Sashe 44
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Motar Doc Hilal ce ta uku a gurin, that's means yana cikin asibitin, safa da marwa ta fara yi tana tunanin ta inda zata fara. Lab ne ya faɗo mata a rai. Da fargaba ta kutsa kai cikin asibitin ta ɗauki hanyar da zata hada ta da lab ɗin, ƙasa-ƙasa take kallon mutane, tana fargabar haɗuwa da Hilal, dan ko ganinta yayi bata san me zata ce masa ba.
Ta tararda mutane da ɗan yawa a gurin da aka tana da dan karɓar results ɗin jini da fitsari, hakan yasa ta zagaya ta shiga ciki tun da ita ba baƙuwar asibitin ba ce.
Biyu daga cikin mutanen da suke gurin sun gane, tun da sun san matar Doc ce, cikin mutunci da far'ar ta gaisa da su tana yi tana kallo ƙofa.
“Habib na ce kun gama gwajin jinin da Doc ya kawo? Za a tafi dashi wani garin ne”
Wanda ta kira da Habib ɗin ya amsa da.
“Eh tun ranar muka shi ba ai”
“Ba yau ya kawo ba?”
“A'a ina jin tun monday ne, Monday or Tuesday? Abbas kai ka bashi ko?”
Wanda aka kira da Abbas ɗin be ma kula.da zancen su ba sai rubuce-rubucen sa yake, Habib ɗin ya kalleta.
“Ina jin Monday ne, an dai kwana biyu yanzu”
Gabanta ya faɗi sosai.
“O'o nasan ya jefar da results ɗin wani wajen shiyasa ya ƙi ya faɗa min, amman yau be kawo maka wani ba?”
“Gaskiya be kawo ba, dan mu muka yi duty safe yanzu zamu tashi”
Nauyi zuciyarta sosai tayi mata har sai da ta tsayi ya gagareta, ta zauna a kujerar dake gurin.
“Amman dan Allah ya za'ayi na samu results ɗin wacan gwajin? Tun da ya ɓatar nasan ba zaku rasa a littafin ku”
“Wallahi da an fito da results ɗin an rubuta a littafi ansa a paper na results ɗin ake kai su ɗakin ajiya, sai dai shi Doc zai iya zuwa yayi ma Doc Omar magana, sai ya bincika masa, amman nan results kawai muke badawa”
“Okay Thank you bari na koma gurin Doc ɗin nayi masa magana”
“Okay a gaida yara”
Ya faɗa yana kallon bayanta, irin ƴan iskan samarin nan ne da basa gani su kauda idonsu.
Ƙafafunta sun mata nauyi, ga idonta dake son ciki da ƙwalla tana mayarwa, akwai ƴar tazara tsakanin office ɗin da lab, hakan ya bata damar tunanin abunda zata cewa Hilal idan ya ganta, idan kuma ta koma bata shiga ba ta san zai iya samu labarin ta shigo cikin asibitin tun da akwai waɗanda suka santa, kuma zasu iya faɗa masa.
_Thank you so much my tomatir my albasa my daddawa my miyar kuka_
Yana dannawa Ƙalsoom reply ɗin ta whatsapp. Rashida ta turo ƙofar office ɗin ta shigo da murmushi a fuskarta.
Tashi yayi daga jinceren da yake saman kujera ya kalli da dariya.
“Surprise surprise surprise”
“Yes Darling, na biyo ta nan baya ne shina nace bari na biyo na ga farinciki na”
Ya ɓata rai sosai lokacin daya lura da yanayin tufafin dake jikinta. Suit ne mai wando ta riga sai ɗan ƙaramin hijabi dake kanta.
“Daman Haka kike fita daga office? Ba mun yi maganar nan dake ba dan me zaki fito baki ɗora abaya a sama ba, a cikin office ɗin ki kawai na yarda ki riƙa zama haka, kika ce kin ji ashe ni kike ma ko? Yana ɗaya daga cikin dalilin daya sa bana son aikin nan na ki, bana son wani na ganin matana abun nan yana min zafi”
Sai a lokacin ta kula da tufafin da suke jikinki, tsabar hankalinta baya jikinta bata ma san ta fito a haka ba. Hannayenta tasa ta laƙamo wuyansa.
“Im sorry Wallahi fitar gaggauwace shiyasa amman ba zan sake ba i promise”
“Yanzu haka kika shigo a asibitin nan kowa na kallon ki? Haba Rashida idan an girma a san an girma mana, kefa uwace kamata yayi idan kin ga Ezzah tayi wannan shigar kiyi mata faɗa ba wai ki yi ba”
Ta saki wutan nasa ta nufi freezer dan ita ba faɗan da yake mata bane a gabanta, abunda ya kawo ta take ƙoƙarin yi, tsayawa tayi ta duba da kyau drinks ɗin da tasan babu a freezer ɗin tace masa tana so.
“Nidai nace kayi haƙuri, kuma ina son nasha coc”
Ta faɗa tana marairaice masa, daman tasan baya shan coca-cola saboda irin abubuwan da ake faɗa akanta, kuma ta san yadda ya tsani kayan yahudawa.
Kamar zai ce mata babu, sai kuma ya ƙyaleta tun da yasan tana da ciki wani abun dole ya ɗaga mata ƙafa, sai dai be sakar mata fuska ba dan har yanzu ransa a ɓace yake, sai kawai ya juya ya fita.
Da sauri ta nufi teburinsa ta fara duba takardun da suke gurin, bata ga abunda take nema ba, hakan yasa ta nufi wata ƴar ƙaramar wardrobe dake gefen kujerar, har ta kai hannu ta buɗe sai kuma wani tunanin ya zo mata.
‘Idan na yamutsa masa takardu dole zai zargi wani abu’
Sai kawai ta fasa buɗewa ta koma ta zauna a kujerarsa ta ɗauki ƙafafunta ta ɗora saman teburin kamar babu abunda yake damunta, alhalin a can cikin zuciyarta tashin hankaline da tunani suka taru suka mata katutu.
Yadda ya fita haka ya dawo fuska a haɗe kamar be taɓa dariya ba, ransa ya sosu sosai da ganin irin dress ɗin data shigo dashi cikin asibitin.
Miƙa mata Coc ɗin yayi ya nufi windows ɗin office ɗin ya rufe. Tashi tayi tare da Coc a hannu daman can ba shanta zata yi ba, bata ma jin zata iya saka wani abu a cikinta yanzu.
“Ni zan wuce”
Ya watsa mata wani kallo.
“Haka zaki fita?”
Ta ɗan kalli jikinta
“To ya zan yi?”
“Ban sani ba”
Ya nufi hanger ɗinsa ya ɗauko labcoat ya ɗora mata sama.
“Kuma kar ki cireta har office”
“Doc zan bi ta lab na karɓi results, nayi mafarkin na haifi ƴan'biyu”
Dariya yayi sosai, wanda be shirya yi ba
“Toh ai ba a jini ake ganin twins ba, kuma ban ma kai awon jinin ba”
“Miyasa?”
“Ba nan za min ba, Asibitin Alex zan kai, saboda asibitin su tafi ta mu kayan aiki”
“Okay”
Ta faɗa zuciyarta cike da jindaɗin jin inda zata kai jinin, wani gurin kuma ta jidaɗin da be riga ya kai ɗin ba.
“To ina ka aje shi? Karka sake ce min ya ɓata kuma”
“Ba zai ɓata ba yana nan cikin mota na”
Ya faɗa yana jan hancinta, ita kuma ta kai bakinta dai-dai nashi tayi masa kiss.
Har gurin mota ya rakata sai da ta shiga yaga tashinta sannan ya koma office ɗin.
A maimakon ta koma asibitin sai kawai ta jiya pharmacy ta siye abu sannan ta ɗauki hanyar da zata kai ta gidan Asmee.
__________________________________________
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 34*
NOT EDITED ⚠️
ASIM POV.
“Naje na biya kuɗin har na magani, sun ce Nurse zata riƙa baka”
Ta faɗa tana hita da ɗan ƙaramin mafecin dake hannunta.
“Mashallah har nawa aka biya ne?”
“Dubu ɗari da goma sha ɗaya, ni ban san dalilin yasa ta kawo ka wannan asibitin ba, ace allura guda dubu tara magani ma shegen tsaɗa”
“Asibitin kuɗi ce fa, ba kiga ɗaki suka ware mana ba”
“Allah dai ya baka lafiya mu bar Asibitin nan, ni ban ma ƙi mun koma gida ba gaba ɗaya”
“Gaskiya ni ba zan koma gida yanzu ba, ana kallo kayi aure ka auri masu abu sai kuma aga yadda na dawo da ciwo, kuma a can ai sai ma mun fi jin kunya tun da ƙyale ni zasu yi, maƙiya sai su mana dariya”
“Ai ba za a maka dariya ba kam sai dai a zagi iyayenta”
“Ni dai na fi son zamana nan, a cikin kuɗin ki bani dubu ɗari na bata sai ta siye wasu abubuwan, tun da tace BQ ɗin be ƙone ba sai mu zauna a cikin”
“A'a wane irin dubu ɗari kuma? Dubu shirin ai ya isheta ta siye komai”
“Mama har katifa fa da sauran kayan aiki, ashirin ba zasu isa ba”
“Ni zan je na siyo katifar, da kai na haka kawai za a ɗauki har dubu ɗari a bata, idan an bata nawa ya rage ni bana da lalurar ne? Ban ga dalilin da zata ci amfanin ka kai baka ci nata ba, wallahi tallahi na tsani yarinyar nan saboda iyayenta, sam basu da mutunci”
Asim ya sauke jiyar zuciya.
“Ni bana ma son tunawa da su Wallahi, rai na har ɓaci yake, hmmm Allah dai ya bani lafiya, na warke na tashi garau, Wallahi sai na basu mamaki”
“Ai kana da maƙiya kam Ibrahim Allah dai ya baka lafiya”
Da Amin ya amsa yana gyara zamam ƙafarsa.
RASHIDA POV.
Cikin mintuna ta isa gidan Asmee, tana fito mota Asmee na fitowa daga falo ta tarbeta.
Tashin hankalin dake fuskar Rashida ya ɓatar da na Asmee dan yadda taga Rashida ta rikice ta damu sai ita ta sassautama kanta, a tunaninta Rashida ta damu da matsalar ta ne har haka.
Da suka shiga falo kowanne kasa magana yayi sai kallon kallo suke, Rashida na tunanin ta ina zata fara, Asmee na fargabar irin amsoshi da zata bata.
“Wai ke ya akayi kika yi wannan kuskuren, Asmee dan me zaki cuci kan ki ki cece mu?”
“Rashida na faɗa wani haɗi ne yayi min wanda dole sai an samu sperm ɗin wani”
“Amman ke yanzu dan baki da hankali sai ki bar shi yayi amfani dake? A maimakin kije can waje ki samo wani? Yanzu kin ja mana masifa Asmee”
Rashida ta ƙarasa maganar da kuka.
“Ba ni da tabbacin ina shi ɗin ko bana da, an ban yi gwaji ba, wata mata ce da take zuwa gurinsa aka ce ta kamu”
“Amman yayi ta neman ki ne har da yawa ne?”
“Kin san duk lokacin da kaje da buƙata dole ne sai sun nemi su kwanta da kai”
Kuka ta fara, yana ta dana sanin abunda ta aikata. Sai kusan azahar Rashida ta bar gidan bayan taja mata kunne akan karta kuskure da bari kowa yaji ciki har da mijinta.
Ta tararda mutane da ɗan yawa a gurin da aka tana da dan karɓar results ɗin jini da fitsari, hakan yasa ta zagaya ta shiga ciki tun da ita ba baƙuwar asibitin ba ce.
Biyu daga cikin mutanen da suke gurin sun gane, tun da sun san matar Doc ce, cikin mutunci da far'ar ta gaisa da su tana yi tana kallo ƙofa.
“Habib na ce kun gama gwajin jinin da Doc ya kawo? Za a tafi dashi wani garin ne”
Wanda ta kira da Habib ɗin ya amsa da.
“Eh tun ranar muka shi ba ai”
“Ba yau ya kawo ba?”
“A'a ina jin tun monday ne, Monday or Tuesday? Abbas kai ka bashi ko?”
Wanda aka kira da Abbas ɗin be ma kula.da zancen su ba sai rubuce-rubucen sa yake, Habib ɗin ya kalleta.
“Ina jin Monday ne, an dai kwana biyu yanzu”
Gabanta ya faɗi sosai.
“O'o nasan ya jefar da results ɗin wani wajen shiyasa ya ƙi ya faɗa min, amman yau be kawo maka wani ba?”
“Gaskiya be kawo ba, dan mu muka yi duty safe yanzu zamu tashi”
Nauyi zuciyarta sosai tayi mata har sai da ta tsayi ya gagareta, ta zauna a kujerar dake gurin.
“Amman dan Allah ya za'ayi na samu results ɗin wacan gwajin? Tun da ya ɓatar nasan ba zaku rasa a littafin ku”
“Wallahi da an fito da results ɗin an rubuta a littafi ansa a paper na results ɗin ake kai su ɗakin ajiya, sai dai shi Doc zai iya zuwa yayi ma Doc Omar magana, sai ya bincika masa, amman nan results kawai muke badawa”
“Okay Thank you bari na koma gurin Doc ɗin nayi masa magana”
“Okay a gaida yara”
Ya faɗa yana kallon bayanta, irin ƴan iskan samarin nan ne da basa gani su kauda idonsu.
Ƙafafunta sun mata nauyi, ga idonta dake son ciki da ƙwalla tana mayarwa, akwai ƴar tazara tsakanin office ɗin da lab, hakan ya bata damar tunanin abunda zata cewa Hilal idan ya ganta, idan kuma ta koma bata shiga ba ta san zai iya samu labarin ta shigo cikin asibitin tun da akwai waɗanda suka santa, kuma zasu iya faɗa masa.
_Thank you so much my tomatir my albasa my daddawa my miyar kuka_
Yana dannawa Ƙalsoom reply ɗin ta whatsapp. Rashida ta turo ƙofar office ɗin ta shigo da murmushi a fuskarta.
Tashi yayi daga jinceren da yake saman kujera ya kalli da dariya.
“Surprise surprise surprise”
“Yes Darling, na biyo ta nan baya ne shina nace bari na biyo na ga farinciki na”
Ya ɓata rai sosai lokacin daya lura da yanayin tufafin dake jikinta. Suit ne mai wando ta riga sai ɗan ƙaramin hijabi dake kanta.
“Daman Haka kike fita daga office? Ba mun yi maganar nan dake ba dan me zaki fito baki ɗora abaya a sama ba, a cikin office ɗin ki kawai na yarda ki riƙa zama haka, kika ce kin ji ashe ni kike ma ko? Yana ɗaya daga cikin dalilin daya sa bana son aikin nan na ki, bana son wani na ganin matana abun nan yana min zafi”
Sai a lokacin ta kula da tufafin da suke jikinki, tsabar hankalinta baya jikinta bata ma san ta fito a haka ba. Hannayenta tasa ta laƙamo wuyansa.
“Im sorry Wallahi fitar gaggauwace shiyasa amman ba zan sake ba i promise”
“Yanzu haka kika shigo a asibitin nan kowa na kallon ki? Haba Rashida idan an girma a san an girma mana, kefa uwace kamata yayi idan kin ga Ezzah tayi wannan shigar kiyi mata faɗa ba wai ki yi ba”
Ta saki wutan nasa ta nufi freezer dan ita ba faɗan da yake mata bane a gabanta, abunda ya kawo ta take ƙoƙarin yi, tsayawa tayi ta duba da kyau drinks ɗin da tasan babu a freezer ɗin tace masa tana so.
“Nidai nace kayi haƙuri, kuma ina son nasha coc”
Ta faɗa tana marairaice masa, daman tasan baya shan coca-cola saboda irin abubuwan da ake faɗa akanta, kuma ta san yadda ya tsani kayan yahudawa.
Kamar zai ce mata babu, sai kuma ya ƙyaleta tun da yasan tana da ciki wani abun dole ya ɗaga mata ƙafa, sai dai be sakar mata fuska ba dan har yanzu ransa a ɓace yake, sai kawai ya juya ya fita.
Da sauri ta nufi teburinsa ta fara duba takardun da suke gurin, bata ga abunda take nema ba, hakan yasa ta nufi wata ƴar ƙaramar wardrobe dake gefen kujerar, har ta kai hannu ta buɗe sai kuma wani tunanin ya zo mata.
‘Idan na yamutsa masa takardu dole zai zargi wani abu’
Sai kawai ta fasa buɗewa ta koma ta zauna a kujerarsa ta ɗauki ƙafafunta ta ɗora saman teburin kamar babu abunda yake damunta, alhalin a can cikin zuciyarta tashin hankaline da tunani suka taru suka mata katutu.
Yadda ya fita haka ya dawo fuska a haɗe kamar be taɓa dariya ba, ransa ya sosu sosai da ganin irin dress ɗin data shigo dashi cikin asibitin.
Miƙa mata Coc ɗin yayi ya nufi windows ɗin office ɗin ya rufe. Tashi tayi tare da Coc a hannu daman can ba shanta zata yi ba, bata ma jin zata iya saka wani abu a cikinta yanzu.
“Ni zan wuce”
Ya watsa mata wani kallo.
“Haka zaki fita?”
Ta ɗan kalli jikinta
“To ya zan yi?”
“Ban sani ba”
Ya nufi hanger ɗinsa ya ɗauko labcoat ya ɗora mata sama.
“Kuma kar ki cireta har office”
“Doc zan bi ta lab na karɓi results, nayi mafarkin na haifi ƴan'biyu”
Dariya yayi sosai, wanda be shirya yi ba
“Toh ai ba a jini ake ganin twins ba, kuma ban ma kai awon jinin ba”
“Miyasa?”
“Ba nan za min ba, Asibitin Alex zan kai, saboda asibitin su tafi ta mu kayan aiki”
“Okay”
Ta faɗa zuciyarta cike da jindaɗin jin inda zata kai jinin, wani gurin kuma ta jidaɗin da be riga ya kai ɗin ba.
“To ina ka aje shi? Karka sake ce min ya ɓata kuma”
“Ba zai ɓata ba yana nan cikin mota na”
Ya faɗa yana jan hancinta, ita kuma ta kai bakinta dai-dai nashi tayi masa kiss.
Har gurin mota ya rakata sai da ta shiga yaga tashinta sannan ya koma office ɗin.
A maimakon ta koma asibitin sai kawai ta jiya pharmacy ta siye abu sannan ta ɗauki hanyar da zata kai ta gidan Asmee.
__________________________________________
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 34*
NOT EDITED ⚠️
ASIM POV.
“Naje na biya kuɗin har na magani, sun ce Nurse zata riƙa baka”
Ta faɗa tana hita da ɗan ƙaramin mafecin dake hannunta.
“Mashallah har nawa aka biya ne?”
“Dubu ɗari da goma sha ɗaya, ni ban san dalilin yasa ta kawo ka wannan asibitin ba, ace allura guda dubu tara magani ma shegen tsaɗa”
“Asibitin kuɗi ce fa, ba kiga ɗaki suka ware mana ba”
“Allah dai ya baka lafiya mu bar Asibitin nan, ni ban ma ƙi mun koma gida ba gaba ɗaya”
“Gaskiya ni ba zan koma gida yanzu ba, ana kallo kayi aure ka auri masu abu sai kuma aga yadda na dawo da ciwo, kuma a can ai sai ma mun fi jin kunya tun da ƙyale ni zasu yi, maƙiya sai su mana dariya”
“Ai ba za a maka dariya ba kam sai dai a zagi iyayenta”
“Ni dai na fi son zamana nan, a cikin kuɗin ki bani dubu ɗari na bata sai ta siye wasu abubuwan, tun da tace BQ ɗin be ƙone ba sai mu zauna a cikin”
“A'a wane irin dubu ɗari kuma? Dubu shirin ai ya isheta ta siye komai”
“Mama har katifa fa da sauran kayan aiki, ashirin ba zasu isa ba”
“Ni zan je na siyo katifar, da kai na haka kawai za a ɗauki har dubu ɗari a bata, idan an bata nawa ya rage ni bana da lalurar ne? Ban ga dalilin da zata ci amfanin ka kai baka ci nata ba, wallahi tallahi na tsani yarinyar nan saboda iyayenta, sam basu da mutunci”
Asim ya sauke jiyar zuciya.
“Ni bana ma son tunawa da su Wallahi, rai na har ɓaci yake, hmmm Allah dai ya bani lafiya, na warke na tashi garau, Wallahi sai na basu mamaki”
“Ai kana da maƙiya kam Ibrahim Allah dai ya baka lafiya”
Da Amin ya amsa yana gyara zamam ƙafarsa.
RASHIDA POV.
Cikin mintuna ta isa gidan Asmee, tana fito mota Asmee na fitowa daga falo ta tarbeta.
Tashin hankalin dake fuskar Rashida ya ɓatar da na Asmee dan yadda taga Rashida ta rikice ta damu sai ita ta sassautama kanta, a tunaninta Rashida ta damu da matsalar ta ne har haka.
Da suka shiga falo kowanne kasa magana yayi sai kallon kallo suke, Rashida na tunanin ta ina zata fara, Asmee na fargabar irin amsoshi da zata bata.
“Wai ke ya akayi kika yi wannan kuskuren, Asmee dan me zaki cuci kan ki ki cece mu?”
“Rashida na faɗa wani haɗi ne yayi min wanda dole sai an samu sperm ɗin wani”
“Amman ke yanzu dan baki da hankali sai ki bar shi yayi amfani dake? A maimakin kije can waje ki samo wani? Yanzu kin ja mana masifa Asmee”
Rashida ta ƙarasa maganar da kuka.
“Ba ni da tabbacin ina shi ɗin ko bana da, an ban yi gwaji ba, wata mata ce da take zuwa gurinsa aka ce ta kamu”
“Amman yayi ta neman ki ne har da yawa ne?”
“Kin san duk lokacin da kaje da buƙata dole ne sai sun nemi su kwanta da kai”
Kuka ta fara, yana ta dana sanin abunda ta aikata. Sai kusan azahar Rashida ta bar gidan bayan taja mata kunne akan karta kuskure da bari kowa yaji ciki har da mijinta.