora da yawa akanta, dan ya ɗaukarwa kansa alƙawarin sai ya nuna mata banbancin dake tsakaninsa da Asim na kyauwon hali, duk da suna ɗaya zasu amsa a fagen talauci,so yake Namra tasan ba duka talaka ne mai irin zuciyar Asim ba.
Wani abu yaji yazo ya tsaya masa a zuciya, tun ba aje ko ina ba, yana jin ya fara missig Namra, zata nisanta da shi yanzu, kuma ba lallai bane ya sake ganinta.
Sallama Abbah ce ta katse masa hanzari, ya dawo daga duniyar tunanin da yake ya miƙa idonsa i zuwa inda ƙofar gidan take yana kallon Namra dake riƙe da hannun Anty Amarya. Saman shimfiɗar da Neina tayi musu suka zauna, ita kuma ta zauna a saman ɗaƴar tana gaisawa da Abbah.
“Amman na jidaɗin da kuka zo gurin ƴarku, Namra bata da tunani sai naku, kullum cikin kuka take, nasan babu iyaye na gari da zasu ƙyale ƴarsu, matuƙar ƴar nan ta sunna aka haife ta, su iyaye dole sai kana kai xuciya nesa, sau da yawa ɗa zai aikata abu kai ka daurewa zuciyarka ka ƙyale gudun kar ɗan nan ya faɗawa halaka, kuma idan mutum ya gane kuskurensa babu a abunda ya cancanta da shi sai yafiya da kuma nuna masa illar abun nan da ya aikata, ƴaƴa da mata kamar kiwo ne, ko wanne za a tambaya ubngidansa akan irin kiwon da ya bawa iyalansa, yadda mu muke da haƙƙi akan ƴaƴanmu haka muma ƴaranmu suke da haƙƙi a kan mu. Wallahi kun faranta min zuciya dana ganku da ƙafafunku kun tako cikin gidan nan ku tafi da ƴarku, a halin da Namra take da ace bata haɗu da mu ba da zata iya faɗawa ko wane irin hali, saboda bata san kowa a Kaduna ba, kun ga ko a nan rayuwarta tana cikin haɗari”
“Gangar jikina ne kawai a gida, amman kullum zuciyata tunanin Namra take, ban san aurenta ya mutu ba, da wallahi ba zata zauna ko ina ba sai a gida, kowa kuwa mahaifinta zai zaɓi rabuwa da ni ne, kullum a tunani tana can yana azabbatar da ita, nasan Halin Namra idan abun duniya zai cita ya cinye ba zata faɗawa kowa ba, itace babba amman ita marar wayo da tunani a cikinsu, da wannan tunanin naƙe bachi naƙe tashi wannan tunanin ya kan hanani sukuni wani lokacin, shiyasa ƴan'uwanta suke ganin kamar itace silar ciwon nan nawa, kullum cewa suke, Namra ce ta kwantar da ni, duk da nasan gaskiya suke faɗa amman a haka zan musa musu, kudun kar suce nafi sonta sama da su, ni ko kullum tunanin kar na mutu na barta a cikin wannan halin”
Namra ta kama hannayen Anty Amarya ta riƙe.
“Ba zan sake aikata abu makamancin wannan ba Anty, ni ba zan sake aure ba balle har na tsallake wani sharaɗi na ku, hawayenki ba zai sake zuba a kan Namra ba”
Uffan Abbah be ce ba, idonsa na kan pure water da Maryam ta aje musu mai tsanyi, wadda ta siyo shago.
Maganar duk da suke tana cikin kunnensa, sai dai be jin zai iya furta wata kalma data ɗanganci labarin da suke. Ba laifi sun ɗan yi fira sosai da Neina, kamar waɗanda daman can san juna, sai duk firar da ake Namra na cikin jikin Anty hawaye sun ƙi su tsaya mata. Abbah ya kalli agogonsa tare da miƙewa tsaye yana faɗin.
“Ya kamata mu tafi yanzu, da safe Namra zata zo ta muku sallama kamin mu kama hanya”
Yana faɗar hakan ya saka takalminsa ya nufi ƙofar fita, Lamido da kallo ya bishi yana aunasa a matsayin lallai zai iya aikatawa Namra haka, da ga alamu yana ji da kansa, ko kuma be gama hucewa bane oho.
“Allah sarki Namra, ashe kuwa zamu yi marmarinki”
Uwani ta faɗa cikin rashin jidaɗi, dan har ga Allah ita tana tunanin rabuwa da Namra dan yanzu sun ɗan tsaba da juna.
“Nima ai sai na yi Marmarin ku, mutane masu karamci da sanin darajar ɗan'adam”
Namra ta furta tana mai jin kamar karta tafi ta barsu. Har bakin mota Neina da Uwani da Maryam suka rakosu, ko da suka fito har Abbah ya shiga mota, Anty Amarya ta fara shiga sannan Namra, su Neina na ɗaga musu hannu direban yaja mota.
RASHIDA POV.
Ta rame sosai ta koma kamar ba ita ba, tun ranar da taje gidansu su Teema bata sake leƙa ko ina ba, gurin aikinta sun yi kira sai ta tura musu saƙon bata da lafiya ta email, sannan ta kashe wayarta, saboda yawan kiran da ake mata akan auren Teema da tsohon mijinta. Bata iya cin komai banda tea, sai ɗan lemu wani lokacin, kullum a kwance take salla ce kawai take tashinta. Musamman jiya ta san itace ranar ɗaurin auren Teema da rabin ranta 😢. Babu wanda yasan inda take balle azo gurinta, Momi kuma ta juya mata baya da duk ƴan gidansu, lallai sai yanzu ta gane duniya ta juya mata baya, shiyasa ake cewa idan kana son duniya da yawa ka fara barinta kamin ta barka, idan har ita ta fara barinka to ba zaka ga da kyau ba. Yanzu kan ta fara gane baƙin duhun da yake bibiyarta sai dai bata san iya inda zai tsaya mata ba. knocked ɗin ƙofar falo da taji ana yi ne yasa ta unƙurin tashi taje ta buɗe. A zatonta Momi ce ko wata daga cikin ƴan gidansu, ga mamakinta sai ta ga Asmee.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Rashida haka kika koma?”
Rashida ta sakar mata ƙofar ta dawoɓsaman cushion ta zauna, Asmee ma zama tayi a kujerar dake fuskarta ta Rashida, tana yayw mayafinta.
“Haba Rashida, na san kina son Hilal kuma na san Teema bata kyauta miki ba, amman idan ta samu labarin halin da kika shiga ai daɗi zata ji, kin ware kanki ke kaɗai kina saka damuwa a aranki”
“Ya akayi kika gane gidan nan?”
“Gidanku naje aka kwatantamin nan, zulfa'u da Rafia duk sun je gida sai a ce musu kin yi tafiya, nima ban da na matsa da ba za a faɗa min inda kike ba, dan Allah Rashida ki cire damuwar Teema a ranki”
“Ba auren Teema abunda yake damuna a yanzu ba, irin rayuwar da zata shimfiɗa a cikin gidana yafi damuna, ita zata reni ƴaƴana, kuma wallahi azzalumace zata iya yi musu komai, gata ta iya neman magani zaya iya raba su da ubansu”
“Toh ya zakiyi Wallahi Teema ta ci amana”
“Teema ta ci amana kamar yadda nima na ci amana, ta auren min miji kamar yadda nima nayi taraiya da mijin aminiyata, Asmee duk halin dana shiga a yanzu mijin ki ne sila...”
Asmee ta gyara zama.
“Ban gane ba. Kamar ya mijina ne sila?”
“Kin ci amanar mijinki kin bada kanki ga wasu saboda neman mallakar miji, ahi kuma ya ci amanar ki ya bada kansa gare ni, mijinki shi ya saka min cutar hiv, saboda kin samo gurin wannan bokan kin saka masa, tun daga lokacin da naji kince ana zargin bokan da cuta, hankalina ya tashi saboda nasan bayan mijina, mijinki ne na biyu da nake mu'amala da shi, sanadin hakan naje nayi gwaji, aka tabbatar min da ina ɗauke da cutar, har Hilal ya gane gaskiya yaje yayi gwaji shi baya da shi da ƴaƴansa, da matarsa, sanadin hakan ya sake ni, shi kansa mijinki be san da hakan ba, amman ke nasan kin san kina ɗauke da cutar, saboda haka na ci amana, nima Teena ta ci amanata, sai dai ban san makomar yarana ba, ban san wane irin tarbiya zata basu ba”
Miƙewa Asmee ta yi tsaye gume na keto mata tashin hankali ya hana hawayen dake maƙale a idonta zuba.
“Anty da gaske kece?”
Ta kalli Lamido da Uwani.
“Kuna ganin abinda nake gani, ko dai mafarki nake?”
Lamido ya ɗaga mai cike da ɗaurewar kai, Uwani kuma tace
“Muna gani Namra”
Anty Amarya tasa hannu biyu ta riƙo Namra ta tashe ta tsaye.
“Nice Namra, ba mafarki kike ba, Mahaifinki ma yana nan waje, tare muka zo da shi lokacin komawarki gida yayi”
“Anty waya faɗa muku nan? Na kasa yarda ba mafarki nake ba, kaina nake jin yana juyawa”
Ta miƙe tsaye ta nufi ƙofae waje. A gurin ta samu Abbah tsaye ya maida hannayensa baya kansa ƙasa kamar mai nazari.
“Abbah....”
Ta furta tana kallonsa da kyau da kyau. Ɗan murmurshi yayi kaɗan irin murmushin da be kai zuci ba. Sai kawai Namra ta faɗa jikinsa ta rumgumeshi numfashinta na rawa, kuka yazo mata a lokaci ɗaya.
Sai da tayi kukanta mai isarta taji ta samu natsuwa sannan ta sauko gurin ƙafafunsa ta riƙe.
“Dan Allah Abbah ka yafe min, ban kyauta maka ba, kwata-kwata abunda na aikata be dace ba, Abbah Asim ya sake ni, tsoron abunda zaka min ya hanani komawa gida, dan Allah ka yafe min Abbah”
Kanta ya shafa fuskarsa ba yabo ɓa fallasa.
“Idan ban yafe miki ba, ba zan zo nan ba Namra, nasan yanzu kin riga da kin gane kuskurenki, tashi tsaye kar ki tara mana mutane”
Fitar Namra yaba Anty Amarya gaisawa da ƴan gidan, wato su Neina har take faɗa musu ai tare da Abbah ta suke yana waje.
“Haba kije kice ya shigo mana ya zai tsaya daga waje”
Sannan Anty Amarya ta nufi ƙofa da jimmar faɗa masa sunce ya shigo. Sam sam sam Lamido be jidaɗin ganin iyayen Namra ba, duk wani farinciki da son da yake ta shirya da iyayenta sai yaji baya sonsa, musmaman yadda zuciyarsa take raya masa Yarima ne silar hakan,ko ba komai yasan Namra zata fi son Abdool sama da shi, shi ko yana da ƙudurora da yawa akanta, dan ya ɗaukarwa kansa alƙawarin sai ya nuna mata banbancin dake tsakaninsa da Asim na kyauwon hali, duk da suna ɗaya zasu amsa a fagen talauci,so yake Namra tasan ba duka talaka ne mai irin zuciyar Asim ba.
Wani abu yaji yazo ya tsaya masa a zuciya, tun ba aje ko ina ba, yana jin ya fara missig Namra, zata nisanta da shi yanzu, kuma ba lallai bane ya sake ganinta.
Sallama Abbah ce ta katse masa hanzari, ya dawo daga duniyar tunanin da yake ya miƙa idonsa i zuwa inda ƙofar gidan take yana kallon Namra dake riƙe da hannun Anty Amarya. Saman shimfiɗar da Neina tayi musu suka zauna, ita kuma ta zauna a saman ɗaƴar tana gaisawa da Abbah.
“Amman na jidaɗin da kuka zo gurin ƴarku, Namra bata da tunani sai naku, kullum cikin kuka take, nasan babu iyaye na gari da zasu ƙyale ƴarsu, matuƙar ƴar nan ta sunna aka haife ta, su iyaye dole sai kana kai xuciya nesa, sau da yawa ɗa zai aikata abu kai ka daurewa zuciyarka ka ƙyale gudun kar ɗan nan ya faɗawa halaka, kuma idan mutum ya gane kuskurensa babu a abunda ya cancanta da shi sai yafiya da kuma nuna masa illar abun nan da ya aikata, ƴaƴa da mata kamar kiwo ne, ko wanne za a tambaya ubngidansa akan irin kiwon da ya bawa iyalansa, yadda mu muke da haƙƙi akan ƴaƴanmu haka muma ƴaranmu suke da haƙƙi a kan mu. Wallahi kun faranta min zuciya dana ganku da ƙafafunku kun tako cikin gidan nan ku tafi da ƴarku, a halin da Namra take da ace bata haɗu da mu ba da zata iya faɗawa ko wane irin hali, saboda bata san kowa a Kaduna ba, kun ga ko a nan rayuwarta tana cikin haɗari”
“Gangar jikina ne kawai a gida, amman kullum zuciyata tunanin Namra take, ban san aurenta ya mutu ba, da wallahi ba zata zauna ko ina ba sai a gida, kowa kuwa mahaifinta zai zaɓi rabuwa da ni ne, kullum a tunani tana can yana azabbatar da ita, nasan Halin Namra idan abun duniya zai cita ya cinye ba zata faɗawa kowa ba, itace babba amman ita marar wayo da tunani a cikinsu, da wannan tunanin naƙe bachi naƙe tashi wannan tunanin ya kan hanani sukuni wani lokacin, shiyasa ƴan'uwanta suke ganin kamar itace silar ciwon nan nawa, kullum cewa suke, Namra ce ta kwantar da ni, duk da nasan gaskiya suke faɗa amman a haka zan musa musu, kudun kar suce nafi sonta sama da su, ni ko kullum tunanin kar na mutu na barta a cikin wannan halin”
Namra ta kama hannayen Anty Amarya ta riƙe.
“Ba zan sake aikata abu makamancin wannan ba Anty, ni ba zan sake aure ba balle har na tsallake wani sharaɗi na ku, hawayenki ba zai sake zuba a kan Namra ba”
Uffan Abbah be ce ba, idonsa na kan pure water da Maryam ta aje musu mai tsanyi, wadda ta siyo shago.
Maganar duk da suke tana cikin kunnensa, sai dai be jin zai iya furta wata kalma data ɗanganci labarin da suke. Ba laifi sun ɗan yi fira sosai da Neina, kamar waɗanda daman can san juna, sai duk firar da ake Namra na cikin jikin Anty hawaye sun ƙi su tsaya mata. Abbah ya kalli agogonsa tare da miƙewa tsaye yana faɗin.
“Ya kamata mu tafi yanzu, da safe Namra zata zo ta muku sallama kamin mu kama hanya”
Yana faɗar hakan ya saka takalminsa ya nufi ƙofar fita, Lamido da kallo ya bishi yana aunasa a matsayin lallai zai iya aikatawa Namra haka, da ga alamu yana ji da kansa, ko kuma be gama hucewa bane oho.
“Allah sarki Namra, ashe kuwa zamu yi marmarinki”
Uwani ta faɗa cikin rashin jidaɗi, dan har ga Allah ita tana tunanin rabuwa da Namra dan yanzu sun ɗan tsaba da juna.
“Nima ai sai na yi Marmarin ku, mutane masu karamci da sanin darajar ɗan'adam”
Namra ta furta tana mai jin kamar karta tafi ta barsu. Har bakin mota Neina da Uwani da Maryam suka rakosu, ko da suka fito har Abbah ya shiga mota, Anty Amarya ta fara shiga sannan Namra, su Neina na ɗaga musu hannu direban yaja mota.
RASHIDA POV.
Ta rame sosai ta koma kamar ba ita ba, tun ranar da taje gidansu su Teema bata sake leƙa ko ina ba, gurin aikinta sun yi kira sai ta tura musu saƙon bata da lafiya ta email, sannan ta kashe wayarta, saboda yawan kiran da ake mata akan auren Teema da tsohon mijinta. Bata iya cin komai banda tea, sai ɗan lemu wani lokacin, kullum a kwance take salla ce kawai take tashinta. Musamman jiya ta san itace ranar ɗaurin auren Teema da rabin ranta 😢. Babu wanda yasan inda take balle azo gurinta, Momi kuma ta juya mata baya da duk ƴan gidansu, lallai sai yanzu ta gane duniya ta juya mata baya, shiyasa ake cewa idan kana son duniya da yawa ka fara barinta kamin ta barka, idan har ita ta fara barinka to ba zaka ga da kyau ba. Yanzu kan ta fara gane baƙin duhun da yake bibiyarta sai dai bata san iya inda zai tsaya mata ba. knocked ɗin ƙofar falo da taji ana yi ne yasa ta unƙurin tashi taje ta buɗe. A zatonta Momi ce ko wata daga cikin ƴan gidansu, ga mamakinta sai ta ga Asmee.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Rashida haka kika koma?”
Rashida ta sakar mata ƙofar ta dawoɓsaman cushion ta zauna, Asmee ma zama tayi a kujerar dake fuskarta ta Rashida, tana yayw mayafinta.
“Haba Rashida, na san kina son Hilal kuma na san Teema bata kyauta miki ba, amman idan ta samu labarin halin da kika shiga ai daɗi zata ji, kin ware kanki ke kaɗai kina saka damuwa a aranki”
“Ya akayi kika gane gidan nan?”
“Gidanku naje aka kwatantamin nan, zulfa'u da Rafia duk sun je gida sai a ce musu kin yi tafiya, nima ban da na matsa da ba za a faɗa min inda kike ba, dan Allah Rashida ki cire damuwar Teema a ranki”
“Ba auren Teema abunda yake damuna a yanzu ba, irin rayuwar da zata shimfiɗa a cikin gidana yafi damuna, ita zata reni ƴaƴana, kuma wallahi azzalumace zata iya yi musu komai, gata ta iya neman magani zaya iya raba su da ubansu”
“Toh ya zakiyi Wallahi Teema ta ci amana”
“Teema ta ci amana kamar yadda nima na ci amana, ta auren min miji kamar yadda nima nayi taraiya da mijin aminiyata, Asmee duk halin dana shiga a yanzu mijin ki ne sila...”
Asmee ta gyara zama.
“Ban gane ba. Kamar ya mijina ne sila?”
“Kin ci amanar mijinki kin bada kanki ga wasu saboda neman mallakar miji, ahi kuma ya ci amanar ki ya bada kansa gare ni, mijinki shi ya saka min cutar hiv, saboda kin samo gurin wannan bokan kin saka masa, tun daga lokacin da naji kince ana zargin bokan da cuta, hankalina ya tashi saboda nasan bayan mijina, mijinki ne na biyu da nake mu'amala da shi, sanadin hakan naje nayi gwaji, aka tabbatar min da ina ɗauke da cutar, har Hilal ya gane gaskiya yaje yayi gwaji shi baya da shi da ƴaƴansa, da matarsa, sanadin hakan ya sake ni, shi kansa mijinki be san da hakan ba, amman ke nasan kin san kina ɗauke da cutar, saboda haka na ci amana, nima Teena ta ci amanata, sai dai ban san makomar yarana ba, ban san wane irin tarbiya zata basu ba”
Miƙewa Asmee ta yi tsaye gume na keto mata tashin hankali ya hana hawayen dake maƙale a idonta zuba.