Sashe 13
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ban san miyasa Namra ta tsane ni har haka ba, ban san abunda na tsare mata ba, na rasa gane kanta”
“Uzair, inda har ba Allah yayi auren nan naku ba, bana jin zata zauna gidanka ko da ka aureta, kuma Wallahi a yadda zuciyar Namra take ko kashe ka zata iya yi ko kuma tayi maka wata illar, tun da bata son ka”
“Daman abunda Hajiyata take ta faɗa kenan, ni ina ganin gaskiya haƙura zan yi, ƙara taje ta auri wanda take so kawai”
“Da kam yafi maka, dan wannan auren ba zai yi ƙarƙo ba, sannan bana jin wannan yaron daya ɗauke ta ze barta haka nan, kar ayi maka kwashe-kashe”
“Barin ze fi tun da har zuciyarta wani take so, kuma duk macen da zata iya bin saurayinta kinsan ta girma”
“Ashe kai ma kana da tunani, fasa auren akam zai fiye maka”
Daga haka suka yi sallama. shi kuma ya sauka saman gadon ya nufi bathroom.
Sai tara da ƴan mintuna ya shirya, be damu da breakfast ya fito ya nufi parking space. Lokacin Yasmin har ta daɗe da barin gidan. Direct gidan Mahaifiyarsa ya nufa Hajiya Binta. A can ya yi breakfast yana labarta mata abunda ya faru, sai tace masa ai Hajiya Barau ta kira ta ta faɗa mata komai. Ta ji daɗin maganar da yayi ta basa auren Namra, ita daman zuciyarta bata natsu da aurensa da Namra ba, tun lokacin da tayi masa ƙazafi.
NAMRA POV.
Cikin ikon Allah numfashinta ya dawo, sai aka ɗaura mata drip,
Sai dai bata farka ba sai kusan Asuba, a lokacin Mama Zainab ce kawai a ɗakin, dan Hajiya da Hindatu tun cikin dare suka koma gida.
Kuma har garin Allah ya waye babu wanda ya leƙosu sai Amira, ita ma sai goma har da rabi sannan ta iso.
Namra na zaune jugummm tana tunani hawaye na bin fuskarta. Amira na shiga ta je da gudu ta rumgume Namra tana kuka.
“Wallahi da ba'a ganki ba Namra, da kashe kai na zan yi”
Namra ta share hawayenta, ta kalli Amira.
“Amira ina Asim yake?”
Gabanta ya faɗi, har sai da ta haɗiye yawun bakinta ta.
“Ina Asim yake Amira? Taya Asim ya zo gidan ku har ya baki wannan number?”
Nan ma kasa amsawa ta yi sai kukan munafurci take, zuciyarta na tsara mata irin ƙaryar da zata yi Namra dan kare kanta. kamin ta amkaro har Namra ta ƙara mata wata tambayar.
“Amira ki amsa min mana, ina Asim? Amira number da kika ba ni bata Asim ba ce, lokacin dana je ba Asim na gani ba Uzair na gani, faɗa min ta ya haka ya faru?”
Har lokacin Amira shiru take, bakinta sai rawa yake ta kasa magana. Hakan ya tabbatar ma Namra abunda take zargi.
“Uzair ya haɗa kai da ke an cuce ni”
Dam! Dam!! Dam!!! Zuciyar Amira take bugawa har cikin ƙwaƙwalwarta, ja ta yi da baya tana girgiza ma Namra kai hawaye na fita a idonta.
“Ki zargi kowa da cin amanarki, amman ban da ni, har a bada Amira ba zata taɓa cin amanar Namra ba”
Namra ta ɗaga mata kai tana hawaye.
“Asim ma ba zai iya cin amana ta ba, karki yaudari kanki wajen nuna min Asim yana so ya cuce ni. Amman ke Uzair zai iya siyen ki ya biya ki dan ya cimma burinshi, babu wanda ze fahimci ni, na ɓata ran kowa, ban san hali da Mahaifana suke ciki ba, sanadin ke da Uzair”
“Namra karki yanke hukuncin abunda baki sani ba, zan iya dafa miki qur'ane Namra, ban haɗa kai da Uzair ba dan na cuce ki.
Namra ta ya zan haɗa kai da wani ya wulaƙanta ki a titi? Har sai jama'ar unguwarku sun ɗaiko ki su kawo gidanku, Kuma su bada shaidar sun ji muryar Asim kuma sun ji an kira sunansa.
Namra tun da na bar gidan ku, ban rumtsa ba saboda tunanin da kukan rashin sanin halin da kike ciki, kina fita Maryam ta shigo ni ta ɗaurawa laifi tace ni ce silar komai, na yi tunani ke zaki bada shaida akaina ashe na yi kuskure.
Namra ki faɗa min dalili ɗaya, da zai sa na cuce ki, faɗa min Namra? Kinsan a iya zamantakewar mu da ke duk wanda ya ci amanar wani Allah sai ya fitar masa da haƙƙinsa”
Da wani irin kuka ta ƙarasa maganar kamar ta sheɗe. Kalamata sun sa jikin Namra sanyi, sai zargin da take mata ya soma raguwa, sai dai har yanzu bata ji zuciyarta ta natsu da Amira ba.
Kan ta ya kulle, ita dai tasan ba mafarki tayi ba, tabbas ta yi ido huɗu da Uzair kuma ya riƙa ta, sai dai bayan nan bata san wani abunda ya faru ba.
‘Taya Uzair yazo gurin? Miye dalilin da zai sa Uzair ya yi min haka? Taya Amira zata cu ni ta’
Sune tambayoyin da suka tsaya mata a rai, kuma suke ƙoƙari riƙita mata ƙwaƙwalwa.
Jin Amira ta dafa ta ya dawo da ita daga dogon tunanin da take.
“Namra kin fi kowa sanin ni wace ce...”
Bata ƙarasa Namra ta kai hannu ta riƙa hannunta.
“Ki yi haƙuri, kaina a kulle yake, a yanzu bana iya banbance gaskiya da ƙarya, bana iya tantance komai na rasa gane abunda yake faruwa da ni...”
Da kuka ta ƙarasa maganar, sai Amira ta rumgume ta suna kukan tare.
Shigowar Mama Zainab ne yasa suka tsagaita kukan, suka share hawayensu.
“Kuka fa ba zai muku ba, abunda ya faru ya riga ya faru sai dai a tari gaba. Likitan ya rubuta miki wani magani?”
Ta tambaya dan ɗazu Likitan daya shigo ne yasa ta fita, ta basu guri. Namra ta ɗauki takardar dake gefenta ta miƙa mata.
“Bai rubuta min komai ba, ya dai bani takardar sallama, yace bayan sati biyu na dawo”
Mama Zainab ta karɓa tana faɗin
“Masha Allah, sai ki tashi muyi harama, dan yanzu Hajiya Raliya ta kira ni wai tana son ta zo Mamanki ta hanata, kuma ƙara mu koma gida kar a fara mana taro, tun da babu wanda yaji abunda ya faru sai ƴan gida”
Namra ta lumshe ido ta jin wani abu daya tsaya mata a zuciya.
Amira ce taje ta biya komai da komai sannan ta zo ta riƙa Namra suka fita tare.
HILAL POV.
A gajiye ya fito asibitin, daker yake driving saboda gajiya, dan wuni yayi yana aiki, har jin yake kamar fever na son rufe shi.
Yau kan baya iya bin gosulon nan na government house, saboda taron da ake.
Sai kawai ya hanka ta cikin estate dan samawa kansa sauƙi sai dai tafiyar zata masa nisa sosai tun da ya biyo doguwar hanya.
“Subhanallah”
Ya faɗa lokacin da idanuwansa sukayi arba da wata kyakkyawar fuska, dake takowa izuwa hanyar daya fito. Sai ya rage gudun da yake, ya mai cigaba da kallonta.
Tana da kyau sosai mai jan hakali da saka natsuwar zuci, sai dai fuskarta kawai yake iya gani, domin jikinta rufe yake da ƙaton hijabi. Hakan kuma ba ƙaramin burgeshi yayi ba, ganinta cikin kamala ga tafiyarta a natse.
Kamin ta ƙaraso kusa da shi ya faka gefen ti-ti yana ƙare mata kallo.
Tana da tsayi da dogon hanci ga idonta dara-dara, farin fuskarta fes, sai dai a iya yadda ya fahimta kamar bata da jiki sosai.
Dai-dai lokacin data kawo kusa da shi sai ya sauke gilashin motarsa yana miƙa mata sallama.
“Assalamu alaikum Malama”
“Wa'alaikassalam”
Ta amsa mishi da zazzaƙar muryarta sai dai hakan be sa ta tsaya ba, sai ta cigaba da tafiyarta kamar ba ita ta amsa masa sallamar ba.
Da sauri Doctor Hilal ya buɗe motar ya fito ya biyo ta da ƙafa.
“Dan Allah ɗan tsaya na tambaye ki wani abu”
Allah daya haɗa ta dashi yasa ta tsaya, da badan haka ba babu abunda ze sa ta tsaya dan iya yanzu ta sallama a lamarin maza.
“Dan Allah ke matar aure ce?”
“A'a”
“Dan Allah ya sunan ki, kuma ina ne gidan ku?”
Sai a lokacin ta kalleshi, wani faɗuwa gabanta yayi lokacin da idonta suka sauka cikin nasa, kyausa yayi mata kwargiji, wanda yasa tayi saurin sauke idonta ƙasa, tana sauraren bugun zuciyarta.
“Miyasa ka tambaya?”
“I ask you first”
Ba amfanin yin ƙarya, dole ta faɗa masa gaskiya.
“Sunana Ummul-Kalsoom amman ana kira da Kalsoom, gidan mu yana ta nan gaba number 5 gidan Alhaji Faruk Kafinta”
“Toh na gode”
Bata sake ce masa komai ba, ta cigaba da tafiyarta. Shi kuma ya bita da kallo har sai da yaga inda ta shiga, sannan ya shiga motar yana murmushi, a take ya ji duk gajiyar da take tare dashi ta wartsake, cikin farinciki da annashuwa ya kunna motar ya hau ti-ti.
__________________________
What do you expect next?
http://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa11.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 11*
NAMRA POV.
Keke Napep Amira ta tare musu ta faɗa masa inda ze kai su, sannan suka shiga.
Be sauke su ko'ina ba sai Ƙofar gidan, Amira ta biya shi sannan ta riƙa hannu Namra suka shiga cikin gidan.
Kamar mai nauyin ƙafa haka Namra take tafiya tana hawaye, gaban na bugawa da ƙarfi. Da wane ido zata kalli Anty Amarya? Idan Abbah ya kalleta me zata ce masa.
Mama Zainab ce gaba da sallama sannan Namra, sai Amira ta biyo baya. Hajiya Raliya ta amsa musu sallamar, Anty Amarya kam yi tayi kamar ma bata gansu ba, ta tashi tayi ta nufi kitchin.
Saman Kujera Amira ta zaunar da Namra, sai ta zauna kusa da ita tana amsa ya jikin da Hajiya Raliya take mata.
“Da sauki har an sallamota”
“Wallahi babu yadda ba mu yi ba ni da Aisha da Hindu muje ganin ki amman Larai ta hana, sai gashi Abbanki ya zo shi yace kar wanda ya fita da sunan ganin ki a gidan nan, toh kar ma ya kuskura ya dawo”
Fashewa ta yi da kuka, ta kwantar da kanta jikin Amira dake hawaye.
Shigowar Hajiya Barau ne yasa ta noke kanta, Amira da Mama Zainab suka amsa mata. Idonta kar kan Namra sai kallon jikinta take.
“Uzair, inda har ba Allah yayi auren nan naku ba, bana jin zata zauna gidanka ko da ka aureta, kuma Wallahi a yadda zuciyar Namra take ko kashe ka zata iya yi ko kuma tayi maka wata illar, tun da bata son ka”
“Daman abunda Hajiyata take ta faɗa kenan, ni ina ganin gaskiya haƙura zan yi, ƙara taje ta auri wanda take so kawai”
“Da kam yafi maka, dan wannan auren ba zai yi ƙarƙo ba, sannan bana jin wannan yaron daya ɗauke ta ze barta haka nan, kar ayi maka kwashe-kashe”
“Barin ze fi tun da har zuciyarta wani take so, kuma duk macen da zata iya bin saurayinta kinsan ta girma”
“Ashe kai ma kana da tunani, fasa auren akam zai fiye maka”
Daga haka suka yi sallama. shi kuma ya sauka saman gadon ya nufi bathroom.
Sai tara da ƴan mintuna ya shirya, be damu da breakfast ya fito ya nufi parking space. Lokacin Yasmin har ta daɗe da barin gidan. Direct gidan Mahaifiyarsa ya nufa Hajiya Binta. A can ya yi breakfast yana labarta mata abunda ya faru, sai tace masa ai Hajiya Barau ta kira ta ta faɗa mata komai. Ta ji daɗin maganar da yayi ta basa auren Namra, ita daman zuciyarta bata natsu da aurensa da Namra ba, tun lokacin da tayi masa ƙazafi.
NAMRA POV.
Cikin ikon Allah numfashinta ya dawo, sai aka ɗaura mata drip,
Sai dai bata farka ba sai kusan Asuba, a lokacin Mama Zainab ce kawai a ɗakin, dan Hajiya da Hindatu tun cikin dare suka koma gida.
Kuma har garin Allah ya waye babu wanda ya leƙosu sai Amira, ita ma sai goma har da rabi sannan ta iso.
Namra na zaune jugummm tana tunani hawaye na bin fuskarta. Amira na shiga ta je da gudu ta rumgume Namra tana kuka.
“Wallahi da ba'a ganki ba Namra, da kashe kai na zan yi”
Namra ta share hawayenta, ta kalli Amira.
“Amira ina Asim yake?”
Gabanta ya faɗi, har sai da ta haɗiye yawun bakinta ta.
“Ina Asim yake Amira? Taya Asim ya zo gidan ku har ya baki wannan number?”
Nan ma kasa amsawa ta yi sai kukan munafurci take, zuciyarta na tsara mata irin ƙaryar da zata yi Namra dan kare kanta. kamin ta amkaro har Namra ta ƙara mata wata tambayar.
“Amira ki amsa min mana, ina Asim? Amira number da kika ba ni bata Asim ba ce, lokacin dana je ba Asim na gani ba Uzair na gani, faɗa min ta ya haka ya faru?”
Har lokacin Amira shiru take, bakinta sai rawa yake ta kasa magana. Hakan ya tabbatar ma Namra abunda take zargi.
“Uzair ya haɗa kai da ke an cuce ni”
Dam! Dam!! Dam!!! Zuciyar Amira take bugawa har cikin ƙwaƙwalwarta, ja ta yi da baya tana girgiza ma Namra kai hawaye na fita a idonta.
“Ki zargi kowa da cin amanarki, amman ban da ni, har a bada Amira ba zata taɓa cin amanar Namra ba”
Namra ta ɗaga mata kai tana hawaye.
“Asim ma ba zai iya cin amana ta ba, karki yaudari kanki wajen nuna min Asim yana so ya cuce ni. Amman ke Uzair zai iya siyen ki ya biya ki dan ya cimma burinshi, babu wanda ze fahimci ni, na ɓata ran kowa, ban san hali da Mahaifana suke ciki ba, sanadin ke da Uzair”
“Namra karki yanke hukuncin abunda baki sani ba, zan iya dafa miki qur'ane Namra, ban haɗa kai da Uzair ba dan na cuce ki.
Namra ta ya zan haɗa kai da wani ya wulaƙanta ki a titi? Har sai jama'ar unguwarku sun ɗaiko ki su kawo gidanku, Kuma su bada shaidar sun ji muryar Asim kuma sun ji an kira sunansa.
Namra tun da na bar gidan ku, ban rumtsa ba saboda tunanin da kukan rashin sanin halin da kike ciki, kina fita Maryam ta shigo ni ta ɗaurawa laifi tace ni ce silar komai, na yi tunani ke zaki bada shaida akaina ashe na yi kuskure.
Namra ki faɗa min dalili ɗaya, da zai sa na cuce ki, faɗa min Namra? Kinsan a iya zamantakewar mu da ke duk wanda ya ci amanar wani Allah sai ya fitar masa da haƙƙinsa”
Da wani irin kuka ta ƙarasa maganar kamar ta sheɗe. Kalamata sun sa jikin Namra sanyi, sai zargin da take mata ya soma raguwa, sai dai har yanzu bata ji zuciyarta ta natsu da Amira ba.
Kan ta ya kulle, ita dai tasan ba mafarki tayi ba, tabbas ta yi ido huɗu da Uzair kuma ya riƙa ta, sai dai bayan nan bata san wani abunda ya faru ba.
‘Taya Uzair yazo gurin? Miye dalilin da zai sa Uzair ya yi min haka? Taya Amira zata cu ni ta’
Sune tambayoyin da suka tsaya mata a rai, kuma suke ƙoƙari riƙita mata ƙwaƙwalwa.
Jin Amira ta dafa ta ya dawo da ita daga dogon tunanin da take.
“Namra kin fi kowa sanin ni wace ce...”
Bata ƙarasa Namra ta kai hannu ta riƙa hannunta.
“Ki yi haƙuri, kaina a kulle yake, a yanzu bana iya banbance gaskiya da ƙarya, bana iya tantance komai na rasa gane abunda yake faruwa da ni...”
Da kuka ta ƙarasa maganar, sai Amira ta rumgume ta suna kukan tare.
Shigowar Mama Zainab ne yasa suka tsagaita kukan, suka share hawayensu.
“Kuka fa ba zai muku ba, abunda ya faru ya riga ya faru sai dai a tari gaba. Likitan ya rubuta miki wani magani?”
Ta tambaya dan ɗazu Likitan daya shigo ne yasa ta fita, ta basu guri. Namra ta ɗauki takardar dake gefenta ta miƙa mata.
“Bai rubuta min komai ba, ya dai bani takardar sallama, yace bayan sati biyu na dawo”
Mama Zainab ta karɓa tana faɗin
“Masha Allah, sai ki tashi muyi harama, dan yanzu Hajiya Raliya ta kira ni wai tana son ta zo Mamanki ta hanata, kuma ƙara mu koma gida kar a fara mana taro, tun da babu wanda yaji abunda ya faru sai ƴan gida”
Namra ta lumshe ido ta jin wani abu daya tsaya mata a zuciya.
Amira ce taje ta biya komai da komai sannan ta zo ta riƙa Namra suka fita tare.
HILAL POV.
A gajiye ya fito asibitin, daker yake driving saboda gajiya, dan wuni yayi yana aiki, har jin yake kamar fever na son rufe shi.
Yau kan baya iya bin gosulon nan na government house, saboda taron da ake.
Sai kawai ya hanka ta cikin estate dan samawa kansa sauƙi sai dai tafiyar zata masa nisa sosai tun da ya biyo doguwar hanya.
“Subhanallah”
Ya faɗa lokacin da idanuwansa sukayi arba da wata kyakkyawar fuska, dake takowa izuwa hanyar daya fito. Sai ya rage gudun da yake, ya mai cigaba da kallonta.
Tana da kyau sosai mai jan hakali da saka natsuwar zuci, sai dai fuskarta kawai yake iya gani, domin jikinta rufe yake da ƙaton hijabi. Hakan kuma ba ƙaramin burgeshi yayi ba, ganinta cikin kamala ga tafiyarta a natse.
Kamin ta ƙaraso kusa da shi ya faka gefen ti-ti yana ƙare mata kallo.
Tana da tsayi da dogon hanci ga idonta dara-dara, farin fuskarta fes, sai dai a iya yadda ya fahimta kamar bata da jiki sosai.
Dai-dai lokacin data kawo kusa da shi sai ya sauke gilashin motarsa yana miƙa mata sallama.
“Assalamu alaikum Malama”
“Wa'alaikassalam”
Ta amsa mishi da zazzaƙar muryarta sai dai hakan be sa ta tsaya ba, sai ta cigaba da tafiyarta kamar ba ita ta amsa masa sallamar ba.
Da sauri Doctor Hilal ya buɗe motar ya fito ya biyo ta da ƙafa.
“Dan Allah ɗan tsaya na tambaye ki wani abu”
Allah daya haɗa ta dashi yasa ta tsaya, da badan haka ba babu abunda ze sa ta tsaya dan iya yanzu ta sallama a lamarin maza.
“Dan Allah ke matar aure ce?”
“A'a”
“Dan Allah ya sunan ki, kuma ina ne gidan ku?”
Sai a lokacin ta kalleshi, wani faɗuwa gabanta yayi lokacin da idonta suka sauka cikin nasa, kyausa yayi mata kwargiji, wanda yasa tayi saurin sauke idonta ƙasa, tana sauraren bugun zuciyarta.
“Miyasa ka tambaya?”
“I ask you first”
Ba amfanin yin ƙarya, dole ta faɗa masa gaskiya.
“Sunana Ummul-Kalsoom amman ana kira da Kalsoom, gidan mu yana ta nan gaba number 5 gidan Alhaji Faruk Kafinta”
“Toh na gode”
Bata sake ce masa komai ba, ta cigaba da tafiyarta. Shi kuma ya bita da kallo har sai da yaga inda ta shiga, sannan ya shiga motar yana murmushi, a take ya ji duk gajiyar da take tare dashi ta wartsake, cikin farinciki da annashuwa ya kunna motar ya hau ti-ti.
__________________________
What do you expect next?
http://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa11.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 11*
NAMRA POV.
Keke Napep Amira ta tare musu ta faɗa masa inda ze kai su, sannan suka shiga.
Be sauke su ko'ina ba sai Ƙofar gidan, Amira ta biya shi sannan ta riƙa hannu Namra suka shiga cikin gidan.
Kamar mai nauyin ƙafa haka Namra take tafiya tana hawaye, gaban na bugawa da ƙarfi. Da wane ido zata kalli Anty Amarya? Idan Abbah ya kalleta me zata ce masa.
Mama Zainab ce gaba da sallama sannan Namra, sai Amira ta biyo baya. Hajiya Raliya ta amsa musu sallamar, Anty Amarya kam yi tayi kamar ma bata gansu ba, ta tashi tayi ta nufi kitchin.
Saman Kujera Amira ta zaunar da Namra, sai ta zauna kusa da ita tana amsa ya jikin da Hajiya Raliya take mata.
“Da sauki har an sallamota”
“Wallahi babu yadda ba mu yi ba ni da Aisha da Hindu muje ganin ki amman Larai ta hana, sai gashi Abbanki ya zo shi yace kar wanda ya fita da sunan ganin ki a gidan nan, toh kar ma ya kuskura ya dawo”
Fashewa ta yi da kuka, ta kwantar da kanta jikin Amira dake hawaye.
Shigowar Hajiya Barau ne yasa ta noke kanta, Amira da Mama Zainab suka amsa mata. Idonta kar kan Namra sai kallon jikinta take.