Sashe 24
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tun da asuba ya tashi ya haɗa ruwan wanka yayi sannan ya tashe ta, duk yadda yaso ya taimaka mata tayi wanka ƙin yarda tayi a dole ya ƙyaleta tayi da kanta sai zolayarta yake, wai jiya duk ta hajiyar da shi.
Ita kam kunyarsa ma take ji, ta gasa kanta sosai gurin wanka saboda yadda ƙasanta yake mata zafi da raɗaɗi, a tare suka yi sallah. Ita kam bata tsaya komai ba suna sallamewa ta hau gado sai bachi.
Bata farka ba sai tara har da tabi, a lokacin Hilal har ya gama haɗa musu breakfast dan yau Rashida da wuri ta fita ko gaisa bata bari suka yi ba, shi ya kai yara makaranta, sannan ya shigo ɗakin ya tashe ta.
NAMRA POV.
Ta daɗe a gurin tsaye tana tunanin abunda zata cewa Anty Amarya, ita kanta tana buƙatar karatun dan tana da yaƙinin zai taimaki rayuwarta, sai dai tana ganin hakan kamar ba me yiyu bane, tun da Asim yana nuna mata alamun baya son ta cigaba da karatun, gashi ma yace ba nan zasu zauna ba.
“Anty naga zan yi aure shiyasa na bar zancen karatu”
Duk kallonta suka yi suna mamakin irin sakarcin da take ƙoƙarin aikatawa.
“Namra kenan, ai karatu baya hana aure kuma aure baya hana karatu, karki yarda ki bar karatun ki”
“Anty yace ba a nan zamu zauna ba, a katsina zamu zauna”
“Katsina kuma?”
Maryam ta amsa, sai ta taso ta dawo kusa da Namta ta zauna.
“Dan Allah, karki yi haka Anty Namra taya zaki bishi zuwa katsina? Kibar karatun ki? Idan shi be san darajar nashi karatun ba ke ya kamata ace kin san naki, yanzu kina son ki zubar da duk shekarun da kikayi ki zubar da su?”
Anty Amarya ta riƙa hannunta.
“Namra karki yi ma kanki zaɓen tumun dare dan Allah, kar kije kiyi abunda zaki yi nadama”
Fashewa tayi da kuka
“Anty idan nace na zan aure shi zai ce naci amanarsa kuma kin ga yanzu har an yanka masa sadaki taya zan ce na fasa? Bayan kuma Abbah ya bani dama, baya da gurin aje ni a nan sai can, ɗan zuwan nan yayi ya samu aiki da zai iya taimakawa kansa da shi”
Anty Amarya ta dafe kanta tana sauke ajiyar zuciya. Zuwa can ta ɗago ta kalli Namra
“Ki masa magana idan ya aminta zan baku gidan da zaku zauna a nan garin, in yaso sai ku cigaba da karatun ku muga abunda Allah ze yi kuma”
Namra ta jidaɗin abunda Anty take ƙoƙarin mata, cikin murna ta share hawayenta tana mata godiya.
“Na gode sosai Anty, zan masa magana anjima inshallah”
“Ba komai Allah ya sanya alheri”
Daga haka Anty Amarya ta tashi ta nufi ɗakinta. Sai da ta shige sannan Namra ta kalli Maryam tace
“Dan Allah Maryam ina son na nemi taimakon ki”
“Na me?”
“Abu nake son ki ara min dan Allah”
“Minene faɗa min mana, kina abu kamar mai jin kunya na”
Sai da ta sosa gefen wuyanta, cikin jin nauyi da kunya tace
“Kuɗi naƙe son ki ara min, zan yi wani abu ne, kuma kuɗin da yake account ɗina be wuce dubu ɗari takwas ba”
“Kamar nawa kike so?”
“Zan samu 1.5 million?”
“Zaki samu kan, ai kin san budurwar Sadiq ba za'a rasa kuɗi a account ɗin ta ba, kullum Sadiq samin kuɗi yake min Wallahi”
Namra ta harareta
“Dan kuma nace ki ara min kuɗi ai ban ce ki min gori ba, muma na mu lokacin yana zuwa ”
Dariya Maryam tayi ta kai ma Namra dudu a baya.
“Dole nayi miki dariya mana, duk manyan garin nan wasu-wasu ne kawai basu nemi aurenki ba, amman kika ƙi kula kowa ke sai Asim, Allah yasa dai ba auren jari zai yi dake ba”
“Dan Allah ki daina zargin Asim mana haba, ni dai kiyi min transfer kuɗin gobe”
Tashi tayi ta bar mata falon cikin jin zafin furucin Maryam.
*** *** ***
Sai da aka kwana biyu sannan Asim ya samu damar zuwa gurin Namra, duk kuwa da damuwarsa da take da waya, sai yace mata wai neman kuɗi yake.
Guraren takwas da rabi na dare ya shigo gidan, bata ɗauki lokaci ba ta fito cikin hijabi. Sai da suka gaisa sannan ta koro masa da bayanin da gidan da Anty Amarya tace zata basu su zauna.
A maimakon ta ga jindaɗi a fuskarsa sai kawai ta ga ya canja fuska kamar ransa be so ba.
“Har yanzu ƴan gidan ku basu yarda dani ba Namra, har yanzu basa son aure na dake, a tunani zaki iya zama a duk inda zan aje ki, kwata-kwata bana da ra'ayin zama garin nan, a can nake da sana'ah”
“Idan mun zauna a nan zamu iya cigaba da karatun mu, kuma a nan ɗin ma ba zaka rasa sana'ar yi ba”
Miƙewa yayi tsaye irin ya fusata ɗin nan sosai.
“Ba zan zauna a nan ba, Katsina nake son zama, idan kuma baki da ra'ayin aure na kawai ki faɗa min”
Ita miƙewa tayi tsaye tana girgiza masa kai
“Abun be kai ga haka ba Asim, magana ce ta fahimtar juna, bana nufin ƙin aurenka ko kaɗan a cikin rai na”
Takardar dake hannunta ta miƙa masa tare da zinarin da Abbah ya bata ranar da aka musu walima.
“Kaje ka cire wannan kuɗin miliyan biyu ne da dubu ɗari uku, nasan ze isa kayi komai, na mai ƙaramin ƙarfi, ba sai kayi lefe mai yawa ba kala ashirin ma ya isa amman kasa me ɗan tsada dan Allah”
Kawar da kai yayi yaƙi karɓar kuɗin.
“Ni bana buƙatar wannan kuɗin Namra”
“Idan baka amsa ba kana da wata mafitar ne? Wallahi ba zan faɗawa kowa kai na ba ba, dan Allah ka karɓa Asim”
Sai da tayi ta masa magajiya har da kukanta sannan ya karɓa. A fuska yake nuna mata baya son karɓa amman a ransa farinciki ne fess shi da be taɓa mallakar dubu ɗari biyar nasa na kansa ba yau gashi ta miƙa masa million biyu har da wani abu.
Bayan sun yi sallama ta samu Anty Amarya a ɗakinta ta faɗa mata yadda suka yi da Asim, akan ƙin amincewar da yayi na zama garin, sai ta nuna mata wai har ƙanen Babansa ya bashi gida a can, kuma sana'ar da yake acan mai ƙarfi ce wai a ƙarƙashin kamfanin Dangote ya samu suka ɗauke shi.
Bayan Allah ya kyauta babu abunda Anty Amarya tace mata, sai ta taso jiki ba ƙwari ta dawo ɗakinta, zuciyarta a cunkushe, tunaninta a kulle, ya rasa abunda yake mata daɗi har wani jiri take jin yana ɗaukarta.
_____________________________________
WHO CAN'T WAIT FOR THE NEXT CHAPTER?
COMMENT LINE BY LINE!
LOVE YOU ALL FISABILLIAH 💖💖💖
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa19.html
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 19*
Baki har kunne Asim ya isa gida da kuɗin, tun daga yanayin sallamarsa Mama ta gani yana cikin farinciki. A ƙuryar ɗaki ya same ta tana zaune saman sallaya ya zauna kusa da ita yana murmushi.
Wani kallo tayi masa ta ɗauke kai, dan ita yanzu wani haushi ma yake bata ji take kamar tayi ta dukansa. Takardar kuɗin dake aljihunsa ya ciro ya aje mata gaban sallaya tare da zinarin da Namra ta bashi.
Ba a ɓoye zinari yake ba, ko yanzu ka tashi daga bachi aka nuna maka shi zaka iya gane shi, musamman irin wannan na Namra da aka siya daga Dubai. Gabanta ya faɗi, sai ta kalli sarƙar ta kalleshi kusan sau huɗu sannan ta ce
“Ina ka samo wannan sarƙar Ibrahim?”
Da dariya ya amsa mata
“Nawa ne”
“Na ka? Sata ka fara ne? Kamar fa zinari nake gani”
“Ba kama bace zinari ne, wannan kuma takardar kuɗi ce na miliyan biyu da dubu ɗari uku”
Ta daki ƙirji ta da ƙarfi.
“Miliyan biyu Ibrahim? Ina ka samo wannan kuɗi?”
Yanayin yadda tayi masa tambayar da ƙarfi, yasa ƙanensa shigowa ɗakin da gudu suna tambayar miya faru.
“Kuɗi na samo mana miliyan biyu da dubu ɗari uku, ga kuma sarƙar zinari”
Ƙanensa ya zauna kusa da shi da mugun mamaki.
“Ya Asim taya ka ɗauko?”
“Ba ɗaukowa nayi ba, Namra ta bani tace nayi hidima da su”
Duk tsalle suka saka suna murnar Yayansu ya samo kuɗi, sai Mama tayi saurin riƙe so
“Dan Allah ku rufa mana asiri, kar aji a dirar mana cikin daren nan”
Sai da suka natsu sannan ta kalli Asim
“Da gaske ita ta baka Ibrahim?”
“Wallahi ita ta bani yanzu nan, sai da ma nayi kamar ba zan karɓa ba, sannan na karɓa kuma tace ba zata faɗawa kowa ba”
Hannu Mama ta ɗaga sama.
“Al-hamdulillah Allah mun gode maka”
Ƙanensa yayi dariya yana faɗin
“Mama ke da baki son ta”
“Ai suma ba dan Allah zasu aura masa ita ba, kai kana ganin masu kuɗi kamar Alhaji Usman zai yarda Ƴarsa tayi aure irin gidan nan idan ba da wani dalilin ba”
Asim ya sauke ajiyar zuciya kana yace
“Wallahi haka kowa ke faɗa, ni kwata-kwata ma ta fitar min a rai, kawai dai zan aure ta saboda na fita kunyar masu ganin kamar ɓa zata iya auren mutun iri na ba”
Mama ta mere baki
“Wallahi ko rantsuwa nayi ba zan yi kaffara ba, da abun nan be faru ba ba zasu taɓa yarda kmsu barta ta aure ka ba, Amman wannan shi ake cewa gobarar ti-ti ko ba komai dole dai a kira ka da surukin Alhaji Usman kuma ko yaƙi ko ya so dole ne ya samo maka wata hanyar, kuma Allah kaɗai yasan ribar da zaka ci akan wannan auren”
“Haka abokaina ke faɗa, wai wata hanyar ce Allah yayi min”
“Sosai tun dai baka ci amanarta ita ta nemi ta ci taka ai dole Allah ya saka maka”
“Yanzu wannan kuɗin tace min aje a haɗa lefe dasu kuma da su zan kama gidan hayan da zamu zauna a katsina”
“Amman Ibrahim zaman ka a nan be fi ba? Karatun ka fa?”
Ita kam kunyarsa ma take ji, ta gasa kanta sosai gurin wanka saboda yadda ƙasanta yake mata zafi da raɗaɗi, a tare suka yi sallah. Ita kam bata tsaya komai ba suna sallamewa ta hau gado sai bachi.
Bata farka ba sai tara har da tabi, a lokacin Hilal har ya gama haɗa musu breakfast dan yau Rashida da wuri ta fita ko gaisa bata bari suka yi ba, shi ya kai yara makaranta, sannan ya shigo ɗakin ya tashe ta.
NAMRA POV.
Ta daɗe a gurin tsaye tana tunanin abunda zata cewa Anty Amarya, ita kanta tana buƙatar karatun dan tana da yaƙinin zai taimaki rayuwarta, sai dai tana ganin hakan kamar ba me yiyu bane, tun da Asim yana nuna mata alamun baya son ta cigaba da karatun, gashi ma yace ba nan zasu zauna ba.
“Anty naga zan yi aure shiyasa na bar zancen karatu”
Duk kallonta suka yi suna mamakin irin sakarcin da take ƙoƙarin aikatawa.
“Namra kenan, ai karatu baya hana aure kuma aure baya hana karatu, karki yarda ki bar karatun ki”
“Anty yace ba a nan zamu zauna ba, a katsina zamu zauna”
“Katsina kuma?”
Maryam ta amsa, sai ta taso ta dawo kusa da Namta ta zauna.
“Dan Allah, karki yi haka Anty Namra taya zaki bishi zuwa katsina? Kibar karatun ki? Idan shi be san darajar nashi karatun ba ke ya kamata ace kin san naki, yanzu kina son ki zubar da duk shekarun da kikayi ki zubar da su?”
Anty Amarya ta riƙa hannunta.
“Namra karki yi ma kanki zaɓen tumun dare dan Allah, kar kije kiyi abunda zaki yi nadama”
Fashewa tayi da kuka
“Anty idan nace na zan aure shi zai ce naci amanarsa kuma kin ga yanzu har an yanka masa sadaki taya zan ce na fasa? Bayan kuma Abbah ya bani dama, baya da gurin aje ni a nan sai can, ɗan zuwan nan yayi ya samu aiki da zai iya taimakawa kansa da shi”
Anty Amarya ta dafe kanta tana sauke ajiyar zuciya. Zuwa can ta ɗago ta kalli Namra
“Ki masa magana idan ya aminta zan baku gidan da zaku zauna a nan garin, in yaso sai ku cigaba da karatun ku muga abunda Allah ze yi kuma”
Namra ta jidaɗin abunda Anty take ƙoƙarin mata, cikin murna ta share hawayenta tana mata godiya.
“Na gode sosai Anty, zan masa magana anjima inshallah”
“Ba komai Allah ya sanya alheri”
Daga haka Anty Amarya ta tashi ta nufi ɗakinta. Sai da ta shige sannan Namra ta kalli Maryam tace
“Dan Allah Maryam ina son na nemi taimakon ki”
“Na me?”
“Abu nake son ki ara min dan Allah”
“Minene faɗa min mana, kina abu kamar mai jin kunya na”
Sai da ta sosa gefen wuyanta, cikin jin nauyi da kunya tace
“Kuɗi naƙe son ki ara min, zan yi wani abu ne, kuma kuɗin da yake account ɗina be wuce dubu ɗari takwas ba”
“Kamar nawa kike so?”
“Zan samu 1.5 million?”
“Zaki samu kan, ai kin san budurwar Sadiq ba za'a rasa kuɗi a account ɗin ta ba, kullum Sadiq samin kuɗi yake min Wallahi”
Namra ta harareta
“Dan kuma nace ki ara min kuɗi ai ban ce ki min gori ba, muma na mu lokacin yana zuwa ”
Dariya Maryam tayi ta kai ma Namra dudu a baya.
“Dole nayi miki dariya mana, duk manyan garin nan wasu-wasu ne kawai basu nemi aurenki ba, amman kika ƙi kula kowa ke sai Asim, Allah yasa dai ba auren jari zai yi dake ba”
“Dan Allah ki daina zargin Asim mana haba, ni dai kiyi min transfer kuɗin gobe”
Tashi tayi ta bar mata falon cikin jin zafin furucin Maryam.
*** *** ***
Sai da aka kwana biyu sannan Asim ya samu damar zuwa gurin Namra, duk kuwa da damuwarsa da take da waya, sai yace mata wai neman kuɗi yake.
Guraren takwas da rabi na dare ya shigo gidan, bata ɗauki lokaci ba ta fito cikin hijabi. Sai da suka gaisa sannan ta koro masa da bayanin da gidan da Anty Amarya tace zata basu su zauna.
A maimakon ta ga jindaɗi a fuskarsa sai kawai ta ga ya canja fuska kamar ransa be so ba.
“Har yanzu ƴan gidan ku basu yarda dani ba Namra, har yanzu basa son aure na dake, a tunani zaki iya zama a duk inda zan aje ki, kwata-kwata bana da ra'ayin zama garin nan, a can nake da sana'ah”
“Idan mun zauna a nan zamu iya cigaba da karatun mu, kuma a nan ɗin ma ba zaka rasa sana'ar yi ba”
Miƙewa yayi tsaye irin ya fusata ɗin nan sosai.
“Ba zan zauna a nan ba, Katsina nake son zama, idan kuma baki da ra'ayin aure na kawai ki faɗa min”
Ita miƙewa tayi tsaye tana girgiza masa kai
“Abun be kai ga haka ba Asim, magana ce ta fahimtar juna, bana nufin ƙin aurenka ko kaɗan a cikin rai na”
Takardar dake hannunta ta miƙa masa tare da zinarin da Abbah ya bata ranar da aka musu walima.
“Kaje ka cire wannan kuɗin miliyan biyu ne da dubu ɗari uku, nasan ze isa kayi komai, na mai ƙaramin ƙarfi, ba sai kayi lefe mai yawa ba kala ashirin ma ya isa amman kasa me ɗan tsada dan Allah”
Kawar da kai yayi yaƙi karɓar kuɗin.
“Ni bana buƙatar wannan kuɗin Namra”
“Idan baka amsa ba kana da wata mafitar ne? Wallahi ba zan faɗawa kowa kai na ba ba, dan Allah ka karɓa Asim”
Sai da tayi ta masa magajiya har da kukanta sannan ya karɓa. A fuska yake nuna mata baya son karɓa amman a ransa farinciki ne fess shi da be taɓa mallakar dubu ɗari biyar nasa na kansa ba yau gashi ta miƙa masa million biyu har da wani abu.
Bayan sun yi sallama ta samu Anty Amarya a ɗakinta ta faɗa mata yadda suka yi da Asim, akan ƙin amincewar da yayi na zama garin, sai ta nuna mata wai har ƙanen Babansa ya bashi gida a can, kuma sana'ar da yake acan mai ƙarfi ce wai a ƙarƙashin kamfanin Dangote ya samu suka ɗauke shi.
Bayan Allah ya kyauta babu abunda Anty Amarya tace mata, sai ta taso jiki ba ƙwari ta dawo ɗakinta, zuciyarta a cunkushe, tunaninta a kulle, ya rasa abunda yake mata daɗi har wani jiri take jin yana ɗaukarta.
_____________________________________
WHO CAN'T WAIT FOR THE NEXT CHAPTER?
COMMENT LINE BY LINE!
LOVE YOU ALL FISABILLIAH 💖💖💖
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa19.html
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 19*
Baki har kunne Asim ya isa gida da kuɗin, tun daga yanayin sallamarsa Mama ta gani yana cikin farinciki. A ƙuryar ɗaki ya same ta tana zaune saman sallaya ya zauna kusa da ita yana murmushi.
Wani kallo tayi masa ta ɗauke kai, dan ita yanzu wani haushi ma yake bata ji take kamar tayi ta dukansa. Takardar kuɗin dake aljihunsa ya ciro ya aje mata gaban sallaya tare da zinarin da Namra ta bashi.
Ba a ɓoye zinari yake ba, ko yanzu ka tashi daga bachi aka nuna maka shi zaka iya gane shi, musamman irin wannan na Namra da aka siya daga Dubai. Gabanta ya faɗi, sai ta kalli sarƙar ta kalleshi kusan sau huɗu sannan ta ce
“Ina ka samo wannan sarƙar Ibrahim?”
Da dariya ya amsa mata
“Nawa ne”
“Na ka? Sata ka fara ne? Kamar fa zinari nake gani”
“Ba kama bace zinari ne, wannan kuma takardar kuɗi ce na miliyan biyu da dubu ɗari uku”
Ta daki ƙirji ta da ƙarfi.
“Miliyan biyu Ibrahim? Ina ka samo wannan kuɗi?”
Yanayin yadda tayi masa tambayar da ƙarfi, yasa ƙanensa shigowa ɗakin da gudu suna tambayar miya faru.
“Kuɗi na samo mana miliyan biyu da dubu ɗari uku, ga kuma sarƙar zinari”
Ƙanensa ya zauna kusa da shi da mugun mamaki.
“Ya Asim taya ka ɗauko?”
“Ba ɗaukowa nayi ba, Namra ta bani tace nayi hidima da su”
Duk tsalle suka saka suna murnar Yayansu ya samo kuɗi, sai Mama tayi saurin riƙe so
“Dan Allah ku rufa mana asiri, kar aji a dirar mana cikin daren nan”
Sai da suka natsu sannan ta kalli Asim
“Da gaske ita ta baka Ibrahim?”
“Wallahi ita ta bani yanzu nan, sai da ma nayi kamar ba zan karɓa ba, sannan na karɓa kuma tace ba zata faɗawa kowa ba”
Hannu Mama ta ɗaga sama.
“Al-hamdulillah Allah mun gode maka”
Ƙanensa yayi dariya yana faɗin
“Mama ke da baki son ta”
“Ai suma ba dan Allah zasu aura masa ita ba, kai kana ganin masu kuɗi kamar Alhaji Usman zai yarda Ƴarsa tayi aure irin gidan nan idan ba da wani dalilin ba”
Asim ya sauke ajiyar zuciya kana yace
“Wallahi haka kowa ke faɗa, ni kwata-kwata ma ta fitar min a rai, kawai dai zan aure ta saboda na fita kunyar masu ganin kamar ɓa zata iya auren mutun iri na ba”
Mama ta mere baki
“Wallahi ko rantsuwa nayi ba zan yi kaffara ba, da abun nan be faru ba ba zasu taɓa yarda kmsu barta ta aure ka ba, Amman wannan shi ake cewa gobarar ti-ti ko ba komai dole dai a kira ka da surukin Alhaji Usman kuma ko yaƙi ko ya so dole ne ya samo maka wata hanyar, kuma Allah kaɗai yasan ribar da zaka ci akan wannan auren”
“Haka abokaina ke faɗa, wai wata hanyar ce Allah yayi min”
“Sosai tun dai baka ci amanarta ita ta nemi ta ci taka ai dole Allah ya saka maka”
“Yanzu wannan kuɗin tace min aje a haɗa lefe dasu kuma da su zan kama gidan hayan da zamu zauna a katsina”
“Amman Ibrahim zaman ka a nan be fi ba? Karatun ka fa?”