Sashe 87
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ina jin saki uku ne, aure ba zai sake shiga tsakamin mu ba”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, miya kai shi aikata wannan babban kuskure? Har saki uku? Ai idan rai ya ɓace hankali baya gushewa, amman Hilal be yi ɗa ba, ai komai bincike yake so”
Ƙasa tayi da kanta tana kuka.
“Daddyn ki ba zai ji daɗin wannan lamarin ba, ana murna an yi abu sai gashi kuma ya zama na riƙici, ko da yake malamai sun ce idan saki uku aka yi shi a lokaci ɗaya za a iya ɗaukarsa a matsayin ɗaya”
“Ba furtawa yayi ba, a rubuce ya bani”
“Rubuta ya yi saki ɗaya, biyu, uku? Kalsoom bana son ki dawo xaman gidan nan ne, sannan duk wanda ya ji dalilin mutuwar auren ki ba zai aure ki ba, saboda wannan ɓacin suna ne. Nasan ba halin ki bane ko kin ji kin haɗu da mugayen ƙawaye ne masu kai mutum kai hallaka”
“Wallahi ban aikata ba, ke ma zargina kike ko?”
“Ba zargi bane Kalsoom kawai ina tsoron sherin zuciya ne, da kuma kishi, babu abunda basa sawa”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Allah kaɗai zai shede ni shi kaɗai zai shede ni da ban aikata ba”
“Ba zargin ki na ke ba Kalsoom, amman wannan lamarin abu ne mai sarƙaƙiya, ga abincinki ki ci”
Kai ta girgiza hawaye na mata zuba.
“Ki daure dai ki ci, Allah zai kawo mafita inshallah, wallahi wahala bata taɓa tabbata, kuma tun da har ya ci amanar ki sai Allah ya saka miki, Hilal butulu ne”
“Karki ga laifinsa Momi ni na nemi ya sake ni, a tunani na hakan shine mafita, ashe bala'i ne, ni ce na ce yayi min saki uku”
“Subhanallah Kalsoom ke kika jawa kan ki matsala, dam me zaki yi haka? Kin fi son ki dawo gida ki zauna tare da ni? Mutane da suka zage ki lokacin da aure yayi miki tsawaiko su sake buɗe miki sabon shafi? Kin tonawa kan ki asiri kowa zai ji dalilin fitar ki gidan miji, gashi ba saki ɗaya bane balle a gyara saki har uku wallahi baki da hankali Kalsoom kin yi wa kan ki, da wane ido zaki kalli baban ki? So kike ciwon zuciyarsa ya tashi ko?”
Ta ƙasara da kuka. Tana mai jin kamar ta kama Kalsoom ɗin tayi ta dukanta. Wani irin kuka Kalsoom take sai yanzu take nadamar abunda ta aikata.
“Ina takardar take?”
Momi ta katsa mata tsawo. Jikarta ta nunawa Momi tana cigaba da kuka. Tashi Momi tayi taje ta ɗauki jakar ta zazzage kayan ciki sai ga takardar ta faɗo, ita kanta ta ji wani ɗarrr kamar ka ta ɗauki takardar sai dai tana da buƙatar sanin ko saki nawa ne idan da gyara a gyara tun kowa be ji ba.
Warware takardar tayi tana karantawa. Wani dogon tsaki taja lokacin data gama karantawar ta jefa ma Kalsoom takardar ta fice tana faɗin.
“Yayi tunani da hankali wallahi...”
Sai da Kalsoom ta ci kukanta ta ƙoshi sannan ta ɗauki takardar tana dubawa cikin kuka.
_Idan na sake ki ina za ki? Wa kike tunanin zai aure ki a halin da kike ciki yanzu? Kowa yana zargin ki da kin kore Rashida kina son kashe ƴaƴata, saboda basu san dalilin sakinta da na yi ba._
_Zan miki uzuri Kalsoom akan abinda kika aikatawa ɗa na, saboda kin nuna musu so a can baya, xuciya bata da ƙashi, dukan abunda kika aikata dan kina so na ne, kina kishi na shiyasa kika aikata, kina ganin kamar ina son ƴaƴan da ba naki ba da yawa ko?_
_Ba zan sake ki ba, saboda naga so na a idonki, kina neman sakin ne saboda kina ganin kamar shine mafita a gareki ko? To ba zan sake ki ba, har abada haka zamu zauna da ke, amman ba zan sake barin ƴaƴana a tare da ke ba, ba zasu sake raɓar ki ba, saboda zuciyarki ta sauya a yanzu, kin tashi daga Kalsoom ɗin da nasan ki kin koma wata dabam, amman hakan ba zai hana na so ki ba, ba xai hana na xauna da ke ba, ina son ki sosai Kalsoom amman ban cancanci abinda kika min ba, nasan mace ce ke kina da rauni shiyasa kawai na ɗaga miki ƙafa_
_Idan kuma har sakin kike so da gaske sai ki kai ni kotu._
*Ur Faithful Husband*
Shine abinda ya rubuta daga ƙarshe cikin manyan harufa. Rumgume takardar tayi a ƙirjinta tana sauke ajiyar zuciyar da bata san lokacin data zo mata ba.
Wani sanyi ta ji ya saukar mata tun daga saman kai har ƙasan ƙafafunta, nan take ta nemi ciwon kanta da kuka da take ta rasa, wani irin ƙaunar Hilal ne ta ji ya ratsa zuciyarta.
Hijabinta da ta bari falo Momi ta jefa mata.
“Tashi ki koma ɗakin ki tun Mahaifin ki be dawo ba”
Buɗe ido tayi tana kallon Momi da murmushi a fuskarta babu ko kunya.
“Bari na yi sallah”
“Idan kin je can kya yi, amman wlh karki sake kuskure cewa ya sake ki, in ba dan Allah yasa yana da tunani ba ai da shikenan”
Bata musa ma Momi ba ta ɗauki hijabin Momi ta saka ta ɗauki takardar da jakarta ta fito falo ranta tasss kamar ba ita ce ta gama kuka ba. Har bakin gate Momi ta rakata tana mata gargadi, sai da ta hau Napep sannan Momi ta koma ciki tana yi Allah Hamdala tare da sawa Hilal albarka...
*NAMRA POV*
Sai da dare Asim ya dawo, kamar yadda ya saba, idan ka ganshi ba zaka ce shine ya fita da tsoro ba ɗazu, yau yayi ciniki shine sirrin farincikin na yau.
Ba laifi ya ɗan sake fuska ya shigo har da sallama, kamar ba shi ba. Ita kanta Namra da mamaki ta amsa masa sallamar tana ƙara kallon fuskarsa dan ta tantancesa. Ya zauna kusa da ita, yana shewa.(fito)
“Sannu da zuwa”
“Yauwa ya gidan?”
“Gida yana nan yadda ka bar shi, masu gidan ma sun zo guba abun su kuma sun ce mu tashi”
“What? To ina za mu koma? Ai kuɗin dana biya be ƙareba, ba zamu tashi ba wallahi”
“Su zaka faɗawa ba ni ba, ni dai na faɗa masa ya zo da safe ko da dare zai same ka”
“Bari ya zo ɗin amman wallahi ba zamu tashi ba, duk inda za a je sai dai aje, amman wannan iskancin ba zan ɗauke shi ba, haka kawai dan ina talaka sai a nemi wulakanta ni”
“Miye abun wulaƙanci dan masu guri sƴn nemi aba su abun su? Sai mu tashi mu basu gidan su, ni dai na roƙe su akan su bar mu mu zauna bq idan har basu yarda ba shikenan sai mu nemi wani gurin kuma”
“Ai kaji matsalar masu kuɗin nan, wallahi duk inda yake baya ƙaunar talaka”
“Ka cika mai da zazzaɓi ciwo Asim, yanzu sun san kai mai kuɗi ne ko talaka? Amman kasan babu talakan da zai iya kama gida kamar wannan ya zauna ko?”
“Sun san talaka nake mana tun da na zauna bq, nima lokaci na yana zuwa zan yi kuɗi har na mamaki”
“A haka za kayi kuɗi matarka tana cikin ƙunci? Ban taɓa ganin ragon namiji irin ka ba Asim, sai dai na girka na baka da ƙarfin ka da komai?”
“Dan Allah ki yi haƙuri Namra, kin ga ɗan aikin da nake be wuce na samu na shan ruwa ba, amman yanzu na samu wani aiki, sai dai aikin mai gidan ya faɗa min cikin gidan zan koma da zama saboda aike-aike idan sun taso, kuma a matsayin driver zai ɗauke ni kuma yaron gida, tun last week muka yi maganar amman nace ba zan kama aikin ba sai na ji ta bakin ki”
Ta jidaɗi dan tasan aikin ya fi wanda yake yi yanzu, sai dai maganar komawa can ne bata gane ba.
“Amman ka koma can har da ni? Ko ya”
“A'a ni kaɗai zan koma can saboda ya fi son ana kwana ta can”
“Amman kai ba aikin gadi ba ce kuma sai ka kwana ina ma laifin kaje da safe wuni”
“Ba kullum zan riƙa kwana can ba, ina jin wani lokaci ne kawai, kin ga ƙara mu samu mu riƙa wannan aikin kamin mu ga abinda Allah zai yi gaba kuma”
“Allah yasa haka shine mafi alheri”
“Amin ya rabb”
Ya rumgume ta yana murmushin jindaɗi, daman ya faɗa mata ne kawai dan ta karta daina ganinsa da dare, amman ko da tace bata aminta ba zai sa ya fasa aikin ba.
*ABDOOL POV*
Suna dinner yake nanatawa Ummi maganar siyen gidan da zai yi, but still bata yarda ba, duk da ta ga alamun da gaske yake.
“Wai mi za ka yi da gida daya ƙone har xaka siye shi 15m?”
“Just”
Ya faɗa yana ɗaga kafaɗu.
“Dude na bar maka, ko kyauta ma zan iya baka ma”
Amal ta faɗa jikin har rawa yake. Kallon Ummi Abdool yayi yadda take watsawa Amal harara yasa shi dariya, sai ya aje spoon ɗin hannunsa ya tashi ya ɗauki kofin tea ya wuce ɗakinsa. Haka kawai ya samu kansa da murmushi ba dalili.
Wata ƙaruwar durowa ya buɗe ya ɗauko wata ƴar ƙarmar jaka baƙa. Ya nufo part ɗin Ummi hannunsa ɗaya riƙe da tea ɗin.
Saman kujera ya jefar da jakar yana kallon Meesha dan ya yarda da natsuwarta.
“Aisha zo ki cire min 15m a nan, ko wanne 1m ne”
Dinning ɗin ta baro ta zo ta zauna saman kujera ta buɗe kuɗin ta fara ƙirgiwa har ta cire 15m, ta aje gefe.
“Ga su”
Sai ya kalli Ummi
“Ummi ga kuɗin”
“Abdallah ana ciniki dole ne? Na ce ba xa a siyar ba”
“Amman mai abu tace ta siƴar”
“Wai me za ka yi da gidan ne”
“Kawai ki sai da min”
“An siyar maka, shikenan?”
“Thank you”
Ya ɗauki ragowar kuɗin ya maida ɗakinsa. Saman madubi ya ɗora copin tea ɗin ya faɗa saman gaɗon zuciyarsa cike da nishaɗi.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, miya kai shi aikata wannan babban kuskure? Har saki uku? Ai idan rai ya ɓace hankali baya gushewa, amman Hilal be yi ɗa ba, ai komai bincike yake so”
Ƙasa tayi da kanta tana kuka.
“Daddyn ki ba zai ji daɗin wannan lamarin ba, ana murna an yi abu sai gashi kuma ya zama na riƙici, ko da yake malamai sun ce idan saki uku aka yi shi a lokaci ɗaya za a iya ɗaukarsa a matsayin ɗaya”
“Ba furtawa yayi ba, a rubuce ya bani”
“Rubuta ya yi saki ɗaya, biyu, uku? Kalsoom bana son ki dawo xaman gidan nan ne, sannan duk wanda ya ji dalilin mutuwar auren ki ba zai aure ki ba, saboda wannan ɓacin suna ne. Nasan ba halin ki bane ko kin ji kin haɗu da mugayen ƙawaye ne masu kai mutum kai hallaka”
“Wallahi ban aikata ba, ke ma zargina kike ko?”
“Ba zargi bane Kalsoom kawai ina tsoron sherin zuciya ne, da kuma kishi, babu abunda basa sawa”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Allah kaɗai zai shede ni shi kaɗai zai shede ni da ban aikata ba”
“Ba zargin ki na ke ba Kalsoom, amman wannan lamarin abu ne mai sarƙaƙiya, ga abincinki ki ci”
Kai ta girgiza hawaye na mata zuba.
“Ki daure dai ki ci, Allah zai kawo mafita inshallah, wallahi wahala bata taɓa tabbata, kuma tun da har ya ci amanar ki sai Allah ya saka miki, Hilal butulu ne”
“Karki ga laifinsa Momi ni na nemi ya sake ni, a tunani na hakan shine mafita, ashe bala'i ne, ni ce na ce yayi min saki uku”
“Subhanallah Kalsoom ke kika jawa kan ki matsala, dam me zaki yi haka? Kin fi son ki dawo gida ki zauna tare da ni? Mutane da suka zage ki lokacin da aure yayi miki tsawaiko su sake buɗe miki sabon shafi? Kin tonawa kan ki asiri kowa zai ji dalilin fitar ki gidan miji, gashi ba saki ɗaya bane balle a gyara saki har uku wallahi baki da hankali Kalsoom kin yi wa kan ki, da wane ido zaki kalli baban ki? So kike ciwon zuciyarsa ya tashi ko?”
Ta ƙasara da kuka. Tana mai jin kamar ta kama Kalsoom ɗin tayi ta dukanta. Wani irin kuka Kalsoom take sai yanzu take nadamar abunda ta aikata.
“Ina takardar take?”
Momi ta katsa mata tsawo. Jikarta ta nunawa Momi tana cigaba da kuka. Tashi Momi tayi taje ta ɗauki jakar ta zazzage kayan ciki sai ga takardar ta faɗo, ita kanta ta ji wani ɗarrr kamar ka ta ɗauki takardar sai dai tana da buƙatar sanin ko saki nawa ne idan da gyara a gyara tun kowa be ji ba.
Warware takardar tayi tana karantawa. Wani dogon tsaki taja lokacin data gama karantawar ta jefa ma Kalsoom takardar ta fice tana faɗin.
“Yayi tunani da hankali wallahi...”
Sai da Kalsoom ta ci kukanta ta ƙoshi sannan ta ɗauki takardar tana dubawa cikin kuka.
_Idan na sake ki ina za ki? Wa kike tunanin zai aure ki a halin da kike ciki yanzu? Kowa yana zargin ki da kin kore Rashida kina son kashe ƴaƴata, saboda basu san dalilin sakinta da na yi ba._
_Zan miki uzuri Kalsoom akan abinda kika aikatawa ɗa na, saboda kin nuna musu so a can baya, xuciya bata da ƙashi, dukan abunda kika aikata dan kina so na ne, kina kishi na shiyasa kika aikata, kina ganin kamar ina son ƴaƴan da ba naki ba da yawa ko?_
_Ba zan sake ki ba, saboda naga so na a idonki, kina neman sakin ne saboda kina ganin kamar shine mafita a gareki ko? To ba zan sake ki ba, har abada haka zamu zauna da ke, amman ba zan sake barin ƴaƴana a tare da ke ba, ba zasu sake raɓar ki ba, saboda zuciyarki ta sauya a yanzu, kin tashi daga Kalsoom ɗin da nasan ki kin koma wata dabam, amman hakan ba zai hana na so ki ba, ba xai hana na xauna da ke ba, ina son ki sosai Kalsoom amman ban cancanci abinda kika min ba, nasan mace ce ke kina da rauni shiyasa kawai na ɗaga miki ƙafa_
_Idan kuma har sakin kike so da gaske sai ki kai ni kotu._
*Ur Faithful Husband*
Shine abinda ya rubuta daga ƙarshe cikin manyan harufa. Rumgume takardar tayi a ƙirjinta tana sauke ajiyar zuciyar da bata san lokacin data zo mata ba.
Wani sanyi ta ji ya saukar mata tun daga saman kai har ƙasan ƙafafunta, nan take ta nemi ciwon kanta da kuka da take ta rasa, wani irin ƙaunar Hilal ne ta ji ya ratsa zuciyarta.
Hijabinta da ta bari falo Momi ta jefa mata.
“Tashi ki koma ɗakin ki tun Mahaifin ki be dawo ba”
Buɗe ido tayi tana kallon Momi da murmushi a fuskarta babu ko kunya.
“Bari na yi sallah”
“Idan kin je can kya yi, amman wlh karki sake kuskure cewa ya sake ki, in ba dan Allah yasa yana da tunani ba ai da shikenan”
Bata musa ma Momi ba ta ɗauki hijabin Momi ta saka ta ɗauki takardar da jakarta ta fito falo ranta tasss kamar ba ita ce ta gama kuka ba. Har bakin gate Momi ta rakata tana mata gargadi, sai da ta hau Napep sannan Momi ta koma ciki tana yi Allah Hamdala tare da sawa Hilal albarka...
*NAMRA POV*
Sai da dare Asim ya dawo, kamar yadda ya saba, idan ka ganshi ba zaka ce shine ya fita da tsoro ba ɗazu, yau yayi ciniki shine sirrin farincikin na yau.
Ba laifi ya ɗan sake fuska ya shigo har da sallama, kamar ba shi ba. Ita kanta Namra da mamaki ta amsa masa sallamar tana ƙara kallon fuskarsa dan ta tantancesa. Ya zauna kusa da ita, yana shewa.(fito)
“Sannu da zuwa”
“Yauwa ya gidan?”
“Gida yana nan yadda ka bar shi, masu gidan ma sun zo guba abun su kuma sun ce mu tashi”
“What? To ina za mu koma? Ai kuɗin dana biya be ƙareba, ba zamu tashi ba wallahi”
“Su zaka faɗawa ba ni ba, ni dai na faɗa masa ya zo da safe ko da dare zai same ka”
“Bari ya zo ɗin amman wallahi ba zamu tashi ba, duk inda za a je sai dai aje, amman wannan iskancin ba zan ɗauke shi ba, haka kawai dan ina talaka sai a nemi wulakanta ni”
“Miye abun wulaƙanci dan masu guri sƴn nemi aba su abun su? Sai mu tashi mu basu gidan su, ni dai na roƙe su akan su bar mu mu zauna bq idan har basu yarda ba shikenan sai mu nemi wani gurin kuma”
“Ai kaji matsalar masu kuɗin nan, wallahi duk inda yake baya ƙaunar talaka”
“Ka cika mai da zazzaɓi ciwo Asim, yanzu sun san kai mai kuɗi ne ko talaka? Amman kasan babu talakan da zai iya kama gida kamar wannan ya zauna ko?”
“Sun san talaka nake mana tun da na zauna bq, nima lokaci na yana zuwa zan yi kuɗi har na mamaki”
“A haka za kayi kuɗi matarka tana cikin ƙunci? Ban taɓa ganin ragon namiji irin ka ba Asim, sai dai na girka na baka da ƙarfin ka da komai?”
“Dan Allah ki yi haƙuri Namra, kin ga ɗan aikin da nake be wuce na samu na shan ruwa ba, amman yanzu na samu wani aiki, sai dai aikin mai gidan ya faɗa min cikin gidan zan koma da zama saboda aike-aike idan sun taso, kuma a matsayin driver zai ɗauke ni kuma yaron gida, tun last week muka yi maganar amman nace ba zan kama aikin ba sai na ji ta bakin ki”
Ta jidaɗi dan tasan aikin ya fi wanda yake yi yanzu, sai dai maganar komawa can ne bata gane ba.
“Amman ka koma can har da ni? Ko ya”
“A'a ni kaɗai zan koma can saboda ya fi son ana kwana ta can”
“Amman kai ba aikin gadi ba ce kuma sai ka kwana ina ma laifin kaje da safe wuni”
“Ba kullum zan riƙa kwana can ba, ina jin wani lokaci ne kawai, kin ga ƙara mu samu mu riƙa wannan aikin kamin mu ga abinda Allah zai yi gaba kuma”
“Allah yasa haka shine mafi alheri”
“Amin ya rabb”
Ya rumgume ta yana murmushin jindaɗi, daman ya faɗa mata ne kawai dan ta karta daina ganinsa da dare, amman ko da tace bata aminta ba zai sa ya fasa aikin ba.
*ABDOOL POV*
Suna dinner yake nanatawa Ummi maganar siyen gidan da zai yi, but still bata yarda ba, duk da ta ga alamun da gaske yake.
“Wai mi za ka yi da gida daya ƙone har xaka siye shi 15m?”
“Just”
Ya faɗa yana ɗaga kafaɗu.
“Dude na bar maka, ko kyauta ma zan iya baka ma”
Amal ta faɗa jikin har rawa yake. Kallon Ummi Abdool yayi yadda take watsawa Amal harara yasa shi dariya, sai ya aje spoon ɗin hannunsa ya tashi ya ɗauki kofin tea ya wuce ɗakinsa. Haka kawai ya samu kansa da murmushi ba dalili.
Wata ƙaruwar durowa ya buɗe ya ɗauko wata ƴar ƙarmar jaka baƙa. Ya nufo part ɗin Ummi hannunsa ɗaya riƙe da tea ɗin.
Saman kujera ya jefar da jakar yana kallon Meesha dan ya yarda da natsuwarta.
“Aisha zo ki cire min 15m a nan, ko wanne 1m ne”
Dinning ɗin ta baro ta zo ta zauna saman kujera ta buɗe kuɗin ta fara ƙirgiwa har ta cire 15m, ta aje gefe.
“Ga su”
Sai ya kalli Ummi
“Ummi ga kuɗin”
“Abdallah ana ciniki dole ne? Na ce ba xa a siyar ba”
“Amman mai abu tace ta siƴar”
“Wai me za ka yi da gidan ne”
“Kawai ki sai da min”
“An siyar maka, shikenan?”
“Thank you”
Ya ɗauki ragowar kuɗin ya maida ɗakinsa. Saman madubi ya ɗora copin tea ɗin ya faɗa saman gaɗon zuciyarsa cike da nishaɗi.