Sashe 141
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da gudu mai aikinsu ta so kansa tana tambayar ba'asi. Ganin abun ba na banza ba ne ƴasa ta fita neman mai gadi ko zai iya taimakawa. Ko da Mai gadin ya shigo Uzair wani abu yake kamar mai ɗaukar rai. Da sauri Mai gadi ya kira Yasmin ya faɗa mata abinda yake gudana.
YASMIN POV.
“Zan turo maka number ka kira mahaifiyarsa ka faɗa mata”
Amsar da Yasmin ta mayar masa kenan ta katse kiran, ta aika masa number sannan ta cigaba da kuka tana zanawa mahaifiyarta abubuwan da Uzair yake mata wanda hakan kawai ya isa ya tabbatar da gaskiyar abunda ya yi ma ɗanta, bayan ta fito gidansu Namra ta nufo gidansu dan ta na jin bata buƙatar komawa gidan a yanzu.
“Ko ma minene shiru ya kamata ki yi ki rufawa mijinki asiri”
“Irin wannan rufa Asirin ne yasa mata da yawa maza suke cutar da su, idan aka muku fyaɗe ko aka yi ma ƴaƴansu, wannan abun yana cutar da mata da yawa, mu muke faɗar a daina ɓoye abu a riƙa fitowa a ana faɗa yau kuma sai a same ni da wannan aikin na ɓoyewa? Ɓoyewar nan da ake shi kw basu damar ƙara aikata abunda suke aikatawa, at least ko da ba a hukunta su ba, duniya zata kunyata su kuma asan ko su waye, ban ga dalilin rufawa Uzair asiri ba ko da kuwa ubana ne balle mijina, ina yawan faɗar cewa ni dai i would never in my life encourage anyone to live with an adulterer tun da har Allah ya ce a jifasu su mutu, they are as good as useless to be seen alive in this world, sai kuma na zama ni ce zan rufa masa asiri miye amfanin aikina?”
“Nidan indai zaki ɗauki shawarata ban ga abun burgewa ga mace ta kai mijinta kotu ba da sunan wai yayi ma ɗansa fyaɗe, kina da hujja ne?”
“Ko bana da ita dole zan samo ta”
“Ni kam ba da yawun baki na ba Yasmin wannan sam be dace ba, idan ma zama ne ba zaki iya da shi ba, sai ki nemi ya rabu da ke kawai ki hutu”
Ajiyar zuciya ta sauke mai nauyi.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
AMIRA POV.
“ji na yi gidan nan ya isheni ina ta jin kamar idan ban gudu ba wani abun zai iya faruwa da ni. Ban tsaya ɗaukar komai ba sai kuɗi, tun daga lokacin da na bar gidan nan nahau mota na kama hanya ban sake sanin inda nake ba, ban san inda direba ya sauke ni ba ban san ya nayi rayuwa ba, sai a ƴan kwanakin nan da wannan sojan ya tsince ni a bolar gidansu, shine yayi ta min addu'ah da komai har hankalina ya dawo, na faɗa masa inda nake ya saka direba ya kawo ni gida”
Duk kai suka girgiza cike da tausaya musamman Ammy da ke kuka kamar yadda Amira ta ke yi.
“Amman Namra ta ci amanar abota, ai gashi nan ta fara ganin abunta, ɗazu-ɗazu hajiya Haulat ta ƙira ta faɗa min ita ta dawo gida aure ya mutu, kuma ance can gidan auren ta ci kwakwarta”
Salman Big bro nasu ya kalli Ammy dake wannan maganar yana faɗin
“Ai ba laifinta ba ne, ita Amira ai cin amanar ta tashi yi, da yanzu da gaske ne idan an sakawa Namra wannan abun maganin zai kamata ai kim ga ita ta ci amana kenan, waya sani ma ko koma miki ne yayi, a haɗa baki da ke a sace ta har a ayi mata ƙazafi, wallahi kun ci amanar juna ke da ita”
Abban Amira ya ɗaga masa hannu cikin ɓacin rai.
“Idan kasan bakin ka ba alheri zai faɗa ba, ka tashi kawai ka bar falon nan. Allah zai saka miki Amira zura mata ido kawai daga ita har ɗan'uwan na ta”
“Wane irin a sa muku ido? Aja mata haƙƙinta dai, babu irin abunda ba'ayi ba amman yarinyar nan ita da mahaifiyarta suka tsaya kai da fata akan babu hannunsu a ɓatan Amira, aka kiɗa aka raya aka daka yarinyar ta ƙeƙashe ƙasa tace bata san gaibu ba akan ɓatan Amira sai yanzu kuma gaskiya ta bayyana za'ace a ƙyaleta”
Taɓe baki Salim yayi ya miƙe tsaye ya fice daga falon.
“Babu wani haƙƙi da za a ja mata ku zuba musu ido kawai, ko bayan rage kika zagaya kika ɗauki wani hukunci sai na ɓata miki rai Wallahi, tun da na ce a bar maganar nan barinta shine ya fi kawai”
Ya miƙe tsaye ya fice daga falon. Kuka sosai Amira take, sai dai ba kuka dawowa gida ba, kukan rabuwa da Abdool tana jin kamar zata mutu idan ta tuna baya kusa da ita a yanzu.
ABDOOL POV.
Ya ware hannayensa.
“You see Ummi na faɗa miki Mai Martaba bashi da matsala, na zauna na fahimtar da shi kuma ya fahimta”
“Hakan na da kyau ai, sauran yarinyar ko?”
“Wannan ba matsala ba ne, zan ji da shi, so na ke sai an kwana biyu sai naje na ganta ko?”
Ummi tasa dariya, the way da yake mata maganar kamar wani ƙaramin yaro.
“Allah ya baka sa'ah”
“Amin my happiness. This week zan koma aiki, hutun mu ya ƙare”
“Ai daman ai baka yi hutu ba, ina fatar da kana da number wayarta”
“Wallahi bana da ita saboda yarinyar akwai jan aji amman zan sa a nema min. Am ɗazu mun yi waya da mahaifiyar Amira ta isa gida lafiya ƙalau”
“Mashallah, yau za su kwana cikin farinciki, ita kanta zata fi sakewa”
Kafaɗunsa ya ɗaga irin ina ruwana ɗin nan. Ummi ta watsa masa harara.
“Bari yarinyar nan ta ƙi amincewa da kai, ta yi ta baka wahala”
Ya sa dariya.
“Haba Ummi karki min baki mana”
Ya miƙe tsaye ya fice yana dariya.
ASIM POV.
Da rana ya sauka sokoto, kai tsaye gidansu ya nufa, duk da be so sake dawowa garin ba tare da an canja musu gida ba, sai dai matsalar har yanzu ba a samu gidan da suke so ba. Mama ta yi mamakin ganinsa sosai tun da be kirata ya faɗa mata zai zo ba balle ta tanadar masa da wani abu.
“Wannan zuwa haka ba waya ga shi komai ba a tanadar maka ba”
“Ba komai nima zuwan ya kamani ne kawai”
“To Allah yasa dai lafiya”
“Lafiya ƙalau, na ji ance Namra tana garin nan ne, shiyasa na zo dan zan maida aurena ne”
Mama ta daki ƙirji.
“Auren ka Asim? Kai kam mi ya kai ka daga Allah ya raba da ƙaddara”
“Kin san tana da ciki fa na sake ta, ni gaskiya yanzu so na ke na maidata”
“Amman Asim kana ganin zaka iya tunkarar gidansu yanzu ka ce zaka maida aurenta, mahaifinta ai sai ya yanka namanka da wannan fitinanniyar ƙanwarta”
“Koma minene dai sai naje gidan, ai yanzu be isa ya wulaƙanta ni ba, dan na fi ƙarfinsa Wallahi”
Tattaunawa suka soma yi kan maganar aurensa da Mardiya da irin abubuwan da ya shirya, sannan ya bijiro mata da maganar samun gidan, a nan take labarta masa am samu wani a Abdullahi Fodio Road amman wai har miliyan uku, ita gani take kamar yayi tsada, waɗannan da ake samu kusa kuma duk bata son unguwar.
“Ƙar hakan ya dame ki, indai gida yayi miki za a biya kuɗi a saka komai sabo sai ku koma”
“Yanzu kana da har miliyan uku na gidanmu?”
“Akwai su, zinari fa na ke siyarwa, kin san kuɗin da mike samu kuwa?”
“Allah ya ƙara arziki ai haka nake so, sai ka samu kawon ka Na Malam ku yi magana shi ya san inda gidan ya ke”
Haka suka wuni suna fira sallah ce kawai ke tashinsa, sai da akayi magariba sannan ya shiga yayi wanka ya shirya cikin ƙananan tufafi ya saka turare ya shigo ɗakinta.
“Mama ni zanje wani guri da abokina sai gobe zamu dawo”
“To Allah ya tsare hanya”
Ya sa kai ya fice sai ƙamshin turare yake. Be daɗe da fita ba aka aiko ana yi ma Hajara sallama.
“Je kace tana nan zuwa”
Sai Hajara ta tashi ta ɗauki kayan kwaliyarta ta gyara fuskarta sannan ta saka Hijabinta ta fice. Bayan fitarta Mama ta ɗauki tabarma ta shinfiɗa a waje ta zauna tana sauraren Garkuwa Fm.
Tana haka sai ga Hajara ta dawo, ta doso inda take.
“Mama Yaya Asim ya bar makulli a ɗauko wayarsa a mota ya barta sai kiransa ake, kuma Mahmud (Saurayin da ya zo gurinta) Idan wasu suka ga wayar zasu iya fasa gilashin motar su ɗauka”
“Amman ya fita da wayarsa, sai dai idan ba ɗaya ba ce, lalaba aljihun wandon da ya cire ɗazu ko daki samu makullin ni dai be ba ni ba”
Ta faɗa tana tsakalen haƙori, da karen darbejiya bushesshe. Hajara ta nufi ɗakin Mama inda ya sarkafa wandonsa ta soma lalabawa ta ji kuɗi mai mugun yawa kamin ta yi arba da makulin.
“Ga makullin nan bari na ɗauko, amman Mama kin ji Aljihun yaya kuɗi cike”
“Ke da gaske?”
Mama ta yi sauri ta tashi ta nufi ɗakin. Hannu tasa cikin aljihunsa ta ciro rabonta saka inda take ajiyar kuɗi, sannan ta koma waje gurin tabarmarta zauna. Sai ga Hajara ta shigo da wayoyi biyu da makullin sannan kuma da Apple hannunta.
“Aje masa, wannan karki canye ki rage min”
Ta miƙa mata wayoyin da Apple ta juya, hankalinta yana gurin Mahmud kar ya ce ta bar shi.
“Ina kika samo tuffah”
“A motar Yaya”
Mama ta yi murmushin jidaɗi.
“Oh Yaro yayi kuɗi har tuffa ake ci a mota yanzu haka ya manta da ita da wayoyin nasa da ya bari, ko da yake abun ba ɗaya ba naga fa ya fita da wasu”
Ta faɗa tana gantsara apple ɗin, babu ko bismilah balle kuma ta damu da wankewa. Haka ta kama shi ta wanke tass tana cewa idan Hajara ta zo ta bata kuɗi ta siya wani wani tun da akwai shi a titi, har ta ƙaro mata ma dan wannan ma ta jidaɗinsa. Sau biyu ana kiran wayar Asim sai ta ɗauka ta ce baya kusa.
YASMIN POV.
“Zan turo maka number ka kira mahaifiyarsa ka faɗa mata”
Amsar da Yasmin ta mayar masa kenan ta katse kiran, ta aika masa number sannan ta cigaba da kuka tana zanawa mahaifiyarta abubuwan da Uzair yake mata wanda hakan kawai ya isa ya tabbatar da gaskiyar abunda ya yi ma ɗanta, bayan ta fito gidansu Namra ta nufo gidansu dan ta na jin bata buƙatar komawa gidan a yanzu.
“Ko ma minene shiru ya kamata ki yi ki rufawa mijinki asiri”
“Irin wannan rufa Asirin ne yasa mata da yawa maza suke cutar da su, idan aka muku fyaɗe ko aka yi ma ƴaƴansu, wannan abun yana cutar da mata da yawa, mu muke faɗar a daina ɓoye abu a riƙa fitowa a ana faɗa yau kuma sai a same ni da wannan aikin na ɓoyewa? Ɓoyewar nan da ake shi kw basu damar ƙara aikata abunda suke aikatawa, at least ko da ba a hukunta su ba, duniya zata kunyata su kuma asan ko su waye, ban ga dalilin rufawa Uzair asiri ba ko da kuwa ubana ne balle mijina, ina yawan faɗar cewa ni dai i would never in my life encourage anyone to live with an adulterer tun da har Allah ya ce a jifasu su mutu, they are as good as useless to be seen alive in this world, sai kuma na zama ni ce zan rufa masa asiri miye amfanin aikina?”
“Nidan indai zaki ɗauki shawarata ban ga abun burgewa ga mace ta kai mijinta kotu ba da sunan wai yayi ma ɗansa fyaɗe, kina da hujja ne?”
“Ko bana da ita dole zan samo ta”
“Ni kam ba da yawun baki na ba Yasmin wannan sam be dace ba, idan ma zama ne ba zaki iya da shi ba, sai ki nemi ya rabu da ke kawai ki hutu”
Ajiyar zuciya ta sauke mai nauyi.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
AMIRA POV.
“ji na yi gidan nan ya isheni ina ta jin kamar idan ban gudu ba wani abun zai iya faruwa da ni. Ban tsaya ɗaukar komai ba sai kuɗi, tun daga lokacin da na bar gidan nan nahau mota na kama hanya ban sake sanin inda nake ba, ban san inda direba ya sauke ni ba ban san ya nayi rayuwa ba, sai a ƴan kwanakin nan da wannan sojan ya tsince ni a bolar gidansu, shine yayi ta min addu'ah da komai har hankalina ya dawo, na faɗa masa inda nake ya saka direba ya kawo ni gida”
Duk kai suka girgiza cike da tausaya musamman Ammy da ke kuka kamar yadda Amira ta ke yi.
“Amman Namra ta ci amanar abota, ai gashi nan ta fara ganin abunta, ɗazu-ɗazu hajiya Haulat ta ƙira ta faɗa min ita ta dawo gida aure ya mutu, kuma ance can gidan auren ta ci kwakwarta”
Salman Big bro nasu ya kalli Ammy dake wannan maganar yana faɗin
“Ai ba laifinta ba ne, ita Amira ai cin amanar ta tashi yi, da yanzu da gaske ne idan an sakawa Namra wannan abun maganin zai kamata ai kim ga ita ta ci amana kenan, waya sani ma ko koma miki ne yayi, a haɗa baki da ke a sace ta har a ayi mata ƙazafi, wallahi kun ci amanar juna ke da ita”
Abban Amira ya ɗaga masa hannu cikin ɓacin rai.
“Idan kasan bakin ka ba alheri zai faɗa ba, ka tashi kawai ka bar falon nan. Allah zai saka miki Amira zura mata ido kawai daga ita har ɗan'uwan na ta”
“Wane irin a sa muku ido? Aja mata haƙƙinta dai, babu irin abunda ba'ayi ba amman yarinyar nan ita da mahaifiyarta suka tsaya kai da fata akan babu hannunsu a ɓatan Amira, aka kiɗa aka raya aka daka yarinyar ta ƙeƙashe ƙasa tace bata san gaibu ba akan ɓatan Amira sai yanzu kuma gaskiya ta bayyana za'ace a ƙyaleta”
Taɓe baki Salim yayi ya miƙe tsaye ya fice daga falon.
“Babu wani haƙƙi da za a ja mata ku zuba musu ido kawai, ko bayan rage kika zagaya kika ɗauki wani hukunci sai na ɓata miki rai Wallahi, tun da na ce a bar maganar nan barinta shine ya fi kawai”
Ya miƙe tsaye ya fice daga falon. Kuka sosai Amira take, sai dai ba kuka dawowa gida ba, kukan rabuwa da Abdool tana jin kamar zata mutu idan ta tuna baya kusa da ita a yanzu.
ABDOOL POV.
Ya ware hannayensa.
“You see Ummi na faɗa miki Mai Martaba bashi da matsala, na zauna na fahimtar da shi kuma ya fahimta”
“Hakan na da kyau ai, sauran yarinyar ko?”
“Wannan ba matsala ba ne, zan ji da shi, so na ke sai an kwana biyu sai naje na ganta ko?”
Ummi tasa dariya, the way da yake mata maganar kamar wani ƙaramin yaro.
“Allah ya baka sa'ah”
“Amin my happiness. This week zan koma aiki, hutun mu ya ƙare”
“Ai daman ai baka yi hutu ba, ina fatar da kana da number wayarta”
“Wallahi bana da ita saboda yarinyar akwai jan aji amman zan sa a nema min. Am ɗazu mun yi waya da mahaifiyar Amira ta isa gida lafiya ƙalau”
“Mashallah, yau za su kwana cikin farinciki, ita kanta zata fi sakewa”
Kafaɗunsa ya ɗaga irin ina ruwana ɗin nan. Ummi ta watsa masa harara.
“Bari yarinyar nan ta ƙi amincewa da kai, ta yi ta baka wahala”
Ya sa dariya.
“Haba Ummi karki min baki mana”
Ya miƙe tsaye ya fice yana dariya.
ASIM POV.
Da rana ya sauka sokoto, kai tsaye gidansu ya nufa, duk da be so sake dawowa garin ba tare da an canja musu gida ba, sai dai matsalar har yanzu ba a samu gidan da suke so ba. Mama ta yi mamakin ganinsa sosai tun da be kirata ya faɗa mata zai zo ba balle ta tanadar masa da wani abu.
“Wannan zuwa haka ba waya ga shi komai ba a tanadar maka ba”
“Ba komai nima zuwan ya kamani ne kawai”
“To Allah yasa dai lafiya”
“Lafiya ƙalau, na ji ance Namra tana garin nan ne, shiyasa na zo dan zan maida aurena ne”
Mama ta daki ƙirji.
“Auren ka Asim? Kai kam mi ya kai ka daga Allah ya raba da ƙaddara”
“Kin san tana da ciki fa na sake ta, ni gaskiya yanzu so na ke na maidata”
“Amman Asim kana ganin zaka iya tunkarar gidansu yanzu ka ce zaka maida aurenta, mahaifinta ai sai ya yanka namanka da wannan fitinanniyar ƙanwarta”
“Koma minene dai sai naje gidan, ai yanzu be isa ya wulaƙanta ni ba, dan na fi ƙarfinsa Wallahi”
Tattaunawa suka soma yi kan maganar aurensa da Mardiya da irin abubuwan da ya shirya, sannan ya bijiro mata da maganar samun gidan, a nan take labarta masa am samu wani a Abdullahi Fodio Road amman wai har miliyan uku, ita gani take kamar yayi tsada, waɗannan da ake samu kusa kuma duk bata son unguwar.
“Ƙar hakan ya dame ki, indai gida yayi miki za a biya kuɗi a saka komai sabo sai ku koma”
“Yanzu kana da har miliyan uku na gidanmu?”
“Akwai su, zinari fa na ke siyarwa, kin san kuɗin da mike samu kuwa?”
“Allah ya ƙara arziki ai haka nake so, sai ka samu kawon ka Na Malam ku yi magana shi ya san inda gidan ya ke”
Haka suka wuni suna fira sallah ce kawai ke tashinsa, sai da akayi magariba sannan ya shiga yayi wanka ya shirya cikin ƙananan tufafi ya saka turare ya shigo ɗakinta.
“Mama ni zanje wani guri da abokina sai gobe zamu dawo”
“To Allah ya tsare hanya”
Ya sa kai ya fice sai ƙamshin turare yake. Be daɗe da fita ba aka aiko ana yi ma Hajara sallama.
“Je kace tana nan zuwa”
Sai Hajara ta tashi ta ɗauki kayan kwaliyarta ta gyara fuskarta sannan ta saka Hijabinta ta fice. Bayan fitarta Mama ta ɗauki tabarma ta shinfiɗa a waje ta zauna tana sauraren Garkuwa Fm.
Tana haka sai ga Hajara ta dawo, ta doso inda take.
“Mama Yaya Asim ya bar makulli a ɗauko wayarsa a mota ya barta sai kiransa ake, kuma Mahmud (Saurayin da ya zo gurinta) Idan wasu suka ga wayar zasu iya fasa gilashin motar su ɗauka”
“Amman ya fita da wayarsa, sai dai idan ba ɗaya ba ce, lalaba aljihun wandon da ya cire ɗazu ko daki samu makullin ni dai be ba ni ba”
Ta faɗa tana tsakalen haƙori, da karen darbejiya bushesshe. Hajara ta nufi ɗakin Mama inda ya sarkafa wandonsa ta soma lalabawa ta ji kuɗi mai mugun yawa kamin ta yi arba da makulin.
“Ga makullin nan bari na ɗauko, amman Mama kin ji Aljihun yaya kuɗi cike”
“Ke da gaske?”
Mama ta yi sauri ta tashi ta nufi ɗakin. Hannu tasa cikin aljihunsa ta ciro rabonta saka inda take ajiyar kuɗi, sannan ta koma waje gurin tabarmarta zauna. Sai ga Hajara ta shigo da wayoyi biyu da makullin sannan kuma da Apple hannunta.
“Aje masa, wannan karki canye ki rage min”
Ta miƙa mata wayoyin da Apple ta juya, hankalinta yana gurin Mahmud kar ya ce ta bar shi.
“Ina kika samo tuffah”
“A motar Yaya”
Mama ta yi murmushin jidaɗi.
“Oh Yaro yayi kuɗi har tuffa ake ci a mota yanzu haka ya manta da ita da wayoyin nasa da ya bari, ko da yake abun ba ɗaya ba naga fa ya fita da wasu”
Ta faɗa tana gantsara apple ɗin, babu ko bismilah balle kuma ta damu da wankewa. Haka ta kama shi ta wanke tass tana cewa idan Hajara ta zo ta bata kuɗi ta siya wani wani tun da akwai shi a titi, har ta ƙaro mata ma dan wannan ma ta jidaɗinsa. Sau biyu ana kiran wayar Asim sai ta ɗauka ta ce baya kusa.