Sashe 110
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Fine as you wish, amman aikin ka fa”
“Mun samu hutu ai ko ka manta?”
“Haka ne, to ba matsala amman dai karka ɗauki lokaci i have surprise for you”
“Thank you super Dad”
Daga haka ya kashe wayar ya kalli Sadauki dake front seat ya ce.
“Mai Martaba ya ce sauran za su iya kama hanya yanzu kai kawai zaka tsaya sai jibi za mu koma”
“An gama Yarima, Allah ya ƙara maka lafiya”
Be amsa ba sai kawai ya maida hankalinsa kan titi. Can kuma ya kalli agogo hannunsa.
“Yaushe zamu isa Kaduna?”
“Allah ya taimaki Yarima, nan da minti goma sha biyar zamu isa”
Daga nan be sake cewa komai ba har suka isa masaukinsa. Su suka buɗe masa mota ya fito suka rufa masa baya suna masa kirari, iya ƙofar falon suka tsaya. Sai ya juyo ya kalli Sadauki ya ce.
“A ba ko wannensu 30k kai kuma ka shirya anjima zamu je mu duba marar lafiyar nan”
“An gama Yarima, takawarka lafiya ɗan sarki jikan sarki, an gama ɗan adalin Sarki”
Sai da ya shige sannan suka janyo ƙofar suka rufe masa. Alkyabar jikinsa ya fara cirewa sannan ya buɗe maɓallan rigarsa, ya kishingida saman kujera, ya lumshe ido.
Tun da ya shiga ciki be fito ba sai da aka yi kiran sallah magariba daman basu baro zariya ba sai da aka yi la'asar.
Tare da Sadauki suka yi sallah a masallacin da ke kusa da gidan, sannan suka nufo gida. A hanyar su ta dawowa ne Abdool yake masa jan kunne.
“Bana son abunda kake min, karka sake ɗauko min takalmi ka aje min, kuma daga yau kar na sake jin wani kirari nawa a bakin ka, ka kira ni da Abdool kawai ko Yarima amman ba sai ka min kirare ba”
“Allah ya taimake ka za a daina”
Ya faɗa cikin girmamawa.
“Zaka iya tuna inda muka je gidan mai Napep ɗin nan da muka kaɗe?”
“Allah ya taimake ka, zan gane”
“To za mu koma mu duba shi, akwai canji a hannunka ko? Zamu siya musu fruits”
“An gama Yarima”
“Zan shiga na canja sai muje”
“A canja da kyau ɗan Sarki, Allah yaja zamanin ka”
Kallo ɗaya Abdool yayi masa ya kauda ido yana girgiza kai.
******************
Bayan salla magariba Uwani ta shigo ɗakin ta kunna mata kendir, ta aje mata maltina da Madara da kuma tea mai kauri, tare da biredi.
“Kuma ɗawainiya da ni na gode sosai”
Mirmushi Uwani ta yi
“Ba komai ai yi ma kai ne. Ki ci dai ki samu karfin jiki”
“Ni kaina ina son na samu ƙarfin jikin ko zan samu damar komawa gurin iyayena”
“Tafiya za ki yi?”
“Gobe na ke so idan Allah ya yarje min”
“Amman ina laifin ko nan da sati idan kin ƙara jin sauƙi?”
“Wata ƙila idan suka ga na samu sauƙi su ƙi karɓa na, amman ganina a hakan zai sa su tausaya min”
“Amman dai da kin yi haƙuri har ki ji sauƙi”
“Ina son tafiyar ne”
“To bari na faɗawa Neina”
Ta juya cikin rashin jidaɗi dan yanzu sun ɗan fara sabawa da Namra, zancen tafiyarta be mata daɗi ba.
“Neina wai kin ji Namra zata tafi”
Abunda ta fito tana faɗa kenan, ganin Yarima yasa ta yi saurin sadda kanta ƙasa jikinta ya shiga rawa.
“Barka da dare”
“Barka...”
Ya amsa kaɗan-kaɗan yana tsaye kan Lamido, dan ya kasa zama tun da ya shigo gidan yanzu ma ya samu kansa da ƙyamar gidan. Farar shadda dake jikinsa sai ƙara haska shi take. Uwani ta yi mamakin ganin sa ba dogorai, sai dai haka be hana ta gane shi ba.
Unƙurawa Lamido yayi ya tashi zaune daga kwance da yake, dan zuwan Abdool be sashi ya ɗago ba duk da cika masa ido da yayi, da kuma kwarjinin da ya yi masa, yana jin rashin sakewa da Abdool wata ƙila saboda ba matsayin ɗaya ba, ko kuma dan kaɗewar da yayi masa ne ya hana shi ganin farinsa sai haushinsa yake ji. A ƙoƙarinsa na avoiding ɗin Yarima ya kalli Uwani da Neina ya ce.
“Wani abu aka mata ne?”
“A'a wallahi sai dai ko ta gaji da zama ne, ko tana son ta koma Katsina ne”
Cewar Neina. Sai Uwani ta amsa da
“A'a wai ta ce tana son ta koma gida ne, ko zasu tausaya mata su karɓe ta, kuma wai gobe zata je, kamar wace ake kora”
“Amman Namra bata da tunani, taya zata koma gurin iyayenta cikin wannan hali?”
“Wlh kuwa, ni ma na ce ta yi haƙuri dai har gaba...”
Tsawa Sadauki ya katsawa Uwani, wanda shi kansa Lamido sai da ya zabura balle kuma Neina da daman jikinta rawa yake, ganin ɗan sarki tsaye a gidansu.
“Ke ƴar talakawa ba a wata magana a gaban Ɗan Sarki, kama kan ki ki iya bakin ki...”
Sosai Uwani ta shiga natsuwarta tsabar tsoro ma har ji tayi kamar ta amayar da hanjin cikinta. Abdool kuma wa watsa ma Sadauki Harara, dan sosai yake jin daɗin maganar da suke, sarau zuciyarsa ta raya masa da Namra ake, duk da bashi da tabbacin hakan.
Tsawar da Sadauki yayi ma Uwani ne yasa Namra ta san da akwai baƙo a gidan dan ta ji muryar da ba ta ɗan gidan ba. Hakan yasa ta aje maltinar dake hannunta, ta gyara tsawyuwar Hijabin dake jikinta ta leƙo ƙofar ɗakin.
Bata gane ko waye ba, bata kuma ta mu da ta sani ɗin ba, sai kawai ta juya ta koma ɗakin. Shi kam Abdool sarai ya gane ta, dan ya daɗe da haddace fuskarta, duk da duhun magariba ya fara saukowa hakan be hana shi gane ta ba.
Ya daidaita tsayuwar hannayensa da ke cikin aljihu, ya juya ba tare daya ce da su komai ba, sai sadauki ne yake musu Allah ya ƙara lafiya, duk suka amsa da Ameen ban da Lamido.
Be yarda yayi ma Abdool kallon banza ba, ko wata yassar magana sai da ya juya baya ya fice.
“Wani zai nunawa isa, girman kan tsiya”
“Aa Lamido karka jawa kanka, dan Allah ka iya bakin ka”
Neina ta faɗa zuciyarta cike da tsoro. Wani wawan tsaki Lamido yaja ya wuyar da fuskarsa zuwa ɗakin da Namra take ciki.
**************
Tafiya yake guda guda yana tsotsar bakinsa kamar mai shan minti. Jinginawa yayi da motar da suka zo, yana kallon Sadauki yana tsaya gefensa cike da ladabi.
“A bincika min baƙuwar fuskar da take gidan nan, wacce ta zo daga Katsina i can't recall her name amman ai ka ji yarinyar da suke magana akai ko?”
“Za a bincika, Allah yaja zamanin ka, ya ƙara maka lafiya”
Wannan karon Abdool da kansa yayi driver zuwa suka ɗauki hanyar masaukinsa, sai tariyar maganar su Uwani yake, yana analyzing.
ASIM POV.
Ledodin dake hannunsa ya dire mata yana sauke gajiya tare da miƙa mata ragowar canji.
“Yayi Kyau Asim kana ƙoƙari sosai. Ya kamata ka hutu kam nima zan je gida na da yake can cikin gari dan yata zata zo, kuma bata san ina wannan sana'ar ba, dole acan nake sauka idan zata zo, dan haka zaka yi hutun kwana biyu sai kaje gurin matar ka ku yi murnar mota ka ɗauke ta kuje gari ku shana”
Ya ɗan yi murmushi tare da sosa kansa, shi kansa ya jidaɗin wannan hutun da zata ba shi dan zai bashi dama ya je gurin baƙuwarsa, kuma daman can yana son ɗaukar Mardiya su fita gari.
“Ai bana da mata Hajiya bana da mata yanzu, ina dai kam nema”
Ta masa kallon rashin fahimta.
“ Kamar ya ba nasan kana da mata ba ada?”
“Eh mun ɗan samu matsala ne, har mun rabu ai”
“Subhanalillahi, kai kam Asim me ya kai ka?mata mai haƙuri da juriya haka? Me ta maka”
“Wlh Hajiya ta cika kwaɗayi ne, ga complain akan aiki nan, shiyasa kawai naga rabuwar ta fi, yanzu dai wata na ke so idan Allah ya yarda”
Idan ran Hajiya Sadiya yayi dubu ya ɓace a yanzu dam bata jidaɗin maganar nan ta Asim ba
“Amman Wallahi sam ba ka yi tunani ba, taya zaka sakin matar da ta rufa maka Asiri har haka, ka gaggauta mayarda matar ka matuƙar tana son mu shirya da kai, ni bana son ana ciwa mace mutuci”
“Wallahi Hajiya bana jin daɗin zama da ita ne, duk ita ce silar halin rayuwar dana shiga, sam arziki na da nata be haɗu ba, daman can ban yi istiƙara ba na aure ta, yanzu muna rabuwa komai nawa ya dawo daidai, arziki sai shigowa yake”
“Na dai faɗa maka, rufin asirin ka ka maida auren ka a yanzu duk inda matar ka take ka yi gaggawar mayar da ita shine kwanciyar hankalin ka, kaje ka yi tunani, ni sam bana son ana wulaƙanta mace akan aure, to kacewa iyayenta me? Sam dam baka da tunani Asim, idan ma akan aikin ka ai da ka yi sahawara da ni dole za mu samu mafita yadda za'ayi”
Miƙewa ta yi tsaye cike da ɓacin rai ta nƴfi ɗakinta. Shi kam Asim da kallo ya bi ta yana mamakin yadda ta haƙiƙan akan Namra kamar wata ƴar'uwata, tunani yake yi da ace ya fada nata gaskiyar rabuwarsu da Namra akan ciki ne wata ƙila ma ranta ya fi haka ɓaci.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *68 NOT EDITED*
Ta ina zai fara neman ta? Taya ma zai je neman yarinyar da yake ganin rabuwa da ita kamar ya huta da ƙaya ne?
“Zata dawo, na san bata je gidan su ai da yanxu an kira ni, amman na san zata dawo gare ni dole, amman neman ta yanzu a gare ni ai aiki ne sabo, kuma zata jidaɗi sosai idan har na neme ta”
Abunda yake faɗa kenan yana tuƙa motarsa a hankali. Wayarsa ce ta yi ringing, da sauri ya ɗauka ganin mai kiran har da murmushi a fuskarsa.
“Hello Babe”
“Hey how are you?”
“Fine i'm just thinking of you”
“Kar ka damu ai gobe za mu haɗu, zaka gan ni a fuska nima na gan ka a fuska”
“I can't wait, me kike so a shirya miki?”
“Na yi waya da Mom nawa zata shirya min komai”
“Mun samu hutu ai ko ka manta?”
“Haka ne, to ba matsala amman dai karka ɗauki lokaci i have surprise for you”
“Thank you super Dad”
Daga haka ya kashe wayar ya kalli Sadauki dake front seat ya ce.
“Mai Martaba ya ce sauran za su iya kama hanya yanzu kai kawai zaka tsaya sai jibi za mu koma”
“An gama Yarima, Allah ya ƙara maka lafiya”
Be amsa ba sai kawai ya maida hankalinsa kan titi. Can kuma ya kalli agogo hannunsa.
“Yaushe zamu isa Kaduna?”
“Allah ya taimaki Yarima, nan da minti goma sha biyar zamu isa”
Daga nan be sake cewa komai ba har suka isa masaukinsa. Su suka buɗe masa mota ya fito suka rufa masa baya suna masa kirari, iya ƙofar falon suka tsaya. Sai ya juyo ya kalli Sadauki ya ce.
“A ba ko wannensu 30k kai kuma ka shirya anjima zamu je mu duba marar lafiyar nan”
“An gama Yarima, takawarka lafiya ɗan sarki jikan sarki, an gama ɗan adalin Sarki”
Sai da ya shige sannan suka janyo ƙofar suka rufe masa. Alkyabar jikinsa ya fara cirewa sannan ya buɗe maɓallan rigarsa, ya kishingida saman kujera, ya lumshe ido.
Tun da ya shiga ciki be fito ba sai da aka yi kiran sallah magariba daman basu baro zariya ba sai da aka yi la'asar.
Tare da Sadauki suka yi sallah a masallacin da ke kusa da gidan, sannan suka nufo gida. A hanyar su ta dawowa ne Abdool yake masa jan kunne.
“Bana son abunda kake min, karka sake ɗauko min takalmi ka aje min, kuma daga yau kar na sake jin wani kirari nawa a bakin ka, ka kira ni da Abdool kawai ko Yarima amman ba sai ka min kirare ba”
“Allah ya taimake ka za a daina”
Ya faɗa cikin girmamawa.
“Zaka iya tuna inda muka je gidan mai Napep ɗin nan da muka kaɗe?”
“Allah ya taimake ka, zan gane”
“To za mu koma mu duba shi, akwai canji a hannunka ko? Zamu siya musu fruits”
“An gama Yarima”
“Zan shiga na canja sai muje”
“A canja da kyau ɗan Sarki, Allah yaja zamanin ka”
Kallo ɗaya Abdool yayi masa ya kauda ido yana girgiza kai.
******************
Bayan salla magariba Uwani ta shigo ɗakin ta kunna mata kendir, ta aje mata maltina da Madara da kuma tea mai kauri, tare da biredi.
“Kuma ɗawainiya da ni na gode sosai”
Mirmushi Uwani ta yi
“Ba komai ai yi ma kai ne. Ki ci dai ki samu karfin jiki”
“Ni kaina ina son na samu ƙarfin jikin ko zan samu damar komawa gurin iyayena”
“Tafiya za ki yi?”
“Gobe na ke so idan Allah ya yarje min”
“Amman ina laifin ko nan da sati idan kin ƙara jin sauƙi?”
“Wata ƙila idan suka ga na samu sauƙi su ƙi karɓa na, amman ganina a hakan zai sa su tausaya min”
“Amman dai da kin yi haƙuri har ki ji sauƙi”
“Ina son tafiyar ne”
“To bari na faɗawa Neina”
Ta juya cikin rashin jidaɗi dan yanzu sun ɗan fara sabawa da Namra, zancen tafiyarta be mata daɗi ba.
“Neina wai kin ji Namra zata tafi”
Abunda ta fito tana faɗa kenan, ganin Yarima yasa ta yi saurin sadda kanta ƙasa jikinta ya shiga rawa.
“Barka da dare”
“Barka...”
Ya amsa kaɗan-kaɗan yana tsaye kan Lamido, dan ya kasa zama tun da ya shigo gidan yanzu ma ya samu kansa da ƙyamar gidan. Farar shadda dake jikinsa sai ƙara haska shi take. Uwani ta yi mamakin ganin sa ba dogorai, sai dai haka be hana ta gane shi ba.
Unƙurawa Lamido yayi ya tashi zaune daga kwance da yake, dan zuwan Abdool be sashi ya ɗago ba duk da cika masa ido da yayi, da kuma kwarjinin da ya yi masa, yana jin rashin sakewa da Abdool wata ƙila saboda ba matsayin ɗaya ba, ko kuma dan kaɗewar da yayi masa ne ya hana shi ganin farinsa sai haushinsa yake ji. A ƙoƙarinsa na avoiding ɗin Yarima ya kalli Uwani da Neina ya ce.
“Wani abu aka mata ne?”
“A'a wallahi sai dai ko ta gaji da zama ne, ko tana son ta koma Katsina ne”
Cewar Neina. Sai Uwani ta amsa da
“A'a wai ta ce tana son ta koma gida ne, ko zasu tausaya mata su karɓe ta, kuma wai gobe zata je, kamar wace ake kora”
“Amman Namra bata da tunani, taya zata koma gurin iyayenta cikin wannan hali?”
“Wlh kuwa, ni ma na ce ta yi haƙuri dai har gaba...”
Tsawa Sadauki ya katsawa Uwani, wanda shi kansa Lamido sai da ya zabura balle kuma Neina da daman jikinta rawa yake, ganin ɗan sarki tsaye a gidansu.
“Ke ƴar talakawa ba a wata magana a gaban Ɗan Sarki, kama kan ki ki iya bakin ki...”
Sosai Uwani ta shiga natsuwarta tsabar tsoro ma har ji tayi kamar ta amayar da hanjin cikinta. Abdool kuma wa watsa ma Sadauki Harara, dan sosai yake jin daɗin maganar da suke, sarau zuciyarsa ta raya masa da Namra ake, duk da bashi da tabbacin hakan.
Tsawar da Sadauki yayi ma Uwani ne yasa Namra ta san da akwai baƙo a gidan dan ta ji muryar da ba ta ɗan gidan ba. Hakan yasa ta aje maltinar dake hannunta, ta gyara tsawyuwar Hijabin dake jikinta ta leƙo ƙofar ɗakin.
Bata gane ko waye ba, bata kuma ta mu da ta sani ɗin ba, sai kawai ta juya ta koma ɗakin. Shi kam Abdool sarai ya gane ta, dan ya daɗe da haddace fuskarta, duk da duhun magariba ya fara saukowa hakan be hana shi gane ta ba.
Ya daidaita tsayuwar hannayensa da ke cikin aljihu, ya juya ba tare daya ce da su komai ba, sai sadauki ne yake musu Allah ya ƙara lafiya, duk suka amsa da Ameen ban da Lamido.
Be yarda yayi ma Abdool kallon banza ba, ko wata yassar magana sai da ya juya baya ya fice.
“Wani zai nunawa isa, girman kan tsiya”
“Aa Lamido karka jawa kanka, dan Allah ka iya bakin ka”
Neina ta faɗa zuciyarta cike da tsoro. Wani wawan tsaki Lamido yaja ya wuyar da fuskarsa zuwa ɗakin da Namra take ciki.
**************
Tafiya yake guda guda yana tsotsar bakinsa kamar mai shan minti. Jinginawa yayi da motar da suka zo, yana kallon Sadauki yana tsaya gefensa cike da ladabi.
“A bincika min baƙuwar fuskar da take gidan nan, wacce ta zo daga Katsina i can't recall her name amman ai ka ji yarinyar da suke magana akai ko?”
“Za a bincika, Allah yaja zamanin ka, ya ƙara maka lafiya”
Wannan karon Abdool da kansa yayi driver zuwa suka ɗauki hanyar masaukinsa, sai tariyar maganar su Uwani yake, yana analyzing.
ASIM POV.
Ledodin dake hannunsa ya dire mata yana sauke gajiya tare da miƙa mata ragowar canji.
“Yayi Kyau Asim kana ƙoƙari sosai. Ya kamata ka hutu kam nima zan je gida na da yake can cikin gari dan yata zata zo, kuma bata san ina wannan sana'ar ba, dole acan nake sauka idan zata zo, dan haka zaka yi hutun kwana biyu sai kaje gurin matar ka ku yi murnar mota ka ɗauke ta kuje gari ku shana”
Ya ɗan yi murmushi tare da sosa kansa, shi kansa ya jidaɗin wannan hutun da zata ba shi dan zai bashi dama ya je gurin baƙuwarsa, kuma daman can yana son ɗaukar Mardiya su fita gari.
“Ai bana da mata Hajiya bana da mata yanzu, ina dai kam nema”
Ta masa kallon rashin fahimta.
“ Kamar ya ba nasan kana da mata ba ada?”
“Eh mun ɗan samu matsala ne, har mun rabu ai”
“Subhanalillahi, kai kam Asim me ya kai ka?mata mai haƙuri da juriya haka? Me ta maka”
“Wlh Hajiya ta cika kwaɗayi ne, ga complain akan aiki nan, shiyasa kawai naga rabuwar ta fi, yanzu dai wata na ke so idan Allah ya yarda”
Idan ran Hajiya Sadiya yayi dubu ya ɓace a yanzu dam bata jidaɗin maganar nan ta Asim ba
“Amman Wallahi sam ba ka yi tunani ba, taya zaka sakin matar da ta rufa maka Asiri har haka, ka gaggauta mayarda matar ka matuƙar tana son mu shirya da kai, ni bana son ana ciwa mace mutuci”
“Wallahi Hajiya bana jin daɗin zama da ita ne, duk ita ce silar halin rayuwar dana shiga, sam arziki na da nata be haɗu ba, daman can ban yi istiƙara ba na aure ta, yanzu muna rabuwa komai nawa ya dawo daidai, arziki sai shigowa yake”
“Na dai faɗa maka, rufin asirin ka ka maida auren ka a yanzu duk inda matar ka take ka yi gaggawar mayar da ita shine kwanciyar hankalin ka, kaje ka yi tunani, ni sam bana son ana wulaƙanta mace akan aure, to kacewa iyayenta me? Sam dam baka da tunani Asim, idan ma akan aikin ka ai da ka yi sahawara da ni dole za mu samu mafita yadda za'ayi”
Miƙewa ta yi tsaye cike da ɓacin rai ta nƴfi ɗakinta. Shi kam Asim da kallo ya bi ta yana mamakin yadda ta haƙiƙan akan Namra kamar wata ƴar'uwata, tunani yake yi da ace ya fada nata gaskiyar rabuwarsu da Namra akan ciki ne wata ƙila ma ranta ya fi haka ɓaci.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *68 NOT EDITED*
Ta ina zai fara neman ta? Taya ma zai je neman yarinyar da yake ganin rabuwa da ita kamar ya huta da ƙaya ne?
“Zata dawo, na san bata je gidan su ai da yanxu an kira ni, amman na san zata dawo gare ni dole, amman neman ta yanzu a gare ni ai aiki ne sabo, kuma zata jidaɗi sosai idan har na neme ta”
Abunda yake faɗa kenan yana tuƙa motarsa a hankali. Wayarsa ce ta yi ringing, da sauri ya ɗauka ganin mai kiran har da murmushi a fuskarsa.
“Hello Babe”
“Hey how are you?”
“Fine i'm just thinking of you”
“Kar ka damu ai gobe za mu haɗu, zaka gan ni a fuska nima na gan ka a fuska”
“I can't wait, me kike so a shirya miki?”
“Na yi waya da Mom nawa zata shirya min komai”