Sashe 52
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Na gode daman nima ba zan wuce kwana biyun ba, Allah kara maka lafiya”
Har cikin ƙasan zuciyarta take jin son Asim, sam bata iya gani illarsa, saboda zuciyarta tana muradinsa, a take zuciyarta ta fara raya mata ya ɓoye mata maganar kuɗin wata ƙila saboda karta sa ci suna da kuɗi, kuma ita kanta bata san yadda yayi ya samun kuɗin adashen ba, sai dai abunda ya faɗa a wacan lokacin ya tsaya mata a rai, a duk lokacin data tuna sai ta ji babu daɗi, har zuciyarta ta zarge shi akan haka.
HILAL POV.
A haukace ya isa asibiti, dan a tunaninsa Rashida ta mutu, shi da kansa ya kai ta emergency room, tare da taimakon wasu Nurses ya shiga neman numfashinta.
Da taimakon Allah komai ya daidaita, sannan ya ɗaura mata drip, yayi mata allurar. Tsaye yayi cikin ɗakin yana kallonta bayan Nurses ɗin sun fita.
Wayarsa ya shiga lalabe sam ya manta da tana ciki mota, sai yanzu. Fita yayi be daɗe ba ya dawo tare da rigar asibiti da wasu kayan aiki, sai ya canja mata tufafin jikinta, ya gyara mata jikinta sannan ya saka mata rigar, sai ya kira wata ma'aikaciyar gurin mai share-share ta kwashe kayan.
Zaunawa yayi a gurin ya ɗafa kansa, sai ga wasu daga cikin abokan aikinsa sun shigo duba ta, sama-sama ya amsa musu, suma sun ga damuwa ƙarara a fuskarsa, sun lura da yanayinsa, duk a tunaninsu saboda Madam bata da lafiya ne.
Fatan sauƙi suka mata sannan suka fita, shi kuma ya tashi yaje gurin motarsa ya ɗauki wayarsa ya kira Hajiyarsa ya faɗa mata, sannan ya kira Momy ita ma ya faɗa mata.
A cikin motar ya shiga ya zauna ya tasa abunda ke masa daɗi duniya, baya son yaransa su san komai a tsakanin su, kuma be san wane bayani zai yi ma Hajiyarsa ba da Momy, sam baya son duniya tasan abunda Rashida ta aikata, sai dai kuma be san yadda zai yi yayi ya ɓoye ba, cox he's no more to her.
Be ɗago kansa daga tunanin da yake ba, wayarsa tayi ringing, number Momy ce a rikice take tambayarsa wane ɗaki Rashida take.
Sai da ya buɗe Motar ya fito sannan ya amsa ta.
“Kin shigo Asibitin ne ?”
“Eh ina emergency”
“Okay tsaya a gurin zan ƙaraso yanzu”
Ya kashe wayar tare da rufe motar, sannan ya nufi gurin da yake zaton take. Tun daga nesa ya hango ƙannenta biyu. Cikin rashin kuzari ya ƙarasa inda suke ya gaishe ta, su kuma ƙannen suka gaishe shi. Sannan ya wuce dasu zuwa ɗakin da take.
Ganin halin da take cikin yasa Momy har ta fara hawaye, kallon ta kawai Hilal yayi yana ayyana irin abunda zata ji idana kace mata ƴarta na ɗauke da cuta mai ƙaryar garƙuwar jiki.
“Momy karku taɓa ta, ko da ta farka ne”
“Toh amman mi ya same ta haka ne?”
“Ta samu Miscarriage ne”
“Subhanallahi Allah ya bata lafiya”
“Amin”
Ya koma ya jingina da bangon ɗakin yana kallonta, ɗaya daga cikin ƙanwarta ta warware carpet ɗin da suka zo da shi ta shinfiɗa a gurin. Ta miƙawa Hilal Kujera, sai kawai ya girgiza mata kai.
“No Thanks”
A gurin yayi ta tsayi har Hajiya ta iso, ita sai da ta kira shi, yaje ya taho da ita sai suka gaisa da Momy, ta duba ta tayi mata fatan sauƙi sannan ta fito. Tare suka jero da ɗanta sai gaisuwar girmamawa ake mata, dan kowa ya ganta ya ga Hilal yasan itace mahaifiyarsa.
“Yanzu haka baƙin kishi ne ta sawa kanta, gashi yanzu kun yi losing wannan baby”
Shi dai be ce komai ba, ya buɗe mata Mota. sai da ta shiga, ta zauna sannan yayi mata sai da safe direba ya wuce da ita, shi kuma ya juyo ya dawo cikin asibitin.
Lokacin daya dawo, sai ya zauna saman gadon kusa da ita, babu abunda yake kallon sai fuskarta, rayuwarta da tasa yake ta tunani, irin yadda suka so junansu har suka haifi ƴaƴansu, yanzu kuma lokaci ɗaya komai yana shirin sauya musu, he just can't believe ace Rashida ta ci amanarsa da wani, haƙiƙa yana da tambayoyin da suke buƙatar amsa daga gareta.
“Ai da ka tashi kaje gida, tun da ga mu muma ai mun isa mu kula da ita”
Can ciki ya ji muryar Momy tana masa magana. Sai ya tashi cikin rashin ƙwarin jiki yayi musu sai da safe ya fice.
NAMRA POV.
Daga asibitin sai ta wuce bank, layi ta bi sai da ka kai gareta sannan tayi checking balance ɗinta, dubu ɗari huɗu ta hansin ta gani, a tunaninta ko Anty Amarya ta ƙaro mata wasu ne, sai kawai ta cire kuɗin gaba ɗaya, cikin farinciki da jindaɗi.
Kamin ta isa gida sai ta ta fara biyawa ta gidan dillaliya, ta ƙirga kuɗinta ta bata, sannan tasa a kira mutumen da yayi musu wacan rubutun yayi masu sheida saboda wata rana.
Sauran kuɗin daya rage mata sai taje kasuwa ta siye kuloli, da ƴan wasu kayan aiki da basu kai sun kawo ba, data dawo gida sai ta wanke kuloli ta siye abincin ta nufi asibitin da shi.
Ta jidaɗin ganin Asim a tsaye yana ɗan takawa, Mama na tiƙe da shi, suna zuwa ƙarshen ɗakin suna dawowa, wani farinciki ne ya mamayeta, bata san lokacin data aje kulolin ba ta tsaya tana kallonsu.
Hamdala take yi ma Allah cikin ranta, tana jindaɗin yadda taga mijin nata yau ya fara taka ƙasa, Mama ma farinciki take sosai daman ta fi kowa son haka dan zaman asibitin ya isheta.
Sun kusa minti latalin suna, suna zagaye ɗakin sannan Mama ta zaunar da shi saman gado.
“Allah ya bi da lafiya ya ƙara sauki”
Ita da Asim suka haɗa baki gurin amsawa da Ameen. Sannan ta zuwa ya fice.
Namra ta kalli Asim da far'ah a fuskarta.
“Da nice nace za kayi wannan yawo zaka ce min ba aka iya ba”
Ɗan murmushi yayi, shi kansa yana cikin jindaɗi a yau.
“Alhamdullillah, ban zaci zan iya ba”
“Ai babu abunda za a iya matuƙar aba'a gwada ba, Allah ya nuna min ka tashi ka koma kamar yadda kake”
“Ameen”
Ta kwantar da kanta saman jikinsa. Shi kuma yayi shiru yana nazarin rayuwarsa, irin mutanen da sukajuya masa baya yake lissafi a zuciyarsa, ace har abokansa da yake ganin sun kai amman kowa ya kasa takowa ya zo ganinsa
“Hmmm”
Ya furta a fili, yana sauke ajiyar zuciya. Sai Namra ta kalleshi
“lafiya?”
“Lafiya ƙalau, kawai ina tunanin tafiyarki ne, Mama tace karki je yanzu, idan ma wani abun ne ai aiko miki kawai, kuma ki faɗa wata komai ta waya kawai, tama kira ba ki nan”
Shuru Namra tayi bata ce komai ba, sai dai maganar tasa bata mata daɗi ba. Hannu ya kai ya shafa ta.
“Namra have you ever noticed that Anty bata taɓa kira kai tsaye da sunan jin jikina ba? Haba Namra ai ko wani na kashe musu sa ɗaga min ƙafaa balle auren ƴar su na ke, abun nan ya ɓata ran Mama sosai, nima shiyasa a duk lokacin dana ga ɓacin rai a fuskarta sai nawa rai ya ɓace, daman irin wannan ake gudu aje ayi aure a kasa samun kwanciyar hankali”
Shiru tayi tana taɓin hannunta, ita kanta tasan iyayenta basu kyauta ba, akan abunda aka yi mata kuma Asim yana da gaskiya kan abunda yake faɗa, tasan Abbah kam ba zai zo ganinsa ba, amman ya kamata ace ko Maryam ce ta zo ganinta, ganin yadda suke da ita jini ɗaya, amman ko waya bata taɓa bugo mata ba.
Anya ta cancanci su juya mata baya har haka?
Ba su da wani excuse akan haka, sai dai a yanzu bata son ta zurfafa amincinta ga Asim tun bayar maganar su da taji da Mama.
Kamar ya san abunda yake ransa, sai kawai ya rumgume ta.
“Ina son ki, kuma bana tunanin akwai abunda zai raba ni da ke, ina son na ɗanɗana miki rayuwar da baki taɓa mfarkin shigarta ba, irin rayuwar jindaɗin da tafi ta gidan ku, sai dai ina gudun ranar da zaki rabu da ni saboda wani baƙin talauci ko mugu abu ya same ni”
“Ba zan taɓa rabuwa da kai ba Asim na maka alƙawari, ko a wane hali na samu kai na, zan zama mai biyayyah a gare ka, zan maka sadaukarwar da ba kowa ce mace ce zata iya ba, son nuna maka son da ba kafai ake samun irinsa ba.
Sai dai ni zuciyarta ta kasa Aminta da kai, kana ɓoye min wani abu naka Asim”
Gabansa ya faɗi, yana Allah-Allah idan ba wani zancen nasu ta ji ba.
“Me zan ɓoye miki? Miyasa zuciyarki ta manta da waye Asim a duniyarta, taya Asim zai cuce ki, Asim be aure dan tsinkayar wani abu na gidan ku ba, shiyasa tun farko ban so na aure ki saboda na san zaki yi tunanin saboda haka na aure ki”
Jikinta ya mutu, hawayen da taga yana zuba a idon Asim ya tsayar da nata hawayen, a take ta manta da zargin da take masa, wani irin son sa da ƙaunarsa suka mamaye mata zuciya.
MORNING UPDATED
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
_Write by_
*Khadeeja Candy*
*PAGE - 39*
NOT EDITED ⚠
Ko da ya isa gida, Kalsoom na zaune a balcony tana zaman jiransa, hankalinta ya tashi sosai, ji take kamar itace a halin da Rashida take ciki.
Tana ganin yayi parking, ta tashi da sauri ta ƙarasa inda yake ta buɗe masa motar.
»“Ya jikinta? Da sauƙi?”
Ido ya sakar mata kamar yau ya fara ganinta, be ce mata komai ba kuma be kashe motar ba, balle ma ya fito. Ita kuma duk ta tsorata, gabanta sai faɗuwa yake kar ta ji mummunan labari.
“Dan Allah ka min magana mana”
Ta masa maganar irin tana daf da yin kuka. Sai a sannan ya kashe motar ya fito, ya ɗora kansa saman na ta, ya kai hannu ya riƙe hannunta yana sauke ajiyar zuciya.
“Da sauƙi ta samu bachi”
“Amman ka kira gida ka faɗa musu?”
“Na faɗa”
“Sun zo?”
“Sun zo”
“Allah ya bata lafiya, amman dai be zube duka ba ko?”
Har cikin ƙasan zuciyarta take jin son Asim, sam bata iya gani illarsa, saboda zuciyarta tana muradinsa, a take zuciyarta ta fara raya mata ya ɓoye mata maganar kuɗin wata ƙila saboda karta sa ci suna da kuɗi, kuma ita kanta bata san yadda yayi ya samun kuɗin adashen ba, sai dai abunda ya faɗa a wacan lokacin ya tsaya mata a rai, a duk lokacin data tuna sai ta ji babu daɗi, har zuciyarta ta zarge shi akan haka.
HILAL POV.
A haukace ya isa asibiti, dan a tunaninsa Rashida ta mutu, shi da kansa ya kai ta emergency room, tare da taimakon wasu Nurses ya shiga neman numfashinta.
Da taimakon Allah komai ya daidaita, sannan ya ɗaura mata drip, yayi mata allurar. Tsaye yayi cikin ɗakin yana kallonta bayan Nurses ɗin sun fita.
Wayarsa ya shiga lalabe sam ya manta da tana ciki mota, sai yanzu. Fita yayi be daɗe ba ya dawo tare da rigar asibiti da wasu kayan aiki, sai ya canja mata tufafin jikinta, ya gyara mata jikinta sannan ya saka mata rigar, sai ya kira wata ma'aikaciyar gurin mai share-share ta kwashe kayan.
Zaunawa yayi a gurin ya ɗafa kansa, sai ga wasu daga cikin abokan aikinsa sun shigo duba ta, sama-sama ya amsa musu, suma sun ga damuwa ƙarara a fuskarsa, sun lura da yanayinsa, duk a tunaninsu saboda Madam bata da lafiya ne.
Fatan sauƙi suka mata sannan suka fita, shi kuma ya tashi yaje gurin motarsa ya ɗauki wayarsa ya kira Hajiyarsa ya faɗa mata, sannan ya kira Momy ita ma ya faɗa mata.
A cikin motar ya shiga ya zauna ya tasa abunda ke masa daɗi duniya, baya son yaransa su san komai a tsakanin su, kuma be san wane bayani zai yi ma Hajiyarsa ba da Momy, sam baya son duniya tasan abunda Rashida ta aikata, sai dai kuma be san yadda zai yi yayi ya ɓoye ba, cox he's no more to her.
Be ɗago kansa daga tunanin da yake ba, wayarsa tayi ringing, number Momy ce a rikice take tambayarsa wane ɗaki Rashida take.
Sai da ya buɗe Motar ya fito sannan ya amsa ta.
“Kin shigo Asibitin ne ?”
“Eh ina emergency”
“Okay tsaya a gurin zan ƙaraso yanzu”
Ya kashe wayar tare da rufe motar, sannan ya nufi gurin da yake zaton take. Tun daga nesa ya hango ƙannenta biyu. Cikin rashin kuzari ya ƙarasa inda suke ya gaishe ta, su kuma ƙannen suka gaishe shi. Sannan ya wuce dasu zuwa ɗakin da take.
Ganin halin da take cikin yasa Momy har ta fara hawaye, kallon ta kawai Hilal yayi yana ayyana irin abunda zata ji idana kace mata ƴarta na ɗauke da cuta mai ƙaryar garƙuwar jiki.
“Momy karku taɓa ta, ko da ta farka ne”
“Toh amman mi ya same ta haka ne?”
“Ta samu Miscarriage ne”
“Subhanallahi Allah ya bata lafiya”
“Amin”
Ya koma ya jingina da bangon ɗakin yana kallonta, ɗaya daga cikin ƙanwarta ta warware carpet ɗin da suka zo da shi ta shinfiɗa a gurin. Ta miƙawa Hilal Kujera, sai kawai ya girgiza mata kai.
“No Thanks”
A gurin yayi ta tsayi har Hajiya ta iso, ita sai da ta kira shi, yaje ya taho da ita sai suka gaisa da Momy, ta duba ta tayi mata fatan sauƙi sannan ta fito. Tare suka jero da ɗanta sai gaisuwar girmamawa ake mata, dan kowa ya ganta ya ga Hilal yasan itace mahaifiyarsa.
“Yanzu haka baƙin kishi ne ta sawa kanta, gashi yanzu kun yi losing wannan baby”
Shi dai be ce komai ba, ya buɗe mata Mota. sai da ta shiga, ta zauna sannan yayi mata sai da safe direba ya wuce da ita, shi kuma ya juyo ya dawo cikin asibitin.
Lokacin daya dawo, sai ya zauna saman gadon kusa da ita, babu abunda yake kallon sai fuskarta, rayuwarta da tasa yake ta tunani, irin yadda suka so junansu har suka haifi ƴaƴansu, yanzu kuma lokaci ɗaya komai yana shirin sauya musu, he just can't believe ace Rashida ta ci amanarsa da wani, haƙiƙa yana da tambayoyin da suke buƙatar amsa daga gareta.
“Ai da ka tashi kaje gida, tun da ga mu muma ai mun isa mu kula da ita”
Can ciki ya ji muryar Momy tana masa magana. Sai ya tashi cikin rashin ƙwarin jiki yayi musu sai da safe ya fice.
NAMRA POV.
Daga asibitin sai ta wuce bank, layi ta bi sai da ka kai gareta sannan tayi checking balance ɗinta, dubu ɗari huɗu ta hansin ta gani, a tunaninta ko Anty Amarya ta ƙaro mata wasu ne, sai kawai ta cire kuɗin gaba ɗaya, cikin farinciki da jindaɗi.
Kamin ta isa gida sai ta ta fara biyawa ta gidan dillaliya, ta ƙirga kuɗinta ta bata, sannan tasa a kira mutumen da yayi musu wacan rubutun yayi masu sheida saboda wata rana.
Sauran kuɗin daya rage mata sai taje kasuwa ta siye kuloli, da ƴan wasu kayan aiki da basu kai sun kawo ba, data dawo gida sai ta wanke kuloli ta siye abincin ta nufi asibitin da shi.
Ta jidaɗin ganin Asim a tsaye yana ɗan takawa, Mama na tiƙe da shi, suna zuwa ƙarshen ɗakin suna dawowa, wani farinciki ne ya mamayeta, bata san lokacin data aje kulolin ba ta tsaya tana kallonsu.
Hamdala take yi ma Allah cikin ranta, tana jindaɗin yadda taga mijin nata yau ya fara taka ƙasa, Mama ma farinciki take sosai daman ta fi kowa son haka dan zaman asibitin ya isheta.
Sun kusa minti latalin suna, suna zagaye ɗakin sannan Mama ta zaunar da shi saman gado.
“Allah ya bi da lafiya ya ƙara sauki”
Ita da Asim suka haɗa baki gurin amsawa da Ameen. Sannan ta zuwa ya fice.
Namra ta kalli Asim da far'ah a fuskarta.
“Da nice nace za kayi wannan yawo zaka ce min ba aka iya ba”
Ɗan murmushi yayi, shi kansa yana cikin jindaɗi a yau.
“Alhamdullillah, ban zaci zan iya ba”
“Ai babu abunda za a iya matuƙar aba'a gwada ba, Allah ya nuna min ka tashi ka koma kamar yadda kake”
“Ameen”
Ta kwantar da kanta saman jikinsa. Shi kuma yayi shiru yana nazarin rayuwarsa, irin mutanen da sukajuya masa baya yake lissafi a zuciyarsa, ace har abokansa da yake ganin sun kai amman kowa ya kasa takowa ya zo ganinsa
“Hmmm”
Ya furta a fili, yana sauke ajiyar zuciya. Sai Namra ta kalleshi
“lafiya?”
“Lafiya ƙalau, kawai ina tunanin tafiyarki ne, Mama tace karki je yanzu, idan ma wani abun ne ai aiko miki kawai, kuma ki faɗa wata komai ta waya kawai, tama kira ba ki nan”
Shuru Namra tayi bata ce komai ba, sai dai maganar tasa bata mata daɗi ba. Hannu ya kai ya shafa ta.
“Namra have you ever noticed that Anty bata taɓa kira kai tsaye da sunan jin jikina ba? Haba Namra ai ko wani na kashe musu sa ɗaga min ƙafaa balle auren ƴar su na ke, abun nan ya ɓata ran Mama sosai, nima shiyasa a duk lokacin dana ga ɓacin rai a fuskarta sai nawa rai ya ɓace, daman irin wannan ake gudu aje ayi aure a kasa samun kwanciyar hankali”
Shiru tayi tana taɓin hannunta, ita kanta tasan iyayenta basu kyauta ba, akan abunda aka yi mata kuma Asim yana da gaskiya kan abunda yake faɗa, tasan Abbah kam ba zai zo ganinsa ba, amman ya kamata ace ko Maryam ce ta zo ganinta, ganin yadda suke da ita jini ɗaya, amman ko waya bata taɓa bugo mata ba.
Anya ta cancanci su juya mata baya har haka?
Ba su da wani excuse akan haka, sai dai a yanzu bata son ta zurfafa amincinta ga Asim tun bayar maganar su da taji da Mama.
Kamar ya san abunda yake ransa, sai kawai ya rumgume ta.
“Ina son ki, kuma bana tunanin akwai abunda zai raba ni da ke, ina son na ɗanɗana miki rayuwar da baki taɓa mfarkin shigarta ba, irin rayuwar jindaɗin da tafi ta gidan ku, sai dai ina gudun ranar da zaki rabu da ni saboda wani baƙin talauci ko mugu abu ya same ni”
“Ba zan taɓa rabuwa da kai ba Asim na maka alƙawari, ko a wane hali na samu kai na, zan zama mai biyayyah a gare ka, zan maka sadaukarwar da ba kowa ce mace ce zata iya ba, son nuna maka son da ba kafai ake samun irinsa ba.
Sai dai ni zuciyarta ta kasa Aminta da kai, kana ɓoye min wani abu naka Asim”
Gabansa ya faɗi, yana Allah-Allah idan ba wani zancen nasu ta ji ba.
“Me zan ɓoye miki? Miyasa zuciyarki ta manta da waye Asim a duniyarta, taya Asim zai cuce ki, Asim be aure dan tsinkayar wani abu na gidan ku ba, shiyasa tun farko ban so na aure ki saboda na san zaki yi tunanin saboda haka na aure ki”
Jikinta ya mutu, hawayen da taga yana zuba a idon Asim ya tsayar da nata hawayen, a take ta manta da zargin da take masa, wani irin son sa da ƙaunarsa suka mamaye mata zuciya.
MORNING UPDATED
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
_Write by_
*Khadeeja Candy*
*PAGE - 39*
NOT EDITED ⚠
Ko da ya isa gida, Kalsoom na zaune a balcony tana zaman jiransa, hankalinta ya tashi sosai, ji take kamar itace a halin da Rashida take ciki.
Tana ganin yayi parking, ta tashi da sauri ta ƙarasa inda yake ta buɗe masa motar.
»“Ya jikinta? Da sauƙi?”
Ido ya sakar mata kamar yau ya fara ganinta, be ce mata komai ba kuma be kashe motar ba, balle ma ya fito. Ita kuma duk ta tsorata, gabanta sai faɗuwa yake kar ta ji mummunan labari.
“Dan Allah ka min magana mana”
Ta masa maganar irin tana daf da yin kuka. Sai a sannan ya kashe motar ya fito, ya ɗora kansa saman na ta, ya kai hannu ya riƙe hannunta yana sauke ajiyar zuciya.
“Da sauƙi ta samu bachi”
“Amman ka kira gida ka faɗa musu?”
“Na faɗa”
“Sun zo?”
“Sun zo”
“Allah ya bata lafiya, amman dai be zube duka ba ko?”