Sashe 144
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin kuka Rashida take maganar gwanin ban tausayi. Hajiya ta share hawayenta tana kallon Ezzah.
“Miya faru faɗa mana”
Ras Ezzah ta zana musu abunda ya faru, duk wani tsoro na teema yau baya tare da ita, tun da ta ji zancen Hilal yace zai raba ta biyu. Duk suka cika da mamaki sai kawai Teema ta ƙara rushewa da kuka, Hajiya ta girgiza kai tana faɗin.
“Amman Fatima kin ban mamaki, kw da ake yabo da salla?”
Hilal yayi saurin ɗaga mata hannu.
“Hajiya dan Allah kar ayi maganar nan a nan, asibiti muke, kullum sai ace nine family na cikin matsala”
“Kai dalla gafara can, kai har yanzu baka san ciwon kanka ba akan ƴaƴanka, ko wace mace ka aura da irin azabar da take gwadawa ƴaƴanka, Kalsoom ta kashe Rafiq wannan kuma tana ƙoƙarin kashe Ulfah wannan wane irin masifa ce”
Rashida ta kalli Hajiya tana hawaye.
“Wallahi ba Kalsoom ba ce ta kashe shi, Wallahi nice ni na kashe ɗana da kai na...”
Sai duk kallo ya koma kan Rashida har Kalsoom ɗin kallonta take. Hajiya tasa wani dogon numfashi ta sauke ta ce
“Muje gida mu yi wannan maganar, Hilal muje gidanka a yi wannan maganar, Ke ki tsaya nan ki kula da Ulfah”
Ta faɗa tana kallon ɗaya daga cikin ƙanensa, sai kawai ta nufi ƙofar fita tare da tawagarta. Rashida ma fita tayi ta rufa musu baya dan ta shirya fasa ƙwan yau kam, bata san gidan Teema ba dan haka ta nufi tsohon gidanta kuma gidan Hilal inda Kalsoom take zaune. Hilal kan sai ya bawa ƴarsa magani tare da allura ta koma bachi sannan ya sako matansa gaba suka kama hanyar gida. Ko da suka shiga falon Hajiya na zaune falon tana jiransu, Ezza kuma na riƙe da Hijabin Kalsoom kamin ta saketa ta nufi gurin uwarta da gudu.
“Maimata abunda kika faɗa ɗazu ko kina da wata shaida”
Cewar Hajiya tana kallonta. Rashida ta girgiza kai.
“Bana da wata shaida sai Allah da kuma Teema, amman Wallahi Kalsoom bata da hannu a mutuwar Rafiq, ni naja komai”
“Kamar ya ki fito ki yi bayani mana”
Hilal ya katsa mata tsawa, Teema ta yi saurin saka baki.
“Karki ci amanata Rashida ni ban san komai akan ɗan ki ba”
Rashida bata kulata ba, ta soma koro da bayani.
“Bayan da Hilal ya sake ni, sai na riƙa zagaya makarantar su Ezzaha ina zana mata irin makirci da rashin kunyar da zata yi ma Kalsoom, ina tunani kamar idan ta yi hakan zai tausaya musu ya dawo da ni, da naga hakan be samu ba, sai na koma bin bokaye, ina neman yadda za ayi Kalsoom ta bar gidan Hilal kuma ya dawo gareni, naje wanu gurin aka mata magani aka sako mata jini, cikin dake jikinta ya kwanta ya ɓace bat, na sake komawa na yi mata wani a wannan karon be faɗa kanta ba, ya faɗa kan ɗa na Rafiq, ni kai na ban san ya faɗa kansa ba, har sai da naje na kaiwa Teema kukana ta kaini gurin wani malami shi ya faɗa min cewar na yi magani ma kishiyata ya faɗa kan ɗa na, shiyasa a asibiti aka rasa gane kan wannan matsalar sai ya nuna guba ne sai kuma ya nuna gas ne, ba komai ba ne sai sihiri. Duk wani shige-shige da nake na magani tare da Teema nake yinsa, ta kai ni gurare da dama, saboda ta fini sanin bokaye, nayi mamakin da aka ce Hilal zai aureta saboda na san an gudu ba a tsira ba ne. Sai dai na ɗauki hakan a matsayin cin amanar aure da nayi na keta haddin Allah na tozarta aure, dole nima Allah ya tozarta ni, na ci amanarki Kalsoom na yi ta miki abubuwa ko a zaman da muka yi da ke a gidan nan, ashe ma ke ƴar'uwata ce ba kishiya ba...”
Kuka take sosai ita da Kalsoom da Teema, sai dai ko wannensu da abunda yake yi ma kuka. Kalsoom babu komai a zuciyarta sai farincikin yau Allah ya wanke ta da kuma tausayin Rashida da ƴaƴanta.
“Na yafe miki Rashida, Wallahi na yafe miki har a bada, kuma na miki alƙawarin zan kula miki da ƴaƴanki fiye da yadda ke zaki kula da su, amman idan Hajiya ta yarda”
Kalsoom ta faɗa tana kallon Hajiya data soke kai tana hawaye.
“Haƙiƙa na cutar da ke Kalsoom, na miki kurkuren fahimta, na ɗauki alhakinki, na cutar da ke matuƙa, Wallahi na ji kunyar kai na sosai”
“Haba Hajiya ai ko nice a matsayin da kike kwatankwacin abunda zan aikata kenan, saboda gaskiya ba ta bayyanaba a lokacin kuma ɗan adam da zahiri yake aiki sanin baɗini kuwa sai Allah, ni dai abunda kawai na ke so ki yarda da ni kawai”
“Wallahi na yarda da ke ɗari bisa ɗari kalsoom, kuma daga yau yaranki gurinki zasu zauna. Teema baki yi ƴa ba, kin bani mamaki, ina gani kamar na ɗauko ma ɗauka mutuniyar kirki ashe ɓara gurbi ce”
Kuka sosai Teema take ta sauka daga saman kujera ta zauna ƙasa kusa da Hajiya ta kama ƙafafunta.
“Wallahi Hajiya ƙarya take min, na miki alƙawarin zan canja daga yau, ba zan sake yin wani abu marar kyau ba”
“Nasa Hilal ya aure ki ne saboda ita tunanin ke ta ƙwaraice, Fatima ko da mun zauna da ke babu aminci a tsakanin ke da mijinki da ƴaƴansa da kuma ni, mace mai shige-shigen malamai iya mata sai Allah karki je ki yi mana irin na Rashida, kin ga ƙara a rabu tun abu be yi nisa ba, kije can Allah ya haɗa ki da rabon ki, ni kan Hilal ba dan kar na zama uwar banza ba da na baka shawarar rabuwa da yarinyar nan...”
Ta ƙarasa tana kallon Hilal. Shi kan uffan be ce ba sai kallon pop yake abun duniya ya taru ya tsaya masa, idan ya shiga wannan ya shiga wannan. Miƙewa ya yi tsaye ya fice cikin rashin daɗin rai.
Bayan fitarsa Hajiya ta miƙe ta fita, ta bar Teema na kuka, Rashida kuma na hawaye. Bata yi minti talatin da fita ba Rashida ta tashi ta fice, a lokacin ne Teema ta kalli Kalsoom ta ce.
“Zan taimaka miki ki haihu, nasan hanyoyin da zan bi ki haihu, wannan cikin na ki yanzu shekarar ɗaya da wata huɗu cikin na biyar, amman idan kika taimaka min kika hana Hilal ya sake ni, ina son ki saka baki a lamarin auren mu domin a yanzu na fuskanci kina da ƙima a gurinsa da kuma mahaifiyarsa fiye da ni”
Ido kawai Kalsoom ta sakar mata tana kallon ikon Allah, ta ya zata ce ta kaita wani gurin bayan yanzu aka gama rigimar tana bin bokaye, ita bata ma tsoron wani ya ji. Kamar daga sama suka ji muryar Hilal da ke tsaye bakin ƙofa rumgume da hannayesa a ƙirji yana kallonsu, dan sam basu san da shigowarsa ba.
“Kalsoom bata iya shige-shige irin na ku ba, kuma idan lokacin haihuwarta yayi zata haihu, ke ai naga haihuwar kike nema miya hanaki bin bokayen su baki haihuwa?”
Ta miƙe tsaye yana kallonshi.
“Haihuwar da na ke so Hilal saboda kai nake son ta, ina son na haihu da kai saboda ina ƙaunar ka ne, yanzun kuma abunda nake ƙoƙarin yi ma saboda ina ƙaunarka ne Hilal, miyasa ka kasa ganin haka? Tun kana mijin Rashida na ke mafarki miji irin ka saboda kana kula da ita yadda ya dace, ashe ma Allah yayi sai na kasance ɗaya daga cikin matan ka, ka tausaya min Hilal, zan iya yi maka alƙawarin ba zan sake bin ko wane malami ba indai wannan ce kawai matsalar...”
Ta ƙarasa tare da risinawa kamar mai neman gafara.
“Ba wannan ce kawai matsalar ba, ko na zauna da ke ba zan aminta da ke ba, kuma mai hali baya fasa halinsa, ai yanzu aka gama wannan rigimar amman kika ɗaga ido kika kalli Kalsoom har kina neman ki taimaketa, dan ta saka kar na sake ke, kin manta ita da ke duka a ƙarƙashin kulawata kuke? Hajiya ma dake gindaya min sharaɗi yin abu ko hani ta bani umarnin idan na ga dama na sake ki, tun dan me zaki dawo gurin Mamata kina neman ta taimake akan abunda zan iya yanke hukuncinsa yanzu?”
Kalsoom ta girgiza masa kai.
“Saboda ta san zan iya saka ka yi ne...”
“Kalsoom karki saka bakin ki cikin wannan maganar please”
Teema ta hasala ta miƙe tsaye cikin ɓacin rai da zafin zuciya.
“Ka daɗe baka sake ni ba Hilal, ni wannan wuƙancin da Rashida take ɗauka ni bana ɗaukarsa, sai kace kai ne kaɗai na miji ana magana kana ƙara butsewa, ka sake mana ai ni tafi nono fari, zaman gidanka ko zaman wahala haka kawai za ku ɗauko ni wani kula da yara wato ga ƴar aiki kenan ko saboda an maida ni shim mai ruwa uku sha-sha-sha, da ƙurciyata na lalata kaina gurin gina rayuwar ƴaƴan wata nawa ko zuwa duniya ba su yi ba”
“Shiyasa kike cutar da su? To Allah ya toni asirin ki, kuma ki je na sake ki saki ɗaya...!”
“Ai ni da uku ka yi da ka fi burgeni”
“Ɗayan dai zan miki ƙyaji da shi”
“Tafi nono fari, ai ba kai ne autan maza ba”
“Na sani shiyasa na sake ki saboda ki samu damar auren wani”
“Aiko zaka gani dan sai kasan kayi hasarar mace irina”
Ta kaɓe masa Hijab ɗinta ta fice kamar zata tashi sama.
“Hakan be dace ba Hilal kana wasa da saki, daga wannan maganar zaka ce ka saketa kuma kana ganin yadda take ta lallaɓaka akan ka barta ɗakinta...”
“Na faɗa miki babu ruwanki da irin maganganun nan, kin cika salo da saka kanki cikin irin lamurran nan shiyasa komai aka yi sai a kin saka bakin ki shiyasa komai ake ɗora miki laifi”
“Amman....”
“Na ce ki min shiru ko?”
Uffan bata sake cewa ba sai ta cigaba da wasa da kan Ezzah shi kuma ya juya ya fice.
UZAIR POV.
“Miya faru faɗa mana”
Ras Ezzah ta zana musu abunda ya faru, duk wani tsoro na teema yau baya tare da ita, tun da ta ji zancen Hilal yace zai raba ta biyu. Duk suka cika da mamaki sai kawai Teema ta ƙara rushewa da kuka, Hajiya ta girgiza kai tana faɗin.
“Amman Fatima kin ban mamaki, kw da ake yabo da salla?”
Hilal yayi saurin ɗaga mata hannu.
“Hajiya dan Allah kar ayi maganar nan a nan, asibiti muke, kullum sai ace nine family na cikin matsala”
“Kai dalla gafara can, kai har yanzu baka san ciwon kanka ba akan ƴaƴanka, ko wace mace ka aura da irin azabar da take gwadawa ƴaƴanka, Kalsoom ta kashe Rafiq wannan kuma tana ƙoƙarin kashe Ulfah wannan wane irin masifa ce”
Rashida ta kalli Hajiya tana hawaye.
“Wallahi ba Kalsoom ba ce ta kashe shi, Wallahi nice ni na kashe ɗana da kai na...”
Sai duk kallo ya koma kan Rashida har Kalsoom ɗin kallonta take. Hajiya tasa wani dogon numfashi ta sauke ta ce
“Muje gida mu yi wannan maganar, Hilal muje gidanka a yi wannan maganar, Ke ki tsaya nan ki kula da Ulfah”
Ta faɗa tana kallon ɗaya daga cikin ƙanensa, sai kawai ta nufi ƙofar fita tare da tawagarta. Rashida ma fita tayi ta rufa musu baya dan ta shirya fasa ƙwan yau kam, bata san gidan Teema ba dan haka ta nufi tsohon gidanta kuma gidan Hilal inda Kalsoom take zaune. Hilal kan sai ya bawa ƴarsa magani tare da allura ta koma bachi sannan ya sako matansa gaba suka kama hanyar gida. Ko da suka shiga falon Hajiya na zaune falon tana jiransu, Ezza kuma na riƙe da Hijabin Kalsoom kamin ta saketa ta nufi gurin uwarta da gudu.
“Maimata abunda kika faɗa ɗazu ko kina da wata shaida”
Cewar Hajiya tana kallonta. Rashida ta girgiza kai.
“Bana da wata shaida sai Allah da kuma Teema, amman Wallahi Kalsoom bata da hannu a mutuwar Rafiq, ni naja komai”
“Kamar ya ki fito ki yi bayani mana”
Hilal ya katsa mata tsawa, Teema ta yi saurin saka baki.
“Karki ci amanata Rashida ni ban san komai akan ɗan ki ba”
Rashida bata kulata ba, ta soma koro da bayani.
“Bayan da Hilal ya sake ni, sai na riƙa zagaya makarantar su Ezzaha ina zana mata irin makirci da rashin kunyar da zata yi ma Kalsoom, ina tunani kamar idan ta yi hakan zai tausaya musu ya dawo da ni, da naga hakan be samu ba, sai na koma bin bokaye, ina neman yadda za ayi Kalsoom ta bar gidan Hilal kuma ya dawo gareni, naje wanu gurin aka mata magani aka sako mata jini, cikin dake jikinta ya kwanta ya ɓace bat, na sake komawa na yi mata wani a wannan karon be faɗa kanta ba, ya faɗa kan ɗa na Rafiq, ni kai na ban san ya faɗa kansa ba, har sai da naje na kaiwa Teema kukana ta kaini gurin wani malami shi ya faɗa min cewar na yi magani ma kishiyata ya faɗa kan ɗa na, shiyasa a asibiti aka rasa gane kan wannan matsalar sai ya nuna guba ne sai kuma ya nuna gas ne, ba komai ba ne sai sihiri. Duk wani shige-shige da nake na magani tare da Teema nake yinsa, ta kai ni gurare da dama, saboda ta fini sanin bokaye, nayi mamakin da aka ce Hilal zai aureta saboda na san an gudu ba a tsira ba ne. Sai dai na ɗauki hakan a matsayin cin amanar aure da nayi na keta haddin Allah na tozarta aure, dole nima Allah ya tozarta ni, na ci amanarki Kalsoom na yi ta miki abubuwa ko a zaman da muka yi da ke a gidan nan, ashe ma ke ƴar'uwata ce ba kishiya ba...”
Kuka take sosai ita da Kalsoom da Teema, sai dai ko wannensu da abunda yake yi ma kuka. Kalsoom babu komai a zuciyarta sai farincikin yau Allah ya wanke ta da kuma tausayin Rashida da ƴaƴanta.
“Na yafe miki Rashida, Wallahi na yafe miki har a bada, kuma na miki alƙawarin zan kula miki da ƴaƴanki fiye da yadda ke zaki kula da su, amman idan Hajiya ta yarda”
Kalsoom ta faɗa tana kallon Hajiya data soke kai tana hawaye.
“Haƙiƙa na cutar da ke Kalsoom, na miki kurkuren fahimta, na ɗauki alhakinki, na cutar da ke matuƙa, Wallahi na ji kunyar kai na sosai”
“Haba Hajiya ai ko nice a matsayin da kike kwatankwacin abunda zan aikata kenan, saboda gaskiya ba ta bayyanaba a lokacin kuma ɗan adam da zahiri yake aiki sanin baɗini kuwa sai Allah, ni dai abunda kawai na ke so ki yarda da ni kawai”
“Wallahi na yarda da ke ɗari bisa ɗari kalsoom, kuma daga yau yaranki gurinki zasu zauna. Teema baki yi ƴa ba, kin bani mamaki, ina gani kamar na ɗauko ma ɗauka mutuniyar kirki ashe ɓara gurbi ce”
Kuka sosai Teema take ta sauka daga saman kujera ta zauna ƙasa kusa da Hajiya ta kama ƙafafunta.
“Wallahi Hajiya ƙarya take min, na miki alƙawarin zan canja daga yau, ba zan sake yin wani abu marar kyau ba”
“Nasa Hilal ya aure ki ne saboda ita tunanin ke ta ƙwaraice, Fatima ko da mun zauna da ke babu aminci a tsakanin ke da mijinki da ƴaƴansa da kuma ni, mace mai shige-shigen malamai iya mata sai Allah karki je ki yi mana irin na Rashida, kin ga ƙara a rabu tun abu be yi nisa ba, kije can Allah ya haɗa ki da rabon ki, ni kan Hilal ba dan kar na zama uwar banza ba da na baka shawarar rabuwa da yarinyar nan...”
Ta ƙarasa tana kallon Hilal. Shi kan uffan be ce ba sai kallon pop yake abun duniya ya taru ya tsaya masa, idan ya shiga wannan ya shiga wannan. Miƙewa ya yi tsaye ya fice cikin rashin daɗin rai.
Bayan fitarsa Hajiya ta miƙe ta fita, ta bar Teema na kuka, Rashida kuma na hawaye. Bata yi minti talatin da fita ba Rashida ta tashi ta fice, a lokacin ne Teema ta kalli Kalsoom ta ce.
“Zan taimaka miki ki haihu, nasan hanyoyin da zan bi ki haihu, wannan cikin na ki yanzu shekarar ɗaya da wata huɗu cikin na biyar, amman idan kika taimaka min kika hana Hilal ya sake ni, ina son ki saka baki a lamarin auren mu domin a yanzu na fuskanci kina da ƙima a gurinsa da kuma mahaifiyarsa fiye da ni”
Ido kawai Kalsoom ta sakar mata tana kallon ikon Allah, ta ya zata ce ta kaita wani gurin bayan yanzu aka gama rigimar tana bin bokaye, ita bata ma tsoron wani ya ji. Kamar daga sama suka ji muryar Hilal da ke tsaye bakin ƙofa rumgume da hannayesa a ƙirji yana kallonsu, dan sam basu san da shigowarsa ba.
“Kalsoom bata iya shige-shige irin na ku ba, kuma idan lokacin haihuwarta yayi zata haihu, ke ai naga haihuwar kike nema miya hanaki bin bokayen su baki haihuwa?”
Ta miƙe tsaye yana kallonshi.
“Haihuwar da na ke so Hilal saboda kai nake son ta, ina son na haihu da kai saboda ina ƙaunar ka ne, yanzun kuma abunda nake ƙoƙarin yi ma saboda ina ƙaunarka ne Hilal, miyasa ka kasa ganin haka? Tun kana mijin Rashida na ke mafarki miji irin ka saboda kana kula da ita yadda ya dace, ashe ma Allah yayi sai na kasance ɗaya daga cikin matan ka, ka tausaya min Hilal, zan iya yi maka alƙawarin ba zan sake bin ko wane malami ba indai wannan ce kawai matsalar...”
Ta ƙarasa tare da risinawa kamar mai neman gafara.
“Ba wannan ce kawai matsalar ba, ko na zauna da ke ba zan aminta da ke ba, kuma mai hali baya fasa halinsa, ai yanzu aka gama wannan rigimar amman kika ɗaga ido kika kalli Kalsoom har kina neman ki taimaketa, dan ta saka kar na sake ke, kin manta ita da ke duka a ƙarƙashin kulawata kuke? Hajiya ma dake gindaya min sharaɗi yin abu ko hani ta bani umarnin idan na ga dama na sake ki, tun dan me zaki dawo gurin Mamata kina neman ta taimake akan abunda zan iya yanke hukuncinsa yanzu?”
Kalsoom ta girgiza masa kai.
“Saboda ta san zan iya saka ka yi ne...”
“Kalsoom karki saka bakin ki cikin wannan maganar please”
Teema ta hasala ta miƙe tsaye cikin ɓacin rai da zafin zuciya.
“Ka daɗe baka sake ni ba Hilal, ni wannan wuƙancin da Rashida take ɗauka ni bana ɗaukarsa, sai kace kai ne kaɗai na miji ana magana kana ƙara butsewa, ka sake mana ai ni tafi nono fari, zaman gidanka ko zaman wahala haka kawai za ku ɗauko ni wani kula da yara wato ga ƴar aiki kenan ko saboda an maida ni shim mai ruwa uku sha-sha-sha, da ƙurciyata na lalata kaina gurin gina rayuwar ƴaƴan wata nawa ko zuwa duniya ba su yi ba”
“Shiyasa kike cutar da su? To Allah ya toni asirin ki, kuma ki je na sake ki saki ɗaya...!”
“Ai ni da uku ka yi da ka fi burgeni”
“Ɗayan dai zan miki ƙyaji da shi”
“Tafi nono fari, ai ba kai ne autan maza ba”
“Na sani shiyasa na sake ki saboda ki samu damar auren wani”
“Aiko zaka gani dan sai kasan kayi hasarar mace irina”
Ta kaɓe masa Hijab ɗinta ta fice kamar zata tashi sama.
“Hakan be dace ba Hilal kana wasa da saki, daga wannan maganar zaka ce ka saketa kuma kana ganin yadda take ta lallaɓaka akan ka barta ɗakinta...”
“Na faɗa miki babu ruwanki da irin maganganun nan, kin cika salo da saka kanki cikin irin lamurran nan shiyasa komai aka yi sai a kin saka bakin ki shiyasa komai ake ɗora miki laifi”
“Amman....”
“Na ce ki min shiru ko?”
Uffan bata sake cewa ba sai ta cigaba da wasa da kan Ezzah shi kuma ya juya ya fice.
UZAIR POV.