Sashe 167
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan abunda Abbah ya faɗa sai Anty ta ɗora da nata nasihar akan rayuwa da kuma zaman aure kamar yadda tayi mata a can gida. Abbah ma sai da ya kara mata da wani abu, sannan suka mata sallama saboda yau zasu koma, aiko nan Namra tasa musu kuka kamar zasu yi rabuwar har abada har Anty sai da tayi kuka, sai da Ummi ta shigo.ta fita da ita sannan ta tsagaita kuka da take. Sai dai Hajiya Sadiya kan har aka koma gida kuka take, a motar Hajiya Mairo ke ce mata ta barsa da Allah ai ga amana nan ta fara kamashi, a tunaninta Hajiya Sadiya tana kuka ne saboda ƙazafin da Asim yayi mata.
Ko da suka isa gidan ana shirye-shiye fara walimar da Ummi ta shirya zata yi, wasu tufafin Ummi ta ɗauko ma Namra sanna aka kora Mai Makeup cikin ƙanƙanen lokaci da canja mata kamanin zuwa na amare, sannan ta ɗaura mata ɗankwali.
Fauza da Haleema ne suka riƙa hannun Namra suka fita da ita gurin walimar suka zaunar da ita a muhallin da aka tanada na zaman Amarya. Kowa ya fita zuwa gurin Walimar banda Hajiya Sadiya da ke ƙunshe cikin ɗakin tana aikin kuka, sai kuma Ummi dake cikin gida tana gyara wasu abubuwan, sai da Hajiya Sadiya ta tabbatar hankalin kowa yana can gurin walimar sannan ta suɗaɗa ta fita ta bar gidan gaba ɗaya.
Anyi walima lafiya, kuma an tashi kowa na sam barka da yabawa. Bayan mutane sun watse ne Ummi tasa Namra a mota ita da su Maryam da Raihanatu da kuma Gwaggo Ramatu aka maida su masaukinsu tare da sauran mutane da suka zo walima, bayan sun koma gida ne Namra take labarta musu abunda ya faru.
ASIM POV.
Babu mai mota a cikinsu kasancewar Mai Martaba shi ya aika aka ɗaukosu hara Asim ɗin, a dole tasa sai da suka fita masarautar gaba ɗaya sannan suka samu Napep suka hau, sauran kuma suka hau wata Napep ɗin ana shawarar inda za a kai shi, wasu su ce asibiti wasu kuma su ce gida ya kamata a barshi albashi sai a fidda masa konon rantsuwar da yayi. Daker aka shiga Napep ɗin da shi saboda ƙafafunsa da basa tafiya, ko da suka isa fida a wahale yake saboda shi kaɗai yasan abunda yake ji a jikinsa.
A falon Amarya aka aje shi a take ta bada kuɗi aka je aka siyo gero aka cire masa kono sai dai abunda basu gane ba ai ba shi yayi rantsuwarba, shi isgili yayi na cewar kada Allah ya tashe shi lafiya idan har ƙarya yayi. Babu irin kuka da Mardiya ba tayi ba sai nanata zancen take wai daman tasan haka zai faru tun da yace be sake ta bayan kuma ya san ya sake ta.
Ganin har rana ta faɗi babu wani sauyi, yasa suka ɗauke shi zuwa asibiti, ana kiran magariba aka bashi gado, likitoci suka shiga bashi taimakon gaggawa, sannan suka tura shi ɗakin hoto. Allura suka masa a nan ya samu bachi.
***
Ƙarfe tara dai-dai aka jera motoci ƙofar gidan da su Namra suke wato masaukinsu. Hajiya Shafa da wasu family na mai Martaba suka shiga ciki suka yi bikon amarya da kuɗi da kuma siyayya.
Ana guda aka fito da Namra tana cikin lifaya fuskarta a lulluɓe, sai ƙamshin turare take.
Barorinta suka buɗe mata mota ta shiga sai aka maida ƙofar motar aka rufe, sai sauran suka shiga sauran motocin, aka akama hanyar gidan Mai Martaba da ita, lokacin da aka shiga da ita faɗar Mai Martaba na shaƙe da mutane da kuma talakawa, sai ta yi gaisuwar ban girma Mai Martaba yayi musu addu'a sannan aka shiga ɗakin ɗayar matarsa tayi musu addu'ah sannan aka yi canji mutane da wato mutanen da suka je bikonta ba su zasu raka ta ɗakinta ba.
Ko da aka isa da ita ɗakinta shaɗaya har ta gota, babu wanda beyi mamakin ganin irin gidan da aka kaita ba duk kuwa da kasancewar dare ne, baka iya banbance shi da rana saboda hasken da gidan ke da shi, yanayin gidan zuwa fenti da kwaliyar gidan duka irin na masarautarsu ne yayi, wani abun burgewa kuma yadda aka ƙawata gidan da komai fari kamar fentin gidan, wato furnitures da aka zubawa Namra komai fari ne har labulayenta, da center carpet, kai har agogon bangonta fari ne, duk inda suka yi masu camera na biye suna ɗauka, tun farkon fitowarta har zuwa gaisuwa da kuma kawo ta gidan.
A ɗakin da yafi ko wannne haɗuwa aka kaita, kasancewar ɗakuna biyar ne a gidan kuma ko wanne sai da aka saka masa kaya, sai ta hau tsakiyar gadon ta zauna, kanta lulluɓe da mayafi.
Wasu daga dangin ango suka mata Allah sa albarka suka fice, sannan wasu daga ƴan'uwanta suka kama hanya, sai aka bar Maryam kawai sai Raihanatu da kuma wata ƴar'uwarsu Husaina.
Bayan kamar minti talatin sai suka soma jin busa da algaita da kirari irinta ta ƴaƴan sarakuna, shi ma mai nasa video yana biye da shi yana ɗauka. Har aka shigo da shi cikin ɗakin, sai ya zauna bakin gado yana ƙamshin turare, fuskarsa ta sha rawani kamar Mahaifinsa. Abokaninsa sai zolayarasa suke shi ko bakinsa har kunne.
Nasiha suka musu akan zamantakewar aure da kuma haƙuri, masu auren cikinsu sai zolayar samarin suke, wasu kuma na zolayar Abdool wai ango sai sha mai. Sai da suka ga shabiyu ta gota sannan suka musu addu'ah da fatan alheri, sannan suka saka Maryam da waɗanda suke tare gaba, har wasu na cewa suna son Maryam a zatonsu budurwa ce.
[8/5, 7:03 PM] Khadeeja Candy♥: *96*
Bayan abokansa sun wuce Abdool ya tashi ya rufe ƙofor falo ya dawo ɗakin fuskarsa da murmushi, rawanin kansa ya fara cirewa ya aje sannan cire babbar rigarsa.
“Amaryata wacce ta wacce amarya tsada”
Ya kai hannu zai yaye gyalenta, sai ta matsa baya ta ƙara jan gyalen ya sauko. Matsawa yayi kusa da ita ya sake miƙa hannun sai ta kauce hannunta mai zanen lalle ta ziro masa. Murmushi yayi yasa hannunsa aljihu ya ɗauko wani ɗan ƙaramin box ya ɗora mata saman hannu, sai ya miƙa hannun ya yaye mata mayafin. Idonta a rufe fuskarta ɗauke da murmushi
“Har da idon sai na siya...?”
“Ai kace wannan amaryar ta fi ko wace Amarya tsada”
Murmushi ya sake yi sai ya cire tsadadden agogon hannunsa ya ɗora mata saman hannu, sai a lokacin ta buɗe ido ta saka su cikin nashi haƙoranta a washe.
“Kin manta ban siye murmushin ba”
“Maganar ma ai baka siya ba an yi maka nasiha ne kawai”
Hannu ya kai ya riƙa gefen fuskarta yana shafa shi da babban yatsansa.
“Godiya ga Ubangijin da ya mallaka min wannan halittar, lallai na fi ko wane Namiji sa'a a duniyar nan”
“Kana koɗa Namra da yawa, har kana sa tana jin kamar ta fi ko wace mace zama sarauniya”
“Na haɗu da mata da yawa ciki da wajen ƙasar nan amman babu wacce ta sace min zuciya sai Namra, she ko ma ƙaramar sarauniyace ba”
Lumshe ido tayi tana murmushi. Box ɗin ya amsa ya buɗe ya fiddo zobe mai kyau ya kama hannunta ya saka mata.
“I Love you so Much Abnam”
“Na gode sosai”
Matsawa yayi kusa da ita.
“Godiya kawai? Ai hausawa na cewa yaba kyauta tukuici”
Ta rufe fuskarta domin ta gano ma'anar zancensa. Shi ma dariyar ya yi, ya jata ƙirjinsa ya rumgume, a hankali ya sauke numfashi ya ɗora kansa kaman nata.
“Gani komai nake kamar a mafarki, ina tuna lokacin da na fara ganinki irin halin rayuwar da na shiga saboda ke kuma gashu yanzu komai ya zama tarihi, inshallah ni ne mijinki ke kuma matana har Aljanna”
Lafewa ta yi a ƙirjinsa kamar babu wanzuwarta a doron ƙasa, gudun zuciyarsa take sauraren tana auna yada nata zuciyar yake hawa da sauka tare da ta shi.
Sun daɗe a haka sannan ya ɗagota ya mata kiss saman ido.
“Karki min bachi saman jiki kisa na ƙarye”
Tayi dariya tana bugar masa chest.
“Ouuuuch”
Ya faɗa yana kanne mata ido ɗaya. Shi ya fara sauka saman gadon sannan ya miƙa mata hannun, ta riƙa hannunsa ta sauƙo suka shiga bathroom ɗin tare, shi ya fara alwalar sannan ya taimaka mata ita ma tayi suka fito. Sallaya biyu ya shinfiɗa ɗaya a gaba ɗayar kuma tana baya da shi kaɗan.
Mayafinta ya ɗauka ta rufe jikinta kasancewar fafaɗa ne kuma mai kauri. Yana gaba tana biye har suka yi raka'ah biyu, sannan suka sallame. Hannunsa ya ɗaga masa ya riƙa kwaroro musu addu'ah tana amsawa da amin sanna suka shafa, sai ya juyo ya kalleta.
“Hajiya Akwai wata sunnar bayan wannan?”
Ta zare masa ido. Sai ta gurgiza masa kai alamar a'a. Dariya yayi ya tashi ya ɗauko ledojin da gefen gadon ya kawo gabanta ya aje, sannan ya fita daga ɗaga ɗakin gaba ɗaya. Be ɗauki dogon lokaci ba sai gashi ya dawo da plate da cup ta aje a gabanta sannan ya zauna yaja ledar ya buɗe ya fido ƙatuwar kaza ta ɗora saman plate ɗin sai ya mayardar ragowar gajin a gefe ɗaya, ya buɗe madara ya zuba musu a cup ɗaya sannan yasa hannu ɓare kazar ya soma kai mata a baki. Kawar da fuska ta yi tana murmushi.
“Ki taimaki bawan Allah nan ki bar shi ya ciyarda dake a wannan daren da yafi ko wane dare muhimmanci da daraja a gareshi”
“Na hutar da kai, zan iya wannan aikin”
“Ai bana son hutun ne, idan dare ya lula ke da kanki zaki min kukan gajiya ki neman na hutar da ni, amman ba yanzu ba yanzu ai ai ba aiki na ke ba”
Ko da suka isa gidan ana shirye-shiye fara walimar da Ummi ta shirya zata yi, wasu tufafin Ummi ta ɗauko ma Namra sanna aka kora Mai Makeup cikin ƙanƙanen lokaci da canja mata kamanin zuwa na amare, sannan ta ɗaura mata ɗankwali.
Fauza da Haleema ne suka riƙa hannun Namra suka fita da ita gurin walimar suka zaunar da ita a muhallin da aka tanada na zaman Amarya. Kowa ya fita zuwa gurin Walimar banda Hajiya Sadiya da ke ƙunshe cikin ɗakin tana aikin kuka, sai kuma Ummi dake cikin gida tana gyara wasu abubuwan, sai da Hajiya Sadiya ta tabbatar hankalin kowa yana can gurin walimar sannan ta suɗaɗa ta fita ta bar gidan gaba ɗaya.
Anyi walima lafiya, kuma an tashi kowa na sam barka da yabawa. Bayan mutane sun watse ne Ummi tasa Namra a mota ita da su Maryam da Raihanatu da kuma Gwaggo Ramatu aka maida su masaukinsu tare da sauran mutane da suka zo walima, bayan sun koma gida ne Namra take labarta musu abunda ya faru.
ASIM POV.
Babu mai mota a cikinsu kasancewar Mai Martaba shi ya aika aka ɗaukosu hara Asim ɗin, a dole tasa sai da suka fita masarautar gaba ɗaya sannan suka samu Napep suka hau, sauran kuma suka hau wata Napep ɗin ana shawarar inda za a kai shi, wasu su ce asibiti wasu kuma su ce gida ya kamata a barshi albashi sai a fidda masa konon rantsuwar da yayi. Daker aka shiga Napep ɗin da shi saboda ƙafafunsa da basa tafiya, ko da suka isa fida a wahale yake saboda shi kaɗai yasan abunda yake ji a jikinsa.
A falon Amarya aka aje shi a take ta bada kuɗi aka je aka siyo gero aka cire masa kono sai dai abunda basu gane ba ai ba shi yayi rantsuwarba, shi isgili yayi na cewar kada Allah ya tashe shi lafiya idan har ƙarya yayi. Babu irin kuka da Mardiya ba tayi ba sai nanata zancen take wai daman tasan haka zai faru tun da yace be sake ta bayan kuma ya san ya sake ta.
Ganin har rana ta faɗi babu wani sauyi, yasa suka ɗauke shi zuwa asibiti, ana kiran magariba aka bashi gado, likitoci suka shiga bashi taimakon gaggawa, sannan suka tura shi ɗakin hoto. Allura suka masa a nan ya samu bachi.
***
Ƙarfe tara dai-dai aka jera motoci ƙofar gidan da su Namra suke wato masaukinsu. Hajiya Shafa da wasu family na mai Martaba suka shiga ciki suka yi bikon amarya da kuɗi da kuma siyayya.
Ana guda aka fito da Namra tana cikin lifaya fuskarta a lulluɓe, sai ƙamshin turare take.
Barorinta suka buɗe mata mota ta shiga sai aka maida ƙofar motar aka rufe, sai sauran suka shiga sauran motocin, aka akama hanyar gidan Mai Martaba da ita, lokacin da aka shiga da ita faɗar Mai Martaba na shaƙe da mutane da kuma talakawa, sai ta yi gaisuwar ban girma Mai Martaba yayi musu addu'a sannan aka shiga ɗakin ɗayar matarsa tayi musu addu'ah sannan aka yi canji mutane da wato mutanen da suka je bikonta ba su zasu raka ta ɗakinta ba.
Ko da aka isa da ita ɗakinta shaɗaya har ta gota, babu wanda beyi mamakin ganin irin gidan da aka kaita ba duk kuwa da kasancewar dare ne, baka iya banbance shi da rana saboda hasken da gidan ke da shi, yanayin gidan zuwa fenti da kwaliyar gidan duka irin na masarautarsu ne yayi, wani abun burgewa kuma yadda aka ƙawata gidan da komai fari kamar fentin gidan, wato furnitures da aka zubawa Namra komai fari ne har labulayenta, da center carpet, kai har agogon bangonta fari ne, duk inda suka yi masu camera na biye suna ɗauka, tun farkon fitowarta har zuwa gaisuwa da kuma kawo ta gidan.
A ɗakin da yafi ko wannne haɗuwa aka kaita, kasancewar ɗakuna biyar ne a gidan kuma ko wanne sai da aka saka masa kaya, sai ta hau tsakiyar gadon ta zauna, kanta lulluɓe da mayafi.
Wasu daga dangin ango suka mata Allah sa albarka suka fice, sannan wasu daga ƴan'uwanta suka kama hanya, sai aka bar Maryam kawai sai Raihanatu da kuma wata ƴar'uwarsu Husaina.
Bayan kamar minti talatin sai suka soma jin busa da algaita da kirari irinta ta ƴaƴan sarakuna, shi ma mai nasa video yana biye da shi yana ɗauka. Har aka shigo da shi cikin ɗakin, sai ya zauna bakin gado yana ƙamshin turare, fuskarsa ta sha rawani kamar Mahaifinsa. Abokaninsa sai zolayarasa suke shi ko bakinsa har kunne.
Nasiha suka musu akan zamantakewar aure da kuma haƙuri, masu auren cikinsu sai zolayar samarin suke, wasu kuma na zolayar Abdool wai ango sai sha mai. Sai da suka ga shabiyu ta gota sannan suka musu addu'ah da fatan alheri, sannan suka saka Maryam da waɗanda suke tare gaba, har wasu na cewa suna son Maryam a zatonsu budurwa ce.
[8/5, 7:03 PM] Khadeeja Candy♥: *96*
Bayan abokansa sun wuce Abdool ya tashi ya rufe ƙofor falo ya dawo ɗakin fuskarsa da murmushi, rawanin kansa ya fara cirewa ya aje sannan cire babbar rigarsa.
“Amaryata wacce ta wacce amarya tsada”
Ya kai hannu zai yaye gyalenta, sai ta matsa baya ta ƙara jan gyalen ya sauko. Matsawa yayi kusa da ita ya sake miƙa hannun sai ta kauce hannunta mai zanen lalle ta ziro masa. Murmushi yayi yasa hannunsa aljihu ya ɗauko wani ɗan ƙaramin box ya ɗora mata saman hannu, sai ya miƙa hannun ya yaye mata mayafin. Idonta a rufe fuskarta ɗauke da murmushi
“Har da idon sai na siya...?”
“Ai kace wannan amaryar ta fi ko wace Amarya tsada”
Murmushi ya sake yi sai ya cire tsadadden agogon hannunsa ya ɗora mata saman hannu, sai a lokacin ta buɗe ido ta saka su cikin nashi haƙoranta a washe.
“Kin manta ban siye murmushin ba”
“Maganar ma ai baka siya ba an yi maka nasiha ne kawai”
Hannu ya kai ya riƙa gefen fuskarta yana shafa shi da babban yatsansa.
“Godiya ga Ubangijin da ya mallaka min wannan halittar, lallai na fi ko wane Namiji sa'a a duniyar nan”
“Kana koɗa Namra da yawa, har kana sa tana jin kamar ta fi ko wace mace zama sarauniya”
“Na haɗu da mata da yawa ciki da wajen ƙasar nan amman babu wacce ta sace min zuciya sai Namra, she ko ma ƙaramar sarauniyace ba”
Lumshe ido tayi tana murmushi. Box ɗin ya amsa ya buɗe ya fiddo zobe mai kyau ya kama hannunta ya saka mata.
“I Love you so Much Abnam”
“Na gode sosai”
Matsawa yayi kusa da ita.
“Godiya kawai? Ai hausawa na cewa yaba kyauta tukuici”
Ta rufe fuskarta domin ta gano ma'anar zancensa. Shi ma dariyar ya yi, ya jata ƙirjinsa ya rumgume, a hankali ya sauke numfashi ya ɗora kansa kaman nata.
“Gani komai nake kamar a mafarki, ina tuna lokacin da na fara ganinki irin halin rayuwar da na shiga saboda ke kuma gashu yanzu komai ya zama tarihi, inshallah ni ne mijinki ke kuma matana har Aljanna”
Lafewa ta yi a ƙirjinsa kamar babu wanzuwarta a doron ƙasa, gudun zuciyarsa take sauraren tana auna yada nata zuciyar yake hawa da sauka tare da ta shi.
Sun daɗe a haka sannan ya ɗagota ya mata kiss saman ido.
“Karki min bachi saman jiki kisa na ƙarye”
Tayi dariya tana bugar masa chest.
“Ouuuuch”
Ya faɗa yana kanne mata ido ɗaya. Shi ya fara sauka saman gadon sannan ya miƙa mata hannun, ta riƙa hannunsa ta sauƙo suka shiga bathroom ɗin tare, shi ya fara alwalar sannan ya taimaka mata ita ma tayi suka fito. Sallaya biyu ya shinfiɗa ɗaya a gaba ɗayar kuma tana baya da shi kaɗan.
Mayafinta ya ɗauka ta rufe jikinta kasancewar fafaɗa ne kuma mai kauri. Yana gaba tana biye har suka yi raka'ah biyu, sannan suka sallame. Hannunsa ya ɗaga masa ya riƙa kwaroro musu addu'ah tana amsawa da amin sanna suka shafa, sai ya juyo ya kalleta.
“Hajiya Akwai wata sunnar bayan wannan?”
Ta zare masa ido. Sai ta gurgiza masa kai alamar a'a. Dariya yayi ya tashi ya ɗauko ledojin da gefen gadon ya kawo gabanta ya aje, sannan ya fita daga ɗaga ɗakin gaba ɗaya. Be ɗauki dogon lokaci ba sai gashi ya dawo da plate da cup ta aje a gabanta sannan ya zauna yaja ledar ya buɗe ya fido ƙatuwar kaza ta ɗora saman plate ɗin sai ya mayardar ragowar gajin a gefe ɗaya, ya buɗe madara ya zuba musu a cup ɗaya sannan yasa hannu ɓare kazar ya soma kai mata a baki. Kawar da fuska ta yi tana murmushi.
“Ki taimaki bawan Allah nan ki bar shi ya ciyarda dake a wannan daren da yafi ko wane dare muhimmanci da daraja a gareshi”
“Na hutar da kai, zan iya wannan aikin”
“Ai bana son hutun ne, idan dare ya lula ke da kanki zaki min kukan gajiya ki neman na hutar da ni, amman ba yanzu ba yanzu ai ai ba aiki na ke ba”