Sashe 172
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta ture masa hannu ta nufi ɗakinta. Binta yayi yana rarraahinta shi kanshi yasan tayi missing ɗin gidan, sai dai shi baya son ta je ko'ina saboda cikin nan nata gani yake kamar da ta ɗaga wani abun zai same shi, hakan yasa indai ba aiki yake ba kullum yana gida saboda yi kula da ita da kuma kama mata wani aikin duk da likita yace ta riƙa ɗan wala jininta.
Duk ta bi ta motsaye ta tsomaye saboda cikin ya janye ta, Abdool kawai ke ta ƙiba abunsa hankalinsa kwance bashi da matsala ta ko'ina. Ita kaɗai ke ta fama ɗan chat ɗin da take tana rage kewa yanzu duk ta tattara ta watsar komai baya mata daɗin a duniyar nan, cikin ma ji take kamar ta cire shi ta aje. Wani lokacin idan suna fira da Abdool ta kance ashe haka iyaye suke ji shiyasa ake cewa ƴaƴa suna da haƙƙin iyaye, haka zata zauna tana masa kuka kamar ƙaramar yarinya, wai cikin ya haye mata zuciya ko ya taushe mata mara.
Kusan kullum shi yake daba abinci saboda bata cin abincin kowa sai nasa, ko takeaway yayi musu sai dai ya cinƴe abunsa wai warinsa take ji, ko ita ta girka abincin bata cinsa sai dai Abdallah yayi mata, da wasa-wasa ya ƙware gurin girki saboda yau idan yayi mata wannan gobe wacan zai mata.
[8/7, 2:48 PM] Khadeeja Candy♥: Ranar Monday EDD ta ya cika amman bata haihu ba sai wata assabar a babban asibitin Abuja, murna gurin Abdallah kamar ya soye Namra da yaron da ta haifa ya cinye dan tsabar jindaɗi da farinciki, Allah ya nuna masa ya ga jikansa ta ɓangaren Abdallah.
Mai Martaba ma sai ya rasa inda zai sa ransa saboda farinciki, tun a waya yasa aka turo masa hoton jaririn ta whatsapp. Ƴan uwan Abdallah babu wanda be saka hoton a instagram ba, a can sokoto ma murna suke, family Abbah da kuma Mai Martaba da suke Abuja suka ne suka riƙa kula Namra, awarta guɗu a asibiti bayan ta haihu sai da suka sa ta yi bachi sannan suka sallameta.
Ko da ta dawo gida yamma yayi a dole ta haƙura ta bi jirgin gobe. Tare da family Abdallah suka sauka sokoto, su sukaje da kansu suka kai Namra har gida, iya gata an nunawa Namra ta ko wane ɓangare.
An zuba mata kayaɓ barka kamar ba gobe, kayan jariri sai ka ɗauka wani ƙaramin shago za a buɗe na siyar da kayan jarirai, ga shi ƴan uwa sai kawo mata ake ta ko'ina.
Ranar suna yaro ya ci sunan Mai Martaba, wato Ahmad, akayi masa laƙani da Sultan. An kashe naira ranar suna kamar ba a san zafin nemanta ba, duk faɗin gidan sai da ya cika da jama'a, musamman ma da yamma da ƴan'uwansu Abdallah suka zo da kuma na Ummi. An ci ana sha kuma an watse cikin farinciki da kwanciyar hankali, kowa sai yabon bikin yake ana Allah sam barka.
Duk bayan kwana biyu sai Abdool ya zo sokoto ganin ɗansa, kira kan waya kan waya ta safe daban ta rana daban ta dare ma haka. Kamin ta yi arba'in duk ya takura, kunyar Anty yasa ya kasa magana har sai da ta ƙara sati biyu sama sannan aka maida ta Abuja, tare da bayinta guda biyu sabida su taimaka mata hidimar gida.
Komai ya koma musu kamar su suka tsarawa kansu yadda rayuwar zata zo musu, suna bawa junansu kulawa yadda ya kamata, sai dai wani lokacin tana fuskantar matsala ta ɓangare Abdallah saboda zafin kishi da yake da shi. Lokuta da dama yakan hanata zuwa wani gurin ita kaɗai duk kuwa da kasancewar a garin Abuja ne amman ganin yake kamar wani zai mata magana idan ta fita ba tare da shi ba.
Yau ma duk da tana son fitar dole ta haƙura har sai da yawo, ya ci abincin yayi wanka sannan ya ɗauki Sultan ita kuma ta riƙa jakarta suka fita, shi yake driving Sultan na jikinsa rumgume ita kuma tana front seat har suka isa, wani babban Shopping.
Tana gaba yana biye haka suka shiga shopping ɗin. Yana riƙe da Sultan har ta siye abunda duk zata siya aka zo gurin biyan kuɗi ya bada atm ɗinsa aka cire adaɗin kuɗin da ta kashe, sannan suka koma cikin motar ya ɗauki hanyar gidansu Hajiya Umaima, wato Ƙanwar Mai Martaba wacce take nan Abuja.
Ta tarbesu da far'ah daman ta jima tana masa magana akan ya kawo mata Namra. Hannu ta kai ta karɓi Sultan da ke hannun Abdool tana faɗin
“Ai har na yi fushi na ce ba zan sake maka magana ba”
“Ko yanzu ai nice na matsa”
“No.wonder ni nasan sai ƴata”
“Haba Hajiya taya zaki biyeta ni nace ta shirya mu zo fa”
Hajiya Umaimai tayi dariya.
“Duk abunda zaka faɗa ba zan yarda ba. Mardiya kawo lemu kamin abinci ya ƙarasa”
Ta ƙarasa tana ƙwalawa mai aikinta kira, ba a ɗauki tsawon lokaci ba sai ga Mardiya ta fito daga kitchen ɗauke da drinks da cups. Gabanta ya faɗi lokacin da tayi arba da Namra, ita kanta Namra tayi mamakin ganinta sai dai daga ita ha4 Mardiyar babu wanda ya iya yima wani magana, har sai da ta wuce sannan Namra ta kalli Hajiya Umaima ta ce
“Hajiya ina kika san Mardiya?”
“Wallahi daga Katsina aka kawo ta, na ce a nemo min wace zata riƙa taya ni aiki ne sai aka kawo min ita, kin santa ne?”
“Eh a Katsina take shiyasa na yi mamaki ganinta nan”
“Aiki ta zo yau satinta biyu ma”
“Allah sarki”
Umaima ta miƙawa Namra Sultan.
“Bari na duba abincin nan, kar na shiga muku da yaro Kitchen”
Abdool yayi dariya
“Wai ina su Jamila ne?”
“Wlh duk sunje biki kasan halin ƙanen naka sai a hankali idan kunnensu ya ji biki, ba manyan ba ba yara ba”
Hajiya Umaima na shiga Kitchen sai Namra ta miƙe tsaye ta miƙawa Abdool Sultan ta nufi ɗakin da ta hango Mardiya ta shiga. Da sallama ta shiga, amman Mardiya bata iya amsa mata ba saboda bata son ta gano kuka, gyaran ɗakin ta tarar tana yi. Har Namra ta juya zata fita sai Mardiya ta juyo ta ce.
“Namra Asim ya mutu, Asim ya koma ga Ubangijinsa”
Namra ta juyo tana zaro ido.
“Yaushe? Miya same shi?”
“Rashin lafiyar da ta kama shi a faɗar Sarkin Katsina bata barsa ba sai da ta tafi da ransa”
“Innalillahi wa'inna ilaihi”
Ta faɗa tana dafe kanta hawaye na zubar mata. Mardiya ta risina ƙasa tana kuka.
“Namra ki taimaki Asim ki taimake ni ki yafe mana, amanarki da na ci ta hanani sukuni, duk wanɗanda na yi ma zalumcin na nemi yafiyarsu ke kaɗai kika rage min, na tsorata da irin mutuwar da Asim yayi, bana son na yi irin mutuwarsa”
Namra ta duƙo dai-dai Mardiya tana dafata.
“Miya samu Asim?”
Babu abunda ta ɓoye mata daga rayuwar Asim daga rashin lafiyarsa da kuma mutuwarsa zuwa irin rayuwar luwaɗin da tasan yana yi, ga kuma saduwar da yake yi da ita ta baya.
“Bayan mun gama wanka aka raba mana gadon kuɗin da ya bari na gida da filayen da ya siyar, a take nawa kuɗin suka ƙare gidan da na siya kuma ya ƙone, ga rashin lafiyar da take jikina saboda saduwar da yake yi da Ni ta baya, a duk lokacin da wannan ƙaiƙayin ya taso min sai na ji kamar zan mutu, na kasa daina mafarkin wuta Namra, ada ina tunanin ko wutar da na kunna miki ce gidanki ya ƙone, amman sai nake ganin kamar har da wutar lahira ce take jirana, ki taimake ni ki yafe min Namra, na ci amanarki, na han'ince ki, na cutarda ke”
Wani kuka take marar murya saboda bata son Hajiya Umaima ta ji.
“Na yafe miki Mardiya shi ma Asim na yafe masa, Allah ya masa rahama”
Ta miƙe tsaye tana hawaye.
“Ki rufa min asiri karki faɗawa kowa sirrin, yana ɗaya daga cikin dalilin da ya sa na bar Katsina na dawo nan ga aiki saboda na canjawa kai na rayuwa, kuma na rufawa kai na asiri da abunda zan ci, na taimaki uwata da ƙannena”
“Babu wanda zai ji, na miki alƙawari ba zan taɓa faɗawa kowa ba”
Sai da ta share hawayen sannan ta fice. Sai dai hakan be hana Abdool gane ta yi kuka ba. Tana zaunawa kusa da shi ya kalleta ya ce
“Kin yi kuka saboda kinji Asim ya rasu ko?”
Da sauri ta kalleshi.
“Ka sani kenan?”
“Abnam har gobe kina son Asim”
“No ba haka ba ne, kawai ina tausayinsa ne”
“Tausayi ne silar so”
“Ba irin wacan tausayin ba”
Ya miƙe tsaye tare da ɗansa, ya ɗauki car keys ɗinsa ya fice. Tana zaune a gurin ta ji tashin motarsa. Lumshe ido ta yi ta buɗe sannan ta ɗago tana amsa maganar da Hajiya Umaima ke mata.
“Lafiya Babangida ya tafi?”
“Wai zai ga wani abokinsa ne, yace idan an ɗan jima kisa direba ya kai ni”
“Okay toh taso muje ɗaki ga abincin nan Mardiya zata kawo yau mun ranar girki”
“Wallahi Hajiya na ci abinci”
“Ai nasan kin ci abincin, karki so ma min musu ba tarbiya ba ce”
Da murmushi Namra ta tashi ta bita suka shiga ɗaki. Kamin ta gama cin abinci ayi sallah la'asar har ta tsawwala saboda tunanin Abdool yana can gida cikin ɓacin rai. Tana gama sallah la'asar ta yi ma Hajiya Umaima magana tasa ka direba ya kai ta gida. Bata same shi a falo ba, hakan tasa ta nufi ɗakinsa, kwance ta hango shi saman gado, Sultan na saman ƙirjinsa idonsa a lumshe kamar mai bachi.
Tasan ba bachi yake ba, domin be saba bachin yamma ba, sai dai wannan baya rasa nasaba da ɓacin ran da take tunanin ya sawa kansa akan abunda har ga Allah ba haka yake ba. Be buɗe ido ba har ta ƙarasa kusa da shi ta zauna saman gado.
“Ya Omri...”
“Abnam please, bana son na fara ganin laifinki, bana son zuciyata na ƙonuwa akan ki ina gudun na fara ganin baƙinki, dan Allah ki fita sai zuwa anjima”
Duk ta bi ta motsaye ta tsomaye saboda cikin ya janye ta, Abdool kawai ke ta ƙiba abunsa hankalinsa kwance bashi da matsala ta ko'ina. Ita kaɗai ke ta fama ɗan chat ɗin da take tana rage kewa yanzu duk ta tattara ta watsar komai baya mata daɗin a duniyar nan, cikin ma ji take kamar ta cire shi ta aje. Wani lokacin idan suna fira da Abdool ta kance ashe haka iyaye suke ji shiyasa ake cewa ƴaƴa suna da haƙƙin iyaye, haka zata zauna tana masa kuka kamar ƙaramar yarinya, wai cikin ya haye mata zuciya ko ya taushe mata mara.
Kusan kullum shi yake daba abinci saboda bata cin abincin kowa sai nasa, ko takeaway yayi musu sai dai ya cinƴe abunsa wai warinsa take ji, ko ita ta girka abincin bata cinsa sai dai Abdallah yayi mata, da wasa-wasa ya ƙware gurin girki saboda yau idan yayi mata wannan gobe wacan zai mata.
[8/7, 2:48 PM] Khadeeja Candy♥: Ranar Monday EDD ta ya cika amman bata haihu ba sai wata assabar a babban asibitin Abuja, murna gurin Abdallah kamar ya soye Namra da yaron da ta haifa ya cinye dan tsabar jindaɗi da farinciki, Allah ya nuna masa ya ga jikansa ta ɓangaren Abdallah.
Mai Martaba ma sai ya rasa inda zai sa ransa saboda farinciki, tun a waya yasa aka turo masa hoton jaririn ta whatsapp. Ƴan uwan Abdallah babu wanda be saka hoton a instagram ba, a can sokoto ma murna suke, family Abbah da kuma Mai Martaba da suke Abuja suka ne suka riƙa kula Namra, awarta guɗu a asibiti bayan ta haihu sai da suka sa ta yi bachi sannan suka sallameta.
Ko da ta dawo gida yamma yayi a dole ta haƙura ta bi jirgin gobe. Tare da family Abdallah suka sauka sokoto, su sukaje da kansu suka kai Namra har gida, iya gata an nunawa Namra ta ko wane ɓangare.
An zuba mata kayaɓ barka kamar ba gobe, kayan jariri sai ka ɗauka wani ƙaramin shago za a buɗe na siyar da kayan jarirai, ga shi ƴan uwa sai kawo mata ake ta ko'ina.
Ranar suna yaro ya ci sunan Mai Martaba, wato Ahmad, akayi masa laƙani da Sultan. An kashe naira ranar suna kamar ba a san zafin nemanta ba, duk faɗin gidan sai da ya cika da jama'a, musamman ma da yamma da ƴan'uwansu Abdallah suka zo da kuma na Ummi. An ci ana sha kuma an watse cikin farinciki da kwanciyar hankali, kowa sai yabon bikin yake ana Allah sam barka.
Duk bayan kwana biyu sai Abdool ya zo sokoto ganin ɗansa, kira kan waya kan waya ta safe daban ta rana daban ta dare ma haka. Kamin ta yi arba'in duk ya takura, kunyar Anty yasa ya kasa magana har sai da ta ƙara sati biyu sama sannan aka maida ta Abuja, tare da bayinta guda biyu sabida su taimaka mata hidimar gida.
Komai ya koma musu kamar su suka tsarawa kansu yadda rayuwar zata zo musu, suna bawa junansu kulawa yadda ya kamata, sai dai wani lokacin tana fuskantar matsala ta ɓangare Abdallah saboda zafin kishi da yake da shi. Lokuta da dama yakan hanata zuwa wani gurin ita kaɗai duk kuwa da kasancewar a garin Abuja ne amman ganin yake kamar wani zai mata magana idan ta fita ba tare da shi ba.
Yau ma duk da tana son fitar dole ta haƙura har sai da yawo, ya ci abincin yayi wanka sannan ya ɗauki Sultan ita kuma ta riƙa jakarta suka fita, shi yake driving Sultan na jikinsa rumgume ita kuma tana front seat har suka isa, wani babban Shopping.
Tana gaba yana biye haka suka shiga shopping ɗin. Yana riƙe da Sultan har ta siye abunda duk zata siya aka zo gurin biyan kuɗi ya bada atm ɗinsa aka cire adaɗin kuɗin da ta kashe, sannan suka koma cikin motar ya ɗauki hanyar gidansu Hajiya Umaima, wato Ƙanwar Mai Martaba wacce take nan Abuja.
Ta tarbesu da far'ah daman ta jima tana masa magana akan ya kawo mata Namra. Hannu ta kai ta karɓi Sultan da ke hannun Abdool tana faɗin
“Ai har na yi fushi na ce ba zan sake maka magana ba”
“Ko yanzu ai nice na matsa”
“No.wonder ni nasan sai ƴata”
“Haba Hajiya taya zaki biyeta ni nace ta shirya mu zo fa”
Hajiya Umaimai tayi dariya.
“Duk abunda zaka faɗa ba zan yarda ba. Mardiya kawo lemu kamin abinci ya ƙarasa”
Ta ƙarasa tana ƙwalawa mai aikinta kira, ba a ɗauki tsawon lokaci ba sai ga Mardiya ta fito daga kitchen ɗauke da drinks da cups. Gabanta ya faɗi lokacin da tayi arba da Namra, ita kanta Namra tayi mamakin ganinta sai dai daga ita ha4 Mardiyar babu wanda ya iya yima wani magana, har sai da ta wuce sannan Namra ta kalli Hajiya Umaima ta ce
“Hajiya ina kika san Mardiya?”
“Wallahi daga Katsina aka kawo ta, na ce a nemo min wace zata riƙa taya ni aiki ne sai aka kawo min ita, kin santa ne?”
“Eh a Katsina take shiyasa na yi mamaki ganinta nan”
“Aiki ta zo yau satinta biyu ma”
“Allah sarki”
Umaima ta miƙawa Namra Sultan.
“Bari na duba abincin nan, kar na shiga muku da yaro Kitchen”
Abdool yayi dariya
“Wai ina su Jamila ne?”
“Wlh duk sunje biki kasan halin ƙanen naka sai a hankali idan kunnensu ya ji biki, ba manyan ba ba yara ba”
Hajiya Umaima na shiga Kitchen sai Namra ta miƙe tsaye ta miƙawa Abdool Sultan ta nufi ɗakin da ta hango Mardiya ta shiga. Da sallama ta shiga, amman Mardiya bata iya amsa mata ba saboda bata son ta gano kuka, gyaran ɗakin ta tarar tana yi. Har Namra ta juya zata fita sai Mardiya ta juyo ta ce.
“Namra Asim ya mutu, Asim ya koma ga Ubangijinsa”
Namra ta juyo tana zaro ido.
“Yaushe? Miya same shi?”
“Rashin lafiyar da ta kama shi a faɗar Sarkin Katsina bata barsa ba sai da ta tafi da ransa”
“Innalillahi wa'inna ilaihi”
Ta faɗa tana dafe kanta hawaye na zubar mata. Mardiya ta risina ƙasa tana kuka.
“Namra ki taimaki Asim ki taimake ni ki yafe mana, amanarki da na ci ta hanani sukuni, duk wanɗanda na yi ma zalumcin na nemi yafiyarsu ke kaɗai kika rage min, na tsorata da irin mutuwar da Asim yayi, bana son na yi irin mutuwarsa”
Namra ta duƙo dai-dai Mardiya tana dafata.
“Miya samu Asim?”
Babu abunda ta ɓoye mata daga rayuwar Asim daga rashin lafiyarsa da kuma mutuwarsa zuwa irin rayuwar luwaɗin da tasan yana yi, ga kuma saduwar da yake yi da ita ta baya.
“Bayan mun gama wanka aka raba mana gadon kuɗin da ya bari na gida da filayen da ya siyar, a take nawa kuɗin suka ƙare gidan da na siya kuma ya ƙone, ga rashin lafiyar da take jikina saboda saduwar da yake yi da Ni ta baya, a duk lokacin da wannan ƙaiƙayin ya taso min sai na ji kamar zan mutu, na kasa daina mafarkin wuta Namra, ada ina tunanin ko wutar da na kunna miki ce gidanki ya ƙone, amman sai nake ganin kamar har da wutar lahira ce take jirana, ki taimake ni ki yafe min Namra, na ci amanarki, na han'ince ki, na cutarda ke”
Wani kuka take marar murya saboda bata son Hajiya Umaima ta ji.
“Na yafe miki Mardiya shi ma Asim na yafe masa, Allah ya masa rahama”
Ta miƙe tsaye tana hawaye.
“Ki rufa min asiri karki faɗawa kowa sirrin, yana ɗaya daga cikin dalilin da ya sa na bar Katsina na dawo nan ga aiki saboda na canjawa kai na rayuwa, kuma na rufawa kai na asiri da abunda zan ci, na taimaki uwata da ƙannena”
“Babu wanda zai ji, na miki alƙawari ba zan taɓa faɗawa kowa ba”
Sai da ta share hawayen sannan ta fice. Sai dai hakan be hana Abdool gane ta yi kuka ba. Tana zaunawa kusa da shi ya kalleta ya ce
“Kin yi kuka saboda kinji Asim ya rasu ko?”
Da sauri ta kalleshi.
“Ka sani kenan?”
“Abnam har gobe kina son Asim”
“No ba haka ba ne, kawai ina tausayinsa ne”
“Tausayi ne silar so”
“Ba irin wacan tausayin ba”
Ya miƙe tsaye tare da ɗansa, ya ɗauki car keys ɗinsa ya fice. Tana zaune a gurin ta ji tashin motarsa. Lumshe ido ta yi ta buɗe sannan ta ɗago tana amsa maganar da Hajiya Umaima ke mata.
“Lafiya Babangida ya tafi?”
“Wai zai ga wani abokinsa ne, yace idan an ɗan jima kisa direba ya kai ni”
“Okay toh taso muje ɗaki ga abincin nan Mardiya zata kawo yau mun ranar girki”
“Wallahi Hajiya na ci abinci”
“Ai nasan kin ci abincin, karki so ma min musu ba tarbiya ba ce”
Da murmushi Namra ta tashi ta bita suka shiga ɗaki. Kamin ta gama cin abinci ayi sallah la'asar har ta tsawwala saboda tunanin Abdool yana can gida cikin ɓacin rai. Tana gama sallah la'asar ta yi ma Hajiya Umaima magana tasa ka direba ya kai ta gida. Bata same shi a falo ba, hakan tasa ta nufi ɗakinsa, kwance ta hango shi saman gado, Sultan na saman ƙirjinsa idonsa a lumshe kamar mai bachi.
Tasan ba bachi yake ba, domin be saba bachin yamma ba, sai dai wannan baya rasa nasaba da ɓacin ran da take tunanin ya sawa kansa akan abunda har ga Allah ba haka yake ba. Be buɗe ido ba har ta ƙarasa kusa da shi ta zauna saman gado.
“Ya Omri...”
“Abnam please, bana son na fara ganin laifinki, bana son zuciyata na ƙonuwa akan ki ina gudun na fara ganin baƙinki, dan Allah ki fita sai zuwa anjima”