Sashe 7
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A fusace ya juya ya fice. Anty Amarya ban da hawaye babu abunda take, sam bata ga laifin Abbah ba, dan tana ganin duk abunda yayi mata ita taja, ita ma kanta kwatankwacin abunda zata iya yi mata kenan, dan bata ga dalilin aibanta Uzair ba dan kawai bata son sa, kasa cewa komai ta yi ta juya cike da baƙinciki ta nufi ɗakinta.
Namra kan na risine gurin tana kuka, Maryam da Aisha na bata haƙuri.
Babu wanda zai fahimce ta saboda babu wanda yaga abunda ta gani, kuma bata da wata sheda da zata nuna.
Hajiya Barau ce ta ɗauki zancen tana yayatawa, wai Namra ta yi ma Uzair ƙazafi dan kawai bata son ta aure shi. Cikin sati maganar ta zagaye familyn su. Wasu kan sun yarda duba da irin kuɗin da suka taso masa lokaci ɗaya, sai dai kyakkyawan halinsa da mutane ke gani ya shafe wacan baƙin fentin da wasu suke ganin Namra ta shafa masa.
Hakan da Namra tayi ba ƙaramin sosa ran Uzair yayi ba, ko ba komai ta ɓata masa suna ta wani ɓangare, ga kuma rashin jutuwa daya samu da Matarsa Yasmin.
A ƴan kwana kin nan sai shiga cikin dangi yayi masa wuya, gani yake kamar sun yarda da abunda Namra ta faɗa, a waya wasu ke kiransa suna nuna masa abunda Namra ta yi bata kyauta ba, wasu har da yi mata Allah ya isa. Amman ita kan Yasmin ko a jikinta, sai ma sha'aninta take kamar abun be dame ta ba.
Babu irin faɗan da mahaifiyarsa bata masa akan ya janye maganar auren nan, amman ya ƙi saboda Abbah yaƙi bashi damar hakan.
“Uzairu ka janye zancen auren nan, ka faɗa maka, duk fa mutumin da yayi maka haka toh ko kashe ka zai iya yi, wannan ƙazafin data maka zai iya shafar har aikinka, ni ban taɓa ganin maƙiyiyi kamar Namra ba, ace ɗan'uwanka,
Aiko kama da gaske ne ka rufa masa asiri”
“Babu komai Umma Allah zai saka min, sai ta ga abunta inshallah”
“Allah dai ya isar maka, amman abun nan ya ɓata min rai matuƙa Wallahi, kai ma dai da hange-hange kake mi Namra take da shi daya fi na Yasmin har kake son aurenta”
“Wallahi Umma tun lokacin dana auri Yasmin ina jin son Namra, kuma wannan walimar da akayi na haddatan ƙur'ane kin san har da ita ciki, shiyasa naji na kwaɗaitu da zama mijinta dan na samu mai bawa ƴaƴana tarbiya, tun da ni da Yasmin ba wani dogon ilmin Islama ne da mu ba, sam ban tsammaci abun zai zama haka ba”
“Toh ai ko ilminta ya zama na banza tun da har ta iya yi ma ɗan'uwanta wannan ƙazafin”
Haka dai suka yi ta hirar Namra Hajiya Binta na tsine mata har aka kira Azahar.
A masallacin gidan yayi sallah, sannan ya koma ciki yayi ma mahaifiyarsa sallama ya fice. Babu abunda yake ji a ransa sai tsanar Namra, ji yake ko kashe ta yayi ba zai huce abunda tayi masa ba.
A dai-dai gate ɗin gidan su Amira yayi parking, sai ya fita ya taka da ƙafa, ya ƙwanƙwasa ƙofar gate ɗin. Mai gadi ne ya leƙo yana tambayar.
“Wanene?”
“Dan Allah Amira na ciki?”
“Eh tana ciki”
“Dan Allah yi min sallama da ita”
“Toh wa zan ce mata?”
“Ce mata manager ne”
Daga haka ya juyo ya dawo gurin motarsa, ya ciro wayarsa yana ƴan danne-danne. Ba a ɗauki dogon lokaci ba sai ga Mai gadin ya dawo yana faɗin
“Wai tace tana zuwa”
Tsayuwarsa ya gyara, yana kallon ƙofar gidan har ta fito.
Cikin rangwaɗa da isa take tafiya har ta ƙaraso kusa da shi da sallama.
“Maraba da sarauniyar kyau, gimbiyar mata, kuma adon mata, nasan ba ki san ni ba amman ni na san ki”
“Na sanka mana, ba kai bane Cousin ɗin Namra”
“I'm glad you remember”
“So what brought you here?”
“Ke ai ba sai kin tambaya ba, mace kyakkyawa irin ki mai hankalin da tarbiya, ai dole ne ta riƙa samun masu ziyartar ta a duk lokaci, son ki ne ya kawo ni, zuciyata ta kasa haƙura da ke na kasa haɗeye yawuna a kan ki, shiyasa kika gan ni a ƙofar gidan ku”
Cikin salon jan hankali yake maganar yana murmushi. Ita kuma sai wani yauƙi take abun ka da mata.
“Na ji matashin darasin ne kawai amman ban fahimcin karatun da yake cikinsa ba”
“Zan miki bita, na kuma fassara miki inda baki gane ba idan har mafaraucin zai samun ganin Gimbiya anjima?”
Shiru tayi tana fari da ido.
“Sai ka shigo, kuma idan ka zo karka tsaya a waje ka shiga harabar gidan, kar ka wuce ƙarfe tara”
“Consider it done my lady”
Buɗe motarsa yayi ya ɗauko bandur ɗin 1k ya miƙa mata.
“Ki shiga da wannan, zan yi farinciki”
A yadda ya karanceta be yi zaton zata karɓa ba, a take murmushi ya bayyana a fuskarta, tasa hannun biyu ta karɓa tana masa godiya
“Na gode sosai”
“Never mention it again, my regards to mom please”
Fari ta ƙara masa da ido
“Sure”
Ta juya ta shige. Wani shu'umin murmushi yayi ya buɗe motarsa ya shiga.
KALSOOM POV.
SIX MONTHS LATER.... Tun da ta dawo daga Seminar take bachin gajiya, ta taje aiki ta dawo sai bachi. Ga kuma ɓacin ran dake tare da ita, da tunani, dan ko ranar da zata tafi seminar ɗin sai da Dad yayi mata jan kunne akan ta kame kanta, ya sake maimata mata irin zagin da ake masa na yaƙi aurar da ita ya barta tana aiki sai yawa take gare gare, Babu kuma yadda zai hana ƴarsa aiki, dan da shi take yima kanta wasu laluraron ba dan kuma ya kasa ɗaukar nauyinta ba, sai dan rashin auren da bata tayi ba, idan har yace zai hanata aiki sai yaga kamar be mata adalci ba, kuma zai tauye mata haƙƙi damuwa zata mata yawa.
Sai dai burin iyaye ne suga sun aurar da ƴarsu sai idan hakan be samu ba, yadda zamani ya lalace komai girman ɗan ka dole ne kasa mishi ido gudun kar ɓata gari su lalata maka shi, musamman ƴa mace.
Ita kanta wani lokancin ba son zuwa seminer take ba, sai dai babu yadda ta iya tun da haka kamfamin MTN ya tsarawa ma'aikatansa.
A ɗayan ɓangare kuma tana ganin kamar iyayenta ba su yarda da ita bane, shiyasa suke takura mata da da yawan tambihi a duk lokacin da zata nisanta da su.
Tana ji a ranta har yanzu iyayenta ba su gama karantar ta bane, dan ta ɗaukarwa kanta alƙwarin duk irin sha'awar dake damunta da son auren da take ba zata taɓa aikata zina ba.
Da yamma ta tashi bachi, bayan ta ci abinci ta koma ɗakinta ta buɗe system tana duba wasu abubuwan. A ɗakin Momy ta same ta tana labarta mata hukuncin da mahaifinta ya yankena haɗata aure da Cousin ɗin ta Abubakar.
Gabanta ya faɗi, duk yadda take son aure bata jin zata iya auren Abubakar, mutumen da duk a familynsu an buga masa tambarin neman matan banza, neman mata kawai yasa ma gaba shiyasa auren ma kwata-kwata baya gabansa gashi yanzu har ya girmi tazurai, ba dan kuma ya rasa matar aure ba.
A cikin yanayin damuwa ta kalli Momy tace
“Amman Momy mi yasa ba'a nemi shawara na ba, kamin ku yanke wannan hukuncin?”
“Yayi hakan ne dan yasan ba zaki bashi kunya ba, kuma ba mahaifinki bane yayi masa magana, mahaifinsa na yayi ma Abbanki magana da amincewar Abubakar ɗin”
Girgiza kai tayi
“Gaskiya ni ba zan iya aurensa ba”
Wannan maganar da Kalsoom tayi ta fusata Momy har tasa ta canja fuska.
“Haba Kalsoom ana son a samu kiyi aure sai kuma kice ba zaki iya aurensa ba? Toh idan ba shi ba kina da wani wanda zaki iya fitarwa a yanzu ne? Ba zaki bar ruwan idon nan ba ko?”
Hannu biyu tasa ta dafe kanta. Sai yaushe Momy zata fahimcin matsalarta ne? Kullum cewa take tana ruwan ido, taƙi ta tsayar da miji, alhalin ba ruwan ido bane, duk mazajen babu na aure ko wanne da tasa matsalar.
Dagowa tayi ta kalli Momy tace
“Yanzu dan kawai ina son aure sai ace duk wanda ya zo min sai na aura? Abunda nake it not calling ruwan ido it calling carefully planning for the future”
Momy ta taɓe baki
“Yanzu dai idan kunya zaki bawa mahaifinki sai kiyi, naji ma yana faɗar baya son aja abun da nisa ina jin ba zaki wuce wata biyu a gida ba idan har kin yarda, kuma ni ban san Abubakar da wani mugun hali ba, yana da rufi asiri yana da kyau kuma baya shaye-shaye, neman mata ne kawai shi ma kuma bamu tabbatar ba tun da bamu taɓa kama shi yana yi ba,
Kuma yanzu ai da wahala ace maza basu san mace ba, ko kuma basu taɓa aikata zina ba, wata ƙila ma idan ya aure ki zai daina”
Idon Kalsoom ya cika da ƙwallah, ganin yadda Momy take gyara Abubakar dan kawai ta aure shi.
“Idan kuma be daina ba, ƴarki zata cutu, Momy kisa wannan a zuciyarki”
Momy ta dafata
“Kiyi auren dan ibada Kalsoom, kuma ki auri Abubakar da zuciya ɗaya”
Tashi Momy tayi ta fice, ta bar Kalsoom cikin tunani da neman zaɓin Allah.
____________________________
Masu karantawa a blogger ina ganin ku fa, amman baku comments, sometimes zan samu mutum 200+ sun leƙa website ɗin amman ba ku comments. Yadda kuka ga Wattpad haka Blogger yake zai nuna masu karantawa, amman babu Comments, ina fatar zaku gyara.
http://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa06.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
Ƴan Taskar Khadeeja Candy wannan shafi na ku ne. Ina jindaɗin Comments ɗin ku keep it up.🌺
*PAGE - 6*
NAMRA POV.
Namra kan na risine gurin tana kuka, Maryam da Aisha na bata haƙuri.
Babu wanda zai fahimce ta saboda babu wanda yaga abunda ta gani, kuma bata da wata sheda da zata nuna.
Hajiya Barau ce ta ɗauki zancen tana yayatawa, wai Namra ta yi ma Uzair ƙazafi dan kawai bata son ta aure shi. Cikin sati maganar ta zagaye familyn su. Wasu kan sun yarda duba da irin kuɗin da suka taso masa lokaci ɗaya, sai dai kyakkyawan halinsa da mutane ke gani ya shafe wacan baƙin fentin da wasu suke ganin Namra ta shafa masa.
Hakan da Namra tayi ba ƙaramin sosa ran Uzair yayi ba, ko ba komai ta ɓata masa suna ta wani ɓangare, ga kuma rashin jutuwa daya samu da Matarsa Yasmin.
A ƴan kwana kin nan sai shiga cikin dangi yayi masa wuya, gani yake kamar sun yarda da abunda Namra ta faɗa, a waya wasu ke kiransa suna nuna masa abunda Namra ta yi bata kyauta ba, wasu har da yi mata Allah ya isa. Amman ita kan Yasmin ko a jikinta, sai ma sha'aninta take kamar abun be dame ta ba.
Babu irin faɗan da mahaifiyarsa bata masa akan ya janye maganar auren nan, amman ya ƙi saboda Abbah yaƙi bashi damar hakan.
“Uzairu ka janye zancen auren nan, ka faɗa maka, duk fa mutumin da yayi maka haka toh ko kashe ka zai iya yi, wannan ƙazafin data maka zai iya shafar har aikinka, ni ban taɓa ganin maƙiyiyi kamar Namra ba, ace ɗan'uwanka,
Aiko kama da gaske ne ka rufa masa asiri”
“Babu komai Umma Allah zai saka min, sai ta ga abunta inshallah”
“Allah dai ya isar maka, amman abun nan ya ɓata min rai matuƙa Wallahi, kai ma dai da hange-hange kake mi Namra take da shi daya fi na Yasmin har kake son aurenta”
“Wallahi Umma tun lokacin dana auri Yasmin ina jin son Namra, kuma wannan walimar da akayi na haddatan ƙur'ane kin san har da ita ciki, shiyasa naji na kwaɗaitu da zama mijinta dan na samu mai bawa ƴaƴana tarbiya, tun da ni da Yasmin ba wani dogon ilmin Islama ne da mu ba, sam ban tsammaci abun zai zama haka ba”
“Toh ai ko ilminta ya zama na banza tun da har ta iya yi ma ɗan'uwanta wannan ƙazafin”
Haka dai suka yi ta hirar Namra Hajiya Binta na tsine mata har aka kira Azahar.
A masallacin gidan yayi sallah, sannan ya koma ciki yayi ma mahaifiyarsa sallama ya fice. Babu abunda yake ji a ransa sai tsanar Namra, ji yake ko kashe ta yayi ba zai huce abunda tayi masa ba.
A dai-dai gate ɗin gidan su Amira yayi parking, sai ya fita ya taka da ƙafa, ya ƙwanƙwasa ƙofar gate ɗin. Mai gadi ne ya leƙo yana tambayar.
“Wanene?”
“Dan Allah Amira na ciki?”
“Eh tana ciki”
“Dan Allah yi min sallama da ita”
“Toh wa zan ce mata?”
“Ce mata manager ne”
Daga haka ya juyo ya dawo gurin motarsa, ya ciro wayarsa yana ƴan danne-danne. Ba a ɗauki dogon lokaci ba sai ga Mai gadin ya dawo yana faɗin
“Wai tace tana zuwa”
Tsayuwarsa ya gyara, yana kallon ƙofar gidan har ta fito.
Cikin rangwaɗa da isa take tafiya har ta ƙaraso kusa da shi da sallama.
“Maraba da sarauniyar kyau, gimbiyar mata, kuma adon mata, nasan ba ki san ni ba amman ni na san ki”
“Na sanka mana, ba kai bane Cousin ɗin Namra”
“I'm glad you remember”
“So what brought you here?”
“Ke ai ba sai kin tambaya ba, mace kyakkyawa irin ki mai hankalin da tarbiya, ai dole ne ta riƙa samun masu ziyartar ta a duk lokaci, son ki ne ya kawo ni, zuciyata ta kasa haƙura da ke na kasa haɗeye yawuna a kan ki, shiyasa kika gan ni a ƙofar gidan ku”
Cikin salon jan hankali yake maganar yana murmushi. Ita kuma sai wani yauƙi take abun ka da mata.
“Na ji matashin darasin ne kawai amman ban fahimcin karatun da yake cikinsa ba”
“Zan miki bita, na kuma fassara miki inda baki gane ba idan har mafaraucin zai samun ganin Gimbiya anjima?”
Shiru tayi tana fari da ido.
“Sai ka shigo, kuma idan ka zo karka tsaya a waje ka shiga harabar gidan, kar ka wuce ƙarfe tara”
“Consider it done my lady”
Buɗe motarsa yayi ya ɗauko bandur ɗin 1k ya miƙa mata.
“Ki shiga da wannan, zan yi farinciki”
A yadda ya karanceta be yi zaton zata karɓa ba, a take murmushi ya bayyana a fuskarta, tasa hannun biyu ta karɓa tana masa godiya
“Na gode sosai”
“Never mention it again, my regards to mom please”
Fari ta ƙara masa da ido
“Sure”
Ta juya ta shige. Wani shu'umin murmushi yayi ya buɗe motarsa ya shiga.
KALSOOM POV.
SIX MONTHS LATER.... Tun da ta dawo daga Seminar take bachin gajiya, ta taje aiki ta dawo sai bachi. Ga kuma ɓacin ran dake tare da ita, da tunani, dan ko ranar da zata tafi seminar ɗin sai da Dad yayi mata jan kunne akan ta kame kanta, ya sake maimata mata irin zagin da ake masa na yaƙi aurar da ita ya barta tana aiki sai yawa take gare gare, Babu kuma yadda zai hana ƴarsa aiki, dan da shi take yima kanta wasu laluraron ba dan kuma ya kasa ɗaukar nauyinta ba, sai dan rashin auren da bata tayi ba, idan har yace zai hanata aiki sai yaga kamar be mata adalci ba, kuma zai tauye mata haƙƙi damuwa zata mata yawa.
Sai dai burin iyaye ne suga sun aurar da ƴarsu sai idan hakan be samu ba, yadda zamani ya lalace komai girman ɗan ka dole ne kasa mishi ido gudun kar ɓata gari su lalata maka shi, musamman ƴa mace.
Ita kanta wani lokancin ba son zuwa seminer take ba, sai dai babu yadda ta iya tun da haka kamfamin MTN ya tsarawa ma'aikatansa.
A ɗayan ɓangare kuma tana ganin kamar iyayenta ba su yarda da ita bane, shiyasa suke takura mata da da yawan tambihi a duk lokacin da zata nisanta da su.
Tana ji a ranta har yanzu iyayenta ba su gama karantar ta bane, dan ta ɗaukarwa kanta alƙwarin duk irin sha'awar dake damunta da son auren da take ba zata taɓa aikata zina ba.
Da yamma ta tashi bachi, bayan ta ci abinci ta koma ɗakinta ta buɗe system tana duba wasu abubuwan. A ɗakin Momy ta same ta tana labarta mata hukuncin da mahaifinta ya yankena haɗata aure da Cousin ɗin ta Abubakar.
Gabanta ya faɗi, duk yadda take son aure bata jin zata iya auren Abubakar, mutumen da duk a familynsu an buga masa tambarin neman matan banza, neman mata kawai yasa ma gaba shiyasa auren ma kwata-kwata baya gabansa gashi yanzu har ya girmi tazurai, ba dan kuma ya rasa matar aure ba.
A cikin yanayin damuwa ta kalli Momy tace
“Amman Momy mi yasa ba'a nemi shawara na ba, kamin ku yanke wannan hukuncin?”
“Yayi hakan ne dan yasan ba zaki bashi kunya ba, kuma ba mahaifinki bane yayi masa magana, mahaifinsa na yayi ma Abbanki magana da amincewar Abubakar ɗin”
Girgiza kai tayi
“Gaskiya ni ba zan iya aurensa ba”
Wannan maganar da Kalsoom tayi ta fusata Momy har tasa ta canja fuska.
“Haba Kalsoom ana son a samu kiyi aure sai kuma kice ba zaki iya aurensa ba? Toh idan ba shi ba kina da wani wanda zaki iya fitarwa a yanzu ne? Ba zaki bar ruwan idon nan ba ko?”
Hannu biyu tasa ta dafe kanta. Sai yaushe Momy zata fahimcin matsalarta ne? Kullum cewa take tana ruwan ido, taƙi ta tsayar da miji, alhalin ba ruwan ido bane, duk mazajen babu na aure ko wanne da tasa matsalar.
Dagowa tayi ta kalli Momy tace
“Yanzu dan kawai ina son aure sai ace duk wanda ya zo min sai na aura? Abunda nake it not calling ruwan ido it calling carefully planning for the future”
Momy ta taɓe baki
“Yanzu dai idan kunya zaki bawa mahaifinki sai kiyi, naji ma yana faɗar baya son aja abun da nisa ina jin ba zaki wuce wata biyu a gida ba idan har kin yarda, kuma ni ban san Abubakar da wani mugun hali ba, yana da rufi asiri yana da kyau kuma baya shaye-shaye, neman mata ne kawai shi ma kuma bamu tabbatar ba tun da bamu taɓa kama shi yana yi ba,
Kuma yanzu ai da wahala ace maza basu san mace ba, ko kuma basu taɓa aikata zina ba, wata ƙila ma idan ya aure ki zai daina”
Idon Kalsoom ya cika da ƙwallah, ganin yadda Momy take gyara Abubakar dan kawai ta aure shi.
“Idan kuma be daina ba, ƴarki zata cutu, Momy kisa wannan a zuciyarki”
Momy ta dafata
“Kiyi auren dan ibada Kalsoom, kuma ki auri Abubakar da zuciya ɗaya”
Tashi Momy tayi ta fice, ta bar Kalsoom cikin tunani da neman zaɓin Allah.
____________________________
Masu karantawa a blogger ina ganin ku fa, amman baku comments, sometimes zan samu mutum 200+ sun leƙa website ɗin amman ba ku comments. Yadda kuka ga Wattpad haka Blogger yake zai nuna masu karantawa, amman babu Comments, ina fatar zaku gyara.
http://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa06.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
Ƴan Taskar Khadeeja Candy wannan shafi na ku ne. Ina jindaɗin Comments ɗin ku keep it up.🌺
*PAGE - 6*
NAMRA POV.