← Book details Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 131 OF 173

Sashe 131

Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Ko kuma kika sani ciki ba, daman ai na daɗe ina zarginki, duk mace da zata bada kanta ga wani namiji ba mutum ɗaya zata tsaya ba, waya sani ma ko mijinki ne ya ɗauko cutar ya saka miki ke kuma kika saka mana, ni ban san ƙaddararta kai ni mu'amala da ke ba”

“Ni bance ka zame min ƙaddara ba kai zaka ce na zame maka? Na rasa abubuwa da dama sanadin mu'alama da kai, ƴan'uwana sun guje ni, mijina ya sake ni, na rasa lafiya ta, da duk wani farinciki nawa sanadinka Bashir, duk kai ka jani ga wannan halaka”

“Ko kuma kika jani ba, da baki sake jikinki ba zan gani ne har na yi sha'awa? Idan baki yarda ba fyaɗe zan miki ne? Baki kiji na faɗa miki da zarar naje aka gwada jinina aka tabbatar ina ɗauke da wannan cutar kutu ce zata raba ni da ke...!”

Yana kaiwa nan ya doshi gurin motarsa. Ita kuwa ta raka shi da maganganu tana hawaye.

“Idan ka fasa kai ni kotu baka haifu ga uwarka da ubanka ba Bashir kai ba ɗan halak ba ne, azzalumi macuci wanda be ji kunya keta dokar Allah, sakarai mai neman Matar abokinsa Allah ya isa tsakanina da kai”

Sai ta ta kunna motarsa ya bar gidan sannan ta durƙushe a gurin tana kuka.

“Kaico na ni Rashida, ina ake siyar da farinciki ne na siya! Ina zan yi musanyar damuwa da kuka na samu sanyin zuciya! Mi na ma duniya haka ne? Miyasa suka ƙaddarori zasu taru a kai na ne? Allah na tuba ka yafe idan zunubi na ne yasa ni a wannan halin”

Kuka take sosai tana ji kamar ƙasa ta haɗiyeta ta mutu ta huta gaba ɗaya da wannan rayuwar. Ra rasa dalilin daya sa rayuwa take koya mata darussan da take ganin bata cancanci koyansu ba.

NAMRA POV.

Kai tsaye direban ya nufi gidan Mai Martaba kamar yadda Yarima ya umarce shi, horn ɗaya yayi aka buɗe musu gate, ɗayan part ɗin gidan ya nufa da su, sai ya faka daidai ƙofar part ɗin ya fito da sauri ya buɗe ma Abbah ƙofa.

“Ya ce akwai komai a ciki, idan akwai abunda kuke buƙata zaku min magana”

Kai kawai Abbah ya ɗaga masa ya nufi ƙofar. Anty Amarya ce ta amsa masa da to, Namra na riƙe da hannun Anty kanta kuma kwance saman kafaɗar Anty, har suka shiga falo, sanyin ac ne ya fara musu martabun, daga bisani ƙamshi ya biyo baya. Kai tsaye Abbah ya nufi wani ɗaki dake ɗayan ɓangare da wasu ɗakunan, yana shiga ya hango manya tufafi kala biyu saman gadon, sai kuma kayan bachi da ba a cire daga leda ba kala ɗaya, an ɗora takalmi da turare da hula mai kyau saman kayan, hakan ya tabbatar masa nan ne ɗakinsa, ɗan murmushi yayi kaɗan ya rage kayan jikinsa ya nufi bathroom.

Mamaki ya cika Namra da Anty Amarya lokacin kowa ya samu tufafin sajawa da kayan bachi saman gadonsa, bama kamar Namra da ta tarar har da pants da pad ya aje mata, ya akayi yasan bata sallah shine abunda ya fi tsaya mata a rai. Bathroom ta shiga, ta yi wanka, sannan ta shirya cikin kayan bachi masu kama da na maza, ta fito ta nufo falo. Anty Amarya da Abbah ta samu zaune a dinning suna cin abinci. Abbah ne ya fara ɗagowa ya kalleta, murmushin da ta gani a fuskarta yasa idonta cika da ƙwalla.

“Toh Sarkin kuka zaki fara ko?”

Cewar Anty Amarya fuskarta ɗauke da annuri, tana miƙawa Abbah tea da ta haɗa masa.

“Komai ya zo min kamar mafarki, gani nake kamar ba gaske bane, ban yi zaton Abbah zai saurare ni haka da wuri ba har ya yafe min, nasan nayi muku abubuwa marar kyau da yawa, amman duk da haka suka samu fili a zuciyarku kuka yafe min”

“Kin cancanci yafiya Mamana, saboda kin gane kuskurenki, sai dai kin shiga rigar mutane masu mutunci wanda hakan yasa kika samu yafiyata a kusa, sai dai ina fatar ba zaki ƙara aikata irin wannan kuskuren ba”

“Wallahi ba zan sake ba Abbah, na maka alƙawari har na koma ga mahallici na,ba zan sake aikata kwatankwacin wannan kuskuren ba”

“Allah yayi miki albarka”

“Amin Abbah na gode, i love you so much”

Ta zo da sauri ta rumgume shi tana kuka. Anty Amarya ta share hawayen idonta tana kallon Abbah.

“Allah ya saka maka da alheri, na gode”

“Yanzu ai ta kuka da ciwon zuciya ya ƙare ko?”

Cewar Abbah fuskarsa da murmushi yana kallon Anty Amarya cike da son Amaryarsa. Daga bisani ya kalli wayarsa da ke saman dinning tana ringing. Hajiya Barau ce rubuce a screem ɗin wayar. Miƙewa yayi tsaye, sannan ya kai hannu ya ɗauki wayar yana danna picking ya nufi bedroom.

A kujerar da ke kusa da Anty Namra ta zauna, tana share hawayen da suka ƙi tsaya mata.

“Na haɗa miki tea zaki sha?”

Ta gyaɗa kai.

“To ki zuba abincin ki ci idan kin gama zan haɗa miki”

“Bana jin yunwa Anty, tea kawai ya isa”

Ajiyar zuciya Anty ta sauke, ta shiga haɗa mata tea, tana faɗin.

“Namra duk kin rame kin koma wata iri, kin yi baƙi sosai, Yarima ya faɗa mana Asim ya sake ki ne saboda kina da ciki!”

Ta gyaɗa kai tana share hawaye.

“Kuma har yanzu be neme ni ba, ina gidansu Lamido cikin ya zube”

“Kin san ciki ba zai taɓa tsayawa a mahaifarki ba Namra saboda matsalar da kika samu, na yi mamaki ma da kika samu ciki bayan an saka miki roba”

“Shi yace sai na cire, kuma da ma samu cikin yace be shirya haihuwa yanzu ba, sai dai na zaɓa tsakanin cikin da shi, ni kuma na ƙi yarda na zubar shiyasa ya sake ni”

“Kin samu ƴancin kan ki yanzu, Allah zai bi miki haƙƙin ki. Amman ina kika haɗu da wannan yaron”

A nan Namra ta kwashe labarin komai na sanin da tayi ma Abdool ta faɗa ma Anty.

“Yana da mutunci sosai, kuma ina fatar zaki masa hallacci duk ranar da ya nemi ladan alherin da yayi miki”

“Kamar ya?”

Ta tambaya dan har ga Allah ita bata gane inda zancen Anty ya dosa ba. Anty ya miƙe tsaye tana murmushi.

“Kamar haka, ki je ki kwanta dare ya yi, zan kira Maryam na ce ta shirya zan vata mamaki, daman ta fi kowa damuwa da auren nan na ki”

“Na gode sosai Anty sai da safe”

Ta daɗe a gurin zaune sai ƙarewa falon kallo take sannan ta tashi ta nufi bedroom.
Har garin Allah ya waye, dan har yanzu ta kasa yarda da abunda ya faru, ganin komai take kamar mafarki. Idonta biyu aka yi kiran sallah asuba, unƙurawa ta yi ta tashi, sai ta nufi gurin maɓallin kutar ɗakin ta kunna. Ta shiga toilet ta tsabtace kanta sannan ta yi wanka ta fito.
Bata tsaya shafa mai ba, ta ɗauki abaya ta saka, sannan ta ɗora da hijab, gefen gado ta zauna sai ta ɗauki carbi tana lazimi, ba ita ta tashi ba sai bakwai da rabi saura, shi ma dan ta ji ana buga ƙofar falon ne.
Bata damu da tambayi ko waye ba kawai ta kai hannu ta buɗe ƙofar. Suna haɗa ido gabanta yayi mugun faɗuwa, da sauri ta sadda kanta ƙasa, shi kam ƙin sauke idonsa ƴayi har ta miƙa masa gaisuwa.

“Ina kwana?”

“Nan ba ina kwana suke cewa ba”

Ɗan murmushi ta yi wanda be kai zuci ba.

“An tashi lafiya?”

“Lafiya ƙalau, i hope you sleep well?”

“I did”

“Amman idonki ya nuna kamar ba ki yi bachi ba”

“Kana da buƙatar wani abun ne?”

Ta tambaya da nufin kawar da maganar. Wani dogon numfashi yaja ya sauke

“Ban sani ba ko kuna da bukata ne, yanzu zan kama hanya, Mai martaba ya kira ni yana da buƙatar gani na, ajima direba zai ɗauke ki zai kai ki a miki passport, da ƙarfe uku jirgi zai tashi, so za a muku duk wani abun da ya kamata, around nine za a kawo muku breakfast. I think Abbah suna bachi, ki faɗa musu na tafi”

Kai ra gyaɗa masa, sai ya zuba hannyensa aljihu ya juya zai wuce.

“Ab...da...llah”

Ta kira sunansa cikin wata irin siga da ba'a taɓa kiransa sunan yayi masa daɗi kamar yadda ita ɗin ta kira shi ba, har cikin zuciyarsa ya ji kiran nata da muryarta dake kamar zata fasa masa kuka. Juyowa yayi ya kalleta da manyan idanuwansa.

“Thank you”

Gira ɗaya ya ɗaga mata, alamar for?

“For helping me out”

Murmushi yayi mata mai fidda annurin fuskarsa.

“Safe flight”

“Wish you the same”

Murmushi yayi mata as respond ya juya ya cigaba da tafiya abunsa, kamar wanda baya son taka ƙasa. Haka kawai ta samu kanta da kasa ɗauke ido a kansa har sai da ya shige part ɗinsa.

ASIM POV.

Kallo Hajiya Sadiya ta bishi da shi, zuciyarta Allah-Allah ya amince.

“Miyasa zaki min tayi mai tsada akan kawai na auri ƴarki?”

“Saboda kai ne kaɗai na yarda da tarbiyarka, kuma nasan ƴata tana son ka, saboda ta nuna min hoton ka har tace zaka zo ka gaishe ni”

“Ko baki bani komai ba zan iya aurenta saboda aurenta na yi niyar yi, amman ki faɗa min gaskiyar abuda kike ɓoyewa wata ƙila zan iya taimakon ki”

“Ko da baka aureta ba, na yarda ka yi zina da ita, idan ta samu ciki sai ka rabu da ita”

“Miyasa sai ni?”

“Saboda ba zan iya facing yata na faɗa mata ta auri wanda bata so ba, kuma nasan ba zan saka ta aikata zina ba”

“Da baki yi gaggauwa ba, da aurin ƴarƙi zan yi, miyasa baki bar ni na aureta ba, iya ka kice min na turo iyayen Sai a ɗaura mana aure. Ki faɗa min gaskiya mana Hajiya”

“Zauna zan faɗa maka komai, saboda na yarda da kai kuma ina fatar zaka taimake ni”

Ya zauna yana fuskantar ta.
Chapter 131 · 0% Book details