Sashe 30
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da ya duba gabanta da bayanta, ya ce ta cire mishi password ya duba komai, sannan suka bata maganin.
Tana fitowa cikin pharmacy ɗin, wani ƙaton mutum ya sha gabanta.
“Malama ana magana da ke a can”
Ya nuna mata wata shegiyar Mota mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali. Ɗauke kai tayi kamar bata ji shi ta cigaba da tafiyar tana kallon ti-ti ko zata samu Napep.
Jin tayi ana binta a baya, kuma ba takun mutum ɗaya ba, juyowar da zata yi sai ƙamshin wani daddaɗan turare ya daki hancinta.
Tsayawa tayi cak tana masa kallin jin dalilin binta da yake shi da bodyguards ɗinsa. Shi kuma ya tsaya a gurin yana mata wani kallo mai wuyar fassara.
Mashallah kyakkyawa ajin farko kuma ajin ƙarshen a kyau. Manyan idanuwansa, su suka fi komai kyau a halinta dake fuskarsa, manya ne sosai farin yayi fari, baƙin kuma kamar an shafa masa kwalli, hancinsa ya zauna a tsakiyar fuskarsa kamar anja masa layi, a ƙasan hancin an yanka masa wani hot lip pink color, shape ɗin fuskarsa mai faɗi kamar ƙirginsa. Robe ce a jikinsa mai kyau da ɗaukar hankali.
Ganin be ce mata komai ba, yasa ta juya da nufin cigaba da tafiyarta. Sai kawai yayi kuskuren kai hannunsa ya riƙa hijabinta, da nufin juwo da ita.
Tassssssss. Ta sauke masa lafiyayyen mari a fuska. Da sauri Bodyguards ɗinsa suka zaburo za su kai mata duka, sai yayi saurin ɗaga musu hannu.
“Baka da hankaline da zaka kai hannunka ka taɓa min Hijabi? An faɗa maka kowa wace mace ce ƴar iska? Kasan muhimmancin hijabi da zaka saka wulaƙantacen hannunka ka taɓa min Hijabi? Ni matar aure ce dan haka ka shiga hankalin ka”
Duk balbalin bala'in da take masa, kallonta yake fuskarsa da murmushi, har yanzu sanyin da laushin hannunta yake ji a gefen fuskarsa.
“Nima Mijin aure ne”
Ya faɗa lokacin daya ga tana ƙoƙarin juyawa. Awww Mashallah his voice was soft and sweet, such a nice voice irin ta larabawan nan masu ƙalƙala, wandanda baka gajiya da jin muryar su.
Wani dogon tsaki taja dai-dai lokacin data tsayar da mai Napep ta shiga tayi tafiyarta.
Har cikin ransa yake jin tsakin nata, yana yawo a ƙwaƙwalwarsa kamar wani blood.
“Abdul”
Da sauri wanda ya kira da Abdul ɗin ya matsa kusa dashi yana tsare masa.
“Sir”
“Rubuta Number Mai Napep ɗin can. 771A97K Funtua”
“Yes Sir”
Da sauri ya juya ta nufi gurin da suka yi parking ɗin motocinsu. Shi kam sai da ya daina hango Napep ɗin sannan hankalinsa ya dawo kansa.
‘For the first time in history wata mace ta ɗaga hannu ta mari Abdullah Ahmad Mai-doki’
A zuciyarsa yayi furucin yana mamakin kansa.
“Unique one”
Ya furta a fili. Sannan ya ce su zo da motocin ya shiga suka kama hanya.
Tana isa cikin asibitin ta kai ma likitan maganin yace ta bawa Nurse. Haka suka kwana a kansa ita da Mardiya, ko wanne ya shimfiɗa ɗankwalinsa ya kwanta. Sai dai Mardiya ce kawai tayi bachi Namra kam har safe idonta biyu.
Da safe ita ta bawa Mardiya kuɗi tta siyo abinci a ƙofar asibitin ta karya, ita kam jasa cin komai tayi har likita ya shigo.
Bayan ya gama duba shi ya sake sa masa drip, a cikin drip ɗin yayi masa alluran da aka siyo sannan ya miƙa mata wasu magungunan yace idan ya farka ta bashi.
“Amman likita har yanzu be buɗe ido ba”
“Zai buɗe yana da rai fa, kawai yaji jiki ne, mai yiyu juwa anjima ya buɗe idon, amman inda hali ku kai shi babbar asibitin Katsina dan akwai yiyuwar sai an masa aiki a ƙafarsa, saboda kashinsa na cinya ya shige ciki”
“Innalillahi wa'inna ilaihi”
Ta faɗa tana faɗuwa zaune saman kujerar roba dake gurin.
“Allah ya bashi lafiya”
Wucewa ya yi gurin wasu marar lafiyar ya barta tana aikin kuka. Likitan be yi minti talatin da barin gurin ba, Sai ga Mama ta iso da kukanta. Aiko hankalinta ya tashi sosai da taga yadda fuskar ɗanta ya kumbuɗe kamar an busashi, gaba ɗaya halittarsa ta canja.
Yadda take rusa kuka sai yasa hankalin duk wanda yake gurin ya koma kanta, ƙanwar Asim sai haƙuri take bata tana kuka.
Guraren shaɗaya da rabi Anty Amarya ta iso tare da direban su da Aisha. Namra na ganinta ta fashe ta sabon kuka ta kwantar da kanta jikin Anty Amarya.
Anty Amarya ta danne kukanta, tana lallasar Namra.
“Ki yi haƙuri, Namra ki kwantar da hankalin ki, duk abunda ya kamata ayi masa za'a masa kinji? Idan ma waje ya kamata a fitar da shi za'a fitar, amman ki kwantar da hankalin ki”
Karaf Mama ta tsuma baki, tana mai jin zafin yadda Anty Amarya take lallarsar Namra ita ga ɗanta kwance.
“Ta kwantar da hankali kamar yaya? Ga mijinta kwance ki ce ta kwantar da hankalinta, ta nata ma kike ba ta Ibrahim ba, daman ai nasan ba son ƙwarai kuke masa ba, ni wannan aure bai zo da komai ba sai abun baƙinciki, gashi nan daga shigowarki gidansa ya koma da ƙafa ɗaya”
Da kuka ta ƙarasa maganar. Kallonta kawai Anty Amarya tayi ta ɗauke kai, tana mai jin zafin kalamanta. Bata wani daɗe ba ta tashi ta fito harabar asibitin tare da Namra.
“Allah ya sauwaƙe Namra mu kan za mu koma”
Da sauri Namra ta kalleta
“Yanzu Anty?”
“Eh daman Abbah ki yace min kar na kwana, ƙara mu kama hanya yanzu kin san tafiyar dare bata da kyau, Maryam tace tana gaishe ki”
Nan da nan sai tasa kuka, a zatonta Anty Amarya zata kwana ne. Har suka ƙarasa gurin mota Namra kuka take, daker Anty Amarya ta lallaɓata tayi shiru.
“Anty ba mu da kuɗin biyan Hospital bill, kuma ba ni da ko naira yanzu a hannuna”
Ta faɗa tana ƙara share hawayenta.
“Ai ga mahaifiyarsa can sai ta biya masa”
Anty Amarya ta faɗa tana shirin zama cikin mota. Namra bata ƙara cewa koma, sai idonta dake zubar da ƙwallah.
Sai da Anty Amarya ta rufe motar ta zuƙe gilashin sannan ta ce.
“Zan miki transfer 100k Allah ya bashi lafiya”
“Amin na gode Allah ya kai ku lafiya”
A haka suka yi sallama. Namra ta bi motar tasu da kallo har suka bar asibitin.
____________________________________
Share it please.
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa24.html
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 24*
NOT EDITED ⚠️
Har Anty Amarya ta koma gida tana jin zafin kalaman da Mama ta yi a gabanta. Sai yanzu take jin zafin rashin mayar mata da magana da bata yi ba.
Bayan Sallah Magariba Hajiya Barau ta shigo ɗakin, tana tambayar Anty Amarya ya mai jikin, a lokacin Maryam da Hindatu har Aisha suna ɗaki suna maganar.
“Jiki da sauki sosai, yaji ciwo a ƙafa da hannu, sai gefen fuska”
“Toh Allah ya ƙara sauki ya tsare gaba, mu kam sai an kwana biyu sannan muje mu ganshi”
“Ai ba komai da sauki ma sosai, ƙaddarori ne kawai idan Allah ya kawo”
“Allah ya sauwaƙe ya ɗauke Wahala”
“Ameen”
Ta tashi ta nufi ƙofa tana faɗin
“Maryam ki zo ki karɓo dambu ɗazu Hajiya Hadiza ta aiko min da shi”
Tashi Aisha ta yi, ta bita suka fita tare. Maryam ta yi ƙwafa tana maimaita maganar ɗazu.
“Amman Wallahi matar nan bata da kirki sam, kuma ta ci sa'ah ba da ni aka je Wallahi da sai nayi mata tasss”
“Hmmm kin san wasu ba su iya yarda da ƙaddara ba, idan abu ya same su sai riƙa ganin kamar wani yayi musu ba Allah ba”
Cewar Anty Amarya, tana gyara zamanta. Hindatu tace
“Ni fa gani nake daman can kamar ba son auren take ba, shiyasa ma ya siye gida can su zauna”
Maryam ta ƙara tsire baki
“Ai mune ma ya dace muce haka ba su ba, dan yanzu na san ita za a bari ɗmda wahala, kuma wannan gidan ba siyen shi yayi ba, sai dai idan haya ya kama, idan ma siye yayi Wallahi Anty Namra ce ta bashi kuɗi, dan ta rance 1.5 million gare ni tace kar na faɗa”
Daga Anty Amarya har Hindatu da Aisha data shigo yanzu kallon Maryam suka yi da mamaki.
“Dan Allah da gaske?”
Hindatu ta amsa da ƙarfi. Maryam ta watsa mata harara
“Haka kawai zan ƙirƙiri ƙarya na faɗa, kuma nasan Wallahi shine ya zuga ta yace ta bashi wai kuma fa ta ƙara masa nata masu yawa, idan ba haka ba taya zai yi wannan lefen har ya samu gidan kai ta”
“Ko Motar nan waya sani ko sai dawa zasu yi ta bashi kuɗin, Wallahi Anty Namra bata da wayo sam”
Cewar Aisha tana ɗire wainar gaban Anty Amarya. Gaba ɗaya yanayin Anty Amarya ya canja, sai ta kawar da fuskarta wani gurin tana ƙoƙarin ɓoye damuwarta, babu abunda take tunani sai lamarin Namra.
NAMRA POV.
Asim be farka ba sai washe garin ranar da la'asar, har lokacin Namra bata sa komai a cikinta ba, dan bata jin yunwa ma a tare da ita.
Daker ya buɗe idonsa kumburarrin idonsa sai kuma ya mayar da sauri ya rufe, saboda zafin da yaji suna masa. Hannunsa ɗaya ta kama, idonta cike da ƙwalla.
“Sannu Asim”
Sai ta tashi da sauri taje ta kira likita. Abun ka da Nigeria sai da likitan ya kusan minti ashiri sannan ya iso tare da abun awonsa.
Sama-sama ya duba sa, ya kira sunan sa kusan sau uku, amman be amsa ba, sai motsa ido yake yana jin abunda yake ji.
Likitan ya kalli Namra yace
“Gaskiya bawan Allah nan yana buƙatar kulawar gaggawa, idan hali zan muku transfer zuwa babbar Asibitin Katsina dan ya samu kyakkyawar kulawa indai kuna buƙatar ransa”
A dai-dai lokacin ne Mama ta iso, sai kawai tasa kuka tana faɗin ta bani ta lalace. Nurse ɗin dake tare da Likitan ta katsa mata tsawa
“Haba Inna muna da wasu majiyanta fa, kukan ki zai iya takura musu”
Namra ta share hawayen idonta tana in'inna tace
“Likita a yi mana”
A take ya karɓi file ɗin dake hannun Nurse ɗin ya fiddo wata doguwar takarda, yayi rubuce-rubuce ya miƙa Nurse ɗin yana faɗin.
Tana fitowa cikin pharmacy ɗin, wani ƙaton mutum ya sha gabanta.
“Malama ana magana da ke a can”
Ya nuna mata wata shegiyar Mota mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali. Ɗauke kai tayi kamar bata ji shi ta cigaba da tafiyar tana kallon ti-ti ko zata samu Napep.
Jin tayi ana binta a baya, kuma ba takun mutum ɗaya ba, juyowar da zata yi sai ƙamshin wani daddaɗan turare ya daki hancinta.
Tsayawa tayi cak tana masa kallin jin dalilin binta da yake shi da bodyguards ɗinsa. Shi kuma ya tsaya a gurin yana mata wani kallo mai wuyar fassara.
Mashallah kyakkyawa ajin farko kuma ajin ƙarshen a kyau. Manyan idanuwansa, su suka fi komai kyau a halinta dake fuskarsa, manya ne sosai farin yayi fari, baƙin kuma kamar an shafa masa kwalli, hancinsa ya zauna a tsakiyar fuskarsa kamar anja masa layi, a ƙasan hancin an yanka masa wani hot lip pink color, shape ɗin fuskarsa mai faɗi kamar ƙirginsa. Robe ce a jikinsa mai kyau da ɗaukar hankali.
Ganin be ce mata komai ba, yasa ta juya da nufin cigaba da tafiyarta. Sai kawai yayi kuskuren kai hannunsa ya riƙa hijabinta, da nufin juwo da ita.
Tassssssss. Ta sauke masa lafiyayyen mari a fuska. Da sauri Bodyguards ɗinsa suka zaburo za su kai mata duka, sai yayi saurin ɗaga musu hannu.
“Baka da hankaline da zaka kai hannunka ka taɓa min Hijabi? An faɗa maka kowa wace mace ce ƴar iska? Kasan muhimmancin hijabi da zaka saka wulaƙantacen hannunka ka taɓa min Hijabi? Ni matar aure ce dan haka ka shiga hankalin ka”
Duk balbalin bala'in da take masa, kallonta yake fuskarsa da murmushi, har yanzu sanyin da laushin hannunta yake ji a gefen fuskarsa.
“Nima Mijin aure ne”
Ya faɗa lokacin daya ga tana ƙoƙarin juyawa. Awww Mashallah his voice was soft and sweet, such a nice voice irin ta larabawan nan masu ƙalƙala, wandanda baka gajiya da jin muryar su.
Wani dogon tsaki taja dai-dai lokacin data tsayar da mai Napep ta shiga tayi tafiyarta.
Har cikin ransa yake jin tsakin nata, yana yawo a ƙwaƙwalwarsa kamar wani blood.
“Abdul”
Da sauri wanda ya kira da Abdul ɗin ya matsa kusa dashi yana tsare masa.
“Sir”
“Rubuta Number Mai Napep ɗin can. 771A97K Funtua”
“Yes Sir”
Da sauri ya juya ta nufi gurin da suka yi parking ɗin motocinsu. Shi kam sai da ya daina hango Napep ɗin sannan hankalinsa ya dawo kansa.
‘For the first time in history wata mace ta ɗaga hannu ta mari Abdullah Ahmad Mai-doki’
A zuciyarsa yayi furucin yana mamakin kansa.
“Unique one”
Ya furta a fili. Sannan ya ce su zo da motocin ya shiga suka kama hanya.
Tana isa cikin asibitin ta kai ma likitan maganin yace ta bawa Nurse. Haka suka kwana a kansa ita da Mardiya, ko wanne ya shimfiɗa ɗankwalinsa ya kwanta. Sai dai Mardiya ce kawai tayi bachi Namra kam har safe idonta biyu.
Da safe ita ta bawa Mardiya kuɗi tta siyo abinci a ƙofar asibitin ta karya, ita kam jasa cin komai tayi har likita ya shigo.
Bayan ya gama duba shi ya sake sa masa drip, a cikin drip ɗin yayi masa alluran da aka siyo sannan ya miƙa mata wasu magungunan yace idan ya farka ta bashi.
“Amman likita har yanzu be buɗe ido ba”
“Zai buɗe yana da rai fa, kawai yaji jiki ne, mai yiyu juwa anjima ya buɗe idon, amman inda hali ku kai shi babbar asibitin Katsina dan akwai yiyuwar sai an masa aiki a ƙafarsa, saboda kashinsa na cinya ya shige ciki”
“Innalillahi wa'inna ilaihi”
Ta faɗa tana faɗuwa zaune saman kujerar roba dake gurin.
“Allah ya bashi lafiya”
Wucewa ya yi gurin wasu marar lafiyar ya barta tana aikin kuka. Likitan be yi minti talatin da barin gurin ba, Sai ga Mama ta iso da kukanta. Aiko hankalinta ya tashi sosai da taga yadda fuskar ɗanta ya kumbuɗe kamar an busashi, gaba ɗaya halittarsa ta canja.
Yadda take rusa kuka sai yasa hankalin duk wanda yake gurin ya koma kanta, ƙanwar Asim sai haƙuri take bata tana kuka.
Guraren shaɗaya da rabi Anty Amarya ta iso tare da direban su da Aisha. Namra na ganinta ta fashe ta sabon kuka ta kwantar da kanta jikin Anty Amarya.
Anty Amarya ta danne kukanta, tana lallasar Namra.
“Ki yi haƙuri, Namra ki kwantar da hankalin ki, duk abunda ya kamata ayi masa za'a masa kinji? Idan ma waje ya kamata a fitar da shi za'a fitar, amman ki kwantar da hankalin ki”
Karaf Mama ta tsuma baki, tana mai jin zafin yadda Anty Amarya take lallarsar Namra ita ga ɗanta kwance.
“Ta kwantar da hankali kamar yaya? Ga mijinta kwance ki ce ta kwantar da hankalinta, ta nata ma kike ba ta Ibrahim ba, daman ai nasan ba son ƙwarai kuke masa ba, ni wannan aure bai zo da komai ba sai abun baƙinciki, gashi nan daga shigowarki gidansa ya koma da ƙafa ɗaya”
Da kuka ta ƙarasa maganar. Kallonta kawai Anty Amarya tayi ta ɗauke kai, tana mai jin zafin kalamanta. Bata wani daɗe ba ta tashi ta fito harabar asibitin tare da Namra.
“Allah ya sauwaƙe Namra mu kan za mu koma”
Da sauri Namra ta kalleta
“Yanzu Anty?”
“Eh daman Abbah ki yace min kar na kwana, ƙara mu kama hanya yanzu kin san tafiyar dare bata da kyau, Maryam tace tana gaishe ki”
Nan da nan sai tasa kuka, a zatonta Anty Amarya zata kwana ne. Har suka ƙarasa gurin mota Namra kuka take, daker Anty Amarya ta lallaɓata tayi shiru.
“Anty ba mu da kuɗin biyan Hospital bill, kuma ba ni da ko naira yanzu a hannuna”
Ta faɗa tana ƙara share hawayenta.
“Ai ga mahaifiyarsa can sai ta biya masa”
Anty Amarya ta faɗa tana shirin zama cikin mota. Namra bata ƙara cewa koma, sai idonta dake zubar da ƙwallah.
Sai da Anty Amarya ta rufe motar ta zuƙe gilashin sannan ta ce.
“Zan miki transfer 100k Allah ya bashi lafiya”
“Amin na gode Allah ya kai ku lafiya”
A haka suka yi sallama. Namra ta bi motar tasu da kallo har suka bar asibitin.
____________________________________
Share it please.
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa24.html
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 24*
NOT EDITED ⚠️
Har Anty Amarya ta koma gida tana jin zafin kalaman da Mama ta yi a gabanta. Sai yanzu take jin zafin rashin mayar mata da magana da bata yi ba.
Bayan Sallah Magariba Hajiya Barau ta shigo ɗakin, tana tambayar Anty Amarya ya mai jikin, a lokacin Maryam da Hindatu har Aisha suna ɗaki suna maganar.
“Jiki da sauki sosai, yaji ciwo a ƙafa da hannu, sai gefen fuska”
“Toh Allah ya ƙara sauki ya tsare gaba, mu kam sai an kwana biyu sannan muje mu ganshi”
“Ai ba komai da sauki ma sosai, ƙaddarori ne kawai idan Allah ya kawo”
“Allah ya sauwaƙe ya ɗauke Wahala”
“Ameen”
Ta tashi ta nufi ƙofa tana faɗin
“Maryam ki zo ki karɓo dambu ɗazu Hajiya Hadiza ta aiko min da shi”
Tashi Aisha ta yi, ta bita suka fita tare. Maryam ta yi ƙwafa tana maimaita maganar ɗazu.
“Amman Wallahi matar nan bata da kirki sam, kuma ta ci sa'ah ba da ni aka je Wallahi da sai nayi mata tasss”
“Hmmm kin san wasu ba su iya yarda da ƙaddara ba, idan abu ya same su sai riƙa ganin kamar wani yayi musu ba Allah ba”
Cewar Anty Amarya, tana gyara zamanta. Hindatu tace
“Ni fa gani nake daman can kamar ba son auren take ba, shiyasa ma ya siye gida can su zauna”
Maryam ta ƙara tsire baki
“Ai mune ma ya dace muce haka ba su ba, dan yanzu na san ita za a bari ɗmda wahala, kuma wannan gidan ba siyen shi yayi ba, sai dai idan haya ya kama, idan ma siye yayi Wallahi Anty Namra ce ta bashi kuɗi, dan ta rance 1.5 million gare ni tace kar na faɗa”
Daga Anty Amarya har Hindatu da Aisha data shigo yanzu kallon Maryam suka yi da mamaki.
“Dan Allah da gaske?”
Hindatu ta amsa da ƙarfi. Maryam ta watsa mata harara
“Haka kawai zan ƙirƙiri ƙarya na faɗa, kuma nasan Wallahi shine ya zuga ta yace ta bashi wai kuma fa ta ƙara masa nata masu yawa, idan ba haka ba taya zai yi wannan lefen har ya samu gidan kai ta”
“Ko Motar nan waya sani ko sai dawa zasu yi ta bashi kuɗin, Wallahi Anty Namra bata da wayo sam”
Cewar Aisha tana ɗire wainar gaban Anty Amarya. Gaba ɗaya yanayin Anty Amarya ya canja, sai ta kawar da fuskarta wani gurin tana ƙoƙarin ɓoye damuwarta, babu abunda take tunani sai lamarin Namra.
NAMRA POV.
Asim be farka ba sai washe garin ranar da la'asar, har lokacin Namra bata sa komai a cikinta ba, dan bata jin yunwa ma a tare da ita.
Daker ya buɗe idonsa kumburarrin idonsa sai kuma ya mayar da sauri ya rufe, saboda zafin da yaji suna masa. Hannunsa ɗaya ta kama, idonta cike da ƙwalla.
“Sannu Asim”
Sai ta tashi da sauri taje ta kira likita. Abun ka da Nigeria sai da likitan ya kusan minti ashiri sannan ya iso tare da abun awonsa.
Sama-sama ya duba sa, ya kira sunan sa kusan sau uku, amman be amsa ba, sai motsa ido yake yana jin abunda yake ji.
Likitan ya kalli Namra yace
“Gaskiya bawan Allah nan yana buƙatar kulawar gaggawa, idan hali zan muku transfer zuwa babbar Asibitin Katsina dan ya samu kyakkyawar kulawa indai kuna buƙatar ransa”
A dai-dai lokacin ne Mama ta iso, sai kawai tasa kuka tana faɗin ta bani ta lalace. Nurse ɗin dake tare da Likitan ta katsa mata tsawa
“Haba Inna muna da wasu majiyanta fa, kukan ki zai iya takura musu”
Namra ta share hawayen idonta tana in'inna tace
“Likita a yi mana”
A take ya karɓi file ɗin dake hannun Nurse ɗin ya fiddo wata doguwar takarda, yayi rubuce-rubuce ya miƙa Nurse ɗin yana faɗin.