Sashe 65
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ba'a bori da sanyin jiki yarinya, idan kin shirya aiki kawai ki zube kuɗi ayi miki aiki, a take zaki ga aiki da cikawa”
“Zan biya dubu ɗari”
“Cikin satin nan kuwa zaki ji kyakkyawan labari, dan zamu yanka zaɓar ne mu haɗa da zagen hailarta ne, sai mu yi rubuta da wasu silkulle a saka a tulum sai a je can daji a inda babu mai zuwa a rataye tulon a ƙasan tulun za mu yi ƙaramar huduwa wanda ruwan zai riƙa fita kaɗan-kaɗan, yadda ruwan zai riƙa zuba haka jini zai mata zuba har sai ruwan ya ƙare sai mu sake yin wani. Ya sunan kishiyar taki?”
“Ummul khairi, dan Allah malam a taimaka min dan Allah na kawo kukana gareka, dan Allah a taimaka min”
“Karki samu damuwa ki komawarki gida kawai”
“Malam an bincika min ƙasar nan ? An duba lamurrana?”
“Bancika ba tukuna dan ban ƴi zaton zaki zo yau ba, kuma kin ga akwai mutane da yawa a waje, amman idan na bincika ko a waya ne zan faɗa miki”
“To na gode, dan Allah a bincika min ko zan koma gidan mijina”
“Karki samu damuwa, ƙasa zata bada bayanin komai”
Ta zube masa dubu ɗari kasa sannan ta tashi ta fito, zuciyarta cike da yaƙinin abunda Malamin zai aikata mata.
Har ta dawo gida tunanin zuwa karɓar magani take, akan shawarwarin da likitan ya bata, sai dai kuma ya faɗa mata idan har bata shan magani cutar zata bayyana kanta, kuma rayuwarta zata yanke.
NAMRA POV.
Ko da takwas da rabi tayi Maryam da Hinda har Aisha sun wuce school, da wuri Anty ta shirya ma Abbah breakfast, sannan ta zuba ma Namra nata, ita kuma ta ɗauki nata dana Abbah ta nufi part ɗinsa da shi, dan bata breakfast ita kaɗai indai har Abbah yana ɗakinta ne, sai dai tare da shi. Namra na cikin ci abinci sai ga Hajiya Barau ta shigo mata da nata breakfast, tana far'ah kamar gaske.
Wanda Anty ta zuba mata ma bata ci da yawa ba, balle na Hajiya Barau ko buɗashi ba tayi ba, sai dai tana jin ƙamshin ferfesun kayan ciki na dukan hancinta.
Tashi tayi ta wanka ta shirya cikin wasu tufafin sababin da Maryam ta ɗauko mata, tana cikin ɗaurin ɗankwali Anty Amarya ta shigo.
Ta jidaɗin ganin abincin da Hajiya Barau ta kawo ma Namra sosai, hakan ba ƙaranin faranta ranta yayi ba.
“Ai baki ma ci komai ba”
“Na riga na ƙoshi”
“Namra baki son cin abinci, wannan ma baki ci da yawa ba, gaskiya dole muje asibiti a duba lafiyarki, zan je na gyara sai kije ki gaida Abbah ki”
“Tau”
Ta amsa murya ƙasa-ƙasa tana jin kamar dai kar taje. Ɗankwalin ta aje ta ɗauki hijabin Anty ta saka ta nufi part ɗin Abbah tana wata tafiya kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki.
da Sallama ta shiga sai ta tsaya can bakin ƙofa ta risina ƙasa ta gaishe shi, kanta na ƙasa tana mai jin kunyar haɗa ido da shi.
“Abbah ina kwana? An tashi lafiya?”
“Lafiya ƙalau”
Sai kuma ta rasa me zata sake ce masa.
“Mahaifiyarki ta faɗa miki sati ɗaya na yarda ki yi ko? Dan kin san na gargaɗe karki kuskura dako min gida da sunan fushi ko saki”
Idonta ya cika da hawaye, a take muryarta ta soma rawa.
“Abbah ba fushi na yi ba, na zo ganin gida ne”
“Ko minene dai na faɗa miki duk kika doso min gida da sunan saki, to sai dai mahaifiyarki ta tattara kayanta ku bar min gida, tun da kin zaɓi zama da shi sama da Mahaifin ki sai kije can ku ƙarata”
Da sauri ta ɗago kai ta kalli Abbah, sam bata yi tunanin abun nasa ya kai har haka ba.
“Inshallah haka ba zai faru ba Abbah, amman dan Allah ka yafe min kuma ka fahimce ni”
Da hannu ya yi mata alama da ta tashi ta bashi guri. Da sauri ta tashi ta fice tana kuka. Kamin ta ƙarasa part ɗin Anty Amarya ta tsaya ta share hawayenta, sannan ta shiga.
Lokacin Anty Amarya ta fito daga wanka tana cikin shiryawa, falo Namra ta koma ta zauna sai da Anty Amarya ta gama shirinta ta ɗauko jakarta ta fito suka fita tare.
Driver Abbah ne ya kai su asibiti, sun yi sa'ar ganin likita dan tun kamin su isa Anty ta kaira likitan dake duba su ta faɗa masa, sai yayi ma wata likita magana dan shi be shigo asibitin ba a lokacin.
Mutum biyu aka duba kamin ita, sannan ta shiga tare da Amarya. Bata ɓoye komai ba da taji tayi ma likitar bayani, ita kuma sai ta rubuta mata text ɗin jini da na fitsari, sannan ta tura gurin hoto, dan akwai buƙatar su ga abunda yake ƙasan mararta da take ji yayi mata tsaye gefe ɗaya.
Basu bar Asibitin ba sai da suka je aka musu hoton, aka basu sai suka wuce gurin ɗibar jini aka ɗibi jininta sannan suka bata wani roba ta shiga banɗakin gurin tayi fitsari ta kawo musu, sai suka je sai gobe ta zo ta karɓi results, daga suka koma gurin likitar suka kai mata result ɗin.
“Subhanallahi”
Ta faɗa lokacin da ta kalli hotonnan guda uku da suke guri ɗaya, sannan ta kalli Namra ta ce
“Me kika sha na zubar da ciki?”
Ba Namra har Anty Amarya sai da gabanta ya faɗi.
“Ban sha komai ba”
“Kin yi ɓari amman ko?”
Ta ɗaga mata kai
“Eh na yi”
“Amman ba kije asibiti ba?”
“Na je sai dai ban tsaya ba, saboda lokacin mijina be da lafiya”
“Kin yi kuskure gaskiya, da kin tsaya an duba ki ai, yanzu kin ga rabin cikin yana cikin mahaifarki, hakan ya haddasa miki wannan ciwon da kike ji, mahaifarki ta saki sosai har wani ɓangare na jikin mahaifar ya buɗe ya hudu, jiki be yi saurin ɗauke miki ba lokacin da kika yi ɓarin? Ke duk baki lura ba”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Namra ta faɗa tana kallon Anty Amarya da tashin hankali ya bayyana a fuskarta.
“Yanzu likita me ye abun yi?”
“Za'ayi mata wankin mara ne, sai mu ɗorata akan magunguna, amman gaskiya akwai buƙatar tayi family planning na shekara biyu ko uku gudun karta ɗauki ciki har sai mahaifarta ta warki”
Kuka Namra ta saka tana dafe da cikin nata. Anty Amarya ta riƙa bata haƙuri, tana mamakin lamarin dan ita bata ma san lokacin da tayi ɓarin ba, kuma gani take kamar wani abu ta sha dan ta zubar da cikin.
KALSOOM POV.
Kwata-kwata yanzu bata gane lamarin Ezzah ta ɗauke ta kamar wata maƙiyiyarta, sam bata ma son zama falon idan Kalsoom na nan, abinci ma idan ba Doc ne yake gidan ba, sai ta ƙi ta koma can ɗaki ta keɓe kanta.
Bayan shi babu wata matsala da Kalsoom take fuskanta, ita kuma bata ɗauke ta matsala ba dan ba biye mata zata yi ba, zamanta da Doc lafiya ƙalau sai ƙarin so da ƙauna, ga ɗan cikinta tana raino gwanin sha'awa ɗan satin nan data samu har tayi fari sosai tayi ƙiba ta mulmule kamar ba ita ba, Doc har tsokanarta yake wai shi take tsotsewa ita tana ƙiba shi be gane ba.
Ita kuma ta san babu komai sai kwanciyar hankali da kuma kulawar mijinta da take samu a yanzu, ga Ulfah da Rafiq da suka zame mata tamkar ita ta haife su, dan ko maganar Mamansu basa yi, indai kaga wani baƙin hali to Ezzah da kicifin dan tafi kowa kishin uwarta yanzu.
500k words....
______________________________________________
Littafinan na kuɗi ne, idan kin san baki biya ba, karki karanta.
₦200 zaki turo ta wannan account ɗin 0314795884 Abubakar Hadiza GT Bank.
Sai ki turo da shaidar biyan kudin ta wannan number 08036126660
DON'T READ IF YOU DIDN'T PAY...!
*PAGE - 45*
NOT EDITED ⚠
Sai da Yamma lis Anty da Namra suka dawo gida, bayan sun yi mata wankin mara sai da suka bata 6 hours suka ga condition ɗin ta sannan suka barta ta dawo gida.
Jikinta ya mutu sosai, ga tunanin dake zuciyarta, tana jin gajiya a tare da ita amman tunanin dake cikin zuciyarta ya hana ta tayi bachi bayan sun dawo gida.
Tana jin kamar ta labartawa wani damuwarta, sai dai kuma bata san yadda za su kalli abun ba, ace kamar Asim ya juya mata baya, sannan tana ganin idan har ta faɗa Anty ba zata barta ta cigaba da zama da shi ba, Abbah kuma ba zai yarda ta zauna a gidan ba.
Haka ta kwana ciki damuwa da tunani har garin Allah ya waye, karin safe ma sai da Anty ta tirsasa sannan ta ci.
Tana cin abinci tana kukan zuci, kukan da bata san ranar tsayawar hawayenta ba, kuka maraici amman bana rashin uwa da uba ba, kuka take kukan butulci bayan hallaci kukan nadama da bata da gani.
“Anty Namra kuka kike?”
Hindatu ta tambaya tana dafata, yanayinta duk ya canja ganim ƴar'uwarta cikin damuwa.
Hannu tasa ta taɓa fuskarta dan tabbatar da hawayen ya fito, sai kawai ta share tana murmushi.
“Ban ma san ya fito ba, baki iya sallama ba ne idan kin shigo?”
“Na yi sallama baki dai ji ba ne, me kike ma kuka?”
“Ba komai, dan Allah karki faɗawa kowa kin ji?”
“Tau, ga waya Anty tace na kawo miki Asim.ya kira”
Wayar ta sakarwa ido, kamar mai tsoron karɓa, ji take kamar ba wani abun ƙwarai bane zai faɗa mata, what if yace ya sake ta?
“Anty...”
Hindatu ta kira sunanta ganin yadda ta tsurawa wayar ido tana nazarin zuci. Sai a sannan ta kai hannu ta karɓa, ita kuma ta tashi ta bar mata ɗakin.
Wayar na fara ringing gabanta ya faɗi, ba ƙaramin ƙoƙari ta yi ba wajen picking ɗin call ɗin.
“Assalamu alaikum”
“Wa'alaikissalam Namra”
“Na'am”
“Kin je gida ba tare da kin sanar min ba, miyasa kika je? Kina son ki faɗa musu abunda ya faru ne? Na san ban kyauta miki ba, amman Wallahi sherin sheiɗan ne, ni kaina nasan ban kyauta miki ba, amman ina kishin ki ne Namra dan me zaki bar wani ya rako har cikin asibiti kin ganin hakan kyautawa?”
“Zan biya dubu ɗari”
“Cikin satin nan kuwa zaki ji kyakkyawan labari, dan zamu yanka zaɓar ne mu haɗa da zagen hailarta ne, sai mu yi rubuta da wasu silkulle a saka a tulum sai a je can daji a inda babu mai zuwa a rataye tulon a ƙasan tulun za mu yi ƙaramar huduwa wanda ruwan zai riƙa fita kaɗan-kaɗan, yadda ruwan zai riƙa zuba haka jini zai mata zuba har sai ruwan ya ƙare sai mu sake yin wani. Ya sunan kishiyar taki?”
“Ummul khairi, dan Allah malam a taimaka min dan Allah na kawo kukana gareka, dan Allah a taimaka min”
“Karki samu damuwa ki komawarki gida kawai”
“Malam an bincika min ƙasar nan ? An duba lamurrana?”
“Bancika ba tukuna dan ban ƴi zaton zaki zo yau ba, kuma kin ga akwai mutane da yawa a waje, amman idan na bincika ko a waya ne zan faɗa miki”
“To na gode, dan Allah a bincika min ko zan koma gidan mijina”
“Karki samu damuwa, ƙasa zata bada bayanin komai”
Ta zube masa dubu ɗari kasa sannan ta tashi ta fito, zuciyarta cike da yaƙinin abunda Malamin zai aikata mata.
Har ta dawo gida tunanin zuwa karɓar magani take, akan shawarwarin da likitan ya bata, sai dai kuma ya faɗa mata idan har bata shan magani cutar zata bayyana kanta, kuma rayuwarta zata yanke.
NAMRA POV.
Ko da takwas da rabi tayi Maryam da Hinda har Aisha sun wuce school, da wuri Anty ta shirya ma Abbah breakfast, sannan ta zuba ma Namra nata, ita kuma ta ɗauki nata dana Abbah ta nufi part ɗinsa da shi, dan bata breakfast ita kaɗai indai har Abbah yana ɗakinta ne, sai dai tare da shi. Namra na cikin ci abinci sai ga Hajiya Barau ta shigo mata da nata breakfast, tana far'ah kamar gaske.
Wanda Anty ta zuba mata ma bata ci da yawa ba, balle na Hajiya Barau ko buɗashi ba tayi ba, sai dai tana jin ƙamshin ferfesun kayan ciki na dukan hancinta.
Tashi tayi ta wanka ta shirya cikin wasu tufafin sababin da Maryam ta ɗauko mata, tana cikin ɗaurin ɗankwali Anty Amarya ta shigo.
Ta jidaɗin ganin abincin da Hajiya Barau ta kawo ma Namra sosai, hakan ba ƙaranin faranta ranta yayi ba.
“Ai baki ma ci komai ba”
“Na riga na ƙoshi”
“Namra baki son cin abinci, wannan ma baki ci da yawa ba, gaskiya dole muje asibiti a duba lafiyarki, zan je na gyara sai kije ki gaida Abbah ki”
“Tau”
Ta amsa murya ƙasa-ƙasa tana jin kamar dai kar taje. Ɗankwalin ta aje ta ɗauki hijabin Anty ta saka ta nufi part ɗin Abbah tana wata tafiya kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki.
da Sallama ta shiga sai ta tsaya can bakin ƙofa ta risina ƙasa ta gaishe shi, kanta na ƙasa tana mai jin kunyar haɗa ido da shi.
“Abbah ina kwana? An tashi lafiya?”
“Lafiya ƙalau”
Sai kuma ta rasa me zata sake ce masa.
“Mahaifiyarki ta faɗa miki sati ɗaya na yarda ki yi ko? Dan kin san na gargaɗe karki kuskura dako min gida da sunan fushi ko saki”
Idonta ya cika da hawaye, a take muryarta ta soma rawa.
“Abbah ba fushi na yi ba, na zo ganin gida ne”
“Ko minene dai na faɗa miki duk kika doso min gida da sunan saki, to sai dai mahaifiyarki ta tattara kayanta ku bar min gida, tun da kin zaɓi zama da shi sama da Mahaifin ki sai kije can ku ƙarata”
Da sauri ta ɗago kai ta kalli Abbah, sam bata yi tunanin abun nasa ya kai har haka ba.
“Inshallah haka ba zai faru ba Abbah, amman dan Allah ka yafe min kuma ka fahimce ni”
Da hannu ya yi mata alama da ta tashi ta bashi guri. Da sauri ta tashi ta fice tana kuka. Kamin ta ƙarasa part ɗin Anty Amarya ta tsaya ta share hawayenta, sannan ta shiga.
Lokacin Anty Amarya ta fito daga wanka tana cikin shiryawa, falo Namra ta koma ta zauna sai da Anty Amarya ta gama shirinta ta ɗauko jakarta ta fito suka fita tare.
Driver Abbah ne ya kai su asibiti, sun yi sa'ar ganin likita dan tun kamin su isa Anty ta kaira likitan dake duba su ta faɗa masa, sai yayi ma wata likita magana dan shi be shigo asibitin ba a lokacin.
Mutum biyu aka duba kamin ita, sannan ta shiga tare da Amarya. Bata ɓoye komai ba da taji tayi ma likitar bayani, ita kuma sai ta rubuta mata text ɗin jini da na fitsari, sannan ta tura gurin hoto, dan akwai buƙatar su ga abunda yake ƙasan mararta da take ji yayi mata tsaye gefe ɗaya.
Basu bar Asibitin ba sai da suka je aka musu hoton, aka basu sai suka wuce gurin ɗibar jini aka ɗibi jininta sannan suka bata wani roba ta shiga banɗakin gurin tayi fitsari ta kawo musu, sai suka je sai gobe ta zo ta karɓi results, daga suka koma gurin likitar suka kai mata result ɗin.
“Subhanallahi”
Ta faɗa lokacin da ta kalli hotonnan guda uku da suke guri ɗaya, sannan ta kalli Namra ta ce
“Me kika sha na zubar da ciki?”
Ba Namra har Anty Amarya sai da gabanta ya faɗi.
“Ban sha komai ba”
“Kin yi ɓari amman ko?”
Ta ɗaga mata kai
“Eh na yi”
“Amman ba kije asibiti ba?”
“Na je sai dai ban tsaya ba, saboda lokacin mijina be da lafiya”
“Kin yi kuskure gaskiya, da kin tsaya an duba ki ai, yanzu kin ga rabin cikin yana cikin mahaifarki, hakan ya haddasa miki wannan ciwon da kike ji, mahaifarki ta saki sosai har wani ɓangare na jikin mahaifar ya buɗe ya hudu, jiki be yi saurin ɗauke miki ba lokacin da kika yi ɓarin? Ke duk baki lura ba”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Namra ta faɗa tana kallon Anty Amarya da tashin hankali ya bayyana a fuskarta.
“Yanzu likita me ye abun yi?”
“Za'ayi mata wankin mara ne, sai mu ɗorata akan magunguna, amman gaskiya akwai buƙatar tayi family planning na shekara biyu ko uku gudun karta ɗauki ciki har sai mahaifarta ta warki”
Kuka Namra ta saka tana dafe da cikin nata. Anty Amarya ta riƙa bata haƙuri, tana mamakin lamarin dan ita bata ma san lokacin da tayi ɓarin ba, kuma gani take kamar wani abu ta sha dan ta zubar da cikin.
KALSOOM POV.
Kwata-kwata yanzu bata gane lamarin Ezzah ta ɗauke ta kamar wata maƙiyiyarta, sam bata ma son zama falon idan Kalsoom na nan, abinci ma idan ba Doc ne yake gidan ba, sai ta ƙi ta koma can ɗaki ta keɓe kanta.
Bayan shi babu wata matsala da Kalsoom take fuskanta, ita kuma bata ɗauke ta matsala ba dan ba biye mata zata yi ba, zamanta da Doc lafiya ƙalau sai ƙarin so da ƙauna, ga ɗan cikinta tana raino gwanin sha'awa ɗan satin nan data samu har tayi fari sosai tayi ƙiba ta mulmule kamar ba ita ba, Doc har tsokanarta yake wai shi take tsotsewa ita tana ƙiba shi be gane ba.
Ita kuma ta san babu komai sai kwanciyar hankali da kuma kulawar mijinta da take samu a yanzu, ga Ulfah da Rafiq da suka zame mata tamkar ita ta haife su, dan ko maganar Mamansu basa yi, indai kaga wani baƙin hali to Ezzah da kicifin dan tafi kowa kishin uwarta yanzu.
500k words....
______________________________________________
Littafinan na kuɗi ne, idan kin san baki biya ba, karki karanta.
₦200 zaki turo ta wannan account ɗin 0314795884 Abubakar Hadiza GT Bank.
Sai ki turo da shaidar biyan kudin ta wannan number 08036126660
DON'T READ IF YOU DIDN'T PAY...!
*PAGE - 45*
NOT EDITED ⚠
Sai da Yamma lis Anty da Namra suka dawo gida, bayan sun yi mata wankin mara sai da suka bata 6 hours suka ga condition ɗin ta sannan suka barta ta dawo gida.
Jikinta ya mutu sosai, ga tunanin dake zuciyarta, tana jin gajiya a tare da ita amman tunanin dake cikin zuciyarta ya hana ta tayi bachi bayan sun dawo gida.
Tana jin kamar ta labartawa wani damuwarta, sai dai kuma bata san yadda za su kalli abun ba, ace kamar Asim ya juya mata baya, sannan tana ganin idan har ta faɗa Anty ba zata barta ta cigaba da zama da shi ba, Abbah kuma ba zai yarda ta zauna a gidan ba.
Haka ta kwana ciki damuwa da tunani har garin Allah ya waye, karin safe ma sai da Anty ta tirsasa sannan ta ci.
Tana cin abinci tana kukan zuci, kukan da bata san ranar tsayawar hawayenta ba, kuka maraici amman bana rashin uwa da uba ba, kuka take kukan butulci bayan hallaci kukan nadama da bata da gani.
“Anty Namra kuka kike?”
Hindatu ta tambaya tana dafata, yanayinta duk ya canja ganim ƴar'uwarta cikin damuwa.
Hannu tasa ta taɓa fuskarta dan tabbatar da hawayen ya fito, sai kawai ta share tana murmushi.
“Ban ma san ya fito ba, baki iya sallama ba ne idan kin shigo?”
“Na yi sallama baki dai ji ba ne, me kike ma kuka?”
“Ba komai, dan Allah karki faɗawa kowa kin ji?”
“Tau, ga waya Anty tace na kawo miki Asim.ya kira”
Wayar ta sakarwa ido, kamar mai tsoron karɓa, ji take kamar ba wani abun ƙwarai bane zai faɗa mata, what if yace ya sake ta?
“Anty...”
Hindatu ta kira sunanta ganin yadda ta tsurawa wayar ido tana nazarin zuci. Sai a sannan ta kai hannu ta karɓa, ita kuma ta tashi ta bar mata ɗakin.
Wayar na fara ringing gabanta ya faɗi, ba ƙaramin ƙoƙari ta yi ba wajen picking ɗin call ɗin.
“Assalamu alaikum”
“Wa'alaikissalam Namra”
“Na'am”
“Kin je gida ba tare da kin sanar min ba, miyasa kika je? Kina son ki faɗa musu abunda ya faru ne? Na san ban kyauta miki ba, amman Wallahi sherin sheiɗan ne, ni kaina nasan ban kyauta miki ba, amman ina kishin ki ne Namra dan me zaki bar wani ya rako har cikin asibiti kin ganin hakan kyautawa?”