Sashe 161
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Tashi ka yi tafiyarka”
Har ya miƙe tsaye sai kuma ya ce
“Mai Martaba kar naje gida wani abun ya same ni”
“Babu abunda zai same ka, indai ni na haifi Abdallah ko hararka ba zai sake yi ba”
Da tsinginta ya fice. Sannan Mai Martaba ya kalli Namra ya ce.
“Za a maidaki gurin Ummi ba zaki tare a yau ba, zan yi magana da mahaifinki”
Cikin wani irin nauyin jiki da zuciya Namra ta miƙe tsaye jiri na ɗibarta, aiko tana kaiwa bakin ƙofa ta sai tayi baya-baya ta faɗi ƙasa sumamamiya.
A take Abdool ya manta da agaban Mai Martaba yake, a guje ya ƙarasa inda take yasa hannunshi ya ɗauke yana kiran sunanta amman ina ta riga tayi nisa.
A firgice ya fita da ita a falon kamar wanda ya tallaɓo jaririya. Mamaki da aljab ya hana kowa magana sai kallon ikon Allah suke, Abdool ya talloɓo Namra sai gudu yake ya nufi parking space da ita. Sojojinshi na hango halin da yake da sauri suka buɗe mota ɗayan ya shiga a driver seat yayi ma motar key, Abdool na isa ya saka Namra gidan baya, sannan shi ma ya shiga.
Wasu sojojin suka shiga wata motar suka rufa masa baya.
@360 suka isa asibiti kai tsaye aka wuce da ita emergency, likitoci suka shiga bata taimakon gaggauwa.
Yana gurin zaune ya dafe kai wasu ƴan gidansu suka iso, cikin har da Hajiya Shafa.
Bayan kamar mintuna talatin likitocin suka fito, ɗaya daga cikinsu ne ya tsaya yana yi ma Hajiya bayani wai a barta ta samu bachi sun mata allura saboda akwai gajiya sosai a tare da ita.
Abdool na zaune a gurin har su Hajiya Shafa suka shiga suka fito, tare da sisters na shi.
“Babangida (Sunan da take kiransa da shi kenan kasancewar sunan mahaifin Mai Martaba ne aka sakaasa) Mu zamu tafi tun da abun da sauƙi, kuma likita yace ana buƙatar ta huta, Hajiya kilishi zata tsaya nan ta kwana, kuma ka faɗawa sojojinka kar su bar kowa ya shigo, ga kuma dogarawa nan Mai Martaba ya iko maka in case of...”
Kai kawai ya iya ɗaga mata, sai sisters ɗinsa da waɗanda suka zo tare suka masa Allah ya sauwaƙe.
Sai da suka fice sannan ya miƙe tsaye yana faɗawa sojan da ke kusa da shi cewar kar ya bar kowa ya shigo gurin, yana rufe baki sai ga Asiya Sister shi ta dawo da gudu ta miƙawa sojanshi carpet da hijab.
“Wai ance a bawa Gwaggo”
Da kanshi ya karɓi sallayar da Hijab ɗin ya nufi ɗakin. Wani abun burgewa sai da sojan ya sare masa sannan ya miƙa nasa.
Yana tura ƙofar ɗakin ya hango Namra kwance gefen gadon an ɗaura mata drip. Hajiya Kilishi kuma na zaune saman kujera sai amsa waya take. Tana ganinshi ta miƙe tsaye ta fice, ƙarasawa yayi ya aje carpet ɗin ya zauna saman gadon ya kai hannunshi ya shafa fuskarta. A hankali ya sauke ajiyar zuciya sai ya sauka ya zagaya ta bayanta ya hau saman hagon ya rumgumeta ya luma yatsunsa cikin nata, sai hawaye suka gangaro daga idonshi suka sauka saman ƙananan kitson da ke kanta.
Jin wayarsa na ringing yasa ya fiddota daga aljihun wandonshi ya kashe ta gaba ɗaya, ya lumshe ido yana ƙara janta jikinsa.
A wani ɗakin Hajiya Kilishi ta kwana, domin be sauka daga kan gadon ba sai da aka kira sallah asuba. Sannan ya sauka saman gadon ya shiga banɗakin dake room ɗin yayi alwala ya fito shi da sojojinsa suka nufi masallaci yayinda aka bar dogarawa suna cigaba da gadinta.
Bayan ya fita ne Hajiya Kilishi ya dawo ɗakin ta yi sallah asuba, bayan ta gama ya hau amsa wayar da ake mata dan tambayar jikin Namra. Sai ga Abdool ya dawo ɗakin a dole ta miƙe tana amsa gaisuwarsa ta fice daga ɗakin.
Wannan karon saman kujera ya zauna ya matsa can kusa da fuskarta ya ɗora tashi saman gado ya kwantar, sai hancinshi ya riƙa gogar nata, numfashinsu na taraiyya da juna.
A hankali ta buɗe ido karaf cikin nashi, bakinta da ke saitin nashi yayi ma kiss sannan ya tashi zaune daidai yana riƙa hannunta, sai itama ta tashi tana cigaba da kallonshi idonta sun yi wani fari.
Har cikin jininshi yake jin tsanyin dake cikin hannunta, zuciyarsa cike da tausayinta.
“Sannu”
Ya faɗa yana kai hannu ya shafa gefen fuskarta.
“Sallah”
Ta ce a kasale. Miƙewa yayi tsaye ya shiga bathroom ɗin ɗakin ya ɗauko ƙaramin bokin da ke ciki ya fito sai ya buɗe ƙofar ɗakin yayi magana da boys ɗinsa da suke gurin, sannan ya dawo ya zauna a kusa da ita.
“Za a kawo ruwa yanzu, muje ki yi fitsari”
Ƙoƙarin saukowa ta riƙa yi sai kawai ya ɗauke ta ya nufi bathroom ɗin da ita.
Ƙoƙarin ɗaga mata saket ɗin ya riƙa yi sai ta riƙe, ya kalleta.
“Baki da ƙarfi Abnam”
“Zan iya”
Baya son musa mata, sai kawai ya fito yaja mata ƙofar. Da dafe dafen bango ta yi fitsarin ta fito, sai ya sake ɗaukarta ya maida saman gadon.
“Allah ya baki lafiya”
Ya faɗa yana kwantarda kanta saman kafaɗarshi. Cikin ƙanƙanen lokaci aka buga ƙofar ɗakin sai ya ɗagarda kanta shi kuma ya tashi ya buɗe ya karɓo robar da carton ɗin ruwan faro, sai da ya buɗe ruwan sannan ya zauna kusa da ita ya kama hannayenta ya wanke mata su sau uku, sai ya zuba ruwa a hannunshi ya kai mata a baki ta kurkure bakinta ta zuba cikin robar sai yasa yatsansa ya wanke mata haƙora, sai ya sake zuba ruwan a hannunshi ya kai mata a baki ta kkurkura har sau biyu sannan ya shaƙa mata hanci sai kuma ya riƙa mata hancin ta face, ya wanke mata fuskarta sannan ya wanke hannayenta zuwa murafiƙai, ya shafa mata kai ya ƙwaƙwala mata kunnuwa sai ya saukar da robar ƙasa ƙasa ya kama ƙafafunta ya tsattsafe ya wanke su tas, sannan ya ɗauke robar ya kai bathroom ya fita ya karɓo mata carpet da hijab.
Sai da ya shinfiɗa mata carpet ɗin sannan ya saka mata hijabin, ya sauƙo da ita saman gadon ya tsayar, ganin jikinta rawa yasa ya zaunar da ita, ya tattara hankalinsa ya miƙa mata yana kallon yadda take sallah a zaune cike da tausayawa. Tana ƙarewa ya dawo kusa da ita ya zauna, sai ta kwantar da kanta saman kafaɗarshi tana hawaye. Hannayensa biyu yasa ya ɗago fuskarta ya kai bakinshi daidai hawayenta yayi mata kiss.
“Babu wanda ya isa ya shiga tsakanin mu Inshallah”
Ya faɗa kamar mai raɗa, sai kawai ta fashe da kuka shi kuma ya rumgumeta a ƙirjinsa, ya lumshe ido yana sauraren sautin kukanta dake tashi a hankali.
RASHIDA FINAL POINT OF VIEW (POV).
Ita ce ta biyu wacce ta miƙe tsaye ta yi jawabin bayan shugabar ƙungiyarsu ta gama, kasancewar yanzu ita ce mataimakiyar shugaba, a duk inda za a je da ita ake zuwa cikin da wajen garin kaduna, har South west, south south suke zuwa gurin wayarda kan al'umma akan a daina ƙyamar masu ɗauke da cutar hiv, suna kuma wayarda kai akan masu cutar su daina takura kansu da ganin kamar mutuwarsu tana kusa da su.
Har ƙauyuka suna shiga su wayarda kai, abun yanxu yayi gaba har nijar da sudan ghana sukan leƙa wani lokacin domin halartar taron ƙarawa juna sani ko kuma na ƙungiyoyin duniya qani lokacin ma.har.
Ta tattara rayuwar aure ta aje gefe, duk kuwa da irin tayin da Alhaji bashir da kuma wasu mazan suke mata, bata son abunda zai sake ɗaga mata hankali a yanzu, shiyasa bata kawowa kanta zancen aure a kusa.
A duk lokacin da ta tuna da Kalsoom ce take riƙe da ƴaƴanta sai ta yi ma Allah godiya, domin bata san Kalsoon ƴar'uwa ba ce sai a yanzu, tana ƙoƙari gurin ganin ta bawa yaranta tarbiya, basa mata complain ɗin sun rasa wani abu ko an musu wani abun sai ɗan abunda rai ba zai rasa ba, sai yanzu ta tabbatar good people are still exist, ba ko wace abokiyar zama ce kishiyaba wata kan ƴar'uwa ce.
Bata da matsala ta ko ina a yanzu, sai dai tana nadamar abunda duk ta tuna sai baƙinciki ya rufeta, wato sanadin wannan ciwon nata, a duk lokacin da aka tambaye ta dalilin wannan ciwon nata ta kan ce ta same shi ne ta hanyar ƙarin jini da aka mata, domin kawai ta kare kanta.
Shekara biyar da shiga ƙungiyar zuwa yau rayuwarta ta zama abar kwatance, rayuwarta darasi ce ga duk mace mai irin rayuwarta, ko kuma halinta, ita kanta yanzu ta koyi abubuwa da yawa na rayuwar duniya da kuma zama da mutane.
Ko da aka yi birthday ɗin Izzah tana Abuja gurin wani taro, washe garin ranar da ta dawo taje gidan ta kai musu tsarabarsu da kuma birthday gift ta bawa Izzah.
Ta jidaɗin yadda ta same su, baka iya banbance tsakanin Ƴaƴan Kalsoom da nata a gurin Kalsoom wato Amal da Rafiq da Husna, sam mutum ba zai iya cewa su ne ƴaƴan Kalsoom ba, sau da dama zata bawa su Izza abu ta hana ƴaƴanta.
Bata daɗe a gidan ba duk da ƴaran sun so haka, amman ta ƙi a duk lokacin da taje gidan haka take bata daɗewa take fitowa.
Ko da iso gidanta uku da rabi yayi, dan haka tana shiga bathroom ɗinta ta yi alwalar la'asar ta fito ta shimfiɗa sallaya ta saka hijab taja carbi tana la'zimi kamin lokacin tada sallah yayi.
Wayarta ce tayi ƙara daman ta ji tsayawar mota a harabar gidanta, sai kawai ta miƙe tsaye ta nufi falo ta buɗe masa ƙofa.
“Hajiya...”
“Alhaji Bashir”
Shigowa yayi yana faɗin
“Aiko na taki sa'ah dan ban tsamaci kina garin ba”
“Jiya na dawo”
“Mashallah ya Abujar?”
Ya tambaya yayinda yake ƙoƙarin zaunawa.
“Abuja sai hamdallah, ya aikin naku”
“Aiki da godiya, iv na zo na kawo miki”
“Ba dai na aurenka ba ko?”
“Shi mana ba kin ƙi ni ba”
“Dana ƙi ka ya hana dubu su soka ne?”
“Cikin dubun ai na ƙawo ƙoƙon barata a gareki amman kika ƙi yarda, kuma ni wallahi ko a yanzu kika yarda zan aure ki”
Har ya miƙe tsaye sai kuma ya ce
“Mai Martaba kar naje gida wani abun ya same ni”
“Babu abunda zai same ka, indai ni na haifi Abdallah ko hararka ba zai sake yi ba”
Da tsinginta ya fice. Sannan Mai Martaba ya kalli Namra ya ce.
“Za a maidaki gurin Ummi ba zaki tare a yau ba, zan yi magana da mahaifinki”
Cikin wani irin nauyin jiki da zuciya Namra ta miƙe tsaye jiri na ɗibarta, aiko tana kaiwa bakin ƙofa ta sai tayi baya-baya ta faɗi ƙasa sumamamiya.
A take Abdool ya manta da agaban Mai Martaba yake, a guje ya ƙarasa inda take yasa hannunshi ya ɗauke yana kiran sunanta amman ina ta riga tayi nisa.
A firgice ya fita da ita a falon kamar wanda ya tallaɓo jaririya. Mamaki da aljab ya hana kowa magana sai kallon ikon Allah suke, Abdool ya talloɓo Namra sai gudu yake ya nufi parking space da ita. Sojojinshi na hango halin da yake da sauri suka buɗe mota ɗayan ya shiga a driver seat yayi ma motar key, Abdool na isa ya saka Namra gidan baya, sannan shi ma ya shiga.
Wasu sojojin suka shiga wata motar suka rufa masa baya.
@360 suka isa asibiti kai tsaye aka wuce da ita emergency, likitoci suka shiga bata taimakon gaggauwa.
Yana gurin zaune ya dafe kai wasu ƴan gidansu suka iso, cikin har da Hajiya Shafa.
Bayan kamar mintuna talatin likitocin suka fito, ɗaya daga cikinsu ne ya tsaya yana yi ma Hajiya bayani wai a barta ta samu bachi sun mata allura saboda akwai gajiya sosai a tare da ita.
Abdool na zaune a gurin har su Hajiya Shafa suka shiga suka fito, tare da sisters na shi.
“Babangida (Sunan da take kiransa da shi kenan kasancewar sunan mahaifin Mai Martaba ne aka sakaasa) Mu zamu tafi tun da abun da sauƙi, kuma likita yace ana buƙatar ta huta, Hajiya kilishi zata tsaya nan ta kwana, kuma ka faɗawa sojojinka kar su bar kowa ya shigo, ga kuma dogarawa nan Mai Martaba ya iko maka in case of...”
Kai kawai ya iya ɗaga mata, sai sisters ɗinsa da waɗanda suka zo tare suka masa Allah ya sauwaƙe.
Sai da suka fice sannan ya miƙe tsaye yana faɗawa sojan da ke kusa da shi cewar kar ya bar kowa ya shigo gurin, yana rufe baki sai ga Asiya Sister shi ta dawo da gudu ta miƙawa sojanshi carpet da hijab.
“Wai ance a bawa Gwaggo”
Da kanshi ya karɓi sallayar da Hijab ɗin ya nufi ɗakin. Wani abun burgewa sai da sojan ya sare masa sannan ya miƙa nasa.
Yana tura ƙofar ɗakin ya hango Namra kwance gefen gadon an ɗaura mata drip. Hajiya Kilishi kuma na zaune saman kujera sai amsa waya take. Tana ganinshi ta miƙe tsaye ta fice, ƙarasawa yayi ya aje carpet ɗin ya zauna saman gadon ya kai hannunshi ya shafa fuskarta. A hankali ya sauke ajiyar zuciya sai ya sauka ya zagaya ta bayanta ya hau saman hagon ya rumgumeta ya luma yatsunsa cikin nata, sai hawaye suka gangaro daga idonshi suka sauka saman ƙananan kitson da ke kanta.
Jin wayarsa na ringing yasa ya fiddota daga aljihun wandonshi ya kashe ta gaba ɗaya, ya lumshe ido yana ƙara janta jikinsa.
A wani ɗakin Hajiya Kilishi ta kwana, domin be sauka daga kan gadon ba sai da aka kira sallah asuba. Sannan ya sauka saman gadon ya shiga banɗakin dake room ɗin yayi alwala ya fito shi da sojojinsa suka nufi masallaci yayinda aka bar dogarawa suna cigaba da gadinta.
Bayan ya fita ne Hajiya Kilishi ya dawo ɗakin ta yi sallah asuba, bayan ta gama ya hau amsa wayar da ake mata dan tambayar jikin Namra. Sai ga Abdool ya dawo ɗakin a dole ta miƙe tana amsa gaisuwarsa ta fice daga ɗakin.
Wannan karon saman kujera ya zauna ya matsa can kusa da fuskarta ya ɗora tashi saman gado ya kwantar, sai hancinshi ya riƙa gogar nata, numfashinsu na taraiyya da juna.
A hankali ta buɗe ido karaf cikin nashi, bakinta da ke saitin nashi yayi ma kiss sannan ya tashi zaune daidai yana riƙa hannunta, sai itama ta tashi tana cigaba da kallonshi idonta sun yi wani fari.
Har cikin jininshi yake jin tsanyin dake cikin hannunta, zuciyarsa cike da tausayinta.
“Sannu”
Ya faɗa yana kai hannu ya shafa gefen fuskarta.
“Sallah”
Ta ce a kasale. Miƙewa yayi tsaye ya shiga bathroom ɗin ɗakin ya ɗauko ƙaramin bokin da ke ciki ya fito sai ya buɗe ƙofar ɗakin yayi magana da boys ɗinsa da suke gurin, sannan ya dawo ya zauna a kusa da ita.
“Za a kawo ruwa yanzu, muje ki yi fitsari”
Ƙoƙarin saukowa ta riƙa yi sai kawai ya ɗauke ta ya nufi bathroom ɗin da ita.
Ƙoƙarin ɗaga mata saket ɗin ya riƙa yi sai ta riƙe, ya kalleta.
“Baki da ƙarfi Abnam”
“Zan iya”
Baya son musa mata, sai kawai ya fito yaja mata ƙofar. Da dafe dafen bango ta yi fitsarin ta fito, sai ya sake ɗaukarta ya maida saman gadon.
“Allah ya baki lafiya”
Ya faɗa yana kwantarda kanta saman kafaɗarshi. Cikin ƙanƙanen lokaci aka buga ƙofar ɗakin sai ya ɗagarda kanta shi kuma ya tashi ya buɗe ya karɓo robar da carton ɗin ruwan faro, sai da ya buɗe ruwan sannan ya zauna kusa da ita ya kama hannayenta ya wanke mata su sau uku, sai ya zuba ruwa a hannunshi ya kai mata a baki ta kurkure bakinta ta zuba cikin robar sai yasa yatsansa ya wanke mata haƙora, sai ya sake zuba ruwan a hannunshi ya kai mata a baki ta kkurkura har sau biyu sannan ya shaƙa mata hanci sai kuma ya riƙa mata hancin ta face, ya wanke mata fuskarta sannan ya wanke hannayenta zuwa murafiƙai, ya shafa mata kai ya ƙwaƙwala mata kunnuwa sai ya saukar da robar ƙasa ƙasa ya kama ƙafafunta ya tsattsafe ya wanke su tas, sannan ya ɗauke robar ya kai bathroom ya fita ya karɓo mata carpet da hijab.
Sai da ya shinfiɗa mata carpet ɗin sannan ya saka mata hijabin, ya sauƙo da ita saman gadon ya tsayar, ganin jikinta rawa yasa ya zaunar da ita, ya tattara hankalinsa ya miƙa mata yana kallon yadda take sallah a zaune cike da tausayawa. Tana ƙarewa ya dawo kusa da ita ya zauna, sai ta kwantar da kanta saman kafaɗarshi tana hawaye. Hannayensa biyu yasa ya ɗago fuskarta ya kai bakinshi daidai hawayenta yayi mata kiss.
“Babu wanda ya isa ya shiga tsakanin mu Inshallah”
Ya faɗa kamar mai raɗa, sai kawai ta fashe da kuka shi kuma ya rumgumeta a ƙirjinsa, ya lumshe ido yana sauraren sautin kukanta dake tashi a hankali.
RASHIDA FINAL POINT OF VIEW (POV).
Ita ce ta biyu wacce ta miƙe tsaye ta yi jawabin bayan shugabar ƙungiyarsu ta gama, kasancewar yanzu ita ce mataimakiyar shugaba, a duk inda za a je da ita ake zuwa cikin da wajen garin kaduna, har South west, south south suke zuwa gurin wayarda kan al'umma akan a daina ƙyamar masu ɗauke da cutar hiv, suna kuma wayarda kai akan masu cutar su daina takura kansu da ganin kamar mutuwarsu tana kusa da su.
Har ƙauyuka suna shiga su wayarda kai, abun yanxu yayi gaba har nijar da sudan ghana sukan leƙa wani lokacin domin halartar taron ƙarawa juna sani ko kuma na ƙungiyoyin duniya qani lokacin ma.har.
Ta tattara rayuwar aure ta aje gefe, duk kuwa da irin tayin da Alhaji bashir da kuma wasu mazan suke mata, bata son abunda zai sake ɗaga mata hankali a yanzu, shiyasa bata kawowa kanta zancen aure a kusa.
A duk lokacin da ta tuna da Kalsoom ce take riƙe da ƴaƴanta sai ta yi ma Allah godiya, domin bata san Kalsoon ƴar'uwa ba ce sai a yanzu, tana ƙoƙari gurin ganin ta bawa yaranta tarbiya, basa mata complain ɗin sun rasa wani abu ko an musu wani abun sai ɗan abunda rai ba zai rasa ba, sai yanzu ta tabbatar good people are still exist, ba ko wace abokiyar zama ce kishiyaba wata kan ƴar'uwa ce.
Bata da matsala ta ko ina a yanzu, sai dai tana nadamar abunda duk ta tuna sai baƙinciki ya rufeta, wato sanadin wannan ciwon nata, a duk lokacin da aka tambaye ta dalilin wannan ciwon nata ta kan ce ta same shi ne ta hanyar ƙarin jini da aka mata, domin kawai ta kare kanta.
Shekara biyar da shiga ƙungiyar zuwa yau rayuwarta ta zama abar kwatance, rayuwarta darasi ce ga duk mace mai irin rayuwarta, ko kuma halinta, ita kanta yanzu ta koyi abubuwa da yawa na rayuwar duniya da kuma zama da mutane.
Ko da aka yi birthday ɗin Izzah tana Abuja gurin wani taro, washe garin ranar da ta dawo taje gidan ta kai musu tsarabarsu da kuma birthday gift ta bawa Izzah.
Ta jidaɗin yadda ta same su, baka iya banbance tsakanin Ƴaƴan Kalsoom da nata a gurin Kalsoom wato Amal da Rafiq da Husna, sam mutum ba zai iya cewa su ne ƴaƴan Kalsoom ba, sau da dama zata bawa su Izza abu ta hana ƴaƴanta.
Bata daɗe a gidan ba duk da ƴaran sun so haka, amman ta ƙi a duk lokacin da taje gidan haka take bata daɗewa take fitowa.
Ko da iso gidanta uku da rabi yayi, dan haka tana shiga bathroom ɗinta ta yi alwalar la'asar ta fito ta shimfiɗa sallaya ta saka hijab taja carbi tana la'zimi kamin lokacin tada sallah yayi.
Wayarta ce tayi ƙara daman ta ji tsayawar mota a harabar gidanta, sai kawai ta miƙe tsaye ta nufi falo ta buɗe masa ƙofa.
“Hajiya...”
“Alhaji Bashir”
Shigowa yayi yana faɗin
“Aiko na taki sa'ah dan ban tsamaci kina garin ba”
“Jiya na dawo”
“Mashallah ya Abujar?”
Ya tambaya yayinda yake ƙoƙarin zaunawa.
“Abuja sai hamdallah, ya aikin naku”
“Aiki da godiya, iv na zo na kawo miki”
“Ba dai na aurenka ba ko?”
“Shi mana ba kin ƙi ni ba”
“Dana ƙi ka ya hana dubu su soka ne?”
“Cikin dubun ai na ƙawo ƙoƙon barata a gareki amman kika ƙi yarda, kuma ni wallahi ko a yanzu kika yarda zan aure ki”