Sashe 163
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jin an buga ƙofa yasa tayi saurin janye hannunta daga fuskarsa ta zauna saman gadon tana share hawaye. Haleema ce da Fauza sai Shukura mai aikin Ummi.
Sai da suka fara gaisawa da Abdool sannan ta ƙaraso kusa da Namra tana mata ya jiki.
“Senu senu Ajiya, Allah kew wo sauƙi, Allah baka lafiya get well soon”
“Thank you, ya Mama?”
“Lafiya ƙalau yace a agaise ki”
Haleema ta matsa tana ƙare mata kallon tare da yi mata ya jiki.
“Sannu adda Namra Allah baki lafiya”
Sai Fauza ta ɗora da nata
“Ummi tace a gaishe ki, Allah ƙara sauƙi”
“Amin amin na gode”
Bayan sun dire mata kulolin abinci suka tafi. Da kanshi ya ɗauki plate ya zuba mata abincin da aka kawo ya soma bata da kanshi sai da ya tabbatar ta koshi sannan aje plate ɗin ya ɗauki ruwa ya bata, yana dire kofin sai ga Sisters nashi sun shigo tare da Maryam sun kawo abincin cikin manyan kuloli na alfarma masu mugun tsada.
Da sauri Maryam ta zauna kusa da ita tana mata ya jiki cike da tausayin ƴar'uwarta.
“Na ji sauƙi kin yi waya da Anty?”
“Eh tun ɗazu take son ta yi magana da ke wayarki na hannuna shi kuma wayarsa a kashe, tace mun ma sun kamo hanya ita da Abbah da asubar nan”
“Kin faɗa musu abunda ya faru”
“Eh Abbah ma yace Mai Martaba ya kira shi, Namra karki saka ranki a damuwa Asim yana son ya saka ki cikin matsala ne kawai kuma yana son ganin zubar hawayenki saboda yasan a yanzu ba zaki taɓa dawowa gareshi ba”
Abdool ne yayi saurin katse musu fira saboda baya son sisters ɗinshi su gane inda matsalar take, duk da bashi da tabbacin ko Mai Martaba ya faɗa a masarauta.
“Maryam ku zo ku tafi Doc yace ana buƙatar ta huta sosai”
“Okay Allah ya baki Lafiya”
Maryam ta faɗa idonta cike da ƙwalla ganin hawayen da ke zuba a idanuwan ƴar uwarta. Tare da Sisters ɗinsa suka fita sai ya sake buɗe kulolin ya zuba mata abincin da aka kawo amman bata ci ba shi ma kuma baya jin cin abincin sai kawai ya aje. Yana kallon Likitan da ya turo ƙofar ɗakin ya shigo, murmushi suka yi ma juna shi da da Abdool kamin ya miƙa masa hannu su gaisa.
“Ango Ango daya tare a asibiti, ina fatar dai ba ƙarfin amaryar mu ka ci ba har ka kawo mana ita asibiti, kasan baƙauye be iya sintar agogo ba”
Abdool yayi murmushin ƙasaita Hafiz abokinsa ne tare suka yi karatu a waje.
“Ni dai duba min matata please bana son ƙananan magana”
“Ai yanzu kana da baki jiya da na tsaya iya bayani ai ko kallon inda nake baka yi ba”
“Ai ban ma san da kai ba”
“Ai ba zaka sani ba, hankalinka yana tashe”
Ya shiga duba hannun Namra da Abdool ya cire mata drip. Sannan ya tambayi Namra abunda take ji.
Magani ya rubuta mata sannan ya faɗi yadda za a bata shi ya kuma rubuta musu takardar sallama, daman ba wani ciwon ba ne sai gajiya da kuma iɗima a lokaci ɗaya.
Sai basu bar asibitin ba sai da an gidansu Abdool ta ɓangaren Mai Martaba suka cika motoci suka zo ganin Namra, hakan kuma ba ƙaramin faranta ran Namra yayi ba, at least tasan ta shigo familyn da ake marhabun da ita kuma ake sonta da ɗaukinta ta ko wane ɓangare.
Sai ƙarfe goma sha ɗaya har da rabi sannan suka bar asibitin, Abdool be nufi gida da ita ba kasancewar shi ne yake tuƙin motar sai Sis ɗinsa ɗaya da ke gaban mota yayinda Namra da wasu ƴan gidansu suke baya su uku.
Ya tararda gidan cike da mutane kasancewar har yanzu ƴan biki basu gama watsewa ba, balle ma yau Ummi take da niyar yin nata walimar sai dai wannan abun daya faru ya kashe mata jiki, ganin hakan yasa be shigo ba, sai su Meesha da Ƴan Gidansu wato Maryam da Raihanatu da Gwaggo Ramatu, ba laifi tana iya tafiya dan ta samu ƙwarin jiki sosai tsaɓanin jiya da bata da wani kuzari sosai.
Da kanta take takawa har suka isa bacony ɗin, sannu mutanen da ke cikin falon suka riƙa mata har aka nufi ɗaƙin Ummi da ita saboda Ummi tace a shigo da ita cikin.
Kanta a ƙasa ta shiga ɗakin, dan haka bata iya gane mutanen dake cikin bathroom ɗin sai dai taɓa jin ba Ummi bace kaɗai a ɗakin.
Da ɗai-ɗaya Ummi ta riƙa nuna mata su tan gaishesu a nan Namra take ɗan ɗaga ido ta kallesu saboda ta tantancesu.
Sai sannu suke mata suna tsinewa Asim Albarka duk da basu san shi ba, domin Ummi ta faɗa musu komai, ganin ƴan'uwanta babu abunda zata ɓoye musu.
“Tashi ki zauna saman gadi magana zamu yi”
Ummi ta faɗa fuskarta da murmushi kamar babu damuwa cikin ranta. Sai duk suka tashi suna dariya tare da cewa basu su bata guri, daman ana ta kiransu su zo su duba Donuts ɗin da ake haɗawa idan yayi. Namra na zaunawa saman gado Hajiya Sadiya ta buɗo ƙofar Bathroom ta fito ta fito.
Suka haɗa ido da Namra sai ta yi tsaye jikin ƙofar kamar marar gaskiya, Namra kan saurin kawar da idonta tayi saboda bata gama yarda ita ɗince ba ko a'a idan ɗince miya kawo ta nan? Anya ma itace wannan ta rame sosai kamar ba ita ba, duk jikinta nan ya zube ta koma siririya sosai.
“Hajiya Ƙaraso ku gaisa da ƴar ta ki”
Ummi ta faɗa ba tare da ta lura da halin da take ciki ba, cikin kasala da rashin kuzari ta ƙarasa tana kawarda fuska kamar mai jin kunya. Sai Ummi tace
“Kin ga ɗayar nan itama ƙanwata ce”
Cikin nuna ladabi Namra ta gaisheta.
“Ina lafiya wuni”
Ta amsa murya na rawa idanuwanta kuma na cika da ƙwalla.
“Lafiya Ƙalau ya jikin na ki?”
“Alhamdullah”
“Daman ita ce wacce Abdallah ɗin ya aura?”
Ta tambaya tana kallon Ummi.
“Eh itace”
“Yayi sa'ar mata Allah ya baku zama lafiya”
Ummi ta amsa da Amin, sai Namra ta ɗago kai ta kalleta, Hajiya Sadiya ta sakar mata murmushin da yafi kuka ciwo ta juya ta nufi ƙofa.
KU SANI A CIKIN ADDU'AN KU, ALLAH YA BIYA MIN BUƘATUNA KUMA YA YAYE MIN DAMUWA😭🙏Wallahi I'm not in the good mood today, na yi typing ne kawai saboda nasan kuna jira. Pray for me please included me in your addu'ah ba a rubuce nake so ba a cikin five daily prayers naku nake son ku saka ni Alfarmar Annabin Rahama rasululliah salallahu alaihi wassalam 🙏😭
[8/1, 10:44 PM] Khadeeja Candy♥: *94*
“Ƴata Abdallah ya labarta abunda ya faru, nasan ba komai ba ne wannan sai hassada da neman fitina, komai zai wuce karki saka ranki a damuwa, ni dai nasan ni na haifina nasan halinsa kuma nasan abunda zai iya yi da wanda ba zai iya ba, nasan ɗana ba xai aikata irin wannan abun ba, dan haka na yarda wannan tsohon mijin na ki na neman fitina ne kawai”
Namra ta share hawayen daya zubo mata yana kallon Ummi dake mata magana cike da natsuwa da kuma nuna kulawa.
“Allah na miƙawa almurrana, kuma ni dai nasan a kan gaskiya na ke, wallahi ya sake ni kawai yana neman tayar min da hankalin ne kawai”
“Karki damu Allah baya bachi zai shiga a cikin wannan lamarin, Allah ya miki albarka”
“Amin”
“Ɓari naje na duba aikin da ake kar a min ba daidai, ki kwanta ki hutu”
Kai kawai ta iya ɗagawa, sai Ummi ta miƙe tsaye ta fice. Harabar gidan ta fita gaba ɗaya ta duba yadda ake kwaɓa donuts ɗin, sai Hajiya Sadiya ta kamo hannun Ummi suka nufi can ɓangaren garden inda babu mutane.
“Zuwaira na ce ko Namra tace miki wani abu?”
“A'a magana ce kawai muke akan lamarin auren nan da tsohon mijinta ya ɓullo da wannan lamarin”
“Ok na ɗauka ko tace miki wani abun ne, naga kamar zata yi wata maganar”
“Akwai abunda ya kamata ta faɗa min ne? Ita fa lamarin nan gaba ɗaya ya hanata sukuni”
Shiru Hajiya Sadiya ta yi tana sauke ajiyar zuciya.
“To yanzu ya za'ayi wannan lamarin Zuwaira?”
“Shine abunda nake tunani tunda ya tsaya kai da fata shi be sake ta ba”
“Wallahi yaron nan macuci ne, azzalumi ne kuma mayaudari, maƙetaci ne so yake ya shiga tsakaninsu so yake ya raba su, Asim mugun mutum ne wallahi, a lokacin da ka yi masa hallacin a lokacin yake ƙoƙarin cutar da kai”
Sai kawai ta fashe da kuka ta durƙushe, Ummi mamaki ya hanata cewa komai ga sunanshi da ta ambata, duk da bata da tabbacin sunan ne saboda bata taɓa jin sunan ba.
“Hajiya Sadiya kin sanshi ne?”
Ummi ta faɗa tana dafata. Kamar wacce ta tuno wani abu sai tayi saurin tashi tsaye tana share hawaye.
“Eh na taɓa taimakonsa a lokacin baya da lafiya Wallahi yarinyar nan ita tayi ta wahala da shi, kuma ya taɓa min aiki a lokacin ne ma yake faɗa min ya sake ta”
“Alhamdullilah Allah mun gode maka, kema ai sheida ce”
Ummi ta faɗa cike da farinciki. Sai Hajiya Sadiya ta daki ƙirji ta zaro.
“Ni kuma? Dan girman Allah ki rufa min asiri kar ma ki kawo zance na a gaban kowa, wallahi babu ruwana”
Bata tsaya jiran abunda Ummi zatace ba ta nufi gurin mutane gudun kar Ummi ta sake mata wata maganar, ta tsorata sosai ba kuma dan tana tsoron Asim ba sai dan gudun tonuwar Asirinta, ba dan hakan ba babu abunda zai hana ta ballasawa Asim asiri saboda ya cutar da ita.
ASIM POV.
A tsorace abokaninsa suka kai shi Pharmacy aka bashi magani aka saka masa bandeji a wani gurin sannan aka masa allura, sai suka dawo da shi gidansa saboda baya iya tuƙa motar ma, lokacin da suka sauke shi be shiga part ɗin Amaryarsa ba gudun kar taga halin da ya ke ciki sai ya sauka part ɗin Mardiya. Hankalinta ya tashi sosai ganin mijin a cikin irin wannan yanayin mutumen da ya fita lafiya ƙalau ya dawo haka.
Sai da suka fara gaisawa da Abdool sannan ta ƙaraso kusa da Namra tana mata ya jiki.
“Senu senu Ajiya, Allah kew wo sauƙi, Allah baka lafiya get well soon”
“Thank you, ya Mama?”
“Lafiya ƙalau yace a agaise ki”
Haleema ta matsa tana ƙare mata kallon tare da yi mata ya jiki.
“Sannu adda Namra Allah baki lafiya”
Sai Fauza ta ɗora da nata
“Ummi tace a gaishe ki, Allah ƙara sauƙi”
“Amin amin na gode”
Bayan sun dire mata kulolin abinci suka tafi. Da kanshi ya ɗauki plate ya zuba mata abincin da aka kawo ya soma bata da kanshi sai da ya tabbatar ta koshi sannan aje plate ɗin ya ɗauki ruwa ya bata, yana dire kofin sai ga Sisters nashi sun shigo tare da Maryam sun kawo abincin cikin manyan kuloli na alfarma masu mugun tsada.
Da sauri Maryam ta zauna kusa da ita tana mata ya jiki cike da tausayin ƴar'uwarta.
“Na ji sauƙi kin yi waya da Anty?”
“Eh tun ɗazu take son ta yi magana da ke wayarki na hannuna shi kuma wayarsa a kashe, tace mun ma sun kamo hanya ita da Abbah da asubar nan”
“Kin faɗa musu abunda ya faru”
“Eh Abbah ma yace Mai Martaba ya kira shi, Namra karki saka ranki a damuwa Asim yana son ya saka ki cikin matsala ne kawai kuma yana son ganin zubar hawayenki saboda yasan a yanzu ba zaki taɓa dawowa gareshi ba”
Abdool ne yayi saurin katse musu fira saboda baya son sisters ɗinshi su gane inda matsalar take, duk da bashi da tabbacin ko Mai Martaba ya faɗa a masarauta.
“Maryam ku zo ku tafi Doc yace ana buƙatar ta huta sosai”
“Okay Allah ya baki Lafiya”
Maryam ta faɗa idonta cike da ƙwalla ganin hawayen da ke zuba a idanuwan ƴar uwarta. Tare da Sisters ɗinsa suka fita sai ya sake buɗe kulolin ya zuba mata abincin da aka kawo amman bata ci ba shi ma kuma baya jin cin abincin sai kawai ya aje. Yana kallon Likitan da ya turo ƙofar ɗakin ya shigo, murmushi suka yi ma juna shi da da Abdool kamin ya miƙa masa hannu su gaisa.
“Ango Ango daya tare a asibiti, ina fatar dai ba ƙarfin amaryar mu ka ci ba har ka kawo mana ita asibiti, kasan baƙauye be iya sintar agogo ba”
Abdool yayi murmushin ƙasaita Hafiz abokinsa ne tare suka yi karatu a waje.
“Ni dai duba min matata please bana son ƙananan magana”
“Ai yanzu kana da baki jiya da na tsaya iya bayani ai ko kallon inda nake baka yi ba”
“Ai ban ma san da kai ba”
“Ai ba zaka sani ba, hankalinka yana tashe”
Ya shiga duba hannun Namra da Abdool ya cire mata drip. Sannan ya tambayi Namra abunda take ji.
Magani ya rubuta mata sannan ya faɗi yadda za a bata shi ya kuma rubuta musu takardar sallama, daman ba wani ciwon ba ne sai gajiya da kuma iɗima a lokaci ɗaya.
Sai basu bar asibitin ba sai da an gidansu Abdool ta ɓangaren Mai Martaba suka cika motoci suka zo ganin Namra, hakan kuma ba ƙaramin faranta ran Namra yayi ba, at least tasan ta shigo familyn da ake marhabun da ita kuma ake sonta da ɗaukinta ta ko wane ɓangare.
Sai ƙarfe goma sha ɗaya har da rabi sannan suka bar asibitin, Abdool be nufi gida da ita ba kasancewar shi ne yake tuƙin motar sai Sis ɗinsa ɗaya da ke gaban mota yayinda Namra da wasu ƴan gidansu suke baya su uku.
Ya tararda gidan cike da mutane kasancewar har yanzu ƴan biki basu gama watsewa ba, balle ma yau Ummi take da niyar yin nata walimar sai dai wannan abun daya faru ya kashe mata jiki, ganin hakan yasa be shigo ba, sai su Meesha da Ƴan Gidansu wato Maryam da Raihanatu da Gwaggo Ramatu, ba laifi tana iya tafiya dan ta samu ƙwarin jiki sosai tsaɓanin jiya da bata da wani kuzari sosai.
Da kanta take takawa har suka isa bacony ɗin, sannu mutanen da ke cikin falon suka riƙa mata har aka nufi ɗaƙin Ummi da ita saboda Ummi tace a shigo da ita cikin.
Kanta a ƙasa ta shiga ɗakin, dan haka bata iya gane mutanen dake cikin bathroom ɗin sai dai taɓa jin ba Ummi bace kaɗai a ɗakin.
Da ɗai-ɗaya Ummi ta riƙa nuna mata su tan gaishesu a nan Namra take ɗan ɗaga ido ta kallesu saboda ta tantancesu.
Sai sannu suke mata suna tsinewa Asim Albarka duk da basu san shi ba, domin Ummi ta faɗa musu komai, ganin ƴan'uwanta babu abunda zata ɓoye musu.
“Tashi ki zauna saman gadi magana zamu yi”
Ummi ta faɗa fuskarta da murmushi kamar babu damuwa cikin ranta. Sai duk suka tashi suna dariya tare da cewa basu su bata guri, daman ana ta kiransu su zo su duba Donuts ɗin da ake haɗawa idan yayi. Namra na zaunawa saman gado Hajiya Sadiya ta buɗo ƙofar Bathroom ta fito ta fito.
Suka haɗa ido da Namra sai ta yi tsaye jikin ƙofar kamar marar gaskiya, Namra kan saurin kawar da idonta tayi saboda bata gama yarda ita ɗince ba ko a'a idan ɗince miya kawo ta nan? Anya ma itace wannan ta rame sosai kamar ba ita ba, duk jikinta nan ya zube ta koma siririya sosai.
“Hajiya Ƙaraso ku gaisa da ƴar ta ki”
Ummi ta faɗa ba tare da ta lura da halin da take ciki ba, cikin kasala da rashin kuzari ta ƙarasa tana kawarda fuska kamar mai jin kunya. Sai Ummi tace
“Kin ga ɗayar nan itama ƙanwata ce”
Cikin nuna ladabi Namra ta gaisheta.
“Ina lafiya wuni”
Ta amsa murya na rawa idanuwanta kuma na cika da ƙwalla.
“Lafiya Ƙalau ya jikin na ki?”
“Alhamdullah”
“Daman ita ce wacce Abdallah ɗin ya aura?”
Ta tambaya tana kallon Ummi.
“Eh itace”
“Yayi sa'ar mata Allah ya baku zama lafiya”
Ummi ta amsa da Amin, sai Namra ta ɗago kai ta kalleta, Hajiya Sadiya ta sakar mata murmushin da yafi kuka ciwo ta juya ta nufi ƙofa.
KU SANI A CIKIN ADDU'AN KU, ALLAH YA BIYA MIN BUƘATUNA KUMA YA YAYE MIN DAMUWA😭🙏Wallahi I'm not in the good mood today, na yi typing ne kawai saboda nasan kuna jira. Pray for me please included me in your addu'ah ba a rubuce nake so ba a cikin five daily prayers naku nake son ku saka ni Alfarmar Annabin Rahama rasululliah salallahu alaihi wassalam 🙏😭
[8/1, 10:44 PM] Khadeeja Candy♥: *94*
“Ƴata Abdallah ya labarta abunda ya faru, nasan ba komai ba ne wannan sai hassada da neman fitina, komai zai wuce karki saka ranki a damuwa, ni dai nasan ni na haifina nasan halinsa kuma nasan abunda zai iya yi da wanda ba zai iya ba, nasan ɗana ba xai aikata irin wannan abun ba, dan haka na yarda wannan tsohon mijin na ki na neman fitina ne kawai”
Namra ta share hawayen daya zubo mata yana kallon Ummi dake mata magana cike da natsuwa da kuma nuna kulawa.
“Allah na miƙawa almurrana, kuma ni dai nasan a kan gaskiya na ke, wallahi ya sake ni kawai yana neman tayar min da hankalin ne kawai”
“Karki damu Allah baya bachi zai shiga a cikin wannan lamarin, Allah ya miki albarka”
“Amin”
“Ɓari naje na duba aikin da ake kar a min ba daidai, ki kwanta ki hutu”
Kai kawai ta iya ɗagawa, sai Ummi ta miƙe tsaye ta fice. Harabar gidan ta fita gaba ɗaya ta duba yadda ake kwaɓa donuts ɗin, sai Hajiya Sadiya ta kamo hannun Ummi suka nufi can ɓangaren garden inda babu mutane.
“Zuwaira na ce ko Namra tace miki wani abu?”
“A'a magana ce kawai muke akan lamarin auren nan da tsohon mijinta ya ɓullo da wannan lamarin”
“Ok na ɗauka ko tace miki wani abun ne, naga kamar zata yi wata maganar”
“Akwai abunda ya kamata ta faɗa min ne? Ita fa lamarin nan gaba ɗaya ya hanata sukuni”
Shiru Hajiya Sadiya ta yi tana sauke ajiyar zuciya.
“To yanzu ya za'ayi wannan lamarin Zuwaira?”
“Shine abunda nake tunani tunda ya tsaya kai da fata shi be sake ta ba”
“Wallahi yaron nan macuci ne, azzalumi ne kuma mayaudari, maƙetaci ne so yake ya shiga tsakaninsu so yake ya raba su, Asim mugun mutum ne wallahi, a lokacin da ka yi masa hallacin a lokacin yake ƙoƙarin cutar da kai”
Sai kawai ta fashe da kuka ta durƙushe, Ummi mamaki ya hanata cewa komai ga sunanshi da ta ambata, duk da bata da tabbacin sunan ne saboda bata taɓa jin sunan ba.
“Hajiya Sadiya kin sanshi ne?”
Ummi ta faɗa tana dafata. Kamar wacce ta tuno wani abu sai tayi saurin tashi tsaye tana share hawaye.
“Eh na taɓa taimakonsa a lokacin baya da lafiya Wallahi yarinyar nan ita tayi ta wahala da shi, kuma ya taɓa min aiki a lokacin ne ma yake faɗa min ya sake ta”
“Alhamdullilah Allah mun gode maka, kema ai sheida ce”
Ummi ta faɗa cike da farinciki. Sai Hajiya Sadiya ta daki ƙirji ta zaro.
“Ni kuma? Dan girman Allah ki rufa min asiri kar ma ki kawo zance na a gaban kowa, wallahi babu ruwana”
Bata tsaya jiran abunda Ummi zatace ba ta nufi gurin mutane gudun kar Ummi ta sake mata wata maganar, ta tsorata sosai ba kuma dan tana tsoron Asim ba sai dan gudun tonuwar Asirinta, ba dan hakan ba babu abunda zai hana ta ballasawa Asim asiri saboda ya cutar da ita.
ASIM POV.
A tsorace abokaninsa suka kai shi Pharmacy aka bashi magani aka saka masa bandeji a wani gurin sannan aka masa allura, sai suka dawo da shi gidansa saboda baya iya tuƙa motar ma, lokacin da suka sauke shi be shiga part ɗin Amaryarsa ba gudun kar taga halin da ya ke ciki sai ya sauka part ɗin Mardiya. Hankalinta ya tashi sosai ganin mijin a cikin irin wannan yanayin mutumen da ya fita lafiya ƙalau ya dawo haka.