Sashe 145
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gaba ɗaya jikinsa yayi nauyi ji yake kamar idan ya motsa jikinsa zai rabu biyu, idonsa kawai yake iya zagaye ɗakin da su. Hakan ya bashi damar ganin mutanen da ke ciki a ɗakin ciki har da Abbah.
“Sannu Uzair, Sannu Allah ya baka lafiya”
Shine abunda kowa yake faɗa, sai dai shi abunda be gane ba, miya ke damunsa! Abunda zai iya tunawa kawai yaji abu ya tsikare shi sai ya faɗi, daga nan be iya tuna abunda ya faru.
Be iya amsa musu da komai ba in banda ido da yake binsu da su da kallo, har suka masa sannu suka fice cike da tausayawa. Abbah ne ya zauna kusa da shi sannan Mahaifiyarsa.
“Uzair ka ɗauki abunda ya faru da kai matsayin ƙaddara komai yana zuwa ne daga abunda Allah ya rubuta maka, kuma haƙuri shi ne zai kai ka ga har kaga ka ci riba ka samu a nan ka samu a acan”
“Wai mi yake faruwa da ni ne?”
Sai a lokacin ya samu damar tambaya.
“Uzair ka haɗu da matsala ne a ƙashinka na baya da kuma ƙashinka na ƙafarka, you wouldn't be able to walk again”
“Taya taya za a ce mun haka bayan ba haɗri na yi ba, ba wani ciwo na ji ba haka nan kawai za a ce mun na samu matsala”
“Nima abunda ya ba ni mamaki kenan, za a fitar da kai waje a duba lafiyarka”
“Abbah mi yake faruwa da ni ne?”
“Muma ba mu sani ba, likitan da ya duba ka ya tambaye ni wai ko ka taɓa haɗarin mota nace masa aa, ko ka taɓa yi baka faɗa ba?”
Hawaye suka fara masa zuba.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Wannan wane irin bala'i ne? Miya faru da ni ne haka, Hajiya ko dai mafarki na ke yi? Allah kasa na farka Allah wayyo ni Allah na”
Haka ƴa ɗinga maganganu Abbah sai kallonsa yake cike da tausayawa, suna haka sai ga wasu friends nasa sun shigo duba shi ciki har da Dr Tahir, da wasu abokanin sha-shancinsu na Abuja. Abbah suka fara tambaya ya mai jiki ya amsa musu da sauƙi sannan suka gaishe da Hajiya dake ta sharar hawaye, suka matsa kusa da Uzair suka tsaya suna masa ya jiki.
Amsa musu kawai yake amman kana ganinsa kasan ya rikice, ba fita hanyyacinsa yayi ba, amman wannan ƙaddarar da ta faɗo masa ya gaza yarda da ita, ta ya zai zama haka mutumen da ke tafiya lafiyarsa ƙalau shi ba faɗowa yayi ba shi ba haɗari ba ace ya haɗu da wannan matsalar, ta ya haka zai faru?
Sun aje masa kuɗi mai yawa ban cin siyayyar da suka masa, Abbah na yayi musu godiya, suka kama hanya suna Allah ya sauwaƙe, sai kawai Uzair ya ƙwalawa Tahir kira, cikin sauri ya juyo ya nufo inda yake su kuma sauran abokan suka fice.
“Ina son mu yi magana da kai Abbah dan Allah ku ɗan ba mu guri”
Daga Hajiya har Abbah tashi suka yi suka fita, sai Tahir ya zauna a kujerar da Abbah ya tashi yana fuskantar Uzair ya ce.
“Na je gida na samu baka nan, matar ka ce kawai, naje na saboda na ta buga wayarka ban samu ba, kuma naje guest house ɗin ka baka nan, babu abunda matarka bata faɗa min ba, har ɗan wuta ta kira ni, daman ta san kana wannan harkar ne?”
“Shekaran jiya ta gano, lokacin da na Amira ta aiko min da saƙo, ni zargin nake ma ko ita ce ta yi min wannan asirin na koma haka ne? Da wannan daga gani lamarin iska ne aljanu ne”
“Ko kuma Amira ba saboda ta dawo na samu labarin gurin Yayanta”
“Lallai zata iya min asiri, yarinyar nan muguwace”
“Zata maka ko kuma zai dawo kan ka idan na jikinta ya kare? Kasan fa bokan nan yace maka idan be kama Namra ba, zai dawo gun ka ne, sai gashi ya kama Amira yanzu kuma Amira ta dawo ina tunanin kai zai dawoma”
“Dan Allah Tahir kaje gurin bokan nan ka faɗa nasa halin da muke ciki, idan ma wani ne yayi min ya san yadda zai yi ya kare shi, idan kuma wannan aikin ne ya kare shi dan Allah Tahir”
Tahir ya dafa shi.
“Zanje karka samu damuwa zan je har can na masa magana duk yadda aka yi zuwa yamma zan dawo na faɗa maka”
“Tahir ba sai yamma ba, kaje yanzu baka ganin halin da nake ciki...?”
Ya ƙarasa cikin kuka mai ban tausayi.
“Okay zanje yanzu Allah ya baka lafiya”
“Na gode”
Ya faɗa hawaye na zuba a idonsa. Jikin sanyin jiki Tahir ya fice yana mamakin lamarin Uzair.
ASIM POV.
Yayi rama sosai a ƴan kwanakin nan da aka yi na amsar gaisuwa, Ranar da aka kwana ɗaya da rasuwar Ƴan gidansu Mardiya suka zo har da Mardiyar gurin gaisuwa, a nan ne yake nunawa wasu ita yana cewar ita ce matar da yake son aure.
Bayan an yi addu'ah uku ya ɗaure ya ƙara kwana biyu saboda masu zuwa ƙara masa gaisuwa. A ranar ne Mama Inno ta raba yaran ta ɗauki Hajara da ƙanenta biyu wasu daga ɓangaren mahaifinsu suka raba sauran ƴaƴan, abun gwanin tausayi, ranar Asim ya ci kuka kamar zai haɗiye zuciya ya mutu dan baƙin ciki, ashe Mama bata da rabon ta shiga gidan da yake da niyar sai mata, be taɓa baƙin cikin haɗuwa da Hajiya Sadiya ba sai yau, ji yayi kamar ace tana kusa da shi ya kamata yayi mata gunduwa-gunduwa, gashi ita kuma sai damunsa take da kira, yana ce mata bashi da lafiya.
Be yarda ya labartawa Nably abunda ya faru ba, amman yana faɗa mata bashi da lafiya kuma tace zata zo ganinsa ya hana, ita kuma duk hankalinta ya tashi hakan ya hanata komawa Abuja, dan ya faɗa mata ranar da zai dawo.
Ranar da bar sokoto sai da yayi kamar zai kashe kansa, gudu ya riƙayi da motar yana kuka kamar zai tashi sama. Da wuri ya isa Katsina saboda ya tashi tun asuba ne, ɗan kawai kar Hajiya ta gane halin da yake ciki ne yasa ya sauka nasarawa, dan yin wanka ya shirya ya canja tufafi. Daga wankan har shirin be ɗauke shi minti talatin ba, yana gamawa ya fito ya nufi gurin da motarsa take. Juyowa ya yi yana kallon gidan.
Be taɓa jin yayi missing ɗin Namra ba sai yau, haka kawai yau da ya tuna ta sai ya ji babu daɗi, daya tuna mamarsa sai Namra ta faɗo masa a rai, jikin rashin daɗin rai ya nufi gidan Hajiya Sadiya.
Sai da ya kama hanyar gidan sannan ya kira ya faɗa mata gashi nan ya shigo katsina har ma ya iso gidan.
“Okay okay galni nan zuwa”
Ko minti goma sha biyar ba'ayi ba, sai gata ta iso. Yayita ƙoƙarin danne damuwarsa ya nuna mata mara rashin lafiya ne kawai matsalarsa, bayan sun zauna a falo yake labarta masa yadda rashin lafiyar ta fara da fever kwanansa biyu asibiti.
“Gaskiya ka ji jiki sosai, ka rame Allah ya ƙara lafiya”
Da Amin ya amsa yana mata wani irin kallo wanda shi kaɗai yasan Manufarsa da kuma abinda yake ji a ransa a tare da shi. Ta shi tayi ta shiga ɗaki dan ɗauko masa apple ɗin, shi kuma ya fidɗo wayarsa ya aikawa Nably saƙo.
_Ki same ni a Dahir Exclusive Restaurant, yanzu ina gurin_
In few minutes ta masa reply.
_Okay on my way_
Ya aika mata da saƙon ne a yanzu dan ya samu ta fita gidan kamin Hajiya ta san wani abu kai, dan yasan ba zata bari ta fita ba.
Ta daɗe a ɗakin sannan ta fito riƙe da farin ƙyale da kuma jika ƙarama mai kamar hand bag, jakar ta fara jefa masa.
“Miliyan biyar ne a ciki, dan Allah Asim ka tabbatar ba a samu matsala irin waccan karon ba, ka ɗauki abun nan da muhimmanci sosai”
“Ba za a samu matsala ba wannan karon na miki alƙawari”
Ya faɗa kamar da gaske. Sannan ya miƙa mata hannu, ta bashi apple ɗin ya ɗauki jakar ya fice zuciyarsa har mazari take ya isa gurin da yake zaton Nably ta isa. Yana shiga mota tana kiransa tace masa gata nan gakin gate.
“Gani nan zuwa yanzu”
Ya kashe wayar, a hanya ya tsaya ya siye wani Apple green, sannan ya ƙarasa restaurant ɗin, yana fakin motarsa ya hangota tsaye jikin wata mota da yake zaton ta tace. Tana hangoshi ta ƙaraso kusa da shi idonta tab da ƙwalla, ji tayi kamar ta rumgume shi dan har ga Allah ta yi missing ɗinsa kuma tana son Asim sosai.
“Ya jikinka?”
“Alhamdullah”
Tare suka shiga ciki suka kama tebur, sai yasa aka kawo musu plate da ƴar ƙaramar wuƙa sai fork. Apple ɗin ya fiɗo ya za a mata ɗaya ya ɗauki ɗayan mai green.
“Wannan ita ce tsaraba ta zuciyata na baki ita har abada, wannan kuma ki ɗauke ta a matsayin zuciyarki ce Asim zai cinye”
Dariya ta yi mai cike da shauƙi da kuma so da ƙauna.
“Ai ka daɗe da cinye zuciyata, har ma da ganganjikina gaba ɗaya”
Ya kalli wayarta yana murmushi.
“Ki kashe wayarki kar wani ya dame mu da kira”
Ba musu ta kashe wayar, shi kuma tsoron yake kar Hajiya ta kirata.
“Bana son ki raga komai daga zuciyata. I love you”
“I love you too”
Ta faɗa sannan ta fara hanya apple ɗin ta tasoma ci kamar yadda shi ma ya fara cin nasa, sai fira yake mata kamar gaske ita kuma sai faman murmushi tana faɗa masa irin yadda ta yi missing ɗinsa.
Sai da suka gama cin apple ɗin sannan ya haɗa ma wayarsa alarm ɗin ƙarya ta yadda zai yi kamar an kira shi.
“Ko na miki oder abinci...?”
“A'a na ƙoshi wannan zuciyar taka ba zata bar ni na ci komai ba”
Ya fiddo wayarsa dake saman cinyarsa, yana faɗin.
“Kai Ogaba na kirana”
Yayi picking cikin ladabi kamar gaske.
“Okay to gani zuwa”
Ya sauke wayar tare da miƙewa tsaye.
“Am so sorry Dear Wallahi ana nema Urgent, amman idan kin min izinin tafiya”
“Sannu Uzair, Sannu Allah ya baka lafiya”
Shine abunda kowa yake faɗa, sai dai shi abunda be gane ba, miya ke damunsa! Abunda zai iya tunawa kawai yaji abu ya tsikare shi sai ya faɗi, daga nan be iya tuna abunda ya faru.
Be iya amsa musu da komai ba in banda ido da yake binsu da su da kallo, har suka masa sannu suka fice cike da tausayawa. Abbah ne ya zauna kusa da shi sannan Mahaifiyarsa.
“Uzair ka ɗauki abunda ya faru da kai matsayin ƙaddara komai yana zuwa ne daga abunda Allah ya rubuta maka, kuma haƙuri shi ne zai kai ka ga har kaga ka ci riba ka samu a nan ka samu a acan”
“Wai mi yake faruwa da ni ne?”
Sai a lokacin ya samu damar tambaya.
“Uzair ka haɗu da matsala ne a ƙashinka na baya da kuma ƙashinka na ƙafarka, you wouldn't be able to walk again”
“Taya taya za a ce mun haka bayan ba haɗri na yi ba, ba wani ciwo na ji ba haka nan kawai za a ce mun na samu matsala”
“Nima abunda ya ba ni mamaki kenan, za a fitar da kai waje a duba lafiyarka”
“Abbah mi yake faruwa da ni ne?”
“Muma ba mu sani ba, likitan da ya duba ka ya tambaye ni wai ko ka taɓa haɗarin mota nace masa aa, ko ka taɓa yi baka faɗa ba?”
Hawaye suka fara masa zuba.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Wannan wane irin bala'i ne? Miya faru da ni ne haka, Hajiya ko dai mafarki na ke yi? Allah kasa na farka Allah wayyo ni Allah na”
Haka ƴa ɗinga maganganu Abbah sai kallonsa yake cike da tausayawa, suna haka sai ga wasu friends nasa sun shigo duba shi ciki har da Dr Tahir, da wasu abokanin sha-shancinsu na Abuja. Abbah suka fara tambaya ya mai jiki ya amsa musu da sauƙi sannan suka gaishe da Hajiya dake ta sharar hawaye, suka matsa kusa da Uzair suka tsaya suna masa ya jiki.
Amsa musu kawai yake amman kana ganinsa kasan ya rikice, ba fita hanyyacinsa yayi ba, amman wannan ƙaddarar da ta faɗo masa ya gaza yarda da ita, ta ya zai zama haka mutumen da ke tafiya lafiyarsa ƙalau shi ba faɗowa yayi ba shi ba haɗari ba ace ya haɗu da wannan matsalar, ta ya haka zai faru?
Sun aje masa kuɗi mai yawa ban cin siyayyar da suka masa, Abbah na yayi musu godiya, suka kama hanya suna Allah ya sauwaƙe, sai kawai Uzair ya ƙwalawa Tahir kira, cikin sauri ya juyo ya nufo inda yake su kuma sauran abokan suka fice.
“Ina son mu yi magana da kai Abbah dan Allah ku ɗan ba mu guri”
Daga Hajiya har Abbah tashi suka yi suka fita, sai Tahir ya zauna a kujerar da Abbah ya tashi yana fuskantar Uzair ya ce.
“Na je gida na samu baka nan, matar ka ce kawai, naje na saboda na ta buga wayarka ban samu ba, kuma naje guest house ɗin ka baka nan, babu abunda matarka bata faɗa min ba, har ɗan wuta ta kira ni, daman ta san kana wannan harkar ne?”
“Shekaran jiya ta gano, lokacin da na Amira ta aiko min da saƙo, ni zargin nake ma ko ita ce ta yi min wannan asirin na koma haka ne? Da wannan daga gani lamarin iska ne aljanu ne”
“Ko kuma Amira ba saboda ta dawo na samu labarin gurin Yayanta”
“Lallai zata iya min asiri, yarinyar nan muguwace”
“Zata maka ko kuma zai dawo kan ka idan na jikinta ya kare? Kasan fa bokan nan yace maka idan be kama Namra ba, zai dawo gun ka ne, sai gashi ya kama Amira yanzu kuma Amira ta dawo ina tunanin kai zai dawoma”
“Dan Allah Tahir kaje gurin bokan nan ka faɗa nasa halin da muke ciki, idan ma wani ne yayi min ya san yadda zai yi ya kare shi, idan kuma wannan aikin ne ya kare shi dan Allah Tahir”
Tahir ya dafa shi.
“Zanje karka samu damuwa zan je har can na masa magana duk yadda aka yi zuwa yamma zan dawo na faɗa maka”
“Tahir ba sai yamma ba, kaje yanzu baka ganin halin da nake ciki...?”
Ya ƙarasa cikin kuka mai ban tausayi.
“Okay zanje yanzu Allah ya baka lafiya”
“Na gode”
Ya faɗa hawaye na zuba a idonsa. Jikin sanyin jiki Tahir ya fice yana mamakin lamarin Uzair.
ASIM POV.
Yayi rama sosai a ƴan kwanakin nan da aka yi na amsar gaisuwa, Ranar da aka kwana ɗaya da rasuwar Ƴan gidansu Mardiya suka zo har da Mardiyar gurin gaisuwa, a nan ne yake nunawa wasu ita yana cewar ita ce matar da yake son aure.
Bayan an yi addu'ah uku ya ɗaure ya ƙara kwana biyu saboda masu zuwa ƙara masa gaisuwa. A ranar ne Mama Inno ta raba yaran ta ɗauki Hajara da ƙanenta biyu wasu daga ɓangaren mahaifinsu suka raba sauran ƴaƴan, abun gwanin tausayi, ranar Asim ya ci kuka kamar zai haɗiye zuciya ya mutu dan baƙin ciki, ashe Mama bata da rabon ta shiga gidan da yake da niyar sai mata, be taɓa baƙin cikin haɗuwa da Hajiya Sadiya ba sai yau, ji yayi kamar ace tana kusa da shi ya kamata yayi mata gunduwa-gunduwa, gashi ita kuma sai damunsa take da kira, yana ce mata bashi da lafiya.
Be yarda ya labartawa Nably abunda ya faru ba, amman yana faɗa mata bashi da lafiya kuma tace zata zo ganinsa ya hana, ita kuma duk hankalinta ya tashi hakan ya hanata komawa Abuja, dan ya faɗa mata ranar da zai dawo.
Ranar da bar sokoto sai da yayi kamar zai kashe kansa, gudu ya riƙayi da motar yana kuka kamar zai tashi sama. Da wuri ya isa Katsina saboda ya tashi tun asuba ne, ɗan kawai kar Hajiya ta gane halin da yake ciki ne yasa ya sauka nasarawa, dan yin wanka ya shirya ya canja tufafi. Daga wankan har shirin be ɗauke shi minti talatin ba, yana gamawa ya fito ya nufi gurin da motarsa take. Juyowa ya yi yana kallon gidan.
Be taɓa jin yayi missing ɗin Namra ba sai yau, haka kawai yau da ya tuna ta sai ya ji babu daɗi, daya tuna mamarsa sai Namra ta faɗo masa a rai, jikin rashin daɗin rai ya nufi gidan Hajiya Sadiya.
Sai da ya kama hanyar gidan sannan ya kira ya faɗa mata gashi nan ya shigo katsina har ma ya iso gidan.
“Okay okay galni nan zuwa”
Ko minti goma sha biyar ba'ayi ba, sai gata ta iso. Yayita ƙoƙarin danne damuwarsa ya nuna mata mara rashin lafiya ne kawai matsalarsa, bayan sun zauna a falo yake labarta masa yadda rashin lafiyar ta fara da fever kwanansa biyu asibiti.
“Gaskiya ka ji jiki sosai, ka rame Allah ya ƙara lafiya”
Da Amin ya amsa yana mata wani irin kallo wanda shi kaɗai yasan Manufarsa da kuma abinda yake ji a ransa a tare da shi. Ta shi tayi ta shiga ɗaki dan ɗauko masa apple ɗin, shi kuma ya fidɗo wayarsa ya aikawa Nably saƙo.
_Ki same ni a Dahir Exclusive Restaurant, yanzu ina gurin_
In few minutes ta masa reply.
_Okay on my way_
Ya aika mata da saƙon ne a yanzu dan ya samu ta fita gidan kamin Hajiya ta san wani abu kai, dan yasan ba zata bari ta fita ba.
Ta daɗe a ɗakin sannan ta fito riƙe da farin ƙyale da kuma jika ƙarama mai kamar hand bag, jakar ta fara jefa masa.
“Miliyan biyar ne a ciki, dan Allah Asim ka tabbatar ba a samu matsala irin waccan karon ba, ka ɗauki abun nan da muhimmanci sosai”
“Ba za a samu matsala ba wannan karon na miki alƙawari”
Ya faɗa kamar da gaske. Sannan ya miƙa mata hannu, ta bashi apple ɗin ya ɗauki jakar ya fice zuciyarsa har mazari take ya isa gurin da yake zaton Nably ta isa. Yana shiga mota tana kiransa tace masa gata nan gakin gate.
“Gani nan zuwa yanzu”
Ya kashe wayar, a hanya ya tsaya ya siye wani Apple green, sannan ya ƙarasa restaurant ɗin, yana fakin motarsa ya hangota tsaye jikin wata mota da yake zaton ta tace. Tana hangoshi ta ƙaraso kusa da shi idonta tab da ƙwalla, ji tayi kamar ta rumgume shi dan har ga Allah ta yi missing ɗinsa kuma tana son Asim sosai.
“Ya jikinka?”
“Alhamdullah”
Tare suka shiga ciki suka kama tebur, sai yasa aka kawo musu plate da ƴar ƙaramar wuƙa sai fork. Apple ɗin ya fiɗo ya za a mata ɗaya ya ɗauki ɗayan mai green.
“Wannan ita ce tsaraba ta zuciyata na baki ita har abada, wannan kuma ki ɗauke ta a matsayin zuciyarki ce Asim zai cinye”
Dariya ta yi mai cike da shauƙi da kuma so da ƙauna.
“Ai ka daɗe da cinye zuciyata, har ma da ganganjikina gaba ɗaya”
Ya kalli wayarta yana murmushi.
“Ki kashe wayarki kar wani ya dame mu da kira”
Ba musu ta kashe wayar, shi kuma tsoron yake kar Hajiya ta kirata.
“Bana son ki raga komai daga zuciyata. I love you”
“I love you too”
Ta faɗa sannan ta fara hanya apple ɗin ta tasoma ci kamar yadda shi ma ya fara cin nasa, sai fira yake mata kamar gaske ita kuma sai faman murmushi tana faɗa masa irin yadda ta yi missing ɗinsa.
Sai da suka gama cin apple ɗin sannan ya haɗa ma wayarsa alarm ɗin ƙarya ta yadda zai yi kamar an kira shi.
“Ko na miki oder abinci...?”
“A'a na ƙoshi wannan zuciyar taka ba zata bar ni na ci komai ba”
Ya fiddo wayarsa dake saman cinyarsa, yana faɗin.
“Kai Ogaba na kirana”
Yayi picking cikin ladabi kamar gaske.
“Okay to gani zuwa”
Ya sauke wayar tare da miƙewa tsaye.
“Am so sorry Dear Wallahi ana nema Urgent, amman idan kin min izinin tafiya”