Sashe 38
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta fara hawaye. Dubu biyar ma Dillaliya jin su take kamar ranta balle har dubu ɗari uku da hansin.
“Ni ko yau ina zan samu wannan kuɗi, ba kaya ba kuɗi mutane ba haƙuri ne da su ba, yanzu wanda na karɓar wa kuɗin nan ba yafewa zata yi ba, nima ɗan jari masu son ganin baya na yau burinsu ya cika, na shiga uku na lalace”
Namra tayi mata wani kallo wanda ita ka ɗai ta san fassararsa.
“Allah satki Dillaliya, ke dubu ɗari uku kawai kika rasa, ni ko mijina ya karye cikina ya zube yanzu kuma gidan ya ƙone gaba ɗaya komai be fita ba, kuma yanzu ki zo kina min wannan maganar, ba sai kin yi lunƙe-lunƙe ba, ki kwantar da hankalin ki zan biya ki, sisinki ba zata yi ciwon kai ba Inshallah”
Namra ta ƙarasa maganar da kuka. Wani daɗi da Kunya ya lulluɓe Dillaliya a lokaci ɗaya, daman ita tana ganin alamu tasan Namra ƴar masu kuɗi ce, kuma haka da Namra tace ya ƙara tabbatar mata da zancenta. Sumi-sumi ta tashi tana share hawaye.
“Ba haka bane ƴar nan, Allah dai ya sassauta miki amman ba shine nufi na ba”
Tana ficewa Namra ta rafka uban tagumi tana tunanin rayuwarta. Babu wanda ta faɗo mata a rai sai Hajiya Saratu matar data taimaketa lokacin da Asim be da lafiya, sai dai zuciyarta bata yarda da zata taimaketa dan Allah ba. A ɗayan ɓangare na zuciyarta kuma Anty Amarya take tunani, su biyu nan sune kawai mafitar ta a rayuwa.
KALSOOM POV.
Kwana biyu nan ta miƙa lamarinta ga Ubangiji, nafila dare da Karatun suratul yaseen da Salma ta faɗa mata shi kawai ta sawa gaba.
Yau ma da wuri ta tashi ta shirya musu komai na karya. Amman Rashida bata tsaya karyawa ta fice, yara kuma tasa musu nasu a kula suka tafi makaranta.
Sai da ta sawa Hilal ruwan wanka yayi wanka sannan suka fito dinning sai tsokanarta yake.
“Ni duk gajiyar da ni, sai fama nake, Allah dai yasa ina da juriya ba zan iya zama da ke ba”
Ya kashe mata ido ɗaya, yana ƙoƙarin zaunawa saman kujera. Ita kam ido ta sakar masa tana kallon ikon Allah, daman yasan abunda zata faɗa ne shine ya rigata faɗa.
“Kai dai Allah be raba ka da abun magana ba”
“Ba wani magana sai gaskiya kema ai kin san ina ƙoƙari in ba haka ba ai sai abun yayi min yawa”
Dariya kawai tayi ta cigaba da haɗa masa tea. Shi kuma ya kwantar da kai yana kallon rigar bachinta dake buɗe.
Tana gama haɗa masa tea aka buga ƙofar falo, saurin miƙewa yayi yana faɗin bari na duba, dan nasan ki da shegen salo zaki iya cewa bari ki duba, har wani yaga halalina.
Kai kawai ta girgiza tana dariya, shima dariyar yake har ya isa gaban ƙofar ya buɗe.
Mai Gadi ne jikin ƙofar riƙe da wani farin abu kamar wasiƙa, ya miƙawa Hilal.
“Alhaji, gashi aka ce a bawa Auntie su Ulfah”
“Waya kawo?”
Doc. Ya karɓa yana tambaya.
“Wani ne a mota har ya tafi ma”
“Okay”
Ya mai da ƙofar ya rufe. Sannan ya juyo ya nufo dinning inda take Kalsoom take zaune yana faɗin.
“Ga saƙo aka ce a baki”
“Saƙon me?”
“Oho sai kin buɗe”
Sai da ya zauna sannan ya miƙa mata. Ita kuma ta karɓa da hannu biyu, ba tare da fargabar komai ba ta yage takardar.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Da sauri ta miƙe tsaye tana zaro ido, sai hotuna suka faɗo tare da kofin tea dake gabanta.
“Subhanallah”
Hilal ya faɗa lokacin da idonsa ya sauka kan hotunan.
____________________________________________
#Share
#Comment
#Candy
#Blog
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 29*
NOT EDITED ⚠️
Shiru-shiru Mama bata aga an kawo musu karin safe ba, gashi har rana tayi kuma babu wani labari, ga yunwa tana ji ita da Asim.
Dan yauzu sauki ya fara zo masa yana son abinci sosai har fira ya kan yi sama-sama.
“Hajara tashi na baki kuɗin achaɓa ke je ki karɓa mana abinci wata ƙila na yanzu zata zo ba,marar lafiya kuma sai da abinci, wannan zunzunzun ba amo ba labari,
Ko tana nufin ba zata ake zuwa asibitin bane dan nayi magana?”
Ta ciro naira hansi ta miƙawa ƴarta Hajara.
“Ungo idan kin je ta baki na dawowa”
Da kallo Asim.ya bi ƙanwar tasa, sai da ta fice sannan ya kalli Mama yace
“Wallahi ko maƙiyinka ya faɗa a hali dana shiga sai an tausaya masa, ki duba ki gani ace ina sirikin su amman har yanzu ba su sake zuwa duba ni ba, ai ko wani na kashe musu sa duba ni tun da ƴar su nake aure”
“Hmmm ai Wallahi mutane nan basa son ka da alheri, su fa basu ƙi ka mutu ba, nifa ina zargin kamar ma da sa hannunsu a haɗarin nan da kayi”
“Nima haka nake tunani saboda lokacin dana je karɓar motar sai da suka sa Direban su, ya duba motar gaba da baya sannan aka ba ni key ɗin, sannan idan har ba plan ba taya daga haɗari mota zata kama da wuta haka kawai”
“Ato nifa na faɗa maka ba su ƙi ka mutu ba, sai ƴarsu ta auri wanda take so, daman can ba a banza aka baka ita ba”
“Amman Namra sai naga kamar tsakani da Allah take so na”
“Hmm ai wannan hidumar da tayi maka, saboda itace silar komai shiyasa tayi maka, kuma yanzu kaga ta kama kayan ɗakinta ta sai da dan ace kai ƙa canye komai sai a fara cewa ta sai da komai dalilinka, ai ba zata rasa kuɗin da za'a maka komai a bankinta ba amman ta zaɓi ta siyar da kayan ɗakinta ai kasan da walakin goro a miya”
“Kayan ɗakinta ta siyar?”
Ya tambaya a wahale dan ciwon kan ya fara dawo masa.
“Eh ba shine ka ji jiya ina magana ba, har kake ganin laifina”
Shiru yayi be sake magana ba, sai ciwon kan yake saurare.
NAMRA POV.
Ta ci kuka sosai har sai da ta goɗe Allah, ba tare da ta bari kowa ya gani ba, dan wuni tayi a ɗakin su Mardiya, duk wanda ya zo mata tanzanko sai yayi mata a cikin ɗakin ko kuma daga bakin ƙofar.
Guraren Uku da rabi Hajara ta shigo ɗakin da sallama, Namra ta amsa mata murya can ƙasa-ƙasa.
“Wa'alaikissalam Hajara”
“Na'am Anty naje gidan naga duk ya ƙone aka ce min kina nan”
“Wallahi jiya ne muna dawowa daga asibiti muka tarar ana kashe wutar”
“O'o wannan abun be yi daɗi ba, nima Mamace tace na zo na karɓo abinci tun safe bata gan ki ba shiru, ashe abunda ya faru kenan, Wallahi ba mu sani ba”
Ta faɗa cike da tausayawa.
“Ina Asim ɗin yaji sauƙi?”
“Ya samu sauƙi sosai ɗazu ma har fira muke yi da shi, har shi ma yace na zo na karɓa abincin”
“Bari na baki ƙuɗi ki siya masa na hanya”
Ta tashi cikin rashin kuzari, suka fita a tare daga cikin ɗakin. Kular Maman Mardiya ta ara tana cikin wanke wa, wata maƙociyar su ta shigo tace kiran Namra.
“Kin yi baki masu gida sun zo su duba gidan su”
A take ta aje wankin kular da take ta gyara tsayin Hijabinta ta fita. Manyan motoci ne fake a ƙofar gidan.
Cikin faɗuwar gaba ta nitsa ta shiga cikin gidan tana musu sallama.
“Wa'alaikissalam ke ce matar gidan?”
Hajiyar ta tambaya tana cire gilashin dake zaune a idonta.
“Eh Nice ance masu gida sun zo”
“Eh ina mai gidan na ki?”
“Yana asibiti ba shi da lafiya ne”
“Ayyah so sorry, amman kin san musabbabin tashin wutar ne?”
“A'a wallahi nima asibiti naje ko da na dawo na tarar wuta na ci”
“Allah sarki Allah ya maida alheri, daman mun zo ne mu duba ance muna anyi wuta”
Ta faɗa tana picking ɗin wayar dake hannunta.
“I'm my way Abdool, har na ga gidan ma”
Sai kuma tayi dariya, ta kashe wayar. Tasa hannu a jaka ta ɗauko kuɗi masu ɗan dama ta miƙawa Namra.
“Ga wannan Allah ya tsare gaba”
Har ƙasa Namra ta ɗuka mata.
“Na gode Allah saka miki da alheri”
Murmushi farar Hajiyar tayi
“Ba komai”
Har gaban mota Namra ta raƙa ta ta shiga motar ta wuce, sannan Namra ta koma gidan ta ɗauki kular da plates da cibi, suka fito ita da Hajara.
A bakin titi ta siya musu shinkafa da miya da nama na 1k. Sannan suka tari Napep suka hau.
Daga ita har Hajara sululu suka shiga ɗakin, kama kamar ita dake ta sun-sun da kai bata son a ga kumburin dake fuskarta.
Sai da ta gaisa da Mama sannan ta nufi gurin da Asim yake ta zauna, yana kallonta.
“Ya jikin ka?”
“Alhamdulillah”
“Likitan ya duba...”
Jin abunda Hajara take faɗa yasa ta kasa ƙarasawa. Mama ta ɗora hannu a ka, tana faɗin
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Asim kuma ya kalli Namra cike da tashin hankali. Ita kuma babu abunda take sai kuka.
“We lost everything Asim, i lost my baby, shine naje asibiti ko da na dawo na tarar gidan ya ƙone”
Rumtse ido Asim yayi, zuciyaraa ɗauke da abubuwa biyu, jindaɗin ɓarin da tayi, da kuma baƙincikin ƙonewar da gidan yayi.
Ringing ɗin wayar Asim dake hannun Mama ne yasa ta share munafukan hawayenta ta danna picking tana kara wayar a kunne.
“Wa'alaikissalam.
Lafiya ƙalau
Alhamdulillah”
Shiru ta ɗan yi kamin tace
“Allah sarki. Namra karɓi ga Maman ki”
Hannu Namra ta kai ta karɓa sai ta fice daga ɗakin. Mama ta kalli Asim cikin ruɗu tace
“Ibrahim idan kaji sauƙi ka rabu da yarinyar nan, ina ganin babu alheri a zaman auren ku, wannan irin bala'i haka”
Shi dai be ce mata komai ba, shi ta kansa yake abunda duk yake tunanin zai zame masa alheri yana ƙoƙarin koma masa sheri.
Yanzu da wannen zai ji ciwon jikinsa ko wannan rashin da suka yi?
“Kuma ina ganin abunda yafi kawai ku koma gida, a can ma dole ta samu wani abu saboda a gaban iyayenta take”
Har lokacin be ce komai ba, Hajara tace
“Ni Wallahi duk ta bani tausayi”
“Ni ko yau ina zan samu wannan kuɗi, ba kaya ba kuɗi mutane ba haƙuri ne da su ba, yanzu wanda na karɓar wa kuɗin nan ba yafewa zata yi ba, nima ɗan jari masu son ganin baya na yau burinsu ya cika, na shiga uku na lalace”
Namra tayi mata wani kallo wanda ita ka ɗai ta san fassararsa.
“Allah satki Dillaliya, ke dubu ɗari uku kawai kika rasa, ni ko mijina ya karye cikina ya zube yanzu kuma gidan ya ƙone gaba ɗaya komai be fita ba, kuma yanzu ki zo kina min wannan maganar, ba sai kin yi lunƙe-lunƙe ba, ki kwantar da hankalin ki zan biya ki, sisinki ba zata yi ciwon kai ba Inshallah”
Namra ta ƙarasa maganar da kuka. Wani daɗi da Kunya ya lulluɓe Dillaliya a lokaci ɗaya, daman ita tana ganin alamu tasan Namra ƴar masu kuɗi ce, kuma haka da Namra tace ya ƙara tabbatar mata da zancenta. Sumi-sumi ta tashi tana share hawaye.
“Ba haka bane ƴar nan, Allah dai ya sassauta miki amman ba shine nufi na ba”
Tana ficewa Namra ta rafka uban tagumi tana tunanin rayuwarta. Babu wanda ta faɗo mata a rai sai Hajiya Saratu matar data taimaketa lokacin da Asim be da lafiya, sai dai zuciyarta bata yarda da zata taimaketa dan Allah ba. A ɗayan ɓangare na zuciyarta kuma Anty Amarya take tunani, su biyu nan sune kawai mafitar ta a rayuwa.
KALSOOM POV.
Kwana biyu nan ta miƙa lamarinta ga Ubangiji, nafila dare da Karatun suratul yaseen da Salma ta faɗa mata shi kawai ta sawa gaba.
Yau ma da wuri ta tashi ta shirya musu komai na karya. Amman Rashida bata tsaya karyawa ta fice, yara kuma tasa musu nasu a kula suka tafi makaranta.
Sai da ta sawa Hilal ruwan wanka yayi wanka sannan suka fito dinning sai tsokanarta yake.
“Ni duk gajiyar da ni, sai fama nake, Allah dai yasa ina da juriya ba zan iya zama da ke ba”
Ya kashe mata ido ɗaya, yana ƙoƙarin zaunawa saman kujera. Ita kam ido ta sakar masa tana kallon ikon Allah, daman yasan abunda zata faɗa ne shine ya rigata faɗa.
“Kai dai Allah be raba ka da abun magana ba”
“Ba wani magana sai gaskiya kema ai kin san ina ƙoƙari in ba haka ba ai sai abun yayi min yawa”
Dariya kawai tayi ta cigaba da haɗa masa tea. Shi kuma ya kwantar da kai yana kallon rigar bachinta dake buɗe.
Tana gama haɗa masa tea aka buga ƙofar falo, saurin miƙewa yayi yana faɗin bari na duba, dan nasan ki da shegen salo zaki iya cewa bari ki duba, har wani yaga halalina.
Kai kawai ta girgiza tana dariya, shima dariyar yake har ya isa gaban ƙofar ya buɗe.
Mai Gadi ne jikin ƙofar riƙe da wani farin abu kamar wasiƙa, ya miƙawa Hilal.
“Alhaji, gashi aka ce a bawa Auntie su Ulfah”
“Waya kawo?”
Doc. Ya karɓa yana tambaya.
“Wani ne a mota har ya tafi ma”
“Okay”
Ya mai da ƙofar ya rufe. Sannan ya juyo ya nufo dinning inda take Kalsoom take zaune yana faɗin.
“Ga saƙo aka ce a baki”
“Saƙon me?”
“Oho sai kin buɗe”
Sai da ya zauna sannan ya miƙa mata. Ita kuma ta karɓa da hannu biyu, ba tare da fargabar komai ba ta yage takardar.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Da sauri ta miƙe tsaye tana zaro ido, sai hotuna suka faɗo tare da kofin tea dake gabanta.
“Subhanallah”
Hilal ya faɗa lokacin da idonsa ya sauka kan hotunan.
____________________________________________
#Share
#Comment
#Candy
#Blog
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 29*
NOT EDITED ⚠️
Shiru-shiru Mama bata aga an kawo musu karin safe ba, gashi har rana tayi kuma babu wani labari, ga yunwa tana ji ita da Asim.
Dan yauzu sauki ya fara zo masa yana son abinci sosai har fira ya kan yi sama-sama.
“Hajara tashi na baki kuɗin achaɓa ke je ki karɓa mana abinci wata ƙila na yanzu zata zo ba,marar lafiya kuma sai da abinci, wannan zunzunzun ba amo ba labari,
Ko tana nufin ba zata ake zuwa asibitin bane dan nayi magana?”
Ta ciro naira hansi ta miƙawa ƴarta Hajara.
“Ungo idan kin je ta baki na dawowa”
Da kallo Asim.ya bi ƙanwar tasa, sai da ta fice sannan ya kalli Mama yace
“Wallahi ko maƙiyinka ya faɗa a hali dana shiga sai an tausaya masa, ki duba ki gani ace ina sirikin su amman har yanzu ba su sake zuwa duba ni ba, ai ko wani na kashe musu sa duba ni tun da ƴar su nake aure”
“Hmmm ai Wallahi mutane nan basa son ka da alheri, su fa basu ƙi ka mutu ba, nifa ina zargin kamar ma da sa hannunsu a haɗarin nan da kayi”
“Nima haka nake tunani saboda lokacin dana je karɓar motar sai da suka sa Direban su, ya duba motar gaba da baya sannan aka ba ni key ɗin, sannan idan har ba plan ba taya daga haɗari mota zata kama da wuta haka kawai”
“Ato nifa na faɗa maka ba su ƙi ka mutu ba, sai ƴarsu ta auri wanda take so, daman can ba a banza aka baka ita ba”
“Amman Namra sai naga kamar tsakani da Allah take so na”
“Hmm ai wannan hidumar da tayi maka, saboda itace silar komai shiyasa tayi maka, kuma yanzu kaga ta kama kayan ɗakinta ta sai da dan ace kai ƙa canye komai sai a fara cewa ta sai da komai dalilinka, ai ba zata rasa kuɗin da za'a maka komai a bankinta ba amman ta zaɓi ta siyar da kayan ɗakinta ai kasan da walakin goro a miya”
“Kayan ɗakinta ta siyar?”
Ya tambaya a wahale dan ciwon kan ya fara dawo masa.
“Eh ba shine ka ji jiya ina magana ba, har kake ganin laifina”
Shiru yayi be sake magana ba, sai ciwon kan yake saurare.
NAMRA POV.
Ta ci kuka sosai har sai da ta goɗe Allah, ba tare da ta bari kowa ya gani ba, dan wuni tayi a ɗakin su Mardiya, duk wanda ya zo mata tanzanko sai yayi mata a cikin ɗakin ko kuma daga bakin ƙofar.
Guraren Uku da rabi Hajara ta shigo ɗakin da sallama, Namra ta amsa mata murya can ƙasa-ƙasa.
“Wa'alaikissalam Hajara”
“Na'am Anty naje gidan naga duk ya ƙone aka ce min kina nan”
“Wallahi jiya ne muna dawowa daga asibiti muka tarar ana kashe wutar”
“O'o wannan abun be yi daɗi ba, nima Mamace tace na zo na karɓo abinci tun safe bata gan ki ba shiru, ashe abunda ya faru kenan, Wallahi ba mu sani ba”
Ta faɗa cike da tausayawa.
“Ina Asim ɗin yaji sauƙi?”
“Ya samu sauƙi sosai ɗazu ma har fira muke yi da shi, har shi ma yace na zo na karɓa abincin”
“Bari na baki ƙuɗi ki siya masa na hanya”
Ta tashi cikin rashin kuzari, suka fita a tare daga cikin ɗakin. Kular Maman Mardiya ta ara tana cikin wanke wa, wata maƙociyar su ta shigo tace kiran Namra.
“Kin yi baki masu gida sun zo su duba gidan su”
A take ta aje wankin kular da take ta gyara tsayin Hijabinta ta fita. Manyan motoci ne fake a ƙofar gidan.
Cikin faɗuwar gaba ta nitsa ta shiga cikin gidan tana musu sallama.
“Wa'alaikissalam ke ce matar gidan?”
Hajiyar ta tambaya tana cire gilashin dake zaune a idonta.
“Eh Nice ance masu gida sun zo”
“Eh ina mai gidan na ki?”
“Yana asibiti ba shi da lafiya ne”
“Ayyah so sorry, amman kin san musabbabin tashin wutar ne?”
“A'a wallahi nima asibiti naje ko da na dawo na tarar wuta na ci”
“Allah sarki Allah ya maida alheri, daman mun zo ne mu duba ance muna anyi wuta”
Ta faɗa tana picking ɗin wayar dake hannunta.
“I'm my way Abdool, har na ga gidan ma”
Sai kuma tayi dariya, ta kashe wayar. Tasa hannu a jaka ta ɗauko kuɗi masu ɗan dama ta miƙawa Namra.
“Ga wannan Allah ya tsare gaba”
Har ƙasa Namra ta ɗuka mata.
“Na gode Allah saka miki da alheri”
Murmushi farar Hajiyar tayi
“Ba komai”
Har gaban mota Namra ta raƙa ta ta shiga motar ta wuce, sannan Namra ta koma gidan ta ɗauki kular da plates da cibi, suka fito ita da Hajara.
A bakin titi ta siya musu shinkafa da miya da nama na 1k. Sannan suka tari Napep suka hau.
Daga ita har Hajara sululu suka shiga ɗakin, kama kamar ita dake ta sun-sun da kai bata son a ga kumburin dake fuskarta.
Sai da ta gaisa da Mama sannan ta nufi gurin da Asim yake ta zauna, yana kallonta.
“Ya jikin ka?”
“Alhamdulillah”
“Likitan ya duba...”
Jin abunda Hajara take faɗa yasa ta kasa ƙarasawa. Mama ta ɗora hannu a ka, tana faɗin
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Asim kuma ya kalli Namra cike da tashin hankali. Ita kuma babu abunda take sai kuka.
“We lost everything Asim, i lost my baby, shine naje asibiti ko da na dawo na tarar gidan ya ƙone”
Rumtse ido Asim yayi, zuciyaraa ɗauke da abubuwa biyu, jindaɗin ɓarin da tayi, da kuma baƙincikin ƙonewar da gidan yayi.
Ringing ɗin wayar Asim dake hannun Mama ne yasa ta share munafukan hawayenta ta danna picking tana kara wayar a kunne.
“Wa'alaikissalam.
Lafiya ƙalau
Alhamdulillah”
Shiru ta ɗan yi kamin tace
“Allah sarki. Namra karɓi ga Maman ki”
Hannu Namra ta kai ta karɓa sai ta fice daga ɗakin. Mama ta kalli Asim cikin ruɗu tace
“Ibrahim idan kaji sauƙi ka rabu da yarinyar nan, ina ganin babu alheri a zaman auren ku, wannan irin bala'i haka”
Shi dai be ce mata komai ba, shi ta kansa yake abunda duk yake tunanin zai zame masa alheri yana ƙoƙarin koma masa sheri.
Yanzu da wannen zai ji ciwon jikinsa ko wannan rashin da suka yi?
“Kuma ina ganin abunda yafi kawai ku koma gida, a can ma dole ta samu wani abu saboda a gaban iyayenta take”
Har lokacin be ce komai ba, Hajara tace
“Ni Wallahi duk ta bani tausayi”