Sashe 10
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Uzair sai ka yi haƙuri da lamarin Khadija, har yanzu akwai ƙurciya a tare da ita, kuma ita ba zata gane alfanun wannan auren ba har sai anyi, haƙiƙa ina son Khadija matuƙa sai dai tayi tsalle ne da ɓata rawarta tun daga lokacin data tsaya kai da fata akan lalle ita sai wannan yaron,
na bata dama na fitar da wani ta ƙyale wannan yaron amman sai ta buga min ƙafa a ƙasa ita sai Asim, shiyasa kaga na fita lamarin ta, saboda so da yawa zaka abunda mu iyaye muke hangowa ba shi ƴaƴa ke hangowa ba, a tunanin ta na yi mata hakan ne dan na cutar da ita, tun da ta nuna bata so.
Nasan anbar auren dole a yanzu, amman duk abunda na yi ma Namra ita ta jawa kanta”
Abbah ya ɗaga kai ya sake kallon Uzair da kyau yana mai nuna masa abunda yake faɗi a bakinsa shine a zuciyarsa.
“Uzairu ina fatar zaka riƙa Khadija da amana, kuma zaka nuna mata so da kulawa, irin son da zata san lallai ta yi dacen mahaifinta be mata mugun zaɓi ba, ina son ka sani duk abunda ya samu Namra ni ya sama, kuma zai taɓa mahaifiyarta, ina addu'a wannan aure Allah ya sa masa albarka, ya baku haƙuri zama da junanku”
Jikin Uzair yayi san yi sosai da kalaman da Abbah yayi masa, sai yake jin kamar Abbah ya san abunda yake son aikatawa.
Cikin rashin kuzari ya yi ma Abbah sallama, ya tashi ya fice.
Har ya iso gurin motarsa tunanin kalaman Abbah yake.
‘Abunda duk ya sami Khadija ni ya sama’
Same shi ya fi tsaya masa a rai, tunani yake what if Abbah ya gane gaskiyar dalilinsa na neman aurenta? Shi kuma baya jin yana da wata mafita ta rufa ma kansa asiri bayan wannan, tun shi dai ba zai ce zai kashe Namra ba, gashi ta ce sai ta tona masa asiri.
Ya kwashe minti arba'in a gurin yana tunani, ba tare da ya sani ba. Can sai ya nufi gurin Mai gadin yayi masa magana kan ya shiga yayi masa sallama da Namra.
Cikin girmamawa mai gadin ya nufi part ɗin Anty Amarya, shi kuma ya dawo gurin Motarsa ya tsaya ransa a jagule.
In few minute Mai gadin ya dawo ya shaida masa ance gata nan zuwa. Chanji ya fiddo a aljihunsa ya miƙawa Mai gadin, sannan ya gyara tsayuwarsa yana jiran fitowarta.
Lokacin da Mai gadin ya shigo falon, Anty Amarya, na zaune tare da ƙannensa suna cin abinci, sai tace da Mai gadin yace tana zuwa, sannan ta tashi Maryam ta ce taje ta kirata ɗakinta.
Maryam ta aje littafin dake hannunta ta tashi ta nufi ɗakinta. Tana yin sallama Amira ta zabura kamar marar gaskiya.
“Anty Amira, ina Anty Namra?”
Shiru tayi tana dube-dube kamar mai neman abu, can kuma ta kalli Maryam tace
“Maryam idan na faɗa miki wani abu zaki fahimta ai ko?”
“Uhmm minene?”
“Namra ta fita ɗazu, Asim ne yayi mata texs wai yana son ta zo suyi sallama, shine ta fita tun ɗazu”
Gaban Maryam ya faɗi
“Amman kika barta taje ita kaɗai? Idan wani abun ya same ta fa?”
Shiru tayi tana tunanin ƙaryar da zata ƙaƙaro
“Ba yadda ban yi ba, amman tace ba zan bita ba, wai na tsaya kar a zo nemanta ba'a ga kowa ba, amman bari na kirata”
Cikin sauri ta shiga kiran wayar. Maryam bata tsaya ba, ta juya ta fita.
Daga bakin ƙofa ta tsaya tana kiran Anty Amarya. Daker ta taso saboda abincin da suke ci da kuma firar da suke da ƴan'uwanta.
A tunaninta Maryam zata ce mata Namra taƙi zuwa ne, sai kawai taji wani labari banbaragwai. A take Anty Amarya ta ɗauko wayarta ta shiga kira amman ba a picking.
Sai duk hankalinsu ta tashi, Anty Amarya ta koma ɗakin Namra ta samu Amira zaune tana faman kiran waya.
Anty Amarya ta katsa mata tsawa.
“Ina tace miki zata?”
Jiki na rawa ta amsa ma Anty Amarya dan ta ga ranta ya ɓace sosai.
“Tace min nan bayan layi”
“Amman dai Anty Amira kin yi wawanci Wallahi, shine kika bar ta taje? Maimaiko ki hanata ko ki faɗawa Anty, kuma kika ƙi binta kuje tare”
Maryam ta faɗa tana hararar Amira. Anty Amarya tace
“Ita ma Namra ai da wayon ta”
“Ko da wayonta ai wani abun sai an nuna mata, tun da kinsan yadda Anty Namra take ko ni sai na fita wayo, waya sani ma ko da ke ya haɗa kai kika lallaɓa masa ita ta tafi”
Amira ta kalleta
“Haba Maryam wane irin magana kike haka ne? Kina tunanin ni zan iya cutar da Namra?”
“Waya sani abu a duhu, ƙawayen yanzu ai ba abun yarda bane, kuma Wallahi duk abunda ya samu Namra ki ƙaddara ke ya sama dan ba zan taɓa yafe miki ba”
Amaimakon Amira tayi magana sai kawai ta fashe da kuka, ta tashi ta ɗauki pose ɗinta ta fice tana kuka.
Anty Amarya sai ta hau Maryam da faɗa
“Wai Maryam ba zaki bar fitsarar nan ba ko? Kullum ina miki magana kan shegen bakin nan naki amman baki ji, yanzu miye na wannan furucin fisabillahi? Ita Namra ƙaramar yarinya ce da Amira zata ɗorata a layi ta hau?”
Maryam ta tunzure baki.
“Wallahi zata iya ɗora ta a layi wannan Amirar da kike gani shegen wayo ne da ita, kuma Wallahi tun ba yau na lura kamar tana hassadar Anty Namra, wani fa sam baya son yaga cigaba a gareka sai ci baya, kuma wani maƙiyi na ɓoye ba gane shi ake ba”
Anty Amarya ta katsa mata tsawa
“Zaki je kiyi magana da Uzair, ko tsayawa zaki yi, kina ƙara min ɓacin rai”
Juyawa tayi ta fita tana faɗin
“Wallahi duk wani abu ya samu Anty Namra Amira zan zarga”
Ɗakinta ta shiga ta ɗauki Hijabinta ta saka, sannan ta fito ta nufi harabar gidan gurin da Uzair yake, tana harararsa.
“Bata jindaɗi ba zata iya fitowa ba”
Ta faɗa ba tare data masa sallama ba, kuma bata tsaya jiran abunda zai ce ba ta juya tayi tafiyarta.
Wani kallo ya bita dashi, daman duk cikin Family Abbah Maryam tafi uban kowa tsageranci. Buɗe Motarsa ya yi ya shiga zuciyarsa cike da tunane-tunane, hannu yasa ya shafa kansa, sai ya ciro wayarsa ya nemo wata number ya danna mata kira.
Ana yin picking ya ce
“Tahir kana ina?”
Ban ji me aka ce masa ba, sai kawai yace
“Ok gani nan zuwa yanzu”
Daga haka ya kashe wayar, ya ƙarama gudu. Can kaɗai ne yake jin zai iya tafiya ya fayyace sirrinsa, tun da duk akan layi ɗaya suke.
Sai da ya yi tafiya mai nisa, sannan ya isa bakin wani ƙaton gate.
Horn yayi mai gaɗin ya buɗe masa sannan ya kunna kai cikin ƙaton guesthouse ɗin. Parking ya yi, ya fito ya nufi hanyar shiga gurin. Zazzaune ya tararda su, Tahir da Najeeb. Tun daga ganin yanayin shigowarsa sun san akwai wani abu a ƙasa. Tahir ne ya fara magana
“Lafiya kake Uzair?”
Bakinsa ya cika ma iska ya busar
“Wallahi ina cikin matsala”
“Matsalar me?”
Najeeb ya tambaya, cike da son sanin abunda ke damun amininsa.
Uzair be ɓoye aminansa komai ba, tun daga ganin da Namra tayi ma friends ɗinsa na Abuja har zuwa nemanta da yayi, kuma kalaman da Abbah yayi masa yanzu, sannan ya ɗora da sace ta da yayi.
Tahir ya girgiza kai
“Uzair you Fuck up, ai yin wannan abun da kanka matsala ne, mun riga mun san junan mu toh miye na ɓoyewa kasa kanka a matsala? Yanzu ka sace yarinyar mutane kana ganin asirinka ba ze tunu ba?”
“Nayi tunanin zan iya solved ɗin matsalar ne, da nayi nufin na riƙe ta ne har kwana biyu ta yadda za a yi tunanin ta gudu da bi saurayinta ne. Ga Yasmin ta juya min baya na rasa gane kanta, kuma yanzu idan ta dawo zata iya faɗa asirina ya tonu kuma kasan komai ze iya faruwa, family ni za a zaga kuma.mahaifinta ba zai ƙyale ni ba”
Tahir ya dawo kusa da shi ya dafa shi.
“Ka kwantar da hankalinka, irin wannan yarinyar ta dabara bata musu, kuma irin wannan sirrin ba a sake da shi”
Najeeb yace
“Lallai kam, irin wannan yarinyar malamai za a shiga da ita, fiussss an gama da ita”
Tahir yace
“Shine kawai, yanzu kaje kayi abunda zaka yi da ita, kasa a maida ita gida kamin asuba, zan rubuta maka wani magani ka bata tasha zata manta abunda ya faru, idan Jafar ya dawo zamu zauna mutattauna”
Murmushi jindaɗi yayi, yajin ya samu mafita gurin abokansa.
Cikin kuzari ya tashi bayan Doctor Tahir ya rubuta masa maganin a takarda, ya yi musu sallama ya fice.
__________________________
LOVE YOU ALL FISABILLIAH 💖😘🌺
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 8*
Yana cikin mota yana driving zuwa guesthouse ɗinsa, kiran Najeeb ta shigo wayarsa. Picking yayi ya kara a kunne sai ya mai da tuƙin da hannu ɗaya.
“Hello”
“Uzair kana ina? Ka isa gidan ne?”
“A'a gani dai kan hanyar zuwa siyen maganin”
“Karka siyo ka wuce gidan kawai, idan ka isa ka jira ni gani nan zuwa, kuma ka tabbatar bata farka ba, idan kuma ta riga ta farka, karka bari ta gan ka, ina ka aje ta?”
“A guesthouse ɗina”
Sai ya kashe wayar, ya ƙara ma Motarsa gudu. Yana isa, Najeeb na isa. Sai duk suka yi saurin fitowa Motar. Najeeb ya nufi shi yana faɗin
“Yanzu ya kamata mu mai da ita gida”
“Taya?”
Najeeb ya kalli ko ina na gurin, sannan yace
“Ni zan kaita, faɗa min inda ka ɗauke ta, zanje can na maidata, zamu saka mai gadin nan naka ya je a inda take ya riƙa ihu da neman taimako har mutane su taru su, su nuna masa gidansu, zai bamu haɗin kai dai ko?”
“Me zai hana indai an bashi kuɗi”
Uzair ya faɗa.
“Okay zan tsara masa yadda zai yi, miye sunan Saurayin nata?”
“Asim sunan shi Ibrahim, amman anfi saninsa da Asim”
na bata dama na fitar da wani ta ƙyale wannan yaron amman sai ta buga min ƙafa a ƙasa ita sai Asim, shiyasa kaga na fita lamarin ta, saboda so da yawa zaka abunda mu iyaye muke hangowa ba shi ƴaƴa ke hangowa ba, a tunanin ta na yi mata hakan ne dan na cutar da ita, tun da ta nuna bata so.
Nasan anbar auren dole a yanzu, amman duk abunda na yi ma Namra ita ta jawa kanta”
Abbah ya ɗaga kai ya sake kallon Uzair da kyau yana mai nuna masa abunda yake faɗi a bakinsa shine a zuciyarsa.
“Uzairu ina fatar zaka riƙa Khadija da amana, kuma zaka nuna mata so da kulawa, irin son da zata san lallai ta yi dacen mahaifinta be mata mugun zaɓi ba, ina son ka sani duk abunda ya samu Namra ni ya sama, kuma zai taɓa mahaifiyarta, ina addu'a wannan aure Allah ya sa masa albarka, ya baku haƙuri zama da junanku”
Jikin Uzair yayi san yi sosai da kalaman da Abbah yayi masa, sai yake jin kamar Abbah ya san abunda yake son aikatawa.
Cikin rashin kuzari ya yi ma Abbah sallama, ya tashi ya fice.
Har ya iso gurin motarsa tunanin kalaman Abbah yake.
‘Abunda duk ya sami Khadija ni ya sama’
Same shi ya fi tsaya masa a rai, tunani yake what if Abbah ya gane gaskiyar dalilinsa na neman aurenta? Shi kuma baya jin yana da wata mafita ta rufa ma kansa asiri bayan wannan, tun shi dai ba zai ce zai kashe Namra ba, gashi ta ce sai ta tona masa asiri.
Ya kwashe minti arba'in a gurin yana tunani, ba tare da ya sani ba. Can sai ya nufi gurin Mai gadin yayi masa magana kan ya shiga yayi masa sallama da Namra.
Cikin girmamawa mai gadin ya nufi part ɗin Anty Amarya, shi kuma ya dawo gurin Motarsa ya tsaya ransa a jagule.
In few minute Mai gadin ya dawo ya shaida masa ance gata nan zuwa. Chanji ya fiddo a aljihunsa ya miƙawa Mai gadin, sannan ya gyara tsayuwarsa yana jiran fitowarta.
Lokacin da Mai gadin ya shigo falon, Anty Amarya, na zaune tare da ƙannensa suna cin abinci, sai tace da Mai gadin yace tana zuwa, sannan ta tashi Maryam ta ce taje ta kirata ɗakinta.
Maryam ta aje littafin dake hannunta ta tashi ta nufi ɗakinta. Tana yin sallama Amira ta zabura kamar marar gaskiya.
“Anty Amira, ina Anty Namra?”
Shiru tayi tana dube-dube kamar mai neman abu, can kuma ta kalli Maryam tace
“Maryam idan na faɗa miki wani abu zaki fahimta ai ko?”
“Uhmm minene?”
“Namra ta fita ɗazu, Asim ne yayi mata texs wai yana son ta zo suyi sallama, shine ta fita tun ɗazu”
Gaban Maryam ya faɗi
“Amman kika barta taje ita kaɗai? Idan wani abun ya same ta fa?”
Shiru tayi tana tunanin ƙaryar da zata ƙaƙaro
“Ba yadda ban yi ba, amman tace ba zan bita ba, wai na tsaya kar a zo nemanta ba'a ga kowa ba, amman bari na kirata”
Cikin sauri ta shiga kiran wayar. Maryam bata tsaya ba, ta juya ta fita.
Daga bakin ƙofa ta tsaya tana kiran Anty Amarya. Daker ta taso saboda abincin da suke ci da kuma firar da suke da ƴan'uwanta.
A tunaninta Maryam zata ce mata Namra taƙi zuwa ne, sai kawai taji wani labari banbaragwai. A take Anty Amarya ta ɗauko wayarta ta shiga kira amman ba a picking.
Sai duk hankalinsu ta tashi, Anty Amarya ta koma ɗakin Namra ta samu Amira zaune tana faman kiran waya.
Anty Amarya ta katsa mata tsawa.
“Ina tace miki zata?”
Jiki na rawa ta amsa ma Anty Amarya dan ta ga ranta ya ɓace sosai.
“Tace min nan bayan layi”
“Amman dai Anty Amira kin yi wawanci Wallahi, shine kika bar ta taje? Maimaiko ki hanata ko ki faɗawa Anty, kuma kika ƙi binta kuje tare”
Maryam ta faɗa tana hararar Amira. Anty Amarya tace
“Ita ma Namra ai da wayon ta”
“Ko da wayonta ai wani abun sai an nuna mata, tun da kinsan yadda Anty Namra take ko ni sai na fita wayo, waya sani ma ko da ke ya haɗa kai kika lallaɓa masa ita ta tafi”
Amira ta kalleta
“Haba Maryam wane irin magana kike haka ne? Kina tunanin ni zan iya cutar da Namra?”
“Waya sani abu a duhu, ƙawayen yanzu ai ba abun yarda bane, kuma Wallahi duk abunda ya samu Namra ki ƙaddara ke ya sama dan ba zan taɓa yafe miki ba”
Amaimakon Amira tayi magana sai kawai ta fashe da kuka, ta tashi ta ɗauki pose ɗinta ta fice tana kuka.
Anty Amarya sai ta hau Maryam da faɗa
“Wai Maryam ba zaki bar fitsarar nan ba ko? Kullum ina miki magana kan shegen bakin nan naki amman baki ji, yanzu miye na wannan furucin fisabillahi? Ita Namra ƙaramar yarinya ce da Amira zata ɗorata a layi ta hau?”
Maryam ta tunzure baki.
“Wallahi zata iya ɗora ta a layi wannan Amirar da kike gani shegen wayo ne da ita, kuma Wallahi tun ba yau na lura kamar tana hassadar Anty Namra, wani fa sam baya son yaga cigaba a gareka sai ci baya, kuma wani maƙiyi na ɓoye ba gane shi ake ba”
Anty Amarya ta katsa mata tsawa
“Zaki je kiyi magana da Uzair, ko tsayawa zaki yi, kina ƙara min ɓacin rai”
Juyawa tayi ta fita tana faɗin
“Wallahi duk wani abu ya samu Anty Namra Amira zan zarga”
Ɗakinta ta shiga ta ɗauki Hijabinta ta saka, sannan ta fito ta nufi harabar gidan gurin da Uzair yake, tana harararsa.
“Bata jindaɗi ba zata iya fitowa ba”
Ta faɗa ba tare data masa sallama ba, kuma bata tsaya jiran abunda zai ce ba ta juya tayi tafiyarta.
Wani kallo ya bita dashi, daman duk cikin Family Abbah Maryam tafi uban kowa tsageranci. Buɗe Motarsa ya yi ya shiga zuciyarsa cike da tunane-tunane, hannu yasa ya shafa kansa, sai ya ciro wayarsa ya nemo wata number ya danna mata kira.
Ana yin picking ya ce
“Tahir kana ina?”
Ban ji me aka ce masa ba, sai kawai yace
“Ok gani nan zuwa yanzu”
Daga haka ya kashe wayar, ya ƙarama gudu. Can kaɗai ne yake jin zai iya tafiya ya fayyace sirrinsa, tun da duk akan layi ɗaya suke.
Sai da ya yi tafiya mai nisa, sannan ya isa bakin wani ƙaton gate.
Horn yayi mai gaɗin ya buɗe masa sannan ya kunna kai cikin ƙaton guesthouse ɗin. Parking ya yi, ya fito ya nufi hanyar shiga gurin. Zazzaune ya tararda su, Tahir da Najeeb. Tun daga ganin yanayin shigowarsa sun san akwai wani abu a ƙasa. Tahir ne ya fara magana
“Lafiya kake Uzair?”
Bakinsa ya cika ma iska ya busar
“Wallahi ina cikin matsala”
“Matsalar me?”
Najeeb ya tambaya, cike da son sanin abunda ke damun amininsa.
Uzair be ɓoye aminansa komai ba, tun daga ganin da Namra tayi ma friends ɗinsa na Abuja har zuwa nemanta da yayi, kuma kalaman da Abbah yayi masa yanzu, sannan ya ɗora da sace ta da yayi.
Tahir ya girgiza kai
“Uzair you Fuck up, ai yin wannan abun da kanka matsala ne, mun riga mun san junan mu toh miye na ɓoyewa kasa kanka a matsala? Yanzu ka sace yarinyar mutane kana ganin asirinka ba ze tunu ba?”
“Nayi tunanin zan iya solved ɗin matsalar ne, da nayi nufin na riƙe ta ne har kwana biyu ta yadda za a yi tunanin ta gudu da bi saurayinta ne. Ga Yasmin ta juya min baya na rasa gane kanta, kuma yanzu idan ta dawo zata iya faɗa asirina ya tonu kuma kasan komai ze iya faruwa, family ni za a zaga kuma.mahaifinta ba zai ƙyale ni ba”
Tahir ya dawo kusa da shi ya dafa shi.
“Ka kwantar da hankalinka, irin wannan yarinyar ta dabara bata musu, kuma irin wannan sirrin ba a sake da shi”
Najeeb yace
“Lallai kam, irin wannan yarinyar malamai za a shiga da ita, fiussss an gama da ita”
Tahir yace
“Shine kawai, yanzu kaje kayi abunda zaka yi da ita, kasa a maida ita gida kamin asuba, zan rubuta maka wani magani ka bata tasha zata manta abunda ya faru, idan Jafar ya dawo zamu zauna mutattauna”
Murmushi jindaɗi yayi, yajin ya samu mafita gurin abokansa.
Cikin kuzari ya tashi bayan Doctor Tahir ya rubuta masa maganin a takarda, ya yi musu sallama ya fice.
__________________________
LOVE YOU ALL FISABILLIAH 💖😘🌺
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 8*
Yana cikin mota yana driving zuwa guesthouse ɗinsa, kiran Najeeb ta shigo wayarsa. Picking yayi ya kara a kunne sai ya mai da tuƙin da hannu ɗaya.
“Hello”
“Uzair kana ina? Ka isa gidan ne?”
“A'a gani dai kan hanyar zuwa siyen maganin”
“Karka siyo ka wuce gidan kawai, idan ka isa ka jira ni gani nan zuwa, kuma ka tabbatar bata farka ba, idan kuma ta riga ta farka, karka bari ta gan ka, ina ka aje ta?”
“A guesthouse ɗina”
Sai ya kashe wayar, ya ƙara ma Motarsa gudu. Yana isa, Najeeb na isa. Sai duk suka yi saurin fitowa Motar. Najeeb ya nufi shi yana faɗin
“Yanzu ya kamata mu mai da ita gida”
“Taya?”
Najeeb ya kalli ko ina na gurin, sannan yace
“Ni zan kaita, faɗa min inda ka ɗauke ta, zanje can na maidata, zamu saka mai gadin nan naka ya je a inda take ya riƙa ihu da neman taimako har mutane su taru su, su nuna masa gidansu, zai bamu haɗin kai dai ko?”
“Me zai hana indai an bashi kuɗi”
Uzair ya faɗa.
“Okay zan tsara masa yadda zai yi, miye sunan Saurayin nata?”
“Asim sunan shi Ibrahim, amman anfi saninsa da Asim”