Sashe 153
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“To aure zai miki”
“Anty Aure yanzu? Ni gaskiya ban shirya ba, halin mazan zamanin nan duk yaushe na fita daga wannan rayuwar kuma za a ce na sake wani”
“Toh sai ki tashi ki faɗawa Mahaifinki ai yana part ɗinsa”
Ta yi saurin rufe baki tana dariya, sai ta tashi ta ɗauki shaddar ta fice. Murmushi Anty Amarya ta yi tana unƙurin tashi ta nufi part ɗin Abbah.
Yau weekend ce daman babu aiki kuma babu wani taro ko wani abun da zai fitar da Abbah, dan haka yana part ɗinsa yana hutawa. Da sallama ta shiga, ya amsa mata yana kallon labaran bbc. Plate ɗin dake kusa da shi da ɗauke ta aje ƙasa ta zauna bakinta ƙumshe da murmushi.
“Yanzu na ke shirin kiranki”
“To Allah yasa samu ne”
“Samu ne kan, ɗana nake nemawa auren ƴarki idan kun aminci”
“Ai Abdool ɗana ne ba ɗan ka ba, ni ya kamata na nema masa aure”
Dariya Abbah yayi yace
“Amman miya hana ya biyo ta gefen ki? Ko dai ƴarki bata son sa ne? Bana son na sake mata wani zaɓin ne wanda ba shi ranta yake so ba, kar a sake samun matsala”
“Ba wata matsala, yanzu haka maganar da na gama da ita kenan”
“Toh Allah ya shige mana gaba, amman zan so jin ta bakin Namra”
“Ai gaka gata, waya isa ya shiga tsakanin uba da ƴa?”
Anty Amarya ta faɗa tana dariya.
*** *** ***
Kai ya girgiza mata alamar ba zai karɓa ba.
“Ba dan ki bani abu na zo gidanku ba”
“Ni ma na sani shiyasa na siya maka wannan shaddar, da wata manufa na yi ba”
“Na sani na gode?”
“Ba zaka karɓa ba kenan?”
“Gaskiya bana so”
Miƙewa ta yi tsaye ciki da jin haushin ƙin karɓar da yayi ta baro garden ɗin. Ko da ta shigo falo wayarta dake kan kujera tana ringing cikin sauri ta kai hannu ta ɗauka, Abdool ne rubuce a screen ɗin wayar. Tsayawa tayi kallon wayar sannan ta danna picking ta kara a kunne.
“Abnam gani kan hanya?”
“Ba zaka daina yi min zuwan ba zata ba ko?”
“Zan daina daga ranar da kika zama mallakina”
“Allah ya kawo ka lafiya”
“Amin Sweet Abnam thank you”
Shi kanshi baya son zuwan ba zata da yake mata, sai dai yana yin hakan ne dan ya riski Lamido gani yake kamar ya tare masa komai ƙara dai ya riƙa masa ba zata yadda zai riƙa fahimtar alaƙar dake tsakaninsu.
Kitchen ta shiga ta sarrafa masa abu mai sauƙi sannan ta haɗa masa fruit salad dan ta fahimci yana son sa sosai. Sai kuma ta shiga ta yi wanka ta saka abaya da jan mayafi. Tana jin lokacin da mota ta shigo harabar gidan kuma zuciyarta ta ayyana mata shi ne, amman saboda ƙarfin hali ta ƙi ta fita ta tarbe shi, har sai da ya buga ƙofar falon.
Turare ta ɗauka ta feshe jikinta sannan ta fito falo taje ta buɗe masa ƙofar, jinginawa yayi yana kallonta fuskarsa sa annuri, sai dai hakan be ma murmushinsa damar fitowa ba.
Yadda ƴake kallonta ta yi zaton zai ce mata tayi kyaune kamar yadda ya saba sai kawai taji ya ce.
“Ina Anty?”
“Tana ciki, ka shigo mana”
“No ba sai na shigo ba, ai baki bukatar ganina”
“Nace maka? Abdool miyasa kake irin wannan maganar ne? Sai kace wata maƙiyiyarka kace bana son ganinka”
Ya wara ido.
“Wasa nake miki fa, ai nasan ni kika yi wa wannan kwaliyar”
Sai kuma ta ji kunya.
“Zaka shigo ko part ɗin Abbah zaka je”
“Cikin wata tara kin zama wata babbar mace”
Ya salam. Ta juya ya bar masa jikin ƙofar, sai kawai yayi murmushi ya shigo. Daman gidan ba baƙonsa bane sai dai duk lokacin da zai zo Abbah ne kawai yake sanin shigowarsa garin. Kasa sakewa Namra ta yi haka take duk lokacin da ya shigo part ɗin shi kuma sai ya bi ya tsare ta da ido duk wani motsi nata yana idonsa.
Fruit salad ta fara kawo masa da ruwa sai kuma pineapple juice da ta haɗa masa. Gabanta sai faɗuwa yake kar Anty ta tararda su, tana jin kunyar Anty ta ganta da Abdool sosai.
“Gaskiya na yi sa'a, Matata ga iya abinci ga iya kwalliya ga haƙuri da kawaici”
Ƙasa ta yi da kanta tana murmushi, this is not the first time da yake yaba girkinta a duk lokacin da ta girka masa wani abu.
Kamar munafuka haka take satar kallonsa, yana mata kyau yau fiye da ko yaushe, ga wani ƙyalli da fuskarsa take.
Ƙarar da wayarta ta yi ne ya dukan su suka kalli wayar, ita sam ta ma manta da wayarta tana saman kujera dan tun da tayi waya da shi ta aje ta a gurin. Hannu ya kai ya ɗauka.
“Waye Dr Faruk?”
“Likita na ne”
Ido ya sakar mata kamar be yarda da maganarta ba, kuma yaƙi ta bata wayar sai ringing take.
“Me zai sa ya kira ki yanzu? Baki da lafiya ne?”
Kasa amsa mashi ta yi. A take yanyinsa ya canja sai kawai ya miƙe tsaye ya aje mata wayar ya fice, zuciyarsa na masa mugun zafi.
AMIRA POV.
Kullum cikin ɗaki ta wuni duk tabi ta takura kanta, akan abunda ta san har a bada ba zai taɓa zama nata ba, babu yadda Ammy bata yi akan ta riƙa fita tana shan iska amman ina, har ta gaji yanzu ta saka mata ido sai kuma addu'ah da take mata.
Cikin rashin ƙwarin jiki ta fito ta daga ɗakinta ta haɗawa kanta tea, bayan ta haɗa tea ta zauna a falo, saboda ta samu falon babu kowa a ciki sai tv dake ta aikinsa.
Ƙofar falon aka turo aka shigo, mai gadinsu ne, hannunshi riƙe da wasiƙa, sai da kai ƙasa sannan ya miƙa mata takardar.
“Gashi inji wasu mutane suka ce a baki”
“Su waye?”
“Wlh nima ban sani ba, cikin mota suke kuma sun tafi”
Hannu ta kai ta karɓa, shi kuma ya tashi ya fice, sai da ya fita sannan ta warware takardar ta fara karantawa...
ASIM POV.
Yanzu tsawon wata tara kenan ana abu ɗaya, a duk lokacin da ya gina gida da sunan Mardiya sai gidan ya ƙone, idan ya kama haya ma abu ɗaya ne, tun lokacin da aka ɗaura auren ta gagara tarewa sai dai su kwana a hotel ko kuma gidan abokai, dan ko lokacin da aka ɗaura auren hotel ya kama mata, baya jin zafi cire kuɗi ya gina mata gida ko ya zuba mata dukiya amman ta kasa mararta saboda yawan gobara da take. Ita kanta yanzu abun yana damunta sosai, musamman da ta samu labarin Asim yana neman auren ƴar masu kuɗi, tasan babu namijin da zai juri zama da ita tana gora dole ko wanene ya nemin ƙarin aure, ga mafarkin wutar da take har yanzu bata daina ba, lallai haƙoƙan mutane da yasa yana kanta, domim ba Namra ce kawai ta taɓa cuta ba, mutane da tayi ma cuta suna da yawa ga satar da tayi ta yi, ga kuma yawan banza data ɗaukarwa kanta. Shi kansa Asim sai yanzi ƴake gane yayi zaɓen tumun dare, dan duk ƙyalƙyalin da yake hangowa sai ya tarar na ɗan maciji ne, be same ta a budurwa ba, kuma daman be aureta dan Allah ba, auren sha'awa yayi mata daga lokacin da ya kai ga jikinta sai duk da fita ranshi daman yanzu ba maxe ba burgeshi take ba, wannan ma da zai aureta dan kawai kariyar kai ne, kuma yana son ganin shi wutar take bi ko Mardiya.
Babu irin neman taimakon da ba ayi ba akan wannan matsalar, wani gurin ace aiki ne aka mata wasu kuma su ce iska ne yake mata, tana zuba kuɗi da yawa dan ganin ko za a dace amman babu wani sauƙi sai abunda ya cigaba.
A unguwa kuma sai gulma ake mata kowa da irin abunda yake faɗa, waɗanda suka san halinta suce amanace ciki har da masu cewa ai taci amanar Namra tun da ta aure mata miji....
[7/22, 10:00 PM] Khadeeja Candy♥: *87*
NAMRA POV.
Shiru-shiru bata ga Abdool ya dawo ba, hakan ya tabbatar mata da fushi yayi. Miƙewa tayi tsaye ta fita sai ta hangoshi jikin motarsa yana kallon ƙofar falon. Ƙarasa tayi cikin wani taku mai jan hankali da ƙasaita, ta rumgume hannayenta tana kallonshi.
“Ina da matsalar mahaifa ne Abdallah, ciki baya iya tsayawa tun ina gidan Asim, wannan matsalar ce tasa Dr Faruk ke kula da lafiyata”
Uffan be ce mata ba, sai kawai ya kawardar fuskarsa yana kallon part ɗin Abbah.
“Abdallah...”
“Abnam...”
Ya kira sunanta kamar yadda ta kira nashi, still be kalleta ba.
“Baka yarda da ni ba ko?”
“Babu rashin yarda a tsakani na da ke, sai dai zai fi idan muka bar maganar nan”
Murmushi tayi ta juya koma ciki. Haka ya tsaya a gurin har sai da yaji ya samu sassauci a zuciyarsa sannan ya nufi part ɗin Abbah. A falo ya samu Abbah daman yasan da zuwansa sun samu awa ɗaya suna tattauna akan rayuwa da abubuwan duniya sam ba zaka ce Abdallah ne yake neman auren ƴar Abbah ba, sam ba zaka ce surukinsa ba ne.
*ONE MONTHS LATER...*
Har yanzu jikinsa na nan a yadda yake, Umma yanzu na hausa take nema masa wai ko Allah zaisa a dace.
Bayan ya gama shan magani ya turo kekensa ya fito harabar gidan. Wayarsa dake cikin aljihun wandonsa ya ciro ya kira Tahir.
“Bros ya ne, ya jikin naka ne?”
“Alhamdullah, ya aiki?”
“Mun gode Allah”
“Tahir tun ranar baka sake ce mun komai, ko baka kai mata ba ne?”
“Anty Aure yanzu? Ni gaskiya ban shirya ba, halin mazan zamanin nan duk yaushe na fita daga wannan rayuwar kuma za a ce na sake wani”
“Toh sai ki tashi ki faɗawa Mahaifinki ai yana part ɗinsa”
Ta yi saurin rufe baki tana dariya, sai ta tashi ta ɗauki shaddar ta fice. Murmushi Anty Amarya ta yi tana unƙurin tashi ta nufi part ɗin Abbah.
Yau weekend ce daman babu aiki kuma babu wani taro ko wani abun da zai fitar da Abbah, dan haka yana part ɗinsa yana hutawa. Da sallama ta shiga, ya amsa mata yana kallon labaran bbc. Plate ɗin dake kusa da shi da ɗauke ta aje ƙasa ta zauna bakinta ƙumshe da murmushi.
“Yanzu na ke shirin kiranki”
“To Allah yasa samu ne”
“Samu ne kan, ɗana nake nemawa auren ƴarki idan kun aminci”
“Ai Abdool ɗana ne ba ɗan ka ba, ni ya kamata na nema masa aure”
Dariya Abbah yayi yace
“Amman miya hana ya biyo ta gefen ki? Ko dai ƴarki bata son sa ne? Bana son na sake mata wani zaɓin ne wanda ba shi ranta yake so ba, kar a sake samun matsala”
“Ba wata matsala, yanzu haka maganar da na gama da ita kenan”
“Toh Allah ya shige mana gaba, amman zan so jin ta bakin Namra”
“Ai gaka gata, waya isa ya shiga tsakanin uba da ƴa?”
Anty Amarya ta faɗa tana dariya.
*** *** ***
Kai ya girgiza mata alamar ba zai karɓa ba.
“Ba dan ki bani abu na zo gidanku ba”
“Ni ma na sani shiyasa na siya maka wannan shaddar, da wata manufa na yi ba”
“Na sani na gode?”
“Ba zaka karɓa ba kenan?”
“Gaskiya bana so”
Miƙewa ta yi tsaye ciki da jin haushin ƙin karɓar da yayi ta baro garden ɗin. Ko da ta shigo falo wayarta dake kan kujera tana ringing cikin sauri ta kai hannu ta ɗauka, Abdool ne rubuce a screen ɗin wayar. Tsayawa tayi kallon wayar sannan ta danna picking ta kara a kunne.
“Abnam gani kan hanya?”
“Ba zaka daina yi min zuwan ba zata ba ko?”
“Zan daina daga ranar da kika zama mallakina”
“Allah ya kawo ka lafiya”
“Amin Sweet Abnam thank you”
Shi kanshi baya son zuwan ba zata da yake mata, sai dai yana yin hakan ne dan ya riski Lamido gani yake kamar ya tare masa komai ƙara dai ya riƙa masa ba zata yadda zai riƙa fahimtar alaƙar dake tsakaninsu.
Kitchen ta shiga ta sarrafa masa abu mai sauƙi sannan ta haɗa masa fruit salad dan ta fahimci yana son sa sosai. Sai kuma ta shiga ta yi wanka ta saka abaya da jan mayafi. Tana jin lokacin da mota ta shigo harabar gidan kuma zuciyarta ta ayyana mata shi ne, amman saboda ƙarfin hali ta ƙi ta fita ta tarbe shi, har sai da ya buga ƙofar falon.
Turare ta ɗauka ta feshe jikinta sannan ta fito falo taje ta buɗe masa ƙofar, jinginawa yayi yana kallonta fuskarsa sa annuri, sai dai hakan be ma murmushinsa damar fitowa ba.
Yadda ƴake kallonta ta yi zaton zai ce mata tayi kyaune kamar yadda ya saba sai kawai taji ya ce.
“Ina Anty?”
“Tana ciki, ka shigo mana”
“No ba sai na shigo ba, ai baki bukatar ganina”
“Nace maka? Abdool miyasa kake irin wannan maganar ne? Sai kace wata maƙiyiyarka kace bana son ganinka”
Ya wara ido.
“Wasa nake miki fa, ai nasan ni kika yi wa wannan kwaliyar”
Sai kuma ta ji kunya.
“Zaka shigo ko part ɗin Abbah zaka je”
“Cikin wata tara kin zama wata babbar mace”
Ya salam. Ta juya ya bar masa jikin ƙofar, sai kawai yayi murmushi ya shigo. Daman gidan ba baƙonsa bane sai dai duk lokacin da zai zo Abbah ne kawai yake sanin shigowarsa garin. Kasa sakewa Namra ta yi haka take duk lokacin da ya shigo part ɗin shi kuma sai ya bi ya tsare ta da ido duk wani motsi nata yana idonsa.
Fruit salad ta fara kawo masa da ruwa sai kuma pineapple juice da ta haɗa masa. Gabanta sai faɗuwa yake kar Anty ta tararda su, tana jin kunyar Anty ta ganta da Abdool sosai.
“Gaskiya na yi sa'a, Matata ga iya abinci ga iya kwalliya ga haƙuri da kawaici”
Ƙasa ta yi da kanta tana murmushi, this is not the first time da yake yaba girkinta a duk lokacin da ta girka masa wani abu.
Kamar munafuka haka take satar kallonsa, yana mata kyau yau fiye da ko yaushe, ga wani ƙyalli da fuskarsa take.
Ƙarar da wayarta ta yi ne ya dukan su suka kalli wayar, ita sam ta ma manta da wayarta tana saman kujera dan tun da tayi waya da shi ta aje ta a gurin. Hannu ya kai ya ɗauka.
“Waye Dr Faruk?”
“Likita na ne”
Ido ya sakar mata kamar be yarda da maganarta ba, kuma yaƙi ta bata wayar sai ringing take.
“Me zai sa ya kira ki yanzu? Baki da lafiya ne?”
Kasa amsa mashi ta yi. A take yanyinsa ya canja sai kawai ya miƙe tsaye ya aje mata wayar ya fice, zuciyarsa na masa mugun zafi.
AMIRA POV.
Kullum cikin ɗaki ta wuni duk tabi ta takura kanta, akan abunda ta san har a bada ba zai taɓa zama nata ba, babu yadda Ammy bata yi akan ta riƙa fita tana shan iska amman ina, har ta gaji yanzu ta saka mata ido sai kuma addu'ah da take mata.
Cikin rashin ƙwarin jiki ta fito ta daga ɗakinta ta haɗawa kanta tea, bayan ta haɗa tea ta zauna a falo, saboda ta samu falon babu kowa a ciki sai tv dake ta aikinsa.
Ƙofar falon aka turo aka shigo, mai gadinsu ne, hannunshi riƙe da wasiƙa, sai da kai ƙasa sannan ya miƙa mata takardar.
“Gashi inji wasu mutane suka ce a baki”
“Su waye?”
“Wlh nima ban sani ba, cikin mota suke kuma sun tafi”
Hannu ta kai ta karɓa, shi kuma ya tashi ya fice, sai da ya fita sannan ta warware takardar ta fara karantawa...
ASIM POV.
Yanzu tsawon wata tara kenan ana abu ɗaya, a duk lokacin da ya gina gida da sunan Mardiya sai gidan ya ƙone, idan ya kama haya ma abu ɗaya ne, tun lokacin da aka ɗaura auren ta gagara tarewa sai dai su kwana a hotel ko kuma gidan abokai, dan ko lokacin da aka ɗaura auren hotel ya kama mata, baya jin zafi cire kuɗi ya gina mata gida ko ya zuba mata dukiya amman ta kasa mararta saboda yawan gobara da take. Ita kanta yanzu abun yana damunta sosai, musamman da ta samu labarin Asim yana neman auren ƴar masu kuɗi, tasan babu namijin da zai juri zama da ita tana gora dole ko wanene ya nemin ƙarin aure, ga mafarkin wutar da take har yanzu bata daina ba, lallai haƙoƙan mutane da yasa yana kanta, domim ba Namra ce kawai ta taɓa cuta ba, mutane da tayi ma cuta suna da yawa ga satar da tayi ta yi, ga kuma yawan banza data ɗaukarwa kanta. Shi kansa Asim sai yanzi ƴake gane yayi zaɓen tumun dare, dan duk ƙyalƙyalin da yake hangowa sai ya tarar na ɗan maciji ne, be same ta a budurwa ba, kuma daman be aureta dan Allah ba, auren sha'awa yayi mata daga lokacin da ya kai ga jikinta sai duk da fita ranshi daman yanzu ba maxe ba burgeshi take ba, wannan ma da zai aureta dan kawai kariyar kai ne, kuma yana son ganin shi wutar take bi ko Mardiya.
Babu irin neman taimakon da ba ayi ba akan wannan matsalar, wani gurin ace aiki ne aka mata wasu kuma su ce iska ne yake mata, tana zuba kuɗi da yawa dan ganin ko za a dace amman babu wani sauƙi sai abunda ya cigaba.
A unguwa kuma sai gulma ake mata kowa da irin abunda yake faɗa, waɗanda suka san halinta suce amanace ciki har da masu cewa ai taci amanar Namra tun da ta aure mata miji....
[7/22, 10:00 PM] Khadeeja Candy♥: *87*
NAMRA POV.
Shiru-shiru bata ga Abdool ya dawo ba, hakan ya tabbatar mata da fushi yayi. Miƙewa tayi tsaye ta fita sai ta hangoshi jikin motarsa yana kallon ƙofar falon. Ƙarasa tayi cikin wani taku mai jan hankali da ƙasaita, ta rumgume hannayenta tana kallonshi.
“Ina da matsalar mahaifa ne Abdallah, ciki baya iya tsayawa tun ina gidan Asim, wannan matsalar ce tasa Dr Faruk ke kula da lafiyata”
Uffan be ce mata ba, sai kawai ya kawardar fuskarsa yana kallon part ɗin Abbah.
“Abdallah...”
“Abnam...”
Ya kira sunanta kamar yadda ta kira nashi, still be kalleta ba.
“Baka yarda da ni ba ko?”
“Babu rashin yarda a tsakani na da ke, sai dai zai fi idan muka bar maganar nan”
Murmushi tayi ta juya koma ciki. Haka ya tsaya a gurin har sai da yaji ya samu sassauci a zuciyarsa sannan ya nufi part ɗin Abbah. A falo ya samu Abbah daman yasan da zuwansa sun samu awa ɗaya suna tattauna akan rayuwa da abubuwan duniya sam ba zaka ce Abdallah ne yake neman auren ƴar Abbah ba, sam ba zaka ce surukinsa ba ne.
*ONE MONTHS LATER...*
Har yanzu jikinsa na nan a yadda yake, Umma yanzu na hausa take nema masa wai ko Allah zaisa a dace.
Bayan ya gama shan magani ya turo kekensa ya fito harabar gidan. Wayarsa dake cikin aljihun wandonsa ya ciro ya kira Tahir.
“Bros ya ne, ya jikin naka ne?”
“Alhamdullah, ya aiki?”
“Mun gode Allah”
“Tahir tun ranar baka sake ce mun komai, ko baka kai mata ba ne?”