Sashe 90
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Amira ina tunanin yanzu hankalin ki ya kwanta, natsuwarki kuma ta dawo jikin ki, zama haka ba shi yi, ya kamata ace izuwa yanzu kina gaban iyayenki, ba mu san halin da iyayen ki suke ciki ba, i'm mother too i know how it feel like idan ɗan ka baya kusa da kai, musamman mace”
Ɗagowa tayi ta kalli Ummi idonta cike da ƙwalla.
“Dan Allah Ummi ki min haƙuri ki bar har nan gaba, ni kaɗai nasan halin da nake shiga idan na tuna da iyaye, kuma nasan dole na koma garesu”
Ajiyar zuciya Ummi ta sauke.
“Ba komai Allag yasa haka shi ya fi alheri, Haleema ta baki waya ko?”
“Eh ta ba ni”
“Yana da kyau ki kira wani daga cikin familyn ki ku gaisa”
“Zan yi ƙoƙarin yin haka Ummi na gode”
Ta miƙe tsaye cikin rashin kuzari ta bar ɗakin. Ɗakinta ta dawo ta xauna gefen gado tana kuka, ita kanta tasan abar tausayi ce idan ta tuna da rashin iyayenta.
“Na rasa iyaye saboda kai Uzair, ka cuce ni ka yaudare ni, kai ne ka saka rayuwarta ta koma a haka, na rasa iyayena da duka family amman ba zan rasa Abdool da familyn su ba, ba zan zama loser ba”
A fili tayi furucin zuciyarta cike da yaƙinin abinda bakinta yake faɗa.
“I have to make it work, i can't lose them both, i deserve happiness too”
Saman gadon ta faɗa ta rumgume filo tana wani kuka mai taɓa zuciya.
“Kin cuce ni Namra abotarmu bata amfana min komai ba sai nadama da baƙin ciki, nayi nadamar sanin ki a rayuwata, You and Uzair have to paid for what you both did to me”
Wani kuka take Sosai tana buga ƙafafunta kamar wata ƙaramar yarinya. Turowa ƙofar ɗakin da Haleema tayi ne yasa ta saurin tashi ta goge hawayenta, gabanta sai faɗuwa yake tana ala-ala idan bata ji zancen da ta yi ba.
Kusa da ita Haleema ta zauna cike da tausayawa, dan akan kunnenta Amira ta faɗi komai.
“Kin cancanci farinciki Amira, ba kiyi ƙarya ba kin cancanci komai daga wanda kika sadaukarda ranki gare shi, mu kuma kin cancanci soyayyarmu tun da kika ceto ɗan'uwan mu”
Hannayenta Haleema ta kama, ta riƙe
“Ba zaki rasa mu ba, ba zaki rasa familyn Abdool ba har a bada”
Da mamakin Amira take kallonta kamar wacce bata fahimci inda zantukanta suka dosa ba.
“Na daɗe da fahimtar kina son Ya Abdool, tun lokacin da kika shigo gidan nan, na lƴra da ke Amira kina rasa natsuwarki idan Abdool yana cikin gidan nan, a yanzu ma bayan Number Ummi Numbersa kika tambaya a na biyu, kina son Abdool Amira i can't hide it”
Rumgume ta Amira tayi a ƙirginta gamgam, tana kuka.
*ASIM POV.*
Bayanai gadi ya gama nuna masa ko ina na gidan, sai ya dawo falon dan faɗa ma Hajiya yadda suka yi da mai gaɗin. A inda ya barta a nan ya same ta tana zaune ta ɗora ƙafa ɗaya saman ɗaƴa tana kallon ƙofa kamar ta san da shigowarsa.
Saman kujera ya zauna dan shi yanzu jin gidan yake kamar nasa, yayi sallama sai dai bata amsa masa sallamar ba har ya zauna tana murmushi.
“Hajiya an nuna min komai, gida mashallah”
Sai a lokacin ta buɗe baki tana masa magana kamar mai nauyin baki.
“Amman bana son ka faɗawa kowa abinda ka sani game da ni”
“Hajiya ai ban san komai ba, balle ma na faɗa, kuma ni bana daga cikin mutane nan masu yawan surutu”
“Zaka sani ne ai shiyasa nake gargaɗin ka tun yanzu, zaka san komai a kai na, tun da har ka furta zaka iya yin komai”
“Wallahi zan iya miki komai Hajiya”
“Yayi kyau, kaga ɗakin ka?”
“Eh yayi kyau sosai”
“Anjima zan baka kaje ka siyo abubuwan da babu, sai ka sawa ɗakin, saboda ina son ya zama ɗakin ka na ainahin, so nake ka manta da cewar kana da wata mata dabam”
“Ba komai Hajiya komai kika ce shi za'ayi inshallah”
“Thank you you're very loyal”
Ta tashi ta nufi ɗakinta tana murmushi, har a zuciyarta take jin Asim dan taga alamun zai iya komai na neman kuɗi, haka take so daman.
Shi kuma sai daɗi yake ji yadda take masa, ko kaɗan be kawo komai a ransa ba, abu ɗaya yake tunanin zata nema a gunsa, wata ƙila ba zai wuce sex ba, kuma he's ever ready indai wannan nan ne, sai dai kuma shi ɗin kansa yana buƙatar sanin ko wacece ita, dan be ga alamun tana da yaya ba.
Zuciyarsa cike da nishaɗi ya fiddo ƙaramar wayarsa ya shiga duniyar facebook. Notifications ya tarar mai yawa, ga massage da friend requests. Rabon da hau duniyar facebook tun Namra tana amarya tana ɗan cikin yanayin jindaɗin nan kamin komai ya canja.
Notifications ɗin ya fara dubawa yaga na gani sannan ya shiga massage, ya samu mata da yawa daga cikin masu masa massage kansancewar hoton dake profile ɗinsa yayi kyau, sosai idan ka ganshi sai ka ɗauka wani shege ne.
Sama-sama ya amsa massages ɗin sannan ya duba friend requests yayi accepting wasu ya bar wasu.
Be wani daɗe ba ya sauka daman be cika jindaɗin hawa da ƙaramar waya ba, rabon da yayi chat da babbar waya kuma tun yana farko farkon scul ana yayin karyar nan.
Saukowar Hajiya Sadiya ne yasa shi ɗaga kai yana kallonta. Sai kuma ya sauke irin wai shi ladabi tun da ita ce boss. Keys ɗin mota ta jefa mishi tare da Atm.
“4782 shine password ɗin, ka siye duk abunda ya kamata, ɗan bana son ƙazanta”
Ya ɗauka ya miƙe tsaye har wani zumuɗi yake, zuciyaraa fes.
“Toh Na gode sosai”
Bata amsa shi ba, shi kuma be damu da sai ta amsa ɗin ba sai kawai ya fice yana auna yadda Allah ya maida shi wani a dare ɗaya.
Be sa ko wace mota bace har sai da ya danna makulin tayi ƙara sannan ya nufi motar ya buɗe ya shiga.
‘Kamata yayi na siyar da gidan nan, idan ya zo sai na riƙa juyawa ina siyen zinari ina sai dawa, ga wannan albashi walh nan da nan za ka ga na yi kuɗi, sai dai kuma ban sani ba ko bata son na haɗa da wani aikin, wata ƙila ma zata iya min kyautar mota fa, ji yadda ta yarda da ni nan take har da ba ni atm ɗinta ta faɗa min password, daman mai haƙuri mawadaci’
Shine abinda yake ta saƙawa a zuciyarsa yana tukin motar da yake hango kansa a matsayin wani ƙaramin alhaji.
*RASHIDA POV*
Ajiyar xuciya ta sauke har da hawayen ƙirƙira dan kawai Teema ta tausaya mata, haƙiƙa ciwon ƴa mace na ƴa mace ne Teema ta tausaya mata sosai har tana jin kamar tayi mata maganin matsalarta yanzu.
“Ki kwantar da hankalin ki Rashida, zan taimake ki akwai wani malami yana nan ɗan ƙauye sokoto ne, wlh malamin har ƙasa ƙasa ake ɗaukarsa yayi aiki, aikinsa kamar yankan wuƙa yake, a take komai kike so zai miki zan kai ki gurinsa idan kin shirya”
“To ai ni kullum a shirye na ke, ni ko yanzu kika ce muje zamu je wlh”
“A'a ban da yau dan ban shirya ba amman dai gobe ki zo da wuri sai mu tafi”
“To inshallah zan zo”
“Amman aikin ki fa nasan ba hutu kuke samu ba”
“Karki damu da aikina wannan ita ce muhimmiya”
Teema tayi dariyar mugunta. Tashi Rashida tayi, Teema ta raka ta har gurin motar ta ta shiga motar tana ɗagawa Teema Hannu.
Daga gidan Teema ta wuce Asibiti dan karɓar maganinta, a mota ta tsaya ta saka niƙabi da hijab sannan ta fita.
A wani gurin ta tsaya kusa da inda ake ba da maganin, tana kalle kalle mutane, daman haka take duk ta zo wai gudun kar taga wanda ta sani. Duk da wannan shine zuwanta na biyu.
Bayan ta gama dube dubaneta ta shiga ciki ta ga likita, ya ƙara mata shawarwari, sannan ta fito ta nufi gurin karɓar maganin kai tsaye. Security dake gadin ƙofar asibitin ce ta saka ta cire nikaɓ ɗinta dan haka dokar asibitin ta gada, Rashida bata damu ba ta cire niƙab ɗin daman ko wacan zuwan da tayi sai da tasa ta cire shi.
Da fargaba ta kunna kai a gurin tana ɗan kallon mutane ƙasa-ƙasa, gabanta sai faɗuwa yake kamar zai faɗo. Kamar daga sama taji an dafata ana ƙoƙarin juyowa da ita, juyowar da ta yi sai kawai suka yi ido huɗu da Safiya cikin Uniform ɗinta.
Wani irin kallo Safiya take mata kamar wacce ta rude cox she's can't believe Rashida ce ta gani a nan ƴar'uwarta jininta.
Ita kanta Rashida mamakin ganinta take, dan iya saninta wannan ba asibitun su bace, ya aka yi ta zo nan me ya kawo ta.? Yawu Safiya ta haɗe ta wuce da sauri ta fita daga gurin gudun kar wani daga cikin manyan su ya ganta, daman fitowarta kenan daga wani ɗakin ta hango mai kama da Rashida, ashe ba kama bace, ita ɗin ce amman mai zai kawo Rashida HIV/TB unit.? Shine abinda ya tsaya mata a rai.
Miƙewa Rashida tayi cikin dakewar zuciya ta cigaba da tafiya tana son ɓatarwa da Safiya da lissafi, sai dai kuma yanzu bata san liyin da zata bi, tb ko hiv?
*HILAL POV*
Asibitin ya wuni, da rana ma Hajiya ce ta kawo masa abinci. Duk wanda ya zo sai ya tauyasawa Rafiq ganin yadda ya koma musaki sai dalalar da yawu yake. Tuni Hilal ya ɗosa shi akan magani, yasa aka sake masa wasu hotunan dan ganr ainahin matsalarsa.
Ƴan'uwansa da dama sun yi ta xuwa ganin ɗan nasa, ƴan uwan Rashida ma sun zo, sai dai ba sosai ba, Dady Kalsoom ma ya zo shi da Momy, duk da suna jin nauyi ganin kamar ƴarsu ce ta aikata abun.
Ɗagowa tayi ta kalli Ummi idonta cike da ƙwalla.
“Dan Allah Ummi ki min haƙuri ki bar har nan gaba, ni kaɗai nasan halin da nake shiga idan na tuna da iyaye, kuma nasan dole na koma garesu”
Ajiyar zuciya Ummi ta sauke.
“Ba komai Allag yasa haka shi ya fi alheri, Haleema ta baki waya ko?”
“Eh ta ba ni”
“Yana da kyau ki kira wani daga cikin familyn ki ku gaisa”
“Zan yi ƙoƙarin yin haka Ummi na gode”
Ta miƙe tsaye cikin rashin kuzari ta bar ɗakin. Ɗakinta ta dawo ta xauna gefen gado tana kuka, ita kanta tasan abar tausayi ce idan ta tuna da rashin iyayenta.
“Na rasa iyaye saboda kai Uzair, ka cuce ni ka yaudare ni, kai ne ka saka rayuwarta ta koma a haka, na rasa iyayena da duka family amman ba zan rasa Abdool da familyn su ba, ba zan zama loser ba”
A fili tayi furucin zuciyarta cike da yaƙinin abinda bakinta yake faɗa.
“I have to make it work, i can't lose them both, i deserve happiness too”
Saman gadon ta faɗa ta rumgume filo tana wani kuka mai taɓa zuciya.
“Kin cuce ni Namra abotarmu bata amfana min komai ba sai nadama da baƙin ciki, nayi nadamar sanin ki a rayuwata, You and Uzair have to paid for what you both did to me”
Wani kuka take Sosai tana buga ƙafafunta kamar wata ƙaramar yarinya. Turowa ƙofar ɗakin da Haleema tayi ne yasa ta saurin tashi ta goge hawayenta, gabanta sai faɗuwa yake tana ala-ala idan bata ji zancen da ta yi ba.
Kusa da ita Haleema ta zauna cike da tausayawa, dan akan kunnenta Amira ta faɗi komai.
“Kin cancanci farinciki Amira, ba kiyi ƙarya ba kin cancanci komai daga wanda kika sadaukarda ranki gare shi, mu kuma kin cancanci soyayyarmu tun da kika ceto ɗan'uwan mu”
Hannayenta Haleema ta kama, ta riƙe
“Ba zaki rasa mu ba, ba zaki rasa familyn Abdool ba har a bada”
Da mamakin Amira take kallonta kamar wacce bata fahimci inda zantukanta suka dosa ba.
“Na daɗe da fahimtar kina son Ya Abdool, tun lokacin da kika shigo gidan nan, na lƴra da ke Amira kina rasa natsuwarki idan Abdool yana cikin gidan nan, a yanzu ma bayan Number Ummi Numbersa kika tambaya a na biyu, kina son Abdool Amira i can't hide it”
Rumgume ta Amira tayi a ƙirginta gamgam, tana kuka.
*ASIM POV.*
Bayanai gadi ya gama nuna masa ko ina na gidan, sai ya dawo falon dan faɗa ma Hajiya yadda suka yi da mai gaɗin. A inda ya barta a nan ya same ta tana zaune ta ɗora ƙafa ɗaya saman ɗaƴa tana kallon ƙofa kamar ta san da shigowarsa.
Saman kujera ya zauna dan shi yanzu jin gidan yake kamar nasa, yayi sallama sai dai bata amsa masa sallamar ba har ya zauna tana murmushi.
“Hajiya an nuna min komai, gida mashallah”
Sai a lokacin ta buɗe baki tana masa magana kamar mai nauyin baki.
“Amman bana son ka faɗawa kowa abinda ka sani game da ni”
“Hajiya ai ban san komai ba, balle ma na faɗa, kuma ni bana daga cikin mutane nan masu yawan surutu”
“Zaka sani ne ai shiyasa nake gargaɗin ka tun yanzu, zaka san komai a kai na, tun da har ka furta zaka iya yin komai”
“Wallahi zan iya miki komai Hajiya”
“Yayi kyau, kaga ɗakin ka?”
“Eh yayi kyau sosai”
“Anjima zan baka kaje ka siyo abubuwan da babu, sai ka sawa ɗakin, saboda ina son ya zama ɗakin ka na ainahin, so nake ka manta da cewar kana da wata mata dabam”
“Ba komai Hajiya komai kika ce shi za'ayi inshallah”
“Thank you you're very loyal”
Ta tashi ta nufi ɗakinta tana murmushi, har a zuciyarta take jin Asim dan taga alamun zai iya komai na neman kuɗi, haka take so daman.
Shi kuma sai daɗi yake ji yadda take masa, ko kaɗan be kawo komai a ransa ba, abu ɗaya yake tunanin zata nema a gunsa, wata ƙila ba zai wuce sex ba, kuma he's ever ready indai wannan nan ne, sai dai kuma shi ɗin kansa yana buƙatar sanin ko wacece ita, dan be ga alamun tana da yaya ba.
Zuciyarsa cike da nishaɗi ya fiddo ƙaramar wayarsa ya shiga duniyar facebook. Notifications ya tarar mai yawa, ga massage da friend requests. Rabon da hau duniyar facebook tun Namra tana amarya tana ɗan cikin yanayin jindaɗin nan kamin komai ya canja.
Notifications ɗin ya fara dubawa yaga na gani sannan ya shiga massage, ya samu mata da yawa daga cikin masu masa massage kansancewar hoton dake profile ɗinsa yayi kyau, sosai idan ka ganshi sai ka ɗauka wani shege ne.
Sama-sama ya amsa massages ɗin sannan ya duba friend requests yayi accepting wasu ya bar wasu.
Be wani daɗe ba ya sauka daman be cika jindaɗin hawa da ƙaramar waya ba, rabon da yayi chat da babbar waya kuma tun yana farko farkon scul ana yayin karyar nan.
Saukowar Hajiya Sadiya ne yasa shi ɗaga kai yana kallonta. Sai kuma ya sauke irin wai shi ladabi tun da ita ce boss. Keys ɗin mota ta jefa mishi tare da Atm.
“4782 shine password ɗin, ka siye duk abunda ya kamata, ɗan bana son ƙazanta”
Ya ɗauka ya miƙe tsaye har wani zumuɗi yake, zuciyaraa fes.
“Toh Na gode sosai”
Bata amsa shi ba, shi kuma be damu da sai ta amsa ɗin ba sai kawai ya fice yana auna yadda Allah ya maida shi wani a dare ɗaya.
Be sa ko wace mota bace har sai da ya danna makulin tayi ƙara sannan ya nufi motar ya buɗe ya shiga.
‘Kamata yayi na siyar da gidan nan, idan ya zo sai na riƙa juyawa ina siyen zinari ina sai dawa, ga wannan albashi walh nan da nan za ka ga na yi kuɗi, sai dai kuma ban sani ba ko bata son na haɗa da wani aikin, wata ƙila ma zata iya min kyautar mota fa, ji yadda ta yarda da ni nan take har da ba ni atm ɗinta ta faɗa min password, daman mai haƙuri mawadaci’
Shine abinda yake ta saƙawa a zuciyarsa yana tukin motar da yake hango kansa a matsayin wani ƙaramin alhaji.
*RASHIDA POV*
Ajiyar xuciya ta sauke har da hawayen ƙirƙira dan kawai Teema ta tausaya mata, haƙiƙa ciwon ƴa mace na ƴa mace ne Teema ta tausaya mata sosai har tana jin kamar tayi mata maganin matsalarta yanzu.
“Ki kwantar da hankalin ki Rashida, zan taimake ki akwai wani malami yana nan ɗan ƙauye sokoto ne, wlh malamin har ƙasa ƙasa ake ɗaukarsa yayi aiki, aikinsa kamar yankan wuƙa yake, a take komai kike so zai miki zan kai ki gurinsa idan kin shirya”
“To ai ni kullum a shirye na ke, ni ko yanzu kika ce muje zamu je wlh”
“A'a ban da yau dan ban shirya ba amman dai gobe ki zo da wuri sai mu tafi”
“To inshallah zan zo”
“Amman aikin ki fa nasan ba hutu kuke samu ba”
“Karki damu da aikina wannan ita ce muhimmiya”
Teema tayi dariyar mugunta. Tashi Rashida tayi, Teema ta raka ta har gurin motar ta ta shiga motar tana ɗagawa Teema Hannu.
Daga gidan Teema ta wuce Asibiti dan karɓar maganinta, a mota ta tsaya ta saka niƙabi da hijab sannan ta fita.
A wani gurin ta tsaya kusa da inda ake ba da maganin, tana kalle kalle mutane, daman haka take duk ta zo wai gudun kar taga wanda ta sani. Duk da wannan shine zuwanta na biyu.
Bayan ta gama dube dubaneta ta shiga ciki ta ga likita, ya ƙara mata shawarwari, sannan ta fito ta nufi gurin karɓar maganin kai tsaye. Security dake gadin ƙofar asibitin ce ta saka ta cire nikaɓ ɗinta dan haka dokar asibitin ta gada, Rashida bata damu ba ta cire niƙab ɗin daman ko wacan zuwan da tayi sai da tasa ta cire shi.
Da fargaba ta kunna kai a gurin tana ɗan kallon mutane ƙasa-ƙasa, gabanta sai faɗuwa yake kamar zai faɗo. Kamar daga sama taji an dafata ana ƙoƙarin juyowa da ita, juyowar da ta yi sai kawai suka yi ido huɗu da Safiya cikin Uniform ɗinta.
Wani irin kallo Safiya take mata kamar wacce ta rude cox she's can't believe Rashida ce ta gani a nan ƴar'uwarta jininta.
Ita kanta Rashida mamakin ganinta take, dan iya saninta wannan ba asibitun su bace, ya aka yi ta zo nan me ya kawo ta.? Yawu Safiya ta haɗe ta wuce da sauri ta fita daga gurin gudun kar wani daga cikin manyan su ya ganta, daman fitowarta kenan daga wani ɗakin ta hango mai kama da Rashida, ashe ba kama bace, ita ɗin ce amman mai zai kawo Rashida HIV/TB unit.? Shine abinda ya tsaya mata a rai.
Miƙewa Rashida tayi cikin dakewar zuciya ta cigaba da tafiya tana son ɓatarwa da Safiya da lissafi, sai dai kuma yanzu bata san liyin da zata bi, tb ko hiv?
*HILAL POV*
Asibitin ya wuni, da rana ma Hajiya ce ta kawo masa abinci. Duk wanda ya zo sai ya tauyasawa Rafiq ganin yadda ya koma musaki sai dalalar da yawu yake. Tuni Hilal ya ɗosa shi akan magani, yasa aka sake masa wasu hotunan dan ganr ainahin matsalarsa.
Ƴan'uwansa da dama sun yi ta xuwa ganin ɗan nasa, ƴan uwan Rashida ma sun zo, sai dai ba sosai ba, Dady Kalsoom ma ya zo shi da Momy, duk da suna jin nauyi ganin kamar ƴarsu ce ta aikata abun.