Sashe 40
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Haƙiƙa za mu jarrabe ku da wani abu na tsoro da yunwa da tawayar dukiyoyi da rayuka, da ƴaƴan itatuwa , ka yi albishir ga masu haƙuri (Wajen jure waɗannan jarabce-jarabcen) Waɗanda idan masifa ta same su sai su ce INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN ma'ana :- mu ga Allah muka fito kuma a gare shi za a maiyardar mu. Wanɗannan gafara da kyakkayawan yabo daga Ubangijinsu sun tabbata gare su, da rahama kuma waɗannan sune shiryayyu.” (Baƙara: 155-157)
Tuna waɗannan ayoyin ya ankarar da ita abubuwan data manta, ji tayi kamar an tsikareta, gashin jikinta ya tashi, a nan ta soma tambayar kanta, dan me zata yarda zuciyarta ta rinjayeta ta tsaɓi Ubangijinta? Ta fita daga waɗancan bayin da Allah ke yabo? Ashe Ubangijinta be mata dukan gata ba? Ashe daman Imaninta ƙanƙane ne?
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Ta furta a fili, har sai da mai Napep ɗin ya kalleta.
“Hajiya lafiya dai?”
“Lafiya ƙalau dan Allah juya da ni ka kai ni babbar Asibiti”
“To amman fa wasu kuɗin zaki sake biya”
“Na ji mu tafi”
“Tau Hajiya lafiya kike kuka?”
Sai a lokacin ta tuna da hawayen dake fuskarta, sa sauri ta share hawayen ba tare data ce masa komai ba har suka isa asibitin, sannan ta fita ta ciro kuɗinsa ta ba shi.
Ko da ta shiga cikin ɗakin Asim na zaune, kamsa ya kumbura sosai har idonsa ɗaya ya liƙe, hankalinta ya tashi dan yanzu wannan kumburin ya fi na jiya.
Kusa da shi ta zauna zuciyarta cike da tausayinsa, har idaniyarta na ƙoƙarin zubar masa da ƙwalla.
“Asim kaga har yanzu Anty bata kira ba, kuma bata aiko ba, ni kuma bana da wata mafitar, ga kuɗi da ake bina ma ban san yadda zan yi ba, wannan kumburin naka yana tsorata ni”
Ya matse ƙallah data cika masa ido.
“Namra ko gida za mu koma ne?”
“Idan mun koma za su ce mun kwaso ciwo mun dawo”
“Likita yace idan ba allura nan aka min ba yana da wahala naji sauƙi da wuri”
Hannayenta tasa ta rumgume shi tana kuka. Shi kuma a take yaji sha'awarta ta saukar masa, ya kai hannu yana ɗan shafa ta. Data anƙaro da abunda yake nufi da ita sai tayi saurin ɗagowa daga jikinsa.
“Ina Mama?”
“Tana waje”
Ya sake miƙa hannu yana shafa fuskarta, yana ƙoƙarin ɗaga hijabinta ya zura ɗayan hannunsa ciki.
“Asim asibiti muke fa, kuma dubi halin da kake ciki”
Yawun bakinsa ya haɗe, ba tare daya daina abunda yake mata ba. Ana taɓa ƙofar ɗakin tayi saurin tashi tsaye, shi kuma ya bita da kallo idonsa har sun fara canja kala.
“Mama ina wuni?”
“Lafiya ƙalau ya rana?”
“Alhamdulillah”
Ta ɗan kalleshi cike da kunya, dan gani take kamar Mama ta lura da abunda suke.
“Bari naje gurin Hajara”
Bata jira abunda zai ce ba ta fice. Sai Mama ta zauna a kujerar dake kusa da Asim tana faɗin
“Lamarin nan naka fa ƙaruwa kawai yake yi”
“Tau Mama nayi maganar kuɗin adashen nan kin kawo wasu hujjoji na daban, ko mutuwa na yi ai ke kika rasa ni tun da su ƴar su wani zata aura”
“Shawara da nake kenan a zuciyana, zan je nayi mata bayani sai na karɓo kuɗin daman dubu ɗari uku ne, idan Allah yasa ka samu sauƙi sai a shiga wani kuma”
“Haka yafi, tun da kin ga har yanzu basu saje kira ba ma balle su aiko. Yaushe zaki je?”
“Gobe nake son naje, nima kuɗin da suke hannun na duk sun tafi gurin siyen abinci, ga tufafin nan ƙala ɗaya kullum ƙara naje ya ɗauko wasu tun da waɗanda muka zo da su sun ƙone, da Hajara zan koma in yaso sai na dawo ni kaɗai, daman Haruna ya matsa da maganar yaushe zata dawo”
“Ni Wallahi inda da hali ma da kin tafi yanzu, sai ki dawo gobe da wuri, dan ni kaɗai na san halin da nake ciki, kuma kin ga yanzu aka yi ƙarfe ɗaya, nasan zuwa yamma kin isa”
Ta ɗan yi shiru tana nazari.
“Rana be yi ba?”
“Be yi ba Wallahi, tun da kin ga ma Namra ta zo sai ta zauna nan har ki dawo”
“Tau bari na gani, ai duk na natse ma da wannan kumburin na ka”
Ta tashi ta fita cikin yanayin damuwa. Wayar Asim dake hannun Hajara Namra ta karɓa, ta saka number Babban Yayansu ɗan Hajiya Barau, sai ta matsa can nesa da Hajara ta kira shi.
KALSOOM POV.
Ba itace da girkin ba, amman sanin halin Rashida yasa bata tsaya jiranta ba ta shiga kitchen ta ɗora musu breakfast, daman wani lokacin ita take shirya musu tun da Rashida aiki take zuwa.
Sai da ta shirya komai, na karyawa sannan ta ɗauko kulolin su ta zuba musu abincin su, sannan ta kira su ɗaya bayan ɗaya ta miƙa musu kulolin.
“Ku je gurin mota zan tashi Daddyn ku yanzu”
Ta nufi ɗakinsa, tana buɗe maɓallan rigar bachin ta. A tsakiyar gado yake kwance yana lulluɓe irin yana jin tsayi ɗin nan.
Air conditioner ta fara kashewa sannan ta nufi window ta buɗe su duka ta ɗage labulayen sannan ta nufo inda yake kwance ta yaye bedsheet ɗin tana taɓa masa kunne.
“Likita tashi safiya yayi fa”
Hannu ya kai ya janyo ta saman gadon ya rumgume ta
“Ban gaji da bachi ba”
“Yara suna gurin mota suna jiran ka”
“Ya salam”
Ya ƙara rumgume ta tsamtsam ƙirjinsa, kamar ba zai tashi ba, sai faman lumshe ido yake alamar bachi na masa daɗi.
“Doc. Doc. Doc”
Shiru be motsa bama balle ya amsa ta, hannu ta kai ta murɗa masa kunne, har sai da tayi ƙara ya kama hannunta ya ciza sannan ya tashi, yana jan kitson ta.
“I hate dis Morning”
“Really”
Ta tsire baki tana koyonsa.
“I hate dis Morning”
Ya zare ido, lokacin da idonsa suka kai kan ƙirjinta.
“Wow”
Ya kai hannu zai taɓa ta, ta fisgi kanta cikin zafin nama, ta sauka saman gado ta fice daga ɗakin tana masa dariya.
Tashi yayi ya shiga bathroom ya wanke bakinsa da fuskarsa sannan ya fito ya kai yaran makaranta. Ko da ya dawo babu kowa falo, sai kawai ya nufi ɗakin Rashida dan yaga motarta waje alamar yau bata fita da wuri ba kenan.
Tana ganin ya shigo ta juya kwancinta ta bashi baya. Hakan be da me shi sai ma dariya da yayi ya ƙarasa kusa da ita ya juyo da ita, hawayen daya gani a idonta ya tashi hankalinsa.
“Lafiya Pyar?”
“Bana jindaɗi ne”
“Me ke damun ki”
“Nima ban sani ba”
“Amman miyasa baki faɗa min ba?”
“Taya zan faɗa maka bayan ta shiga haƙƙina taje ta tashe ka, kuma ta san yau ba girkin ta bane”
“Ta riga ta saba ne, saboda kina fita sa sassafe ba tare da kin damu da tashi na ba, balle haɗa mana abun karyawa”
“Ni gaskiya ta daina shiga min haƙƙi bana so”
“Shikenan zan mata magana, amman yanzu faɗa min me kike ji yana damun ki”
“Fever, sneeze, headache and nauseous”
“Zan diɓi jininki da fitsari idan zan fita, yanzu tashi mu karya sai ki sha magana”
Ta ƙara manne masa a jiki.
“A'a ni bana so cin komai”
“Tea fa?”
“Sai dai idan kai zaka haɗa min da kan ka”
“Yes ni zan haɗa miki ai”
Ya faɗa yana murmushi, sannan ya tashi ya fice. Ajiyar zuciya Rashida ta sauke, ranta yana mata ba daɗi, idan har zarginta ya tabbata gasjiyar tana da ciki, tana cikin matsala dan bata iya tantance na waye ne,
‘Taya wani zai gane idan ba ni ma faɗa ba?’
Tambayar da tazo mata kenan a zuciyarta, sai kawai ta tashi ta shiga banɗaki.
Hilal sai da ya shiga ɗakinsa ya ɗauko maganinka sannan ya nufo ɗakin Kalsoom, a lokacin tana zaune gaban madubi tana shiryawa dan fitowarta daga wanka kenan.
Daga bakin ƙofa ya tsaya yana kallonta yace
“Wifey Yau madam babu lafiya, ba zata fito ba tea kawai zata sha, ni ma kuma bana jin cin komai”
Kai ta ɗaga masa tayi murmushin da be kai zuci ba. Har ya wuce, sai kuma ya dawo ya tsaya bakin ƙofar ya miƙa mata hannu.
“Taso na haɗa miki breakfast”
Ba musu ta taso ta miƙa masa hannun ba dan ranta na mata daɗi ba. A kujerar data saba zama ya zaunar da ita, ya ɗauki kofi biyu ya haɗa tea, ya aje mata ɗaya gabanta ya zuba mata ƙwai da sauran abubuwan da suke gurin, sannan yaƴi mata kiss ya ɗauki tea ɗin ya nufi ɗakin Rashida.
Da kallo ta bishi, zuciyarta na sosuwa da lamarinsa, tabbas yana son matarsa fiye da yadda yake son kansa, yanzu ya kasa karyawa saboda bata da lafiya, ta lura da yadda yanayinsa ya canja a take, taya zata shiga rayuwar irin waɗannan ma'auratan sannan tace zata samu farinciki?
Hannu ta kai ta shafa cikinta, hawaye masu zafi suka silalo daga idonta.
Sai da ya bata tea ɗin tasha sannan ya bata magani, sai ya sake fita yaje ya ɗauko wasu robobi guda biyu ya miƙa mata babbar.
“Kiyi fitsari a wannan”
Hannunsa sanye da safa, ya ɗibi jininta ya zuba a ƙaramin robar sannan ya manna mata kaɗa ya lunda mata, ya kwance robar daya ɗaure mata hannun da shi, kwashe kayan yayi ya fice. Bayan kamar thirty minutes ya dawo ɗakin da shirinsa na zuwa office.
Robar fitsarin ya ta bashi, ya karɓa yayi mata kiss, sannan ya fice. Ɗakin Kalsoom ya shiga, tana jin motsinta ta lafe kamar tana bachi, itama kiss ɗin yayi mata sannan ya fice.
Rashida na jin tashin motarsa ta janyo wayarta ta danna number Asmee, ringing huɗu tayi sannan ta ɗauka.
“Asmee an tashi lafiya?”
“Lafiya ƙalau ya gidan?”
Ya amsa mata muryarta da alamar damuwa.
“Asmee yau ba zan samu fita ba, bana jindaɗi, sai dai kr kije idan da hali”
“Me ke damun ki?”
“Abubuwa da yawa ga jikin duk ya min nauyi”
“Ko dai ciki ne?”
“Haka nake tunani nima”
“Allah ya raba lafiya”
Jin ta faɗa ba da wani jindaɗi ba yasa Rashida Tambaya.
“Ya naji muryar ki ba daɗi?”
Tuna waɗannan ayoyin ya ankarar da ita abubuwan data manta, ji tayi kamar an tsikareta, gashin jikinta ya tashi, a nan ta soma tambayar kanta, dan me zata yarda zuciyarta ta rinjayeta ta tsaɓi Ubangijinta? Ta fita daga waɗancan bayin da Allah ke yabo? Ashe Ubangijinta be mata dukan gata ba? Ashe daman Imaninta ƙanƙane ne?
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Ta furta a fili, har sai da mai Napep ɗin ya kalleta.
“Hajiya lafiya dai?”
“Lafiya ƙalau dan Allah juya da ni ka kai ni babbar Asibiti”
“To amman fa wasu kuɗin zaki sake biya”
“Na ji mu tafi”
“Tau Hajiya lafiya kike kuka?”
Sai a lokacin ta tuna da hawayen dake fuskarta, sa sauri ta share hawayen ba tare data ce masa komai ba har suka isa asibitin, sannan ta fita ta ciro kuɗinsa ta ba shi.
Ko da ta shiga cikin ɗakin Asim na zaune, kamsa ya kumbura sosai har idonsa ɗaya ya liƙe, hankalinta ya tashi dan yanzu wannan kumburin ya fi na jiya.
Kusa da shi ta zauna zuciyarta cike da tausayinsa, har idaniyarta na ƙoƙarin zubar masa da ƙwalla.
“Asim kaga har yanzu Anty bata kira ba, kuma bata aiko ba, ni kuma bana da wata mafitar, ga kuɗi da ake bina ma ban san yadda zan yi ba, wannan kumburin naka yana tsorata ni”
Ya matse ƙallah data cika masa ido.
“Namra ko gida za mu koma ne?”
“Idan mun koma za su ce mun kwaso ciwo mun dawo”
“Likita yace idan ba allura nan aka min ba yana da wahala naji sauƙi da wuri”
Hannayenta tasa ta rumgume shi tana kuka. Shi kuma a take yaji sha'awarta ta saukar masa, ya kai hannu yana ɗan shafa ta. Data anƙaro da abunda yake nufi da ita sai tayi saurin ɗagowa daga jikinsa.
“Ina Mama?”
“Tana waje”
Ya sake miƙa hannu yana shafa fuskarta, yana ƙoƙarin ɗaga hijabinta ya zura ɗayan hannunsa ciki.
“Asim asibiti muke fa, kuma dubi halin da kake ciki”
Yawun bakinsa ya haɗe, ba tare daya daina abunda yake mata ba. Ana taɓa ƙofar ɗakin tayi saurin tashi tsaye, shi kuma ya bita da kallo idonsa har sun fara canja kala.
“Mama ina wuni?”
“Lafiya ƙalau ya rana?”
“Alhamdulillah”
Ta ɗan kalleshi cike da kunya, dan gani take kamar Mama ta lura da abunda suke.
“Bari naje gurin Hajara”
Bata jira abunda zai ce ba ta fice. Sai Mama ta zauna a kujerar dake kusa da Asim tana faɗin
“Lamarin nan naka fa ƙaruwa kawai yake yi”
“Tau Mama nayi maganar kuɗin adashen nan kin kawo wasu hujjoji na daban, ko mutuwa na yi ai ke kika rasa ni tun da su ƴar su wani zata aura”
“Shawara da nake kenan a zuciyana, zan je nayi mata bayani sai na karɓo kuɗin daman dubu ɗari uku ne, idan Allah yasa ka samu sauƙi sai a shiga wani kuma”
“Haka yafi, tun da kin ga har yanzu basu saje kira ba ma balle su aiko. Yaushe zaki je?”
“Gobe nake son naje, nima kuɗin da suke hannun na duk sun tafi gurin siyen abinci, ga tufafin nan ƙala ɗaya kullum ƙara naje ya ɗauko wasu tun da waɗanda muka zo da su sun ƙone, da Hajara zan koma in yaso sai na dawo ni kaɗai, daman Haruna ya matsa da maganar yaushe zata dawo”
“Ni Wallahi inda da hali ma da kin tafi yanzu, sai ki dawo gobe da wuri, dan ni kaɗai na san halin da nake ciki, kuma kin ga yanzu aka yi ƙarfe ɗaya, nasan zuwa yamma kin isa”
Ta ɗan yi shiru tana nazari.
“Rana be yi ba?”
“Be yi ba Wallahi, tun da kin ga ma Namra ta zo sai ta zauna nan har ki dawo”
“Tau bari na gani, ai duk na natse ma da wannan kumburin na ka”
Ta tashi ta fita cikin yanayin damuwa. Wayar Asim dake hannun Hajara Namra ta karɓa, ta saka number Babban Yayansu ɗan Hajiya Barau, sai ta matsa can nesa da Hajara ta kira shi.
KALSOOM POV.
Ba itace da girkin ba, amman sanin halin Rashida yasa bata tsaya jiranta ba ta shiga kitchen ta ɗora musu breakfast, daman wani lokacin ita take shirya musu tun da Rashida aiki take zuwa.
Sai da ta shirya komai, na karyawa sannan ta ɗauko kulolin su ta zuba musu abincin su, sannan ta kira su ɗaya bayan ɗaya ta miƙa musu kulolin.
“Ku je gurin mota zan tashi Daddyn ku yanzu”
Ta nufi ɗakinsa, tana buɗe maɓallan rigar bachin ta. A tsakiyar gado yake kwance yana lulluɓe irin yana jin tsayi ɗin nan.
Air conditioner ta fara kashewa sannan ta nufi window ta buɗe su duka ta ɗage labulayen sannan ta nufo inda yake kwance ta yaye bedsheet ɗin tana taɓa masa kunne.
“Likita tashi safiya yayi fa”
Hannu ya kai ya janyo ta saman gadon ya rumgume ta
“Ban gaji da bachi ba”
“Yara suna gurin mota suna jiran ka”
“Ya salam”
Ya ƙara rumgume ta tsamtsam ƙirjinsa, kamar ba zai tashi ba, sai faman lumshe ido yake alamar bachi na masa daɗi.
“Doc. Doc. Doc”
Shiru be motsa bama balle ya amsa ta, hannu ta kai ta murɗa masa kunne, har sai da tayi ƙara ya kama hannunta ya ciza sannan ya tashi, yana jan kitson ta.
“I hate dis Morning”
“Really”
Ta tsire baki tana koyonsa.
“I hate dis Morning”
Ya zare ido, lokacin da idonsa suka kai kan ƙirjinta.
“Wow”
Ya kai hannu zai taɓa ta, ta fisgi kanta cikin zafin nama, ta sauka saman gado ta fice daga ɗakin tana masa dariya.
Tashi yayi ya shiga bathroom ya wanke bakinsa da fuskarsa sannan ya fito ya kai yaran makaranta. Ko da ya dawo babu kowa falo, sai kawai ya nufi ɗakin Rashida dan yaga motarta waje alamar yau bata fita da wuri ba kenan.
Tana ganin ya shigo ta juya kwancinta ta bashi baya. Hakan be da me shi sai ma dariya da yayi ya ƙarasa kusa da ita ya juyo da ita, hawayen daya gani a idonta ya tashi hankalinsa.
“Lafiya Pyar?”
“Bana jindaɗi ne”
“Me ke damun ki”
“Nima ban sani ba”
“Amman miyasa baki faɗa min ba?”
“Taya zan faɗa maka bayan ta shiga haƙƙina taje ta tashe ka, kuma ta san yau ba girkin ta bane”
“Ta riga ta saba ne, saboda kina fita sa sassafe ba tare da kin damu da tashi na ba, balle haɗa mana abun karyawa”
“Ni gaskiya ta daina shiga min haƙƙi bana so”
“Shikenan zan mata magana, amman yanzu faɗa min me kike ji yana damun ki”
“Fever, sneeze, headache and nauseous”
“Zan diɓi jininki da fitsari idan zan fita, yanzu tashi mu karya sai ki sha magana”
Ta ƙara manne masa a jiki.
“A'a ni bana so cin komai”
“Tea fa?”
“Sai dai idan kai zaka haɗa min da kan ka”
“Yes ni zan haɗa miki ai”
Ya faɗa yana murmushi, sannan ya tashi ya fice. Ajiyar zuciya Rashida ta sauke, ranta yana mata ba daɗi, idan har zarginta ya tabbata gasjiyar tana da ciki, tana cikin matsala dan bata iya tantance na waye ne,
‘Taya wani zai gane idan ba ni ma faɗa ba?’
Tambayar da tazo mata kenan a zuciyarta, sai kawai ta tashi ta shiga banɗaki.
Hilal sai da ya shiga ɗakinsa ya ɗauko maganinka sannan ya nufo ɗakin Kalsoom, a lokacin tana zaune gaban madubi tana shiryawa dan fitowarta daga wanka kenan.
Daga bakin ƙofa ya tsaya yana kallonta yace
“Wifey Yau madam babu lafiya, ba zata fito ba tea kawai zata sha, ni ma kuma bana jin cin komai”
Kai ta ɗaga masa tayi murmushin da be kai zuci ba. Har ya wuce, sai kuma ya dawo ya tsaya bakin ƙofar ya miƙa mata hannu.
“Taso na haɗa miki breakfast”
Ba musu ta taso ta miƙa masa hannun ba dan ranta na mata daɗi ba. A kujerar data saba zama ya zaunar da ita, ya ɗauki kofi biyu ya haɗa tea, ya aje mata ɗaya gabanta ya zuba mata ƙwai da sauran abubuwan da suke gurin, sannan yaƴi mata kiss ya ɗauki tea ɗin ya nufi ɗakin Rashida.
Da kallo ta bishi, zuciyarta na sosuwa da lamarinsa, tabbas yana son matarsa fiye da yadda yake son kansa, yanzu ya kasa karyawa saboda bata da lafiya, ta lura da yadda yanayinsa ya canja a take, taya zata shiga rayuwar irin waɗannan ma'auratan sannan tace zata samu farinciki?
Hannu ta kai ta shafa cikinta, hawaye masu zafi suka silalo daga idonta.
Sai da ya bata tea ɗin tasha sannan ya bata magani, sai ya sake fita yaje ya ɗauko wasu robobi guda biyu ya miƙa mata babbar.
“Kiyi fitsari a wannan”
Hannunsa sanye da safa, ya ɗibi jininta ya zuba a ƙaramin robar sannan ya manna mata kaɗa ya lunda mata, ya kwance robar daya ɗaure mata hannun da shi, kwashe kayan yayi ya fice. Bayan kamar thirty minutes ya dawo ɗakin da shirinsa na zuwa office.
Robar fitsarin ya ta bashi, ya karɓa yayi mata kiss, sannan ya fice. Ɗakin Kalsoom ya shiga, tana jin motsinta ta lafe kamar tana bachi, itama kiss ɗin yayi mata sannan ya fice.
Rashida na jin tashin motarsa ta janyo wayarta ta danna number Asmee, ringing huɗu tayi sannan ta ɗauka.
“Asmee an tashi lafiya?”
“Lafiya ƙalau ya gidan?”
Ya amsa mata muryarta da alamar damuwa.
“Asmee yau ba zan samu fita ba, bana jindaɗi, sai dai kr kije idan da hali”
“Me ke damun ki?”
“Abubuwa da yawa ga jikin duk ya min nauyi”
“Ko dai ciki ne?”
“Haka nake tunani nima”
“Allah ya raba lafiya”
Jin ta faɗa ba da wani jindaɗi ba yasa Rashida Tambaya.
“Ya naji muryar ki ba daɗi?”