← Book details Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 128 OF 173

Sashe 128

Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Zan sa ana ma min jirgin da zai je Katsina gobe da wuri zan sauka dan jin ko minene”

“To Allah yasa mu ji alheri, Amman da ka kira Abdulraman (Baban ɗansa) kun je tare, kar ka je kai kaɗai”

Ya ɗora ƙafarsa ɗaya saman ɗaya, Yana sosa gemunsa da hannunsa.

“A'a da Larai zan je (Anty Amarya)”

Uffan Hajiya Barau bata ce ba, dan maganar bata mata daɗi ba, sai kawai ta miƙe tsaye ta fice daga falon.

___________________________________________

There are no words to explain how sorry I am. Nasan duk abunda zan faɗa muku ba zaku yarda ba, wallahi i'm kind of busy those days, ku yi Hakuri dan Allah ku gafarta min Love you all Fisabilliah 🌹

I dedicate this chapter to Hajiya Ramatu, Mrs tijjani, My Asmee, Ahmad Ismael. I really did not know how will to write in words! But your gesture is such 😘 Thank you very much Allah ya ƙara arziki, ya bar zumunci.♥️
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *76*

“Me kike a nan?”

Ya tambaya yana haɗe fuska. Bayanta ta nuna ba tare data juya ba, sai dai bata san abunda zata faɗa masa ba. Ya nunata da phone ɗinsa.

“ I know kin karanta wasiƙar nan Yasmin”

Still wata kalma bata fito daga bakinta, wani kallo take masa kamar mai nazari. Raɓawa yayi gefenta zai wuce sai kuma tsaya yana kallonta ido cikin ido.

“Ba sai mun yi playing wannan game ɗin, nasan ke lauyer ce”

Da kallon mamaki ta bishi, ta kasa gasgata abunda kunnuwanta da idanunta suka ji mata. Me yake nufi da Namra bata zame masa matsala ba ita ba zata zame masa ba? Wacece ita? Da waya yake waya?

Da sauri ta rufa masa, sai ta same shi sitting room ya haɗa kansa da guiwa ya dafe. Tsaye tayi masa aka.

“Me waɗannan abubuwan suke nufi Uzair? Wacece wannan ? Mi kuka aikata kai da Namra? Da wa kake waya?”

Ɗagowa yayi ya kalleta, idonsa sun kaɗe alamar damuwa da ɓacin rai na tare da shi lokaci ɗaya.

“Miyasa kike son saka kanki ga abunda idan kika ji zai iya zame miki matsala? Miya kike son saka kanki ga abunda be kamata ya dame ki ba?”

Ya tambaya muryar ƙasa ƙasa kar ba komai. Zama tayi kusa da shi tana masa kallon mamaki.

“Ni matarka ce Uzair, damuwarka damuwata ce, Namra kuma ƴar'uwata ce, be kamata ka ɓoye min komai ba, please tell me maybe i can help”

ya shafa fuskarsa yana cikama bakinsa iska.

“Is about some business da zamu yi da yayanta, shine take min sheri, shine nace Namra bata zame min matsala ba ita zata zame min yarinyar da ta yi min ƙazafin Luwaɗi”

Wani ɗan murmushi tayi mai cike da rainin hankali, shi kansa ya fuskanci hakan.

“To be frank i read the message, Uzair you can't hide the truth jus...”

Yayi saurin riƙa hannayenta jikinsa a mace.

“Yasmin trust me please, kin san ina son ki”

“Ba maganar so ko ƙi muke a nan ba”

“Just promise me ba zaki bar ni ba”

Hawaye sun zubo mata.

“Idan har zargina ya tabbata a kan ka dole ne zan rabu da kai, ba zan iya zama da mutuemn daya zaɓi saɓon Allah sama da tsoronsa ba, mutumen daya zaɓi zubar da mutuncin iyalansa, zan iya yafe son da nake maka Uzair”

Ya girgiza mata yana ƙara damƙe hannunta cikin nasa.

“No Wallahi sherin sheɗan ne Yasmin, ba da son raina na aikata ba, kuma duk zugar su Najeeb ce, kuma nayi ne dan na kare kai na daga cin mutuncin da Namra ta yi min”

Maganarsa ta sha banban da tunaninta, ita gun data dosa daban shi kuma maganar da yake mata daban.

“Me ka aikata Uzair?”

Ya saki hannayenta.

“Ina ruwanki da abunda na aikata ne Yasmin?”

Ya faɗa a tsawace, sai kuma ya dafe kansa ya miƙe tsaye ya nufi windo.

“Ki tsaya a matsayin ki na matata Yasmin, zai fi miki”

Ta miƙe.tsaye itama cikin ɓacin rai.

“Yes zai fi min idan na rabu da Azzalumin mutun irinka, tirr da halin ka Uzair, ina kotu ina cases ashe akwai babban Case a gidana, nayi nadamar Auren ka a yau nayi nadamar daka kasance a cikin zuri'ar mu, nayi nadamar da ka zama uban ƴaƴana, ashe gaskiya Namra take faɗa, amman ka murje ido ka ƙaryatata...”

Ya juyo a fusace yana nuna saman kamta da ɗan tsayansa.

“Ke je ki faɗawa duniya nine na sace Namra, ni na haɗa kai da amiyarta aka mata asiri ya koma kan ƙawarta, amman karki manta ɗan'uwanki kika tonawa Asiri, kuma mahaifinta zai karɓe komai nasa daga hannuna, but i'm still your husband Yasmin the love of your life kuma uban ƴaƴanki biyu, asirina asirinki ne, kuma tona min asiri kamar tonawa kanki ne da ƴaƴanki”

“Ka buɗe shafin da ban san da shi ba Uzair, ashe kai ka sace ta? Sannan ka haɗa kai da amiyarta ka mata asiri? Wane irin zuciyane da kai Uzair? Wata ƙila ma ita ka aikata mata irin abunda ka aikatawa ɗan ka, you raped your very own son Uzair Allah yayi tirr da halinka”

Dariya ya soma yi ya doso inda take.

“Allah ya faɗa acikin matan ku akwai maƙiyanku, sai yanzu na gane kan ayar nan, amman ke babbar maƙiyiya tace Yasmin, ki rasa abunda zaki zarge ni da shi sai wannan? Kina da wata hujja ne? Ke daina ganin ke lawyer ce zan iya maka ki kotu, akan wannan mummunar kalma da kika jefe ni da ita, ai ko da gaske na aikata masa be kamata ki fito ki jefe ni da wannan maganar ba, idan ma na masa ina ruwanki ɗan ki ne?”

“Shiyasa bana burge ka ko? Baka da time ɗina, saboda ba mata bane a gabanka maza ne, mu kwana gado ɗaya mu tashi amman baka yarda ka bani haƙƙi na ba, da na maka magana, ka ce baka da lafiya, ko na cika desire, ashe kasan abunda kake aikatawa, kasan irin hukuncin da Allah ya tanadarwa masu irin wannan aikin kuwa? Cewa aka ƴi idan an kama su a jefosu daga saman bene su faɗo ƙasa, ko kuma a samu dutse a buga musu a kai, miye bana da shi ne Uzair? Wace hasara ce ta cin maka na neman maza ƴan'uwanka? Uzair me kake ji idan ka neme su?”

Hannayenta ya kama, ya faɗi ƙasan gwuiwoyinsa.

“Ki rufa min asiri Yasmin, ki taimaki rayuwata, kar kowa taji maganar nan, na miki alƙawarin ba zan ƙara ba, kuma zam je nasa a kare asirin dake kan Amira i promise, Yasmin ki dubi girman Allah ki yafe min, sherin zuciya ne, da zama da miyagun abokai”

Kuka da take ne ya ƙaru.

“Ka cutar da yarinyar nan Uzair, kasa mahaifinta da duniya suka zargi ta gudu taje gurin saurayinta ne, sanadinka kowa a familyn mu ya tsane ta, duk halin da ta shiga kai ne Uzair”

“Ki yi ta tunanin wasu har ki manta da ni, ki rufa asirin wasu ni ki tona nawa, idonki yayi ta rufewa akaina har maƙota suji abunda na aikata”

“Ba maƙota kaɗai zasu ji ba, duniya ce zata ji, sai duniya tasan wanene kai, sai kowa yasan abunda ka aikata”

Ya miƙe tsaye

“Wallahi duk kika bari wannan maganar ta fita, sai kin yi nadamar zuwanki duniya, sai kin gwammace kiɗa da karatu, kuma komai na zama ni mijin Yasmin ne, ai komai yana da buƙatar uzuri da bincike, kije duk abunda zaki aikata ki aikata ɗan shege ka fasa, indai kotu kike taƙama da ita sai na nuna miki baki san komai ba akan aikin ki”

“Haka ka ce?”

“Wanda duk yaƙi ji aiba zai ƙi gani ba”

“Baka bani mamaki ba, daman masu aikata irin aikinka ai basa da kunya, kuma basa tsoron Ubangijinsu balle jama'a tirr da halinka, wallahi sai na ƙwatowa Namra haƙƙinta, sai ka raina kan ka Uzair”

“Ni mijinki kike faɗawa haka?”

“Kai mijina ne zaka taka min bayan ɗa?”

“Sai ki fito fili ki faɗa mana, kice ɗana zaki min ƙazafi, ba wai ki raɓa da Namra ba, aikin banza kaiwai... Mtssssswww”

Yaja wani dogon tsaki ya wuce daga falon kamar walƙiya. Ita kamar jiran take ya fita, ta shiga ɗakinta ta zari mayafi ta, ta goyawa Mai mata reno little Namra, ta kama hannun Adnan suka fice.

NAMRA POV.

Da hawayw ta shiga cikin gidan, sai dai kasancewar dare ne, kuma babu wutar nefa a gidan shi ya hana su gane akwai hawaye a fuskar Namra, da wannan tayi nasarar shigewa ɗaki ta kife saman kafitar tana kukanta a hankalin ta yadda ita kaɗai zata iya jin sautin kukanta.

Da sallama Anty Amarya ta shiga cikin gidan, sai duk suka haɗa baki gurin amsa mata, gaisuwa ce ta biyo baya, sannan ta ɗora da tambayar Namra, duk kallon rashin sani suka mata, ko wanne abunda zuciyarsa ta bashi, wata ce ta tare da Yarima, wata ƙila taƙi ta saurareshi ne shiyasa ya turo wata.

“Eh tana nan ciki lafiya?”

Lamido ya tambaya. Cikon murya mai kamar ta kuka Anty Amarya ta ce

“Dan Allah ku yin magana da ita...”

Kamar an jefo Namra haka ta fito daga cikin ɗakin, tana ganin Anty Amarya ta rumtse idonta ta damƙe hannayenta gam, tana maimaita.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”

Saboda ta kasa yarda da abunda kunnuwanta da idonta suke nuna mata, ji take kamar mafarki take kuma ba mafarkin ba ne. Ta buɗe ido ta ƙarasa gaɓan Anty Amarya ta kama hannayenta, ta taɓa ta murja ta sake kallon fuskarta, sai kawai ta rumgume ta fashe da kuka.
Anty Amarya ma kuka take, ita da Namra aka rasa mai rarrashin wani, su kam su Neina sai kallon ikon Allah suke. Kuka sosai Anty Amarya da Namra ke yi kamar an muutuwa, sannan Namra ta zube ƙasan kafafunta ya kama kafafun Anty Amarya.

“Ki yafe min Anty, na tuba dan Allah ki yafe min, ki roƙi Abbah ya yafe min, haƙƙinku ma ta bina Anty, dan Allah ki roƙa min Abbah ya yafe min”
Chapter 128 · 0% Book details