Sashe 84
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“To ai shi ya nuna ita ɗin ce, kuma kasan fa ita ta fitar da Rashida a gidan yanzu kuma tana son ganin bayan ƴaƴanta, gaskiya abun be yi daɗi ba, ai ota Rashida tace ba zata ƙyale ba, dan Asma'u ta ce har ta aika mata sammaci ko? Amman dai ban jidaɗi ba gaskiya”
Hilal ya jingina da kujerarsa yana lilo.
“Ni ne na saki Rashida da kaina san ganin damana, maganar kotu kuma taje duk inda zata je ta kai Kalsoom i will surely depend her”
Alh. Bashir ya masa kallon mamaki.
“Doc kasan abinda kake faɗa kuwa? Ɗan ka ne fa ɗan ka ta nemi kashewa”
“Kana da hujjar ita ɗin ce ta kashe shi? Amanarta na karɓo a gurin iyayenta yanzu haka tana ƙarƙashin kulawa ta ne, dole na yi abunda zan kare ta”
“Kana nufin za ka ci gaba da zama da ita kenan?”
“What do you expect?”
Ya ɗaga kafaɗunsa.
“Nothing, ya mai jiki”
“Da sauƙi bachi ya ke”
“Okay Allah ya ƙara lafiya, ni zam koma da safe zan zo na duba shi”
Hilal ya miƙa masa hannu suka sake gaisawa.
“Na gode sosai”
Wani kallon Alh Bashir yayi masa, yana mamakin yadda Hilal ya sauya masa kamar ba shi, duk irin tare da suke a can baya yana aure Kalsoom duk ya watsar ta ɗauke masa hankali. Lallai yanzu ya yarda da maganar da ake cewa magani tayi masa, tun da har Hilal ya furta zai tsaya mata, bayan kuma ɗansa ne tayi ma wannan karen aiki.
Bayan Alh Bashir ya wuce Hilal ya koma saman kujear ya zauna, yana tunanin maganar sammacin da Alh Bashir yace Rashida ta aika Kalsoom. Duk waɗancan maganganun yayi ne kawai dan ya nuna kamar ya san abinda yake faruwa bayan kuma besan komai, yayi hakan ne dan bayan son ayi Alh Bashir yai insulting ɗin matarsa. Saboda ya tsani haka.
Ajiyar zuciya ya sauke yana tunanin yadda zai ɓullowa lamarin. Sai kuma ya kai hannu ya ɗauki hoton ya buɗe yana dubawa. Abinda ya gani ya tayar masa da hankali, da sauri ya tashi yana ƙara dubawa dan tantance abinda yake ganin ɗin. Da sauri ya bar Office ɗin ya nufi inda zai laƙa hotunan su fito a majigi...
*RASHIDA POV.*
Tana sauke wayar ta ƙara ɓata fuska, zuciyarta ta sosu matuƙa, akan abinda Alh. Bashir ya gama faɗa mata, na cewar Hilal zai tsaya ma Kalsoom, a tunaninta shi da kansa zai saka ta kotu yadda tasan yana jin da ƴaƴansa.
Hawaye suka zubo mata sai tasa hannu ta share. Hankalin ƴan'uwa sai duk ya dawo kanta, daman tun ɗazu maganar da suke kenan har da wata ƙawarta wacce suka yi makaranta a tare.
“Ke mai ya faru?”
Khady ta tambaya tana dafa ta.
“Wani abokinsa ne ya kira ni yanzu yana faɗa min wai Hilal yace zai tsayawa Kalsoom”
Ummu Faisak ta daki ƙirji.
“Da gaske? Lallai wannan Kalsoom ɗin ta wanke ta bashi ya sanyen, kan uban nan ayi ma ɗanka abu amman kasa yin komai har kace zaka tsaya mata”
Dukansu jinjina lamarin suke. Zainab ta kada baki tace
“Wannan abun har ƴan Human Rights sai mun saka, ai idan ya san wata be san wata ba, ƙaramin yaro zaka bari a wulaƙanta yama baki ɗan kawai tun da bayan son zuri'arki”
Ummu ta jinjina kai.
“Hmmm Ai wallahi sai na masa rashin mutucin, dan har a tv sai na nuna su, ai daga ganin wannan abin kinsan Hilal ba cikin hankalinsa yake ba. Kuma wallahi tallahi matuƙar ina numfashi sai Kalsoom.ta bar gidan nan, ba ko mallaka ne aikinta wallahi ko a gabanta bokanci ya yake saƙa sai na nuna mata shayi ruwa ne, ai ko baba da babansa”
Rashida tayi saurin rufe mata baki 5ana kuka.
“Dan Allah ki ƙyaleta, ni dai bana iya, ita ta sani can ita da Allah”
“Ai ban ci ki iya ba bada kuɗin ki zan yi ba, amman wallahi tun da ta taɓa ki sai na taɓa ta”
Wani yatsine yake tana tsine ɗankwali irin ita ga ga tantsiriya ɗin nan. Maimunatu ta girgiza kai
“Daman kin yi sake tun farko Rashida Namiji kamar Hilal kinsan duk wace ta shiga gidansa kan ba fita, ni da nice ke Wallahi da wannan abokin nasa zan aura, in yaso ya mutu....”
Ta murguɗa baki. Fashewa Rashida tayi tda kuka tana narke musu kamar wata ta ƙwarai, su kuma sai tausayinsa suke suna bata haƙuri....
INA JINDAƊIN COMMENTS NA KU. THANKS........🙏
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *56*
Idonsa ya cika da hawaye, jikinsa ya mutu sosai har yana ƙoƙarin zamewa ya faɗi kamar ba Namiji ba.
Hannunya kai ya taɓa hancinsa ya lumshe, tana girgiza kai. Abinda yake bashi mamakin results a yanzu ya nuna ba guba bace gas ya nuna kuma har yayi effecting ɗin ƙwaƙwalwar Rafiq, that's mean zai zama wani iri kenan. Wanda abu ne mai wahala ya koma dai-dai, ko da kuwa an ɗora shi akan ganine.
Ya daɗe idonsa a lumshe, _Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un_ Shine abinda yake ta maimatawa a zuciyarsa. Daker ya buɗe idon ya ƙarasa ya ciro hoton ya bar ɗakin yana mai jin kansa kamar marar lafiya.
Be shiga office ɗinsa ba sai kawai ya nufi ɗakin da Rafiq yake kansa na mugun sarawa. Tsaye yai a bakin ƙofa yana kallon Rafiq cike da tausayin Rafiq, ya daɗe jikin ƙofar kamar mai tsoron ƙarasawa. Juyawa yayi ya koma office ɗinsa, ya zauna kaman kujera ya dafe kansa still takardun na riƙe a hannunsa. Babu abunda ya faɗo masa a rai sai ya sake ɗaukar wani hoton ya gani, wata ƙila wannan ƙarya ya nuna masa...
Ɗaga kai yayi ya sake kallon hotunan, yana sauke ajiyar zuciya. Ya ɗauki mintuna talatin yana kallon hotunan sannan ya buɗe wani gurin ya saka su ya ɗauki abubuwan daya shigo dasu office ɗin ya fito, da kansa ya kulle office ɗin sannan ya nufi ɗakin da Rafiq yake. Har lokacin bachi yake abunsa, be farka ba.
Wani ɗan ƙaramin tebur Hilal ya nufa ya ɗora kayan a kai sannan ya ƙarasa gurin da Rafiq yake yaja kujera ya zauna, ya riƙe hannunsa yana hafawa, wani irin tausayin Rafiq ne ya ke shiga zuciyarsa.
Haka ya zauna ya tsare Rafiq da ido yana jin kamar yayi masa kuka, ko da kuskure bachi be doshi idonsa ba.lokaci lokaci yake sauke ajiyar zuciya kana ya haɗe yawu. Rafiq be farka ba sai kusan uku da rabi na dare. Murje-murje ya fara yana kiran ruwa kamin ya buɗe ido. Da sauri Hilal ya tashi ya buɗe jakar da ya shigo da ita ya haɗa masa tea ya ta sheshi zaune ya soma bashi tea ɗin, yana masa sannu kamar wani babba.
Yana gama shan tea ɗin ya langwaɓarda kansa jikin Hilal bakinsa yai gefe kamar zai talalarda yawu.
“Rafiq”
Hilal ya faɗa yana girgiza sa dan zuciyarsa ta katse gaba ɗaya. Ɗagowa Rafiq yayi kaɗan ya kalli Daddynsa sai ya maida kai gurin ƙofa yana kallo kamar mai jiran shigowar wani.
Can kuma ya ɗaga kai yana kallon ɗakin, kamin ya sake kallon Daddynsa.
Rumgumesa Hilal yayi yana hawaye. Daga bisani ya ɗauko wasu magunguna ya bashi, sannan ya maida shi a ƙirjinsa ya kwantar. Haka suka kwana, Rafiq na kwance a ƙirjinsa, Hilal kuma be rumtsa ba, a kan idonsa aka kira salla asuba. A hankali ya kwantar da Rafiq yai alwala a toilet ɗin ɗakin ya nufi masallacin asibitin.
Ya daɗe yana addu'a bayan yai salla, a nan masallacin ma sai da ya gaisa da wasu da suka sanshi har suna masa ya jikinsa ɗansa.
Sai da ya koma ɗakin ya ganshi sannan ya fito harabar Asibitin yana amsa wayar Hajiya dake tambayarsa ya jikinsa. Be faɗa mata a results ɗin da hoton ya bada ba, dan ba labari bane mai daɗin ji.
Ko da ya isa gida 6:30am, dan garin be ƙarasa wayewa ba a lokacin. A mota ya zauna har 30 ɗin ta ƙarasa sannan ya buɗe ya shigo nufi ƙofar shiga gidan. A kulle ya jita hakan yasa ya kai hannu ya ƙwanƙwasa, sai ya kawar da fuskarsa. Bayan kamar minti biyu zuwa uku Kalsoom ta buɗe ƙofar.
“Sannu da zuwa”
Ta faɗa cikin sanyayayyiyar murya. Be amsa ba be kuma kalleta ba sai kawai ya raɓa gefenta ta shiga cikin falon.
Kai tsaye ɗakin su Ulfah ya nufa, shiri ya tarar suna yi na makarantar boko.Dukansu ya shafa kansu yana masa good morning ɗin da suke masa, sannan yaja su jikinsa ya rumgume.
“Gobe za ku koma gurin Hajiya da zama, a can za ku zauna har na gama gyara wannan gidan”
Ezzah ta daka tsalle, tana murna, Ulfah ma Murna ta yi, dan suna son zuwan gidan Hajiya ko dan su yi wasa da ruwaz ga gidan akwai yara da yawa sa'aninsu.
“Daddy har da Anty?”
Ulfah ta tambaya cikin zumuɗi. Shiru Hilal yayi kamin ya amsa mata.
“A'a Anty a nan zata zauna”
Bata wani damu ba dan tana son gidan Hajiya, sai dai ta san zatayi missing Anty kan sosai, a ranta take auna a weekend zata zo ta ganta.Bayan kamar minti biyar ya miƙe tsaye ya nufi ɗakinsa. Yana tura ƙofar ɗakin yana Kalsoom zaune saman gadonsa tana hawaye.
Be kulata ba ya nufi wardrobe ya buɗe yana cire wasu tufafin. Da kallo ta bishi har ya gama cire kayan sannan ta soma magana cikin muryar tausayi.
“Baka buƙatar canjawa yaran ka gida Hilal, ni kake buƙatar canjaw! Ni kaina ban cancanci zama da ƴaƴan da mahaifinsu be yarda da ni ba, ko kaɗan ɓan ga laifin ka ba akan abinda ka aikata, ko ni kwatankwacin haka zan aikata”
Sauka tayi daga saman gadon ta durƙusa ƙasa ta haɗe hannayenta alamar roƙo.
“Ma gafarta min akan abunda na yi maka Hilal, ba zan sake hararar yaran ka ba balle na cutar da su”
Juyowa yai ya kalleta.
“Kin Aikata kenan?”
Kai ta ɗaga alamar eh.
Hilal ya jingina da kujerarsa yana lilo.
“Ni ne na saki Rashida da kaina san ganin damana, maganar kotu kuma taje duk inda zata je ta kai Kalsoom i will surely depend her”
Alh. Bashir ya masa kallon mamaki.
“Doc kasan abinda kake faɗa kuwa? Ɗan ka ne fa ɗan ka ta nemi kashewa”
“Kana da hujjar ita ɗin ce ta kashe shi? Amanarta na karɓo a gurin iyayenta yanzu haka tana ƙarƙashin kulawa ta ne, dole na yi abunda zan kare ta”
“Kana nufin za ka ci gaba da zama da ita kenan?”
“What do you expect?”
Ya ɗaga kafaɗunsa.
“Nothing, ya mai jiki”
“Da sauƙi bachi ya ke”
“Okay Allah ya ƙara lafiya, ni zam koma da safe zan zo na duba shi”
Hilal ya miƙa masa hannu suka sake gaisawa.
“Na gode sosai”
Wani kallon Alh Bashir yayi masa, yana mamakin yadda Hilal ya sauya masa kamar ba shi, duk irin tare da suke a can baya yana aure Kalsoom duk ya watsar ta ɗauke masa hankali. Lallai yanzu ya yarda da maganar da ake cewa magani tayi masa, tun da har Hilal ya furta zai tsaya mata, bayan kuma ɗansa ne tayi ma wannan karen aiki.
Bayan Alh Bashir ya wuce Hilal ya koma saman kujear ya zauna, yana tunanin maganar sammacin da Alh Bashir yace Rashida ta aika Kalsoom. Duk waɗancan maganganun yayi ne kawai dan ya nuna kamar ya san abinda yake faruwa bayan kuma besan komai, yayi hakan ne dan bayan son ayi Alh Bashir yai insulting ɗin matarsa. Saboda ya tsani haka.
Ajiyar zuciya ya sauke yana tunanin yadda zai ɓullowa lamarin. Sai kuma ya kai hannu ya ɗauki hoton ya buɗe yana dubawa. Abinda ya gani ya tayar masa da hankali, da sauri ya tashi yana ƙara dubawa dan tantance abinda yake ganin ɗin. Da sauri ya bar Office ɗin ya nufi inda zai laƙa hotunan su fito a majigi...
*RASHIDA POV.*
Tana sauke wayar ta ƙara ɓata fuska, zuciyarta ta sosu matuƙa, akan abinda Alh. Bashir ya gama faɗa mata, na cewar Hilal zai tsaya ma Kalsoom, a tunaninta shi da kansa zai saka ta kotu yadda tasan yana jin da ƴaƴansa.
Hawaye suka zubo mata sai tasa hannu ta share. Hankalin ƴan'uwa sai duk ya dawo kanta, daman tun ɗazu maganar da suke kenan har da wata ƙawarta wacce suka yi makaranta a tare.
“Ke mai ya faru?”
Khady ta tambaya tana dafa ta.
“Wani abokinsa ne ya kira ni yanzu yana faɗa min wai Hilal yace zai tsayawa Kalsoom”
Ummu Faisak ta daki ƙirji.
“Da gaske? Lallai wannan Kalsoom ɗin ta wanke ta bashi ya sanyen, kan uban nan ayi ma ɗanka abu amman kasa yin komai har kace zaka tsaya mata”
Dukansu jinjina lamarin suke. Zainab ta kada baki tace
“Wannan abun har ƴan Human Rights sai mun saka, ai idan ya san wata be san wata ba, ƙaramin yaro zaka bari a wulaƙanta yama baki ɗan kawai tun da bayan son zuri'arki”
Ummu ta jinjina kai.
“Hmmm Ai wallahi sai na masa rashin mutucin, dan har a tv sai na nuna su, ai daga ganin wannan abin kinsan Hilal ba cikin hankalinsa yake ba. Kuma wallahi tallahi matuƙar ina numfashi sai Kalsoom.ta bar gidan nan, ba ko mallaka ne aikinta wallahi ko a gabanta bokanci ya yake saƙa sai na nuna mata shayi ruwa ne, ai ko baba da babansa”
Rashida tayi saurin rufe mata baki 5ana kuka.
“Dan Allah ki ƙyaleta, ni dai bana iya, ita ta sani can ita da Allah”
“Ai ban ci ki iya ba bada kuɗin ki zan yi ba, amman wallahi tun da ta taɓa ki sai na taɓa ta”
Wani yatsine yake tana tsine ɗankwali irin ita ga ga tantsiriya ɗin nan. Maimunatu ta girgiza kai
“Daman kin yi sake tun farko Rashida Namiji kamar Hilal kinsan duk wace ta shiga gidansa kan ba fita, ni da nice ke Wallahi da wannan abokin nasa zan aura, in yaso ya mutu....”
Ta murguɗa baki. Fashewa Rashida tayi tda kuka tana narke musu kamar wata ta ƙwarai, su kuma sai tausayinsa suke suna bata haƙuri....
INA JINDAƊIN COMMENTS NA KU. THANKS........🙏
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *56*
Idonsa ya cika da hawaye, jikinsa ya mutu sosai har yana ƙoƙarin zamewa ya faɗi kamar ba Namiji ba.
Hannunya kai ya taɓa hancinsa ya lumshe, tana girgiza kai. Abinda yake bashi mamakin results a yanzu ya nuna ba guba bace gas ya nuna kuma har yayi effecting ɗin ƙwaƙwalwar Rafiq, that's mean zai zama wani iri kenan. Wanda abu ne mai wahala ya koma dai-dai, ko da kuwa an ɗora shi akan ganine.
Ya daɗe idonsa a lumshe, _Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un_ Shine abinda yake ta maimatawa a zuciyarsa. Daker ya buɗe idon ya ƙarasa ya ciro hoton ya bar ɗakin yana mai jin kansa kamar marar lafiya.
Be shiga office ɗinsa ba sai kawai ya nufi ɗakin da Rafiq yake kansa na mugun sarawa. Tsaye yai a bakin ƙofa yana kallon Rafiq cike da tausayin Rafiq, ya daɗe jikin ƙofar kamar mai tsoron ƙarasawa. Juyawa yayi ya koma office ɗinsa, ya zauna kaman kujera ya dafe kansa still takardun na riƙe a hannunsa. Babu abunda ya faɗo masa a rai sai ya sake ɗaukar wani hoton ya gani, wata ƙila wannan ƙarya ya nuna masa...
Ɗaga kai yayi ya sake kallon hotunan, yana sauke ajiyar zuciya. Ya ɗauki mintuna talatin yana kallon hotunan sannan ya buɗe wani gurin ya saka su ya ɗauki abubuwan daya shigo dasu office ɗin ya fito, da kansa ya kulle office ɗin sannan ya nufi ɗakin da Rafiq yake. Har lokacin bachi yake abunsa, be farka ba.
Wani ɗan ƙaramin tebur Hilal ya nufa ya ɗora kayan a kai sannan ya ƙarasa gurin da Rafiq yake yaja kujera ya zauna, ya riƙe hannunsa yana hafawa, wani irin tausayin Rafiq ne ya ke shiga zuciyarsa.
Haka ya zauna ya tsare Rafiq da ido yana jin kamar yayi masa kuka, ko da kuskure bachi be doshi idonsa ba.lokaci lokaci yake sauke ajiyar zuciya kana ya haɗe yawu. Rafiq be farka ba sai kusan uku da rabi na dare. Murje-murje ya fara yana kiran ruwa kamin ya buɗe ido. Da sauri Hilal ya tashi ya buɗe jakar da ya shigo da ita ya haɗa masa tea ya ta sheshi zaune ya soma bashi tea ɗin, yana masa sannu kamar wani babba.
Yana gama shan tea ɗin ya langwaɓarda kansa jikin Hilal bakinsa yai gefe kamar zai talalarda yawu.
“Rafiq”
Hilal ya faɗa yana girgiza sa dan zuciyarsa ta katse gaba ɗaya. Ɗagowa Rafiq yayi kaɗan ya kalli Daddynsa sai ya maida kai gurin ƙofa yana kallo kamar mai jiran shigowar wani.
Can kuma ya ɗaga kai yana kallon ɗakin, kamin ya sake kallon Daddynsa.
Rumgumesa Hilal yayi yana hawaye. Daga bisani ya ɗauko wasu magunguna ya bashi, sannan ya maida shi a ƙirjinsa ya kwantar. Haka suka kwana, Rafiq na kwance a ƙirjinsa, Hilal kuma be rumtsa ba, a kan idonsa aka kira salla asuba. A hankali ya kwantar da Rafiq yai alwala a toilet ɗin ɗakin ya nufi masallacin asibitin.
Ya daɗe yana addu'a bayan yai salla, a nan masallacin ma sai da ya gaisa da wasu da suka sanshi har suna masa ya jikinsa ɗansa.
Sai da ya koma ɗakin ya ganshi sannan ya fito harabar Asibitin yana amsa wayar Hajiya dake tambayarsa ya jikinsa. Be faɗa mata a results ɗin da hoton ya bada ba, dan ba labari bane mai daɗin ji.
Ko da ya isa gida 6:30am, dan garin be ƙarasa wayewa ba a lokacin. A mota ya zauna har 30 ɗin ta ƙarasa sannan ya buɗe ya shigo nufi ƙofar shiga gidan. A kulle ya jita hakan yasa ya kai hannu ya ƙwanƙwasa, sai ya kawar da fuskarsa. Bayan kamar minti biyu zuwa uku Kalsoom ta buɗe ƙofar.
“Sannu da zuwa”
Ta faɗa cikin sanyayayyiyar murya. Be amsa ba be kuma kalleta ba sai kawai ya raɓa gefenta ta shiga cikin falon.
Kai tsaye ɗakin su Ulfah ya nufa, shiri ya tarar suna yi na makarantar boko.Dukansu ya shafa kansu yana masa good morning ɗin da suke masa, sannan yaja su jikinsa ya rumgume.
“Gobe za ku koma gurin Hajiya da zama, a can za ku zauna har na gama gyara wannan gidan”
Ezzah ta daka tsalle, tana murna, Ulfah ma Murna ta yi, dan suna son zuwan gidan Hajiya ko dan su yi wasa da ruwaz ga gidan akwai yara da yawa sa'aninsu.
“Daddy har da Anty?”
Ulfah ta tambaya cikin zumuɗi. Shiru Hilal yayi kamin ya amsa mata.
“A'a Anty a nan zata zauna”
Bata wani damu ba dan tana son gidan Hajiya, sai dai ta san zatayi missing Anty kan sosai, a ranta take auna a weekend zata zo ta ganta.Bayan kamar minti biyar ya miƙe tsaye ya nufi ɗakinsa. Yana tura ƙofar ɗakin yana Kalsoom zaune saman gadonsa tana hawaye.
Be kulata ba ya nufi wardrobe ya buɗe yana cire wasu tufafin. Da kallo ta bishi har ya gama cire kayan sannan ta soma magana cikin muryar tausayi.
“Baka buƙatar canjawa yaran ka gida Hilal, ni kake buƙatar canjaw! Ni kaina ban cancanci zama da ƴaƴan da mahaifinsu be yarda da ni ba, ko kaɗan ɓan ga laifin ka ba akan abinda ka aikata, ko ni kwatankwacin haka zan aikata”
Sauka tayi daga saman gadon ta durƙusa ƙasa ta haɗe hannayenta alamar roƙo.
“Ma gafarta min akan abunda na yi maka Hilal, ba zan sake hararar yaran ka ba balle na cutar da su”
Juyowa yai ya kalleta.
“Kin Aikata kenan?”
Kai ta ɗaga alamar eh.