Sashe 32
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Baki gani ba? Wallahi ban ga inda kika jefar ba, kuma tun da na karɓi jakarki ban ma buɗeta ba, yau ko na shiga uku, da wayar mutane”
A take tasa kuka. Sai Namra ta share hawayenta tana faɗin
“Ƙila ko na jefar a motar matar nan ne ban sani ba”
“Lallai ba zai wuce can ba, amman ni ban ɗaukar miki waya ba Wallahi, sai idan kuma a asibiti kika jefar”
“Bana zargin ki Mardiya, da zan samu rancen kuɗi da sai naje gida ta yanzu, dan hankalina ba a kwance yake ba”
“Amman yanzu dare ne, da kin haƙura har da safe, kin ga ma baki san gidanta ba”
“Ai ta bani addireshinta, dan Allah ki ara min ko ɗari biyu ne naje na duba, kin ga halin da mijina yake ciki”
“Ina da wasu ɗari takwas da aka bani ajiya sai idan sun zan aro miki”
“Aro min dan Allah”
“Bari na ɗauko miki ɗari biyar”
Tashi tayi ta fita, bata daɗe ba ta dawo, ta kawo mata kuɗin. Sai Namra ta ɗauki Hijabita ta saka.
“Dan Allah Mardiya ki zauna nan har na dawo, ina son ki taya ni kwana”
“Tau ba komai Allah ya tsare”
Ta ɗauki katin ta fice, hankalita a tashe. Napep ta tara ta shiga. Su kusan tafiyar rabin awa sannan suka isa unguwar GRA ring.
Gidajen gurin duk masu kyau ne da ɗaukar hankali, abun ka da wanda hankali ba kwance ba haka suka kai ƙarshen unguwar bata gane gidan ba, dan numbobin gidajen sun ɓace mata. Har sai da suka yi tambaya, saɓnan aka nuna musu gidan Hajiya Saratu.
Sai ta da buga ƙofaɗ gate ɗin mai gadin ya buɗe mata, ta tambaya yace mata gidan nan sannan ta sallami mai napep ɗin, shi ma ɗaker ya karɓi ɗari biyu da hansin.
A bakin gate ɗin ta tsaya sai da mai gadin yaje ya faɗawa Hajiyar sannan yayi mata iso.
Tana saka ƙafarta cikin falon ƙashin turare ya fara mata marhabun.
Haka tayi ta doka sallama amman ba a amsa mata ba, sai ta samu guri ta zauna, zuciyarta sam bata natsu da gidan ba.
ta ɗauki tsowon lokaci sannan matar ta fito cikin wata rigar yadi mai shara-shara, kusan ana ganin underwears ɗinta.
Tun da Namra ta kalleta sau ɗaya ta sadda kai bata sake kallonta ba, duk gaisuwar da suka yi idon Namra na ƙasa.
Cikin wani irin karairaiya taje ta ɗauko ma Namra lemu da snack ta kawo mata. Namra bata ci dan basu ne a gabanta ba, kuma ta kasa ɗaga ido ta kalli Matar. Ganin hakan yasa matar ya taso ta dawo kusa da Namra ta zauna, ta kai hannunta dafa Namra tana shafa bayanta duk da kasancewar Namra na cikin Hijabi ne.
“Ki kwantar da hankalin ki miji zai samu sauƙi nayi miki alƙawarin duk abunda tmya dace ayi masa za a masa, dan ya samu lafiya, yanzu me likitocin suka ce ne? Dan daga ganin ki akwai wani a ƙasa”
“Na gode sosai, yanzu sun ce sai an biya kuɗin aiki dana magani, kuma suna buƙatar jini gora uku, shine naso na siyar da wayana na duba ban gani ba, nace ko na manta a motar ki ne”
Wani ƙasaitattacen murmushi tayi, ta girgiza mata kai.
“Baki jefar da komai a mota na ba, amman bari na baki keys ki duba, saboda cire kwankwanto”
Bata jira komai ba, ta tashi ta shiga ɗaki ta ɗauko mata keys ɗin ta miƙa mata.
“Muje ki duba, amman na faɗa miki ba dole sai kin siyar da wayarki zaki iya taimakon mijinki ba”
Namra ta karɓi keys ɗin tana faɗin
“Ba ni da wata mafitar ne sai wannan”
“Kina da mafitoci ba ma ɗaya ba”
Ta faɗa yayinda suke fitowa daga cikin falon suka nufi gurin motocin da suke gidan. Ita da kanta ta nuna mata motar da suka shigo, cikin rawar jiki Namra ta nufi motar ta buɗe tana dubawa. Zuwa Hajiyar tayi bayan Namra ta tsaya tana shafa mata duwawu, tare da faɗin
“Duba da kyau ki gani, amman ni bana tunanin kin bar wani abu a gurin”
Da sauri Namra ta juyo ta fito da jikinta cikin motar tana yima matar wani mugun kallo.
“Miye haka? Ya zaki riƙa taɓa min jiki kamar wata karuwa, ko an faɗa miki ni irin waɗannan mata nan”
Murmushi Hajiyar tayi kamar bata ji zafin kalaman Namra ba.
“Ɓana nufi komai da ke sai Alheri, kina da kyau da duk mace data kalle ki sai tayi sha'awarki, balle kuma namiji, dan haka kiyi amfani da damarki ki taimaki kan ki”
“Ke kuma haka kike? Tirrr da ke daman taimakon da kika min ba dan Allah kika min ba? Saboda wani mugu nufi naki? Toh Allah ya fiki, jikina bana mata irin ki bane, ba kuma na wasu mazan bane, na mijina ne shi kaɗai halalina”
“Hmmm kije kiyi tunani Namra, matuƙar kika amince da buƙata zan miki duk abunda kike so a duniyar nan, idan ma waje ya dace a fitar da mijinki zan sa a fitar da shi”
Namra ta girgiza mata kai.
“Dukiyarki bata burge ni, arzikin gidan mu ya ninka naki sau dubu, ƴan'uwana ne suka juya min baya shiyasa kika ganin a halin da kika tsince ni”
Hawayen ya gangaro daga idon Namra. Hajiyar ta matsa kusa da Namra tana ƙoƙarin dafata.
“Kaicon ki, haƙiƙa ina tausayin rayuwarki, wallahi wata mace bata taɓa burge ni ba kamar ki”
“Ba nice a abun tausayi ba, kece a abar tausayi a ranar da zaki yi nadamar da bata da amfani”
Namra ta buge mata hannu ta juya ta fice daga gidan tana hawaye. Ta daɗe tana tafiya a estates ɗin kamin ta samu Napep. Har ta iso gida hawaye take zuciyarta a cakushe.
Ɗari biyun da hasin da suka yi saura ta miƙawa mai Napep ɗin, ya so yayi magana, sai dai hawayen daya gani a idonta yasa shi tausayinta, ya kaɗa napep ɗinsa yayi gaba.
Mardiya na gani hawaye a fuskar Namra, hankalinta ya tashi, da sauri ta riƙa ta suka zauna saman kujera.
“Lafiya ? Ba acan kika jefar da wayar ba?”
Sai kawai Namra ta fashe da kuka tana riƙe Mardiya kamar ta shige cikin jikinta.
*** *** ***
Ganin dare ya lula Namra bata dawo ba, yasa Mama har zuƙa sosai, a ganinta abun kamar be damu Namra ba. Tun da tana da hanyoyin da zata iya biyan wannan kuɗin. Ita ganin take kamar ma da haɗin kai aka yi masa wani abu yayi haɗari motar, so that idan ya mutu sai ta auri wanda take so.
“Mama ko kuɗin adashe zamu karɓo a biya ina ganin fa kamar bata da kuɗin nan”
Cewar Hajaru, Mama ta kai mata wani mugun zungura
“Duk naji bakin ki yayi maganar adashen nan sai na kusa halaka ki, taya zata ba mu kuɗi bayan mun riga mun zuba, kina ganin kullum zogaron kuɗin zubi take mana. Ai ita ta fimu sanin hanyoyin samo kuɗi, ta nemo ta biya a itace silar komai tun da tasan be wani iya mota ba, tasa ya jawo ta tun daga sokoto har katsina dan kawai su ga bayan shi.
Ni Wallahi ɗana ko mutuwa yayi sai nayi ƙararsu”
Hajaru dai tayi shiru bata sake cewa komai ba, Mama kam sai cika take tana barsewa, ita mai ɗa.
KALSOOM POV.
Babu abunda ta ɓoye Salma na zamantakewar auren da suke yanzu da Hilal.
Ita tafi raja'a akan Hilal baya son haihuwa, daman Asmee takan nuna mata alamun hakan tun lokacin data shigo cikin gidan. Sai dai tunaninta ya sha banban lokacin da Salma take nusar da ita akan wasu abubuwan data manta.
“Haba Kalsoom ke kan ki yanzu ba zaki iya gane wani abu a tare da shi ba? Taya za ace dan kin yi ciki sai ya sauya miki? Baya son haihuwa zai bar matarsa ta haifi yara uku kuma tana aiki?Sherin kishiya yana da yawa Kalsoom musamman na zamanin nan”
“Naga sauyi a ɓangarenta dan duk wani kishi data ɗauka yanzu ta aje shi, bana da matsala da ita”
“Wannan ma kaɗai ya isa ya nuna miki akwai abun da tayi, ki bita a sannu kuma ki yi taka tsantsan da ita. Sannan a duk lokacin da mijinki yake fushi yana hawa sama karki tanka shi, kisa mishi ido, saboda maganar zai iya zama miki illah.
Cigaba da addu'ah, idan zaki iya kiyi alwala a zama ɗaya ki karanta Yasin ƙafa goma sha biyar, ki roƙi Allah, ko kuma ki karanta ayatul kursiyu ɗari uku da sha uku Wallahi duk kika roƙi Allah sai ya amsa miki, ki daure kiyi na tsawon sati acikin kwana uku Allah zai biya miki buƙarta ki.
Sannan ki samu ruwa mai kyau ki watsa a saman rufin ɗaki, idan ya gangaro ki tara abu ya zuba a ciki, ki taceshi ki sha ki wanke kanki, Wallahi indan Asirine akayi miki sai ya karya kuma sai Allah ya nuna miki wanda yayi miki haka a bachin ki, maƙukar kika yi har sau uku”
“Na gode sosai Salma, Allah ya bar zumunci”
“Amin Allah ya baku zama lafiya”
Daga haka ta aje wayar, ta jingina da gadonta tana sauke ajiyar zuciya.
“Kai kayi auren baka huta ba, idan kuma baka yi baka huta ba, da wannen zaka ji”
Yadda ya turo ƙofar ɗakin ya shigo ne yasa ta zabura ta tashi zaune, tana kallon yanayinsa.
“Ina kuɗina dake cikin closet?”
Wani kallon mamaki tayi masa.
“Kuɗi kuma? Ni ban ɗauki kuɗin ka Doc, ban ma san ka aje kuɗi a gurin ba”
“Babu wanda zai ɗaukar min kuɗi bayan ke, dan ke kaɗai kike goge gurin”
“Amman ai ba ni kaɗai bace a gidan nan”
“Mata ta bata taɓa min sata ba, ƴara na kuma basu ɗaukar min kuɗi, sannan basa da wayon da zasu iya ɗaukar dubu ɗari uku da hansi”
Hawaye ya silala a idonta. Ta nuna kanta
“Ni kake zargi kenan, ni na ɗaukar maka kuɗin ko? Haba Doc taya zan ɗaukar maka kuɗi abunda ban taɓa yi ba”
Ƙara haɗe fuska yayi kamar an aiko masa da mutuwa, ya ɗaki mirror ta yana ƙara jadadda mata.
A take tasa kuka. Sai Namra ta share hawayenta tana faɗin
“Ƙila ko na jefar a motar matar nan ne ban sani ba”
“Lallai ba zai wuce can ba, amman ni ban ɗaukar miki waya ba Wallahi, sai idan kuma a asibiti kika jefar”
“Bana zargin ki Mardiya, da zan samu rancen kuɗi da sai naje gida ta yanzu, dan hankalina ba a kwance yake ba”
“Amman yanzu dare ne, da kin haƙura har da safe, kin ga ma baki san gidanta ba”
“Ai ta bani addireshinta, dan Allah ki ara min ko ɗari biyu ne naje na duba, kin ga halin da mijina yake ciki”
“Ina da wasu ɗari takwas da aka bani ajiya sai idan sun zan aro miki”
“Aro min dan Allah”
“Bari na ɗauko miki ɗari biyar”
Tashi tayi ta fita, bata daɗe ba ta dawo, ta kawo mata kuɗin. Sai Namra ta ɗauki Hijabita ta saka.
“Dan Allah Mardiya ki zauna nan har na dawo, ina son ki taya ni kwana”
“Tau ba komai Allah ya tsare”
Ta ɗauki katin ta fice, hankalita a tashe. Napep ta tara ta shiga. Su kusan tafiyar rabin awa sannan suka isa unguwar GRA ring.
Gidajen gurin duk masu kyau ne da ɗaukar hankali, abun ka da wanda hankali ba kwance ba haka suka kai ƙarshen unguwar bata gane gidan ba, dan numbobin gidajen sun ɓace mata. Har sai da suka yi tambaya, saɓnan aka nuna musu gidan Hajiya Saratu.
Sai ta da buga ƙofaɗ gate ɗin mai gadin ya buɗe mata, ta tambaya yace mata gidan nan sannan ta sallami mai napep ɗin, shi ma ɗaker ya karɓi ɗari biyu da hansin.
A bakin gate ɗin ta tsaya sai da mai gadin yaje ya faɗawa Hajiyar sannan yayi mata iso.
Tana saka ƙafarta cikin falon ƙashin turare ya fara mata marhabun.
Haka tayi ta doka sallama amman ba a amsa mata ba, sai ta samu guri ta zauna, zuciyarta sam bata natsu da gidan ba.
ta ɗauki tsowon lokaci sannan matar ta fito cikin wata rigar yadi mai shara-shara, kusan ana ganin underwears ɗinta.
Tun da Namra ta kalleta sau ɗaya ta sadda kai bata sake kallonta ba, duk gaisuwar da suka yi idon Namra na ƙasa.
Cikin wani irin karairaiya taje ta ɗauko ma Namra lemu da snack ta kawo mata. Namra bata ci dan basu ne a gabanta ba, kuma ta kasa ɗaga ido ta kalli Matar. Ganin hakan yasa matar ya taso ta dawo kusa da Namra ta zauna, ta kai hannunta dafa Namra tana shafa bayanta duk da kasancewar Namra na cikin Hijabi ne.
“Ki kwantar da hankalin ki miji zai samu sauƙi nayi miki alƙawarin duk abunda tmya dace ayi masa za a masa, dan ya samu lafiya, yanzu me likitocin suka ce ne? Dan daga ganin ki akwai wani a ƙasa”
“Na gode sosai, yanzu sun ce sai an biya kuɗin aiki dana magani, kuma suna buƙatar jini gora uku, shine naso na siyar da wayana na duba ban gani ba, nace ko na manta a motar ki ne”
Wani ƙasaitattacen murmushi tayi, ta girgiza mata kai.
“Baki jefar da komai a mota na ba, amman bari na baki keys ki duba, saboda cire kwankwanto”
Bata jira komai ba, ta tashi ta shiga ɗaki ta ɗauko mata keys ɗin ta miƙa mata.
“Muje ki duba, amman na faɗa miki ba dole sai kin siyar da wayarki zaki iya taimakon mijinki ba”
Namra ta karɓi keys ɗin tana faɗin
“Ba ni da wata mafitar ne sai wannan”
“Kina da mafitoci ba ma ɗaya ba”
Ta faɗa yayinda suke fitowa daga cikin falon suka nufi gurin motocin da suke gidan. Ita da kanta ta nuna mata motar da suka shigo, cikin rawar jiki Namra ta nufi motar ta buɗe tana dubawa. Zuwa Hajiyar tayi bayan Namra ta tsaya tana shafa mata duwawu, tare da faɗin
“Duba da kyau ki gani, amman ni bana tunanin kin bar wani abu a gurin”
Da sauri Namra ta juyo ta fito da jikinta cikin motar tana yima matar wani mugun kallo.
“Miye haka? Ya zaki riƙa taɓa min jiki kamar wata karuwa, ko an faɗa miki ni irin waɗannan mata nan”
Murmushi Hajiyar tayi kamar bata ji zafin kalaman Namra ba.
“Ɓana nufi komai da ke sai Alheri, kina da kyau da duk mace data kalle ki sai tayi sha'awarki, balle kuma namiji, dan haka kiyi amfani da damarki ki taimaki kan ki”
“Ke kuma haka kike? Tirrr da ke daman taimakon da kika min ba dan Allah kika min ba? Saboda wani mugu nufi naki? Toh Allah ya fiki, jikina bana mata irin ki bane, ba kuma na wasu mazan bane, na mijina ne shi kaɗai halalina”
“Hmmm kije kiyi tunani Namra, matuƙar kika amince da buƙata zan miki duk abunda kike so a duniyar nan, idan ma waje ya dace a fitar da mijinki zan sa a fitar da shi”
Namra ta girgiza mata kai.
“Dukiyarki bata burge ni, arzikin gidan mu ya ninka naki sau dubu, ƴan'uwana ne suka juya min baya shiyasa kika ganin a halin da kika tsince ni”
Hawayen ya gangaro daga idon Namra. Hajiyar ta matsa kusa da Namra tana ƙoƙarin dafata.
“Kaicon ki, haƙiƙa ina tausayin rayuwarki, wallahi wata mace bata taɓa burge ni ba kamar ki”
“Ba nice a abun tausayi ba, kece a abar tausayi a ranar da zaki yi nadamar da bata da amfani”
Namra ta buge mata hannu ta juya ta fice daga gidan tana hawaye. Ta daɗe tana tafiya a estates ɗin kamin ta samu Napep. Har ta iso gida hawaye take zuciyarta a cakushe.
Ɗari biyun da hasin da suka yi saura ta miƙawa mai Napep ɗin, ya so yayi magana, sai dai hawayen daya gani a idonta yasa shi tausayinta, ya kaɗa napep ɗinsa yayi gaba.
Mardiya na gani hawaye a fuskar Namra, hankalinta ya tashi, da sauri ta riƙa ta suka zauna saman kujera.
“Lafiya ? Ba acan kika jefar da wayar ba?”
Sai kawai Namra ta fashe da kuka tana riƙe Mardiya kamar ta shige cikin jikinta.
*** *** ***
Ganin dare ya lula Namra bata dawo ba, yasa Mama har zuƙa sosai, a ganinta abun kamar be damu Namra ba. Tun da tana da hanyoyin da zata iya biyan wannan kuɗin. Ita ganin take kamar ma da haɗin kai aka yi masa wani abu yayi haɗari motar, so that idan ya mutu sai ta auri wanda take so.
“Mama ko kuɗin adashe zamu karɓo a biya ina ganin fa kamar bata da kuɗin nan”
Cewar Hajaru, Mama ta kai mata wani mugun zungura
“Duk naji bakin ki yayi maganar adashen nan sai na kusa halaka ki, taya zata ba mu kuɗi bayan mun riga mun zuba, kina ganin kullum zogaron kuɗin zubi take mana. Ai ita ta fimu sanin hanyoyin samo kuɗi, ta nemo ta biya a itace silar komai tun da tasan be wani iya mota ba, tasa ya jawo ta tun daga sokoto har katsina dan kawai su ga bayan shi.
Ni Wallahi ɗana ko mutuwa yayi sai nayi ƙararsu”
Hajaru dai tayi shiru bata sake cewa komai ba, Mama kam sai cika take tana barsewa, ita mai ɗa.
KALSOOM POV.
Babu abunda ta ɓoye Salma na zamantakewar auren da suke yanzu da Hilal.
Ita tafi raja'a akan Hilal baya son haihuwa, daman Asmee takan nuna mata alamun hakan tun lokacin data shigo cikin gidan. Sai dai tunaninta ya sha banban lokacin da Salma take nusar da ita akan wasu abubuwan data manta.
“Haba Kalsoom ke kan ki yanzu ba zaki iya gane wani abu a tare da shi ba? Taya za ace dan kin yi ciki sai ya sauya miki? Baya son haihuwa zai bar matarsa ta haifi yara uku kuma tana aiki?Sherin kishiya yana da yawa Kalsoom musamman na zamanin nan”
“Naga sauyi a ɓangarenta dan duk wani kishi data ɗauka yanzu ta aje shi, bana da matsala da ita”
“Wannan ma kaɗai ya isa ya nuna miki akwai abun da tayi, ki bita a sannu kuma ki yi taka tsantsan da ita. Sannan a duk lokacin da mijinki yake fushi yana hawa sama karki tanka shi, kisa mishi ido, saboda maganar zai iya zama miki illah.
Cigaba da addu'ah, idan zaki iya kiyi alwala a zama ɗaya ki karanta Yasin ƙafa goma sha biyar, ki roƙi Allah, ko kuma ki karanta ayatul kursiyu ɗari uku da sha uku Wallahi duk kika roƙi Allah sai ya amsa miki, ki daure kiyi na tsawon sati acikin kwana uku Allah zai biya miki buƙarta ki.
Sannan ki samu ruwa mai kyau ki watsa a saman rufin ɗaki, idan ya gangaro ki tara abu ya zuba a ciki, ki taceshi ki sha ki wanke kanki, Wallahi indan Asirine akayi miki sai ya karya kuma sai Allah ya nuna miki wanda yayi miki haka a bachin ki, maƙukar kika yi har sau uku”
“Na gode sosai Salma, Allah ya bar zumunci”
“Amin Allah ya baku zama lafiya”
Daga haka ta aje wayar, ta jingina da gadonta tana sauke ajiyar zuciya.
“Kai kayi auren baka huta ba, idan kuma baka yi baka huta ba, da wannen zaka ji”
Yadda ya turo ƙofar ɗakin ya shigo ne yasa ta zabura ta tashi zaune, tana kallon yanayinsa.
“Ina kuɗina dake cikin closet?”
Wani kallon mamaki tayi masa.
“Kuɗi kuma? Ni ban ɗauki kuɗin ka Doc, ban ma san ka aje kuɗi a gurin ba”
“Babu wanda zai ɗaukar min kuɗi bayan ke, dan ke kaɗai kike goge gurin”
“Amman ai ba ni kaɗai bace a gidan nan”
“Mata ta bata taɓa min sata ba, ƴara na kuma basu ɗaukar min kuɗi, sannan basa da wayon da zasu iya ɗaukar dubu ɗari uku da hansi”
Hawaye ya silala a idonta. Ta nuna kanta
“Ni kake zargi kenan, ni na ɗaukar maka kuɗin ko? Haba Doc taya zan ɗaukar maka kuɗi abunda ban taɓa yi ba”
Ƙara haɗe fuska yayi kamar an aiko masa da mutuwa, ya ɗaki mirror ta yana ƙara jadadda mata.