Sashe 124
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Be ɗago ya kalleta ba, balle ta gane maganarta ta ratsa kunnensa, sai sha'aninsa yake da wayarsa, kamar be san da tsayuwarta a gurin ba.
Tayi tsayuwar minti ɗaya a gurin zuwa biyu, kamin ya ɗago ya kalleta ta cika sosai da taji kamar ta jefa masa wata baƙar magana amman bakinta be bata haɗin kai ba, gashi sai jin take kamar ta jefa masa carpet ɗin, sai dai kwajininsa ya hana hannunta kuzari, ballema ta yi ƙoƙarin yin hakan.
Babu enough hasken da zai iya haske fusakarta sosai, amman hakan be hana shi karantar tana ciki fushi ba, ko ba komai yasan ya ɓata mata lokaci, kuma ya shiga huruminta na ƙinjin gargaɗin da tayi masa akan kar ƙafarsa ta sake tako ƙofar gidansu.
“Ƙomai naki kyau yake min Namra, fushinki da faɗanki da tsawarki duka burgeni suke, abu ɗaƴa ya rage min yanzu na gani naki, shine dariyarki”
Ya faɗa yayinda ya ke cigaba da dannar wayarsa, amman hankalinsa da idonsa suna kan Namra. Wannan karon tayi nasarar yaudarar kanta, har ta samu haɗin kan idanuwanta, ta jefe Abdool da wani shegen kallo.
“Carpet ɗin ka kawai na fito kawo maka, ban fito dan ka yaba fushi ko faɗa na ba, kuma bana tunanin an halicceka dan ka ga dariyata kawai, saboda haka karka ɓatawa kanka lokaci, ka karɓi Carpet ɗin ka”
“Miya hana ki bar carpet ɗin a inda na barta tun ranar? Wane salo ne yasa kika ɗauke ta? Yanzun da nazo na aika nace a bani carpet ne? Wato ba zaki iya ganin abun Abdool ki ƙyale ba ko?”
Wannan karon da murmushi a fuskarsa, ya soka mata wannan maganar, ya gyara tsayuwarsa yana kallon taurarin da suka yi sama ado.
“Ai mu ƴaƴan Sarakuna bama shimfiɗa kuma bama ɗaukewa, wacan karon ma ba na shimfiɗawa kai na bane a karon kai na, nasan wata rana zan rubuta a diary, bayan Mai Martaba da Ummina, na taɓa shimfiɗawa Namra carpet har ma na zauna da ni da ita”
“Amman kai ka baka da aikin yi Wallahi, Allah yayi min tsare da mugun ƙudirinka, baka cikin hayyacinka ne? Miyasa zaka zo kana min wasu kalamai kamar wanda be san halin da nake ciki ba?”
“Ina ma ina da mugun ƙudiri a kanki! Da kin ga yanzu sace ci kawai zan yi na gudu naje nayi rayuwarda da nake so da ke, ni kaina ina mamakin halin dana shiga saboda ke, ban san miyasa ƙwaƙwalwata take ƙoƙarin zautuwa da lamarin ki ba”
Kai ta girgiza ta jefar da carpet ɗin a ƙasa.
“Wallahi baka da tausayi baka da tunani kwata-kwata a zuciyarka, taya zaka kalleni ka yi irin wannan maganar, you're fake Prince ba asalin Yariman ƙwarai bane kai, wata ƙila sarautar ta ku ta ƙauye ce, dan yariman ƙwarai ba zai tsaya mace kamar ni tana faɗa masa magana ba”
Lumshe ido yayi yana murmushi, tare da tsutsar baki kamar mai shan Sweet Candy. Ko da ya buɗe idonsa har ta ɓace daga gurin kamar walkiya.
Murmushin da ke fuskarsa ya faɗaɗa, kamin ya shiga muhalin massages ya aika saƙo. Cikin mintunan da basu fi goma ba, sai ga wata mota ta faka a gurin ɗauke da Anty Amarya da Abbah.
“Ga gidan can”
Ya faɗa yana nuna musu da kai, sannan ya buɗe motarsa ya shiga. Su kuma suka doshi ƙofar gidan, Abbah ne ya tsaya daga waje, Anty Amarya ta kunna kai ciki, zuciyarta sai bugawa take fat fat fat...
HILAL POV.
Ba a'ayi wasu events ban da walima, daman can shi baya ra'ayi sai kuma aka ci sa'ah amaryar tasa uztaziyace ita bata da son duniya. Ranar jumma'ah akayi walimar bayana an saka amarya lalle kamar yadda al'ada ta gada. Sai aka ɗaura aure ranar asabar, an yi taro sosai musamman ta ɓangaren Teema tun da ita aurenta ne na fari, kuma ita ta farko mace da mahaifinta zai fara yi ma aure. Yadda Hilal yaƙe yaƙar baki yana amsa gaisuwar mutane da ala sa albarka sai ka ɗauka auren so da ƙauna ne suka yi shi da Teema, tun da sha biyu aka ɗaura aure aka yi liyafar cin abinci bayan a sauko daga sallar azahar. Shi kam be samu dawowa gidansa ba sai da yamma ta yi lis.
Yadda ya tararda Kalsoom be yi zaton zai same ta haka ba, ta bala'in ruɗashi, kyau tayi har na fitar hankali, bakar shaddace jikinta an mata riga da saket, ɗinkin ya matse ta ya fitarda surar jikinta sosai, ta kashe ɗaure ɗankwalinta ya kalli kudu masu gabas, ga wata uwar kwalliyar kanti da aka mata a fuska, yadda take motsa bakinta ma abun kallo ne.
“Ango ka sha mai”
Ta faɗa tana wani fari da ido. Shi dai mutuwar tsaye yayi a ƙofar falon yana kallonta, sallama ma sai ta gagari bakinsa, ji yayi kamar ya je ya rumgumeta sai dai ƙanenta da kuma Amiyarta Salma dake falon sun han shi rawar gaban hantsi.
Yana amsa gaisuwar da suke masa ya nufi ɗakinsa, zuciyarsa cike da ƙaunar matarsa, dan yaji daɗin halin daya same ta ta bashi ƙwarin guiwa sosai, shi da ya zo da zimmar ya lallaɓata kar ta saka ranta a damuwa, sai gashi yaga kamar ma ta fi shi farinciki.
Babbar rigarsa ya fara cirewa sannan ya zauna saman gado, sai gata ta shigo hannunta riƙe da copin madara ta yanka masa ayaba ciki ta saka sugar kaɗan. Saman ƙafafunsa ta zauna ta riƙa aika masa madarar a baki, shi ko sai wani lumshe ido yake yana buɗewa kamar wani tsohon ɗan iska, kamin yasa hannayensa ya zagaye kunkurunta.
“Wannan ado haka ai sai ki haukata, so kike amaryar nan ta rasa gane kai na ko?”
Murmushi ta yi ta aje kofin a ƙasa tasa hannayenta ta riƙa kunnensa ta ɗora goshinta saman nasa.
“Ai niban yarda zata gane kan ka ba, dan wata mace bata isa ta shigo gidana ta fini gane mijina ba, da dai Rashida ce da ita ba zan musa mata ba, saboda ta rigani saninka, ni kuma a yanzu na fi Amaryar ka sanin waye kai”
Murmushi yayi yana shafa bayanta da suka hannayensa biyu. Dauke kanta tayi daga nassa but stilll hannayenta na rike da kunnensa guda biyu.
“Wai ance ƙawar Rashida ce da gaske?”
Ya ɗaga mata kai yana wani lumshe idonsa da suka kaɗe.
“Uhnn amman ai ba ni nace ina son ta ba, Hajiya ce ta haɗa auren saboda ta yaba da tarbiyarta”
Ta yi murmushi kamar ba komai, alhalin na ciki na ciki.
“To Allah ya baku zama lafiya”
Sai ta saki kunnensa ta riƙa hannayensa dan tana jin yana ƙoƙarin wuce gona da iri, ta miƙe tsaye.
“Ina zaki?”
“Aiki zanje na ƙarasa”
Yayi saurin miƙa hannu ya riƙota.
“Haba karki zalince ni baiwar Allah”
“Ba wani zalinci, nima fa mai tsada ce kamar amarya, dan haka ni jiki zaka siya ba baki ba”
“Ai har kin fi amarya tsada, ke da ga wannan ciki, amman dai amin farashi mai sauƙi ta yadda zan iya biya”
“Ba yanzu zamu yi cininki ba, kai fa ango ne karka manta, nan da ƙarfe goma na dare sai yadda ka ga dama zaka yi da amaryarka”
“Bari wanka da kashi indan ganin hadari, ayi jiran abunda ba tabbas bayan ga ki ina gani”
Ta fisge hannunta ta nufi ƙofa.
“Ni kan nan gani na bari wannan wunin da daren ba nawa ba ne”
Ganin zata fice da gaske yasa shi wara ido, jikinsa a mace yace
“Wai da gaske kike yi? Ki taimaki bawon Allah, karki jefa rayuwarsa cikin haɗari”
“Au naka wasa ne kenan!”
Ta fice tana dariya kamar ba komai, sai dai can cikin zuciyarta ji take kamar an aza mata garwashin wuta a ciki, saboda kishi da baƙinciki. Tana ta ƙoƙarin yaƙar zuciyarta ne, dan bata son ta saka kanta cikin matsala saboda cikin dake jikinta, daman can lafiyar cikin be isheshi ba, idan kuma tace zata saka damuwa a ranta, to zata cutar da kanta ne kawai, tun dai aure an ɗaura, kuma tasan mijinta yana sonta, sai dai ɗan kishi da ba'a rasa ba.
Bayan fitarta, ta shiga bathroom ɗinsa yayi wanka, ya fito ya shirya cikin wata shaddar gizna mai kyau da sheƙi. Yana cikin saka agogon hannunsa Kalsoom ta shigo ɗakin ɗauke da plate ɗin abinci. Fried rice ce and pepper chicken sai ƙamshi take, kallo ɗaya yyi ma abincin ya ɗauke idonsa wai shi ala dole yana fushi da ita.
“Waya ce miki abincin zan ci? Ai ba yunwa na ke ji ba”
“Shikenan kuma ango sai yayi fushi ranar aurensa?”
“Waya ja nayi fushin? Sai ka taɓa abu a hanaka lasawa, ai wannan cin zalin ne”
Gwalo ta mishi taja ƙofar ta fice. Sai ta fashe da dariya.
“I love you”
Ya furta tana shirin zama ya ci abincin. Shi kansa be san yaji yunwa kamar haka ba sai yanzu, tass ya cinye abinci da da lemun kankana data haɗa masa mai lemun tsami ciki da sugar kaɗan, har ƙashin sai da ya taune ya tsotse ruwan, dan yaji daɗin abincin sosai, ga lemun da sanyi sai rmratsa ƙwaƙwalwarsa yake, bayan ya gama ya tashi yana hamdala. Tana shigowa ta saka masa ɗariya, har da riƙe ciki.
“Ni dai nasan mijin Amarya yana jin yunwa”
Shima dariyar kansa yake dan yasan yayi aiki.
“Ai ba ni na ci ba, aljanuna ne suka ci”
Matsawa yayi ya maita kiss a goshi.
“Amarya tace ta yafe miki daren nan na ta”
“Uhmmmm”
Ta wara ido.
“Wace sakaryar amaryace zata yarda ta yafe wannan daren mai tsada a rayuwar ko wacw ya mace, balle kuma da gwarzon namiji kamar ka”
Ya kalli kansa yana wani kaɗe shaddarsa.
“Allah? Ina jin daɗin yadda kike yaba ni”
“Ai ka haɗu ne Malam, dole a faɗa”
Ya riƙa fuskarta ransa fari ƙal da farinciki.
“I love you so so so very much”
Murmushi ta masa as respond, ya fice yana dariya. Sai ta ji tashin motarsa cire ɗankwalinta ta jefar, ta faɗa saman gadonsa ta fashe da kuka.
ASIM POV.
“Yes...!”
Ya bugi ganbun motarsa yana dariyar da har zuciyarsa ita ce.
Tayi tsayuwar minti ɗaya a gurin zuwa biyu, kamin ya ɗago ya kalleta ta cika sosai da taji kamar ta jefa masa wata baƙar magana amman bakinta be bata haɗin kai ba, gashi sai jin take kamar ta jefa masa carpet ɗin, sai dai kwajininsa ya hana hannunta kuzari, ballema ta yi ƙoƙarin yin hakan.
Babu enough hasken da zai iya haske fusakarta sosai, amman hakan be hana shi karantar tana ciki fushi ba, ko ba komai yasan ya ɓata mata lokaci, kuma ya shiga huruminta na ƙinjin gargaɗin da tayi masa akan kar ƙafarsa ta sake tako ƙofar gidansu.
“Ƙomai naki kyau yake min Namra, fushinki da faɗanki da tsawarki duka burgeni suke, abu ɗaƴa ya rage min yanzu na gani naki, shine dariyarki”
Ya faɗa yayinda ya ke cigaba da dannar wayarsa, amman hankalinsa da idonsa suna kan Namra. Wannan karon tayi nasarar yaudarar kanta, har ta samu haɗin kan idanuwanta, ta jefe Abdool da wani shegen kallo.
“Carpet ɗin ka kawai na fito kawo maka, ban fito dan ka yaba fushi ko faɗa na ba, kuma bana tunanin an halicceka dan ka ga dariyata kawai, saboda haka karka ɓatawa kanka lokaci, ka karɓi Carpet ɗin ka”
“Miya hana ki bar carpet ɗin a inda na barta tun ranar? Wane salo ne yasa kika ɗauke ta? Yanzun da nazo na aika nace a bani carpet ne? Wato ba zaki iya ganin abun Abdool ki ƙyale ba ko?”
Wannan karon da murmushi a fuskarsa, ya soka mata wannan maganar, ya gyara tsayuwarsa yana kallon taurarin da suka yi sama ado.
“Ai mu ƴaƴan Sarakuna bama shimfiɗa kuma bama ɗaukewa, wacan karon ma ba na shimfiɗawa kai na bane a karon kai na, nasan wata rana zan rubuta a diary, bayan Mai Martaba da Ummina, na taɓa shimfiɗawa Namra carpet har ma na zauna da ni da ita”
“Amman kai ka baka da aikin yi Wallahi, Allah yayi min tsare da mugun ƙudirinka, baka cikin hayyacinka ne? Miyasa zaka zo kana min wasu kalamai kamar wanda be san halin da nake ciki ba?”
“Ina ma ina da mugun ƙudiri a kanki! Da kin ga yanzu sace ci kawai zan yi na gudu naje nayi rayuwarda da nake so da ke, ni kaina ina mamakin halin dana shiga saboda ke, ban san miyasa ƙwaƙwalwata take ƙoƙarin zautuwa da lamarin ki ba”
Kai ta girgiza ta jefar da carpet ɗin a ƙasa.
“Wallahi baka da tausayi baka da tunani kwata-kwata a zuciyarka, taya zaka kalleni ka yi irin wannan maganar, you're fake Prince ba asalin Yariman ƙwarai bane kai, wata ƙila sarautar ta ku ta ƙauye ce, dan yariman ƙwarai ba zai tsaya mace kamar ni tana faɗa masa magana ba”
Lumshe ido yayi yana murmushi, tare da tsutsar baki kamar mai shan Sweet Candy. Ko da ya buɗe idonsa har ta ɓace daga gurin kamar walkiya.
Murmushin da ke fuskarsa ya faɗaɗa, kamin ya shiga muhalin massages ya aika saƙo. Cikin mintunan da basu fi goma ba, sai ga wata mota ta faka a gurin ɗauke da Anty Amarya da Abbah.
“Ga gidan can”
Ya faɗa yana nuna musu da kai, sannan ya buɗe motarsa ya shiga. Su kuma suka doshi ƙofar gidan, Abbah ne ya tsaya daga waje, Anty Amarya ta kunna kai ciki, zuciyarta sai bugawa take fat fat fat...
HILAL POV.
Ba a'ayi wasu events ban da walima, daman can shi baya ra'ayi sai kuma aka ci sa'ah amaryar tasa uztaziyace ita bata da son duniya. Ranar jumma'ah akayi walimar bayana an saka amarya lalle kamar yadda al'ada ta gada. Sai aka ɗaura aure ranar asabar, an yi taro sosai musamman ta ɓangaren Teema tun da ita aurenta ne na fari, kuma ita ta farko mace da mahaifinta zai fara yi ma aure. Yadda Hilal yaƙe yaƙar baki yana amsa gaisuwar mutane da ala sa albarka sai ka ɗauka auren so da ƙauna ne suka yi shi da Teema, tun da sha biyu aka ɗaura aure aka yi liyafar cin abinci bayan a sauko daga sallar azahar. Shi kam be samu dawowa gidansa ba sai da yamma ta yi lis.
Yadda ya tararda Kalsoom be yi zaton zai same ta haka ba, ta bala'in ruɗashi, kyau tayi har na fitar hankali, bakar shaddace jikinta an mata riga da saket, ɗinkin ya matse ta ya fitarda surar jikinta sosai, ta kashe ɗaure ɗankwalinta ya kalli kudu masu gabas, ga wata uwar kwalliyar kanti da aka mata a fuska, yadda take motsa bakinta ma abun kallo ne.
“Ango ka sha mai”
Ta faɗa tana wani fari da ido. Shi dai mutuwar tsaye yayi a ƙofar falon yana kallonta, sallama ma sai ta gagari bakinsa, ji yayi kamar ya je ya rumgumeta sai dai ƙanenta da kuma Amiyarta Salma dake falon sun han shi rawar gaban hantsi.
Yana amsa gaisuwar da suke masa ya nufi ɗakinsa, zuciyarsa cike da ƙaunar matarsa, dan yaji daɗin halin daya same ta ta bashi ƙwarin guiwa sosai, shi da ya zo da zimmar ya lallaɓata kar ta saka ranta a damuwa, sai gashi yaga kamar ma ta fi shi farinciki.
Babbar rigarsa ya fara cirewa sannan ya zauna saman gado, sai gata ta shigo hannunta riƙe da copin madara ta yanka masa ayaba ciki ta saka sugar kaɗan. Saman ƙafafunsa ta zauna ta riƙa aika masa madarar a baki, shi ko sai wani lumshe ido yake yana buɗewa kamar wani tsohon ɗan iska, kamin yasa hannayensa ya zagaye kunkurunta.
“Wannan ado haka ai sai ki haukata, so kike amaryar nan ta rasa gane kai na ko?”
Murmushi ta yi ta aje kofin a ƙasa tasa hannayenta ta riƙa kunnensa ta ɗora goshinta saman nasa.
“Ai niban yarda zata gane kan ka ba, dan wata mace bata isa ta shigo gidana ta fini gane mijina ba, da dai Rashida ce da ita ba zan musa mata ba, saboda ta rigani saninka, ni kuma a yanzu na fi Amaryar ka sanin waye kai”
Murmushi yayi yana shafa bayanta da suka hannayensa biyu. Dauke kanta tayi daga nassa but stilll hannayenta na rike da kunnensa guda biyu.
“Wai ance ƙawar Rashida ce da gaske?”
Ya ɗaga mata kai yana wani lumshe idonsa da suka kaɗe.
“Uhnn amman ai ba ni nace ina son ta ba, Hajiya ce ta haɗa auren saboda ta yaba da tarbiyarta”
Ta yi murmushi kamar ba komai, alhalin na ciki na ciki.
“To Allah ya baku zama lafiya”
Sai ta saki kunnensa ta riƙa hannayensa dan tana jin yana ƙoƙarin wuce gona da iri, ta miƙe tsaye.
“Ina zaki?”
“Aiki zanje na ƙarasa”
Yayi saurin miƙa hannu ya riƙota.
“Haba karki zalince ni baiwar Allah”
“Ba wani zalinci, nima fa mai tsada ce kamar amarya, dan haka ni jiki zaka siya ba baki ba”
“Ai har kin fi amarya tsada, ke da ga wannan ciki, amman dai amin farashi mai sauƙi ta yadda zan iya biya”
“Ba yanzu zamu yi cininki ba, kai fa ango ne karka manta, nan da ƙarfe goma na dare sai yadda ka ga dama zaka yi da amaryarka”
“Bari wanka da kashi indan ganin hadari, ayi jiran abunda ba tabbas bayan ga ki ina gani”
Ta fisge hannunta ta nufi ƙofa.
“Ni kan nan gani na bari wannan wunin da daren ba nawa ba ne”
Ganin zata fice da gaske yasa shi wara ido, jikinsa a mace yace
“Wai da gaske kike yi? Ki taimaki bawon Allah, karki jefa rayuwarsa cikin haɗari”
“Au naka wasa ne kenan!”
Ta fice tana dariya kamar ba komai, sai dai can cikin zuciyarta ji take kamar an aza mata garwashin wuta a ciki, saboda kishi da baƙinciki. Tana ta ƙoƙarin yaƙar zuciyarta ne, dan bata son ta saka kanta cikin matsala saboda cikin dake jikinta, daman can lafiyar cikin be isheshi ba, idan kuma tace zata saka damuwa a ranta, to zata cutar da kanta ne kawai, tun dai aure an ɗaura, kuma tasan mijinta yana sonta, sai dai ɗan kishi da ba'a rasa ba.
Bayan fitarta, ta shiga bathroom ɗinsa yayi wanka, ya fito ya shirya cikin wata shaddar gizna mai kyau da sheƙi. Yana cikin saka agogon hannunsa Kalsoom ta shigo ɗakin ɗauke da plate ɗin abinci. Fried rice ce and pepper chicken sai ƙamshi take, kallo ɗaya yyi ma abincin ya ɗauke idonsa wai shi ala dole yana fushi da ita.
“Waya ce miki abincin zan ci? Ai ba yunwa na ke ji ba”
“Shikenan kuma ango sai yayi fushi ranar aurensa?”
“Waya ja nayi fushin? Sai ka taɓa abu a hanaka lasawa, ai wannan cin zalin ne”
Gwalo ta mishi taja ƙofar ta fice. Sai ta fashe da dariya.
“I love you”
Ya furta tana shirin zama ya ci abincin. Shi kansa be san yaji yunwa kamar haka ba sai yanzu, tass ya cinye abinci da da lemun kankana data haɗa masa mai lemun tsami ciki da sugar kaɗan, har ƙashin sai da ya taune ya tsotse ruwan, dan yaji daɗin abincin sosai, ga lemun da sanyi sai rmratsa ƙwaƙwalwarsa yake, bayan ya gama ya tashi yana hamdala. Tana shigowa ta saka masa ɗariya, har da riƙe ciki.
“Ni dai nasan mijin Amarya yana jin yunwa”
Shima dariyar kansa yake dan yasan yayi aiki.
“Ai ba ni na ci ba, aljanuna ne suka ci”
Matsawa yayi ya maita kiss a goshi.
“Amarya tace ta yafe miki daren nan na ta”
“Uhmmmm”
Ta wara ido.
“Wace sakaryar amaryace zata yarda ta yafe wannan daren mai tsada a rayuwar ko wacw ya mace, balle kuma da gwarzon namiji kamar ka”
Ya kalli kansa yana wani kaɗe shaddarsa.
“Allah? Ina jin daɗin yadda kike yaba ni”
“Ai ka haɗu ne Malam, dole a faɗa”
Ya riƙa fuskarta ransa fari ƙal da farinciki.
“I love you so so so very much”
Murmushi ta masa as respond, ya fice yana dariya. Sai ta ji tashin motarsa cire ɗankwalinta ta jefar, ta faɗa saman gadonsa ta fashe da kuka.
ASIM POV.
“Yes...!”
Ya bugi ganbun motarsa yana dariyar da har zuciyarsa ita ce.