Sashe 31
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ki basu takardar biyan hospital bill kuma ki faɗa musu inda zasu je su biya”
Daga haka ya wuce, ya bar Nurse ɗin tana duba adadin abunda aka kashe musu, sai ta ware wata takardar ta daban ta rubuta mata kuɗin ta miƙa mata.
“Idan kin wuce pharmacy zaki ga gurin da ake biya, idan kin biya sai ki zo na baki transfer”
Daga haka ta wuce ta bar Namra da Mama tsaye suna hawaye. Zaunawa Mama tayi a kujerar roba da take gurin. Namra kuma ta fito ita da Mardiya tana duba jakarta.
Kwata-kwata kuɗin da yake ciki be wuce ɗari bakwai ba, saboda abincin data siya ma Mama da Mardiya da kuma ƙanwarsa.
“Amman yanzu kina da kuɗin biya kuwa”
Mardiya ta tambaya tana kallon yadda idon Namra ke zubar da ƙwalla.
“Muje ki raka ni na karɓo waya na”
Shine kawai abunda Namra ta faɗa, taja hannun Mardiya suka nufi gate. Napep suka tare suka shiga, ta sauke su dai-dai bakin pharmacy. Namra ta bashi ɗari biyu sannan suka shiga cikin Pharmacy.
Bata sha wahala gurin su gane ta ba, saboda kayan jiya ne a jikinta. Bayan sun gaisa tace
“Ka gane ni?”
“Eh ba kece ta jiya mai waya ba? Ana ta kiran wayar ta tun jiya”
“Dan Allah wayar zaka bani na kira”
“Tau kin zo da kuɗin ko?”
“A'a waya zan kira naji ko an turo”
“Toh sai dai idan nan a zakiyi kiran”
“Eh a nan zan yi”
Sai da suka yi kamar kar su bata sai kuma ɗayan ya ɗauko ya miƙa mata. Number Anty Amarya ta fara kira, daman ta ga missed call nata a calls list. Ringing biyu Anty Amarya ta ɗauka da sallama.
“Anty ina wuni ya hanya?”
“Alhamdulillah ya jikin Asim ɗin?”
“Ba sauƙi Anty yanzu haka likitan ya tura mu
zuwa babbar asibitin Katsina, kuma ba ni kuɗi”
“Allah ya sauwake, nima kuɗin da nace zan aiko miki ban samu ba, daman ina jiran Abbah ku ya bani kuɗin da nake binsa ne sai na aiko miki”
Wani irin abu Namra ta ji ya daki tsakiyar kanta zuwa cikin ƙafafunta. Ta san da gangan Anty Amarya tayi mata haka ba dan bata da kuɗin ba. Da na gode ta amsa mata ta kashe wayar, tana hawaye.
Number Maryam ta lalabo ta danna mata kira, tana yin pincking sai Namra tasa mata kuka.
“Maryam dan Allah taimako nake nema a gareki”
“Taimakon me?”
“Dan Allah kuɗi nake son ki ara min ko nawa ne dan Allah, Wallahi zan biya ki har da waɗancan ma”
“Anty Namra ban taɓa ara miki kuɗi dan ki biyani ba, duk abunda na baki a kyauta nake baki shi, gaskiya yanzu bana da kuɗi hannu na, amman ki tambayi Anty ba za'a rasa ba”
Namra bata ƙara cewa komai ba, sai kawai ta kashe wayar, ta fashe da wani irin kuka mai taɓa zuciya. Mardiya duk sai ta tsargu ta duƙa a gurin tana bata haƙuri.
Wata Hajiya dake kusa da ita ta kalle tana tambayar lafiya. Sai masu pharmacy suka mata bayani, cike da tausayawa ta kalli Namra tace
“Tashi Bawai Allah zan biya miki, Allah ya bashi lafiya”
Gyalenta Namra ta riƙa tana mata godiya.
“Allah ya saka miki da Alheri, na gode sosai”
Sai ta kalli Mutumen.
“Dan Allah ina ka san za'a iya siyen wayar nan?”
“Gaskiya sai kasuwar Ƴan wayoyi, dan wannan wayar mai tsada ce can ne kawai zasu iya siyen ta”
Yana faɗar hakan Mardiya ta zaro ido tana ƙara kallon wayar dake hannun Namra. Hajiyar ta kalleta.
“Haba ke kuwa kar ki siyar da wayar ki mana”
“Dole ne na siyar kuɗin asibiti zan biya”
Namra ta faɗa cikin kuka. Tun daga sama har ƙasa Hajiyar ta kalli Namra sannan tace
“Nawa ne kuɗin?”
“Dubu ashirin da shida da ɗari bakwai”
Hajiyar ta kalli yaron pharmacy
“Nawa ne kuɗin ka har nata?”
“Ya kama dubu takwas da ɗari huɗu”
Dubu tara ra ƙirgo ta miƙa masa, bata tsaya karɓar canja ba, ta kalli Namra.
“Muje cikin Mota na muga marar lafiyar”
Da sauri Namra ta fita ita da Mardiya, har suka riga Hajiyar isa gurin motar. Sai da ta buɗe ta shiga sannan ta buɗe musu tace su shigo.
Namra ce a front seat Mardiya a baya. Hajiyar tana yi tana satar kallon Namra. Ita kuma natsuwarta bata tare da ita, tambayar da take mata ma sama-sama take amsa mata.
“A nan garin kuke?”
“A'a Katsina nake zama, shine ma suka mana transfer zuwa can”
“Allah sarki wane unguwa a katsina, nima a katsina nake”
“Nasarawa”
Ta amsa mata dai'-dai lokacin data tayi parking, a harabar asibitin. Sai da taje ta duba Asim tayi ma mahaifiyarsa sannu ta suka je tare da Namra ta biya mata kuɗin Asibiti. Aiko Namra da dingi mata godiya kamar wanda tayi mata kyautar rai.
“Ba komai Wallahi, ai yi ma kai ne. Muje ki kai musu takardar su baki wacan sai muje katsina ɗin, dan nima yanzu can zan wuce”
Komawa suka yi, Namra taje ta kai ma Nurse ɗin takardar ta bata ta transfer ɗin, sannan ta dawo ta kawo ma Hajiyar. Ita ta ciri kuɗi a jakarta ta miƙawa Mardiya tace taje ta siyo masa shorts da ƴar riga a saka masa. Sannan taje ta biya dubu biyu aka basu ambulance, wanda za'a kai Asima ciki.
Mama da Hajaru (ƙanwar Asim) ne suka shiga ambulance ɗin tare da Asim. Namra da Mardiya kuma suka shiga motar Hajiyar, Tun kamin motar ta tashi Mardiya ta karɓi jakar Namra wai ta kawo ta riƙa mata. Ba musu Namra ta miƙa mata daman jakar ta yi mata nauyi.
Yadda take tuƙa motar kamar wata fitacciyar direba, dan da ita da ambulance ɗin ba zaka iya gane wanda yafi gudu ba.
Daf da Magariba suka isa Katsina, kai tsaye Babbar Asibitin suka suka wuce. Emergency Motar ta shiga Hajiyar na binta a baya. Suna shiga aka karɓe shi aka wuce da shi Anas room wato ɗakunan da aka tana na marar lafiya shi kaɗai dan bashi kulawa na musamman. Sai da Hajiyar ta biya dubu goma sha shida na ɗakin sannan aka aje shi, nan take suka soma bashi kulawar gaggawa abunka da babbar asibiti.
Godiya sosai Namra tayi ma mata har ta rasa yadda zata nuna mata jindaɗinta.
“Babu komai Allah ya bashi lafiya, ni yanzu zan wuce gida idan wani abun ya taso ki neme ni a wannan address ɗin”
Hajiyar ta faɗa tana murmushi tare da miƙa mata katin ta. Da hannu biyu Namra ta karɓa, ta raka ta har gurin motar ta, sannan ta dawo.
A Dai-dai lokacin ne likitan ya fito daga ɗakin da Asim yake ya nufo Mama yana magana da ita.
“Za'ayi masa gyara a cinyar ƙafarsa, sai kuje ku biya kuɗin, kuma za a siye masa jiki kamar na gora uku, kuje kuma ku biya kuɗin magani”
Ya ƙarasa faɗar yana miƙawa Mama takardun hannunsa guda uku. Da muguwar damuwa Mama ta karɓi takardar irin bani da madafa ɗin nan. Sai Namra tasa hannu ta karɓa, tana kallon likitan
“Idan ya kai gobe ba komai?”
“Ba matsala, amman dai ku ƙoƙarta kar ya wuce goben”
“Tau mun gode”
Bayan likitan ya wuce Namra ta shiga kwantar ma Mama hankali
“Mama ki shiga ki zauna da shi, ni zan je gida naga ko akwai abunda zan samo”
“Tau”
Ta faɗa da muryar kuka sannan ta shiga ɗaki. Namra ta juya ita da Mardiya suka nufi gida.
Mai Napep na sauke su Mardiya ta miƙawa Namra jakarta, ta nufi gidansu. Cikin kasalar jiki Namra ta buɗe ƙofar gate ɗin ta shiga. Ta daɗe a tsaye jikin ƙofar falon tana kuka, sannan ta buɗe ta shiga.
Wanka ne abunda ta fara yi, ta saka wasu tufafin sannan ta shiga kitchen ta ɗora indomie, a gaggauce ta dafa ta zuba a kula, ta haɗa ma kanta tea kaɗan ta sha, sannan ta dawo ta fito da tabarma da filo da bargo guda biyu, ta aje falo ta ɗauko plates huɗu da spoons da kofuna ta saka a basket, ta aje a falo. Duk abunda take Asim ne a ranta, tunani take inda zata samo kuɗin da za'ayi masa aiki, har kuma ta gama bata samarwa kanta wata mafita ta bayan ta siyar da wayarta.
Mayafinta ta ɗauka ya saka ta fita ta nufi gidansu Mardiya. Da sallamarta ta shiga, mataɓ gidan suka amsa mata, suna mata ya mai jiki. Sai da ta gama gaisawa da su sannan ta wuce ɓangaren su Mardiya, kasancewar gudan irin tsohon gidan nan ne da ake na dangi mai ɗakuna da yawa.
Bata tararda Mamarta ba, sai Mardiya dake sallah. Zaunawa tayi saman simintin ɗakin tana jira ta gama. Bayan ta sallame ta juyo ta kalli Namra.
“Namra har kin yi wanka?”
“Tun ɗazu, dan Allah so nake ki kai ma Mama abinci da wasu abubuwan da za su buƙata, kuma dan Allah idan kin san inda ake fansar da waya ki kai ni ina son siyar da wayar ne”
“Kai yanzu kam sun tashi kin ga har tara ta gota fa, sai dai gobe, sai na rakaki ki kai”
“Abincin fa?”
“Muje na kai musu”
Ta faɗa tana ƙoƙarin tashi. Tare suka fito gidan. Tun da suka fito Mardiya take abu kamar mai jin kunya, har suka shiga cikin gidan. Namra ta bata kayan ta ɗauko sauran canjin dake jakarta ta miƙa mata wai tayi na okada da su.
Bayan ta wuce, Namra ta sake buɗe jakarta ta ɗauko waya, sai taga wayam, babu waya babu alamunta, a nan fa hankalinta ya tashi, sai ta zazzage jakar gaba ɗaya, bata ga wayar ba.
Jikinta be bata ta jefar da wayar a cikin gidan ba, amman haka tabi ta yamutse gidan tana neman wayar.
Har Mardiya ta dawo bata ganta ba, idonta duk ya rine tana jin kamar tayi kuka ba hawaye.
Ita kanta ta lura da yadda Namra ta ƙara firgicewa.
“Na kai musu, tace wai na faɗa miki likita ya sake zuwa”
Hannu Namra ta ɗora saman kai ta fashe da kuka
“Kai Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, kin ga wayar ma da nake son saidawa ban ganta ba, ko kin ga inda na jefar”
Wani irin dakan ƙirji Mardiya tayi
Daga haka ya wuce, ya bar Nurse ɗin tana duba adadin abunda aka kashe musu, sai ta ware wata takardar ta daban ta rubuta mata kuɗin ta miƙa mata.
“Idan kin wuce pharmacy zaki ga gurin da ake biya, idan kin biya sai ki zo na baki transfer”
Daga haka ta wuce ta bar Namra da Mama tsaye suna hawaye. Zaunawa Mama tayi a kujerar roba da take gurin. Namra kuma ta fito ita da Mardiya tana duba jakarta.
Kwata-kwata kuɗin da yake ciki be wuce ɗari bakwai ba, saboda abincin data siya ma Mama da Mardiya da kuma ƙanwarsa.
“Amman yanzu kina da kuɗin biya kuwa”
Mardiya ta tambaya tana kallon yadda idon Namra ke zubar da ƙwalla.
“Muje ki raka ni na karɓo waya na”
Shine kawai abunda Namra ta faɗa, taja hannun Mardiya suka nufi gate. Napep suka tare suka shiga, ta sauke su dai-dai bakin pharmacy. Namra ta bashi ɗari biyu sannan suka shiga cikin Pharmacy.
Bata sha wahala gurin su gane ta ba, saboda kayan jiya ne a jikinta. Bayan sun gaisa tace
“Ka gane ni?”
“Eh ba kece ta jiya mai waya ba? Ana ta kiran wayar ta tun jiya”
“Dan Allah wayar zaka bani na kira”
“Tau kin zo da kuɗin ko?”
“A'a waya zan kira naji ko an turo”
“Toh sai dai idan nan a zakiyi kiran”
“Eh a nan zan yi”
Sai da suka yi kamar kar su bata sai kuma ɗayan ya ɗauko ya miƙa mata. Number Anty Amarya ta fara kira, daman ta ga missed call nata a calls list. Ringing biyu Anty Amarya ta ɗauka da sallama.
“Anty ina wuni ya hanya?”
“Alhamdulillah ya jikin Asim ɗin?”
“Ba sauƙi Anty yanzu haka likitan ya tura mu
zuwa babbar asibitin Katsina, kuma ba ni kuɗi”
“Allah ya sauwake, nima kuɗin da nace zan aiko miki ban samu ba, daman ina jiran Abbah ku ya bani kuɗin da nake binsa ne sai na aiko miki”
Wani irin abu Namra ta ji ya daki tsakiyar kanta zuwa cikin ƙafafunta. Ta san da gangan Anty Amarya tayi mata haka ba dan bata da kuɗin ba. Da na gode ta amsa mata ta kashe wayar, tana hawaye.
Number Maryam ta lalabo ta danna mata kira, tana yin pincking sai Namra tasa mata kuka.
“Maryam dan Allah taimako nake nema a gareki”
“Taimakon me?”
“Dan Allah kuɗi nake son ki ara min ko nawa ne dan Allah, Wallahi zan biya ki har da waɗancan ma”
“Anty Namra ban taɓa ara miki kuɗi dan ki biyani ba, duk abunda na baki a kyauta nake baki shi, gaskiya yanzu bana da kuɗi hannu na, amman ki tambayi Anty ba za'a rasa ba”
Namra bata ƙara cewa komai ba, sai kawai ta kashe wayar, ta fashe da wani irin kuka mai taɓa zuciya. Mardiya duk sai ta tsargu ta duƙa a gurin tana bata haƙuri.
Wata Hajiya dake kusa da ita ta kalle tana tambayar lafiya. Sai masu pharmacy suka mata bayani, cike da tausayawa ta kalli Namra tace
“Tashi Bawai Allah zan biya miki, Allah ya bashi lafiya”
Gyalenta Namra ta riƙa tana mata godiya.
“Allah ya saka miki da Alheri, na gode sosai”
Sai ta kalli Mutumen.
“Dan Allah ina ka san za'a iya siyen wayar nan?”
“Gaskiya sai kasuwar Ƴan wayoyi, dan wannan wayar mai tsada ce can ne kawai zasu iya siyen ta”
Yana faɗar hakan Mardiya ta zaro ido tana ƙara kallon wayar dake hannun Namra. Hajiyar ta kalleta.
“Haba ke kuwa kar ki siyar da wayar ki mana”
“Dole ne na siyar kuɗin asibiti zan biya”
Namra ta faɗa cikin kuka. Tun daga sama har ƙasa Hajiyar ta kalli Namra sannan tace
“Nawa ne kuɗin?”
“Dubu ashirin da shida da ɗari bakwai”
Hajiyar ta kalli yaron pharmacy
“Nawa ne kuɗin ka har nata?”
“Ya kama dubu takwas da ɗari huɗu”
Dubu tara ra ƙirgo ta miƙa masa, bata tsaya karɓar canja ba, ta kalli Namra.
“Muje cikin Mota na muga marar lafiyar”
Da sauri Namra ta fita ita da Mardiya, har suka riga Hajiyar isa gurin motar. Sai da ta buɗe ta shiga sannan ta buɗe musu tace su shigo.
Namra ce a front seat Mardiya a baya. Hajiyar tana yi tana satar kallon Namra. Ita kuma natsuwarta bata tare da ita, tambayar da take mata ma sama-sama take amsa mata.
“A nan garin kuke?”
“A'a Katsina nake zama, shine ma suka mana transfer zuwa can”
“Allah sarki wane unguwa a katsina, nima a katsina nake”
“Nasarawa”
Ta amsa mata dai'-dai lokacin data tayi parking, a harabar asibitin. Sai da taje ta duba Asim tayi ma mahaifiyarsa sannu ta suka je tare da Namra ta biya mata kuɗin Asibiti. Aiko Namra da dingi mata godiya kamar wanda tayi mata kyautar rai.
“Ba komai Wallahi, ai yi ma kai ne. Muje ki kai musu takardar su baki wacan sai muje katsina ɗin, dan nima yanzu can zan wuce”
Komawa suka yi, Namra taje ta kai ma Nurse ɗin takardar ta bata ta transfer ɗin, sannan ta dawo ta kawo ma Hajiyar. Ita ta ciri kuɗi a jakarta ta miƙawa Mardiya tace taje ta siyo masa shorts da ƴar riga a saka masa. Sannan taje ta biya dubu biyu aka basu ambulance, wanda za'a kai Asima ciki.
Mama da Hajaru (ƙanwar Asim) ne suka shiga ambulance ɗin tare da Asim. Namra da Mardiya kuma suka shiga motar Hajiyar, Tun kamin motar ta tashi Mardiya ta karɓi jakar Namra wai ta kawo ta riƙa mata. Ba musu Namra ta miƙa mata daman jakar ta yi mata nauyi.
Yadda take tuƙa motar kamar wata fitacciyar direba, dan da ita da ambulance ɗin ba zaka iya gane wanda yafi gudu ba.
Daf da Magariba suka isa Katsina, kai tsaye Babbar Asibitin suka suka wuce. Emergency Motar ta shiga Hajiyar na binta a baya. Suna shiga aka karɓe shi aka wuce da shi Anas room wato ɗakunan da aka tana na marar lafiya shi kaɗai dan bashi kulawa na musamman. Sai da Hajiyar ta biya dubu goma sha shida na ɗakin sannan aka aje shi, nan take suka soma bashi kulawar gaggawa abunka da babbar asibiti.
Godiya sosai Namra tayi ma mata har ta rasa yadda zata nuna mata jindaɗinta.
“Babu komai Allah ya bashi lafiya, ni yanzu zan wuce gida idan wani abun ya taso ki neme ni a wannan address ɗin”
Hajiyar ta faɗa tana murmushi tare da miƙa mata katin ta. Da hannu biyu Namra ta karɓa, ta raka ta har gurin motar ta, sannan ta dawo.
A Dai-dai lokacin ne likitan ya fito daga ɗakin da Asim yake ya nufo Mama yana magana da ita.
“Za'ayi masa gyara a cinyar ƙafarsa, sai kuje ku biya kuɗin, kuma za a siye masa jiki kamar na gora uku, kuje kuma ku biya kuɗin magani”
Ya ƙarasa faɗar yana miƙawa Mama takardun hannunsa guda uku. Da muguwar damuwa Mama ta karɓi takardar irin bani da madafa ɗin nan. Sai Namra tasa hannu ta karɓa, tana kallon likitan
“Idan ya kai gobe ba komai?”
“Ba matsala, amman dai ku ƙoƙarta kar ya wuce goben”
“Tau mun gode”
Bayan likitan ya wuce Namra ta shiga kwantar ma Mama hankali
“Mama ki shiga ki zauna da shi, ni zan je gida naga ko akwai abunda zan samo”
“Tau”
Ta faɗa da muryar kuka sannan ta shiga ɗaki. Namra ta juya ita da Mardiya suka nufi gida.
Mai Napep na sauke su Mardiya ta miƙawa Namra jakarta, ta nufi gidansu. Cikin kasalar jiki Namra ta buɗe ƙofar gate ɗin ta shiga. Ta daɗe a tsaye jikin ƙofar falon tana kuka, sannan ta buɗe ta shiga.
Wanka ne abunda ta fara yi, ta saka wasu tufafin sannan ta shiga kitchen ta ɗora indomie, a gaggauce ta dafa ta zuba a kula, ta haɗa ma kanta tea kaɗan ta sha, sannan ta dawo ta fito da tabarma da filo da bargo guda biyu, ta aje falo ta ɗauko plates huɗu da spoons da kofuna ta saka a basket, ta aje a falo. Duk abunda take Asim ne a ranta, tunani take inda zata samo kuɗin da za'ayi masa aiki, har kuma ta gama bata samarwa kanta wata mafita ta bayan ta siyar da wayarta.
Mayafinta ta ɗauka ya saka ta fita ta nufi gidansu Mardiya. Da sallamarta ta shiga, mataɓ gidan suka amsa mata, suna mata ya mai jiki. Sai da ta gama gaisawa da su sannan ta wuce ɓangaren su Mardiya, kasancewar gudan irin tsohon gidan nan ne da ake na dangi mai ɗakuna da yawa.
Bata tararda Mamarta ba, sai Mardiya dake sallah. Zaunawa tayi saman simintin ɗakin tana jira ta gama. Bayan ta sallame ta juyo ta kalli Namra.
“Namra har kin yi wanka?”
“Tun ɗazu, dan Allah so nake ki kai ma Mama abinci da wasu abubuwan da za su buƙata, kuma dan Allah idan kin san inda ake fansar da waya ki kai ni ina son siyar da wayar ne”
“Kai yanzu kam sun tashi kin ga har tara ta gota fa, sai dai gobe, sai na rakaki ki kai”
“Abincin fa?”
“Muje na kai musu”
Ta faɗa tana ƙoƙarin tashi. Tare suka fito gidan. Tun da suka fito Mardiya take abu kamar mai jin kunya, har suka shiga cikin gidan. Namra ta bata kayan ta ɗauko sauran canjin dake jakarta ta miƙa mata wai tayi na okada da su.
Bayan ta wuce, Namra ta sake buɗe jakarta ta ɗauko waya, sai taga wayam, babu waya babu alamunta, a nan fa hankalinta ya tashi, sai ta zazzage jakar gaba ɗaya, bata ga wayar ba.
Jikinta be bata ta jefar da wayar a cikin gidan ba, amman haka tabi ta yamutse gidan tana neman wayar.
Har Mardiya ta dawo bata ganta ba, idonta duk ya rine tana jin kamar tayi kuka ba hawaye.
Ita kanta ta lura da yadda Namra ta ƙara firgicewa.
“Na kai musu, tace wai na faɗa miki likita ya sake zuwa”
Hannu Namra ta ɗora saman kai ta fashe da kuka
“Kai Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, kin ga wayar ma da nake son saidawa ban ganta ba, ko kin ga inda na jefar”
Wani irin dakan ƙirji Mardiya tayi