Sashe 143
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya amsa mata cikin rashin daɗin rai dan zuciyarsa sak yanzu zarginta yake.
“Ina Apple ɗin da kace zaka bawa matarka? Wata ka bawa ne ko mi ya faru? Ni an kira ni sai faɗa suke min, wai an basu tsohuwa, ni kuma na san ba wannan maganar muka yi da kai ba, miya faru ne”
“Apple ɗin faɗuwa yayi a hanya ina da niyar kiranki na faɗa miki, maybe wata ta tsinceta ne”
“Amman Asim sai da na yi ta nanata maka kar a samu matsala yanzu gashi wata banzar tsohowa taje ta samu, garin yaya ma ka jefar da shi? Ko dai baka son kuɗin ne wai?”
“Ina so mana, ai yanzu akwai wani ko?”
“Eh amman sai naje na faɗa musu sai su ban wani, yaushe zaka zo?”
“Nan da kwana biyu”
“Zan je na ƙarɓo maka, amman dan Allah karka min sakakace irin wacan”
“Ba za a samu matsala ba wannan karon sai kin fi kowa farinciki”
“Haka nake so”
Ta katse kiran. Shi ko ya cige baki yana kallon wayar cike da baƙinciki. Yana son ya tambayi Ƙanwarsa yadda aka yi apple ɗin ya fito daga motarsa har Mama ta ci yana tsoron kar ta zargi wani abu.
“Kun samu sa'ar jinin Uwata... Wallahi kin yi nadamar sanina da kika yi a rayuwarki, sai na ɗanɗana miki wannan baƙincikin”
Yayi wulgi da wayar iya ƙarfinsa, yana huci.
UZAIR POV.
Tare da ƙannensa biyu suka iso gidan da kuma mahaifiyarsa, tana ganin irin halin da yake ciki suka ɗauki shi zuwa asibiti.
Emergency suka wuce da shi layin ƴan haɗari aka ware masa ɗaki daban likitoci suka hau duba shi, sai ihu yake kamar wanda be san inda yake ba, bayan sun yi ɗan bincike su aka tura shi gurin hoto, bayan an masa hoton suka sake dawowa da shi ɗakin suka masa allurar bachi, amman kamar an ƙara masa zafin ciwo yake ji gaba ɗaya ya fita hayyacinsa sai ihu yake. A take suka sake rubuta masa wani hoton, aka je aka ɗauka.
Lokacin da aka fito da hoton, sai Likita ya kira Hajiya suka nufi wani ɗakin da ita sai ya ƙala hotunan a jikin computer. Yana nuna mata.
“Ɗan ki ya taɓa yin haɗari?”
“Gaskiya be taɓa ba, amman ban sani ba ko be faɗa min ba”
“Gaskiya ƙashinsa na baya na karye, kuma na cinyarsa ma ya karye, sannan....”
Kamin ya ƙarasa ta miƙe tsaye ta sauri har kujerar da take zaune samanta ta faɗi.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Ganin hakan yasa likitan dakatar da bayaninta, dan ya ga alamun zata fara masa kuka, shi kansa yasan be kamata ya yi mata wannan bayanin ba, ganin tana mace amman babu yadda ya iya tun da babu wani namiji babban da yayi kusa da mahaifiyarsa. Da sauri ta juya ta fice daga office ɗin tana kiran wayar Abbah. Dan babu wanda ya san an kai Uzair Asibiti dan basu faɗa ba, tun bayan da Yasmin ta daqo gida ba ta damu da tasan dalili ba, tana ganin kamar yayi hakan ne saboda ta janye ƙudirinta.
HILAL POV.
“Miya same ƴar ka haka ne Doc?”
Doc Zara ta tambaya cike da mamakin irin ƙunar da Ulfah ta yi. Hannayensa ya zuba aljihu yana sauke ajiyar zuciya, ita kan Teema tuni ta kusa cikin ɗakin tana hawaye kamar gaske.
“Faɗa suka yi da ƴar'uwarta shi ne wai ta watsa mata ruwan miya dake kan wuta”
“Amman gaskiya ya kamata ka sa ido sosai akan yaranka Uzair, irin wannan abun yana sa kisan kai fa”
“Ƙaddarori ne kawai idan Allah ya kawo abu”
“Allah ya tsare gaba, Ina uwargida har yanzu bata haihu ba?”
“Har yanzu fa”
“To Allah ya raba lafiya”
“Amin”
Tun da suka jero suke maganar basu rabu ba sai da ta kawo kusa da pharmacy sannan ta ɗauki wata hanyar shi kuma ya ciro wayarsa ya kira Hajiya ya faɗa mata, ita Rashida text kawai ya aika mata, sai kuma ya kama hanyar gida dan yi ma Ezzah hukunci.
Sai da ya kama hanyar gida sannan ya kira Kalsoom ya faɗa mata halin da ake ciki, dan yasan zata tashi hankalinta sosai.
Bugu ɗaya ta ɗauka.
“Kana ina ne?”
“Ina hanyar gida, na kaita asibiti da sauƙi”
“Na je gida ban samu kowa ba sai Ezzah tana ta kuka, sai ta biyo ni gani cikin asibitin ma”
“Oooooo Kalsoom miyasa baki ragawa kan ki ne? Ba fa ke kaɗai kike ba a yanzu, da izinin wa kika fita, yanzu da wannan tulelen ciki yama zaki yi driving?”
“Napep na hau”
Ajiyar zuciya ya sauke.
“Tau gani nan juyowa”
Ya katse kiran ya juya ya koma hanyar asibitin. Yana isa aibitin su Hajiyarsa na isa yare da Mama ladi (kanwar mahaifiyarsa) da ƙanensa guda biyu. Jerowa suka yi suna tafiya yana yi ma Hajiya bayanin yadda abun ya faru.
Kalsoom na hango shi tafe tare da Hajiya ta ji babu daɗi musamman dan tana tare da Ezzah tasan dole Hajiya za tayi magana wata ƙila ma zata ce ita ce ta haddasa wannan husumar. Duk sai ta rasa yadda zata yi ga tulelen cikin nan ya mata tsaye kamar wacce zata haihu yanzu.
“Hajiya ina wuni”
“Lafiya ƙalau”
Tana amsa gaisuwar da Kalsoom ta yi mata ta wuce bata ko bi ta kanta ba. Hilal ne ya tsaya gurin matarsa.
“Miya hana ki shiga?”
“Ban san ɗakin da aka kai ta ba”
“Tau muje”
“A'a sai Hajiya ta fito, kar ta gan ni da Ezzah”
“Cemin ta yi wai tana tsoron karka dake ta”
“Ai ba duka kaɗai ba karye ta ma zanyi, ba dai ke har kin kai ki ɗauki ruwan zafi ki watsawa ƴar'uwarki ba...?”
Sai kawai Ezzah tasa kuka ta kama Hijabin Kalsoom ta riƙe gamgam tana kuka. Hilal be bi ta kanta ba ya nufi sashen da zai sadashi da ɗakin Ulfah, Kalsoom ta rufa masa baya tana faɗin Ezzah ta yi shiru ba zata bari ya daketa ba.
Ko da suka shiga Hajiya na kusa da Ulfah dake bachi, tana duba ƙonuwar cike da tausayi, can jikin ƙofa Kalsoom ta tsaya tana kallon Ulfah, Ezzah na riƙe da Hijabinta har lokacin tana kuka. Hajiya ta ɗago ta kalli Ezzah cikin tausayi da ɓacin rai ta ce
“Amman Ezzah baki da zuciyar ƙwarai, ko ɗauki ruwan zafi ki watsawa ƴar'uwarki haka?”
“Wallahi ba nice ba Wallahi Mama Teema ce...!”
Ta faɗa cikin kuka.
[7/18, 8:14 PM] Khadeeja Candy♥: *82*
Teema ta katsa mata tsawa tana zare mata ido alamar dik kika faɗa sai na ci ubanki.
“Ke karki min ƙarya, munafukar yarinya fitsararriya”
“Wallahi ba ni bace, ke kika kira ni kika ce na zo naje kitchen na duba Ulfah ta ƙone...”
Hajiya ta kalli Teema ta kalli Ezzah, ƙoƙarin ɗaukar maganar ta ke, sai kawai ta jiyo kukan Teema wai Ezzah ta mata ƙazafi.
“Wallahi ba zan taɓa yafe miki ba, makira kawai munafuka”
“Ezzah kike cewa haka? Sai kace wata babbar mace? To wai kina aikin me haka ya faru”
Cewar Hajiya tana sake da baki. Ta soma bayani tana kuka da kallon Hilal ko zai kareta ɗin nan.
“Ina cikin kitchen ina girki, na ƙare tuwo sai na ce bari na ɗora miya, sai na ce ta daga kamin daddawa ita kuma Ulfah ta gyara min tabarnuwa, ni ban san gardamar mi suke ba sai kawai naji an taɓa tukuyan miyar da ƙarfi sai ihun Ulfah na ji ina juyowa na ga ta juye mata miyar”
Izzah ta tuma ta dire ta sake tuma ta dire tana kuka da jan Hijabin Kalsoom tana faɗin ba ita ba ce, amman babu wanda ya kula ta Hilal in banda harara babu abunda yake mata, yana cike da haushinta sosai Allah ka ɗai ya san irin hukunci da zai mata idan suka koma gida. Sai kawai ta saki Kalsoom ta ruga gurin Hajiya tana kuka.
“Wallahi ba ni bace Hajiya...”
“Hilal ka saurareta mana”
Kalsoom ta faɗa cike da tausayin kukan da Izzah take yi.
Hilal ya girgiza mata kai.
“Ba wani saurare da za'a mata, ai kin san halinta”
Izzah har da faɗuwa take a gurin taɓa tashi ta kama gyalen Hajiya ta riƙe ƙam.
“Ba zaki rufewa mutane ba ki ba, Wallahi zan dake ki yanzu nan, ba sai mun je gida ba”
Hilal ya faɗa ciki fushi yana mai jin kamar ya kamata ya ɓallata gida biyu. Ihunta ne ya tashi Ulfah daman can ba wani dogon bachi ta yi ba, saboda zafin wuta ko an maka allurar ba bari yake ka yi bachi ba.
“Wayyo Allah Momie, Hajiya, Dady ka kai ni inda Momie ko Anty Kalsoom ko inda Hajiya, bana son gurin Mama Teema ta watsa min wuta, wayyo zafi dady zafi Mama Teema ta ƙona ni, Anty Kalsoom, Momie, Hajiya”
Sune ƙawai sabbatun da take tana murza jikinta sai da Hilal ya riƙe mata hannu. Suna haka sai ga Rashida ta shigo hankalinta a tashe, tana kallon Teema hawaye suka fara mata zuba.
“Ɗaya bayan ɗaya za ki bisu ki kashe, na sani Teema kaɗan daga halinki ne amman ki sani kin ci amana kuma kema amana sai ta ci ki”
Sai kuma ta juyo gurin Kalsoom tana kuka, itana Kalsoom ɗin kuka take, Hajiya ma haka, balle Teema dake ƙoƙarin kare kanta, ƙanen Hilal ma babu wanda baya hawaye.
“Kin ci amanata, sai da na ce miki ki riƙe min yara na amman kika ƙi, yanzu ga shi abunda ya faru, bana da kowa a duniyar nan sai su, su ne farinciki na”
Jakar da ke hannunta ta saki ta nufi gurin ƴarta dake sabbatu, magangun ɗazu kawai take maimaitawa. Rashida ta gadon ta riƙe tana kuka.
“Laifina ne, nice ban riƙe mutuncin aurena ba, ni na kasa zama da ku ni na cuceku Ulfah laifi na, kuma na ci amanar matar da ke riƙon ku tsakani da Allah...”
Ezza ta yi gunta da kuka.
“Momie Wallahi ba ni bace, Dady ya ce sai ya raba ni gida biyu.. Wallahi ba ni ba ce”
“Ba zan ɗauka ba, wannan ba zata kwanta jinya ba, ka kama wannan ka karya min ba, ka saurareta Hilal Wallahi ba ita ba ce, karka ɗauki alhakin yarinyar nan Hilal”
“Ina Apple ɗin da kace zaka bawa matarka? Wata ka bawa ne ko mi ya faru? Ni an kira ni sai faɗa suke min, wai an basu tsohuwa, ni kuma na san ba wannan maganar muka yi da kai ba, miya faru ne”
“Apple ɗin faɗuwa yayi a hanya ina da niyar kiranki na faɗa miki, maybe wata ta tsinceta ne”
“Amman Asim sai da na yi ta nanata maka kar a samu matsala yanzu gashi wata banzar tsohowa taje ta samu, garin yaya ma ka jefar da shi? Ko dai baka son kuɗin ne wai?”
“Ina so mana, ai yanzu akwai wani ko?”
“Eh amman sai naje na faɗa musu sai su ban wani, yaushe zaka zo?”
“Nan da kwana biyu”
“Zan je na ƙarɓo maka, amman dan Allah karka min sakakace irin wacan”
“Ba za a samu matsala ba wannan karon sai kin fi kowa farinciki”
“Haka nake so”
Ta katse kiran. Shi ko ya cige baki yana kallon wayar cike da baƙinciki. Yana son ya tambayi Ƙanwarsa yadda aka yi apple ɗin ya fito daga motarsa har Mama ta ci yana tsoron kar ta zargi wani abu.
“Kun samu sa'ar jinin Uwata... Wallahi kin yi nadamar sanina da kika yi a rayuwarki, sai na ɗanɗana miki wannan baƙincikin”
Yayi wulgi da wayar iya ƙarfinsa, yana huci.
UZAIR POV.
Tare da ƙannensa biyu suka iso gidan da kuma mahaifiyarsa, tana ganin irin halin da yake ciki suka ɗauki shi zuwa asibiti.
Emergency suka wuce da shi layin ƴan haɗari aka ware masa ɗaki daban likitoci suka hau duba shi, sai ihu yake kamar wanda be san inda yake ba, bayan sun yi ɗan bincike su aka tura shi gurin hoto, bayan an masa hoton suka sake dawowa da shi ɗakin suka masa allurar bachi, amman kamar an ƙara masa zafin ciwo yake ji gaba ɗaya ya fita hayyacinsa sai ihu yake. A take suka sake rubuta masa wani hoton, aka je aka ɗauka.
Lokacin da aka fito da hoton, sai Likita ya kira Hajiya suka nufi wani ɗakin da ita sai ya ƙala hotunan a jikin computer. Yana nuna mata.
“Ɗan ki ya taɓa yin haɗari?”
“Gaskiya be taɓa ba, amman ban sani ba ko be faɗa min ba”
“Gaskiya ƙashinsa na baya na karye, kuma na cinyarsa ma ya karye, sannan....”
Kamin ya ƙarasa ta miƙe tsaye ta sauri har kujerar da take zaune samanta ta faɗi.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Ganin hakan yasa likitan dakatar da bayaninta, dan ya ga alamun zata fara masa kuka, shi kansa yasan be kamata ya yi mata wannan bayanin ba, ganin tana mace amman babu yadda ya iya tun da babu wani namiji babban da yayi kusa da mahaifiyarsa. Da sauri ta juya ta fice daga office ɗin tana kiran wayar Abbah. Dan babu wanda ya san an kai Uzair Asibiti dan basu faɗa ba, tun bayan da Yasmin ta daqo gida ba ta damu da tasan dalili ba, tana ganin kamar yayi hakan ne saboda ta janye ƙudirinta.
HILAL POV.
“Miya same ƴar ka haka ne Doc?”
Doc Zara ta tambaya cike da mamakin irin ƙunar da Ulfah ta yi. Hannayensa ya zuba aljihu yana sauke ajiyar zuciya, ita kan Teema tuni ta kusa cikin ɗakin tana hawaye kamar gaske.
“Faɗa suka yi da ƴar'uwarta shi ne wai ta watsa mata ruwan miya dake kan wuta”
“Amman gaskiya ya kamata ka sa ido sosai akan yaranka Uzair, irin wannan abun yana sa kisan kai fa”
“Ƙaddarori ne kawai idan Allah ya kawo abu”
“Allah ya tsare gaba, Ina uwargida har yanzu bata haihu ba?”
“Har yanzu fa”
“To Allah ya raba lafiya”
“Amin”
Tun da suka jero suke maganar basu rabu ba sai da ta kawo kusa da pharmacy sannan ta ɗauki wata hanyar shi kuma ya ciro wayarsa ya kira Hajiya ya faɗa mata, ita Rashida text kawai ya aika mata, sai kuma ya kama hanyar gida dan yi ma Ezzah hukunci.
Sai da ya kama hanyar gida sannan ya kira Kalsoom ya faɗa mata halin da ake ciki, dan yasan zata tashi hankalinta sosai.
Bugu ɗaya ta ɗauka.
“Kana ina ne?”
“Ina hanyar gida, na kaita asibiti da sauƙi”
“Na je gida ban samu kowa ba sai Ezzah tana ta kuka, sai ta biyo ni gani cikin asibitin ma”
“Oooooo Kalsoom miyasa baki ragawa kan ki ne? Ba fa ke kaɗai kike ba a yanzu, da izinin wa kika fita, yanzu da wannan tulelen ciki yama zaki yi driving?”
“Napep na hau”
Ajiyar zuciya ya sauke.
“Tau gani nan juyowa”
Ya katse kiran ya juya ya koma hanyar asibitin. Yana isa aibitin su Hajiyarsa na isa yare da Mama ladi (kanwar mahaifiyarsa) da ƙanensa guda biyu. Jerowa suka yi suna tafiya yana yi ma Hajiya bayanin yadda abun ya faru.
Kalsoom na hango shi tafe tare da Hajiya ta ji babu daɗi musamman dan tana tare da Ezzah tasan dole Hajiya za tayi magana wata ƙila ma zata ce ita ce ta haddasa wannan husumar. Duk sai ta rasa yadda zata yi ga tulelen cikin nan ya mata tsaye kamar wacce zata haihu yanzu.
“Hajiya ina wuni”
“Lafiya ƙalau”
Tana amsa gaisuwar da Kalsoom ta yi mata ta wuce bata ko bi ta kanta ba. Hilal ne ya tsaya gurin matarsa.
“Miya hana ki shiga?”
“Ban san ɗakin da aka kai ta ba”
“Tau muje”
“A'a sai Hajiya ta fito, kar ta gan ni da Ezzah”
“Cemin ta yi wai tana tsoron karka dake ta”
“Ai ba duka kaɗai ba karye ta ma zanyi, ba dai ke har kin kai ki ɗauki ruwan zafi ki watsawa ƴar'uwarki ba...?”
Sai kawai Ezzah tasa kuka ta kama Hijabin Kalsoom ta riƙe gamgam tana kuka. Hilal be bi ta kanta ba ya nufi sashen da zai sadashi da ɗakin Ulfah, Kalsoom ta rufa masa baya tana faɗin Ezzah ta yi shiru ba zata bari ya daketa ba.
Ko da suka shiga Hajiya na kusa da Ulfah dake bachi, tana duba ƙonuwar cike da tausayi, can jikin ƙofa Kalsoom ta tsaya tana kallon Ulfah, Ezzah na riƙe da Hijabinta har lokacin tana kuka. Hajiya ta ɗago ta kalli Ezzah cikin tausayi da ɓacin rai ta ce
“Amman Ezzah baki da zuciyar ƙwarai, ko ɗauki ruwan zafi ki watsawa ƴar'uwarki haka?”
“Wallahi ba nice ba Wallahi Mama Teema ce...!”
Ta faɗa cikin kuka.
[7/18, 8:14 PM] Khadeeja Candy♥: *82*
Teema ta katsa mata tsawa tana zare mata ido alamar dik kika faɗa sai na ci ubanki.
“Ke karki min ƙarya, munafukar yarinya fitsararriya”
“Wallahi ba ni bace, ke kika kira ni kika ce na zo naje kitchen na duba Ulfah ta ƙone...”
Hajiya ta kalli Teema ta kalli Ezzah, ƙoƙarin ɗaukar maganar ta ke, sai kawai ta jiyo kukan Teema wai Ezzah ta mata ƙazafi.
“Wallahi ba zan taɓa yafe miki ba, makira kawai munafuka”
“Ezzah kike cewa haka? Sai kace wata babbar mace? To wai kina aikin me haka ya faru”
Cewar Hajiya tana sake da baki. Ta soma bayani tana kuka da kallon Hilal ko zai kareta ɗin nan.
“Ina cikin kitchen ina girki, na ƙare tuwo sai na ce bari na ɗora miya, sai na ce ta daga kamin daddawa ita kuma Ulfah ta gyara min tabarnuwa, ni ban san gardamar mi suke ba sai kawai naji an taɓa tukuyan miyar da ƙarfi sai ihun Ulfah na ji ina juyowa na ga ta juye mata miyar”
Izzah ta tuma ta dire ta sake tuma ta dire tana kuka da jan Hijabin Kalsoom tana faɗin ba ita ba ce, amman babu wanda ya kula ta Hilal in banda harara babu abunda yake mata, yana cike da haushinta sosai Allah ka ɗai ya san irin hukunci da zai mata idan suka koma gida. Sai kawai ta saki Kalsoom ta ruga gurin Hajiya tana kuka.
“Wallahi ba ni bace Hajiya...”
“Hilal ka saurareta mana”
Kalsoom ta faɗa cike da tausayin kukan da Izzah take yi.
Hilal ya girgiza mata kai.
“Ba wani saurare da za'a mata, ai kin san halinta”
Izzah har da faɗuwa take a gurin taɓa tashi ta kama gyalen Hajiya ta riƙe ƙam.
“Ba zaki rufewa mutane ba ki ba, Wallahi zan dake ki yanzu nan, ba sai mun je gida ba”
Hilal ya faɗa ciki fushi yana mai jin kamar ya kamata ya ɓallata gida biyu. Ihunta ne ya tashi Ulfah daman can ba wani dogon bachi ta yi ba, saboda zafin wuta ko an maka allurar ba bari yake ka yi bachi ba.
“Wayyo Allah Momie, Hajiya, Dady ka kai ni inda Momie ko Anty Kalsoom ko inda Hajiya, bana son gurin Mama Teema ta watsa min wuta, wayyo zafi dady zafi Mama Teema ta ƙona ni, Anty Kalsoom, Momie, Hajiya”
Sune ƙawai sabbatun da take tana murza jikinta sai da Hilal ya riƙe mata hannu. Suna haka sai ga Rashida ta shigo hankalinta a tashe, tana kallon Teema hawaye suka fara mata zuba.
“Ɗaya bayan ɗaya za ki bisu ki kashe, na sani Teema kaɗan daga halinki ne amman ki sani kin ci amana kuma kema amana sai ta ci ki”
Sai kuma ta juyo gurin Kalsoom tana kuka, itana Kalsoom ɗin kuka take, Hajiya ma haka, balle Teema dake ƙoƙarin kare kanta, ƙanen Hilal ma babu wanda baya hawaye.
“Kin ci amanata, sai da na ce miki ki riƙe min yara na amman kika ƙi, yanzu ga shi abunda ya faru, bana da kowa a duniyar nan sai su, su ne farinciki na”
Jakar da ke hannunta ta saki ta nufi gurin ƴarta dake sabbatu, magangun ɗazu kawai take maimaitawa. Rashida ta gadon ta riƙe tana kuka.
“Laifina ne, nice ban riƙe mutuncin aurena ba, ni na kasa zama da ku ni na cuceku Ulfah laifi na, kuma na ci amanar matar da ke riƙon ku tsakani da Allah...”
Ezza ta yi gunta da kuka.
“Momie Wallahi ba ni bace, Dady ya ce sai ya raba ni gida biyu.. Wallahi ba ni ba ce”
“Ba zan ɗauka ba, wannan ba zata kwanta jinya ba, ka kama wannan ka karya min ba, ka saurareta Hilal Wallahi ba ita ba ce, karka ɗauki alhakin yarinyar nan Hilal”