Sashe 140
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Wannan tsinin bakin na ki ba, ke me baƙi hali tun da kin yi mugun gado ko? Kije ki kashe min aure! Ke ce uwar rashin kunya uwar gulma ko? Zaki ci ubanki a gidan nan ba dai duk lamanin da na ke miki baki gani ba”
Ta faɗa tana matsar bakinta. Daman ta saba yi mata irin wannan horon a duk lokacin da ta yi mata ba daidai ba. Ta buge mata hannu.
“Ba zaki wuce ba sai na yi ƙwallo da ke?”
Ulfah ta sa kuka.
“Mama Teema Wallahi ba da ni ba”
“Ai ba da ke ba ita kaɗai, ki ki wuce ki gyara min kitchen”
“Tau”
Ta wuce da gudu idonta cike da ƙwalla. Ezzah kuma ta tashi tana kuka ta nufi gurin da ta saba tsayawa kama kunne ta kama kunnenta.
Juyawa Teema ta yi ta koma cikin falon, har ta zauna sai kuma ta miƙe tsaye ta nufi bedroom ɗinta tana ta saƙe-saƙe a ranta. Wani irin ihu ta ji da muryar Ulfah ba shiri ta zaɓura ta fito daga bedroom ɗin a firgice ta nufi kitchen.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Na shiga uku uban waya aike ki taɓa miya?”
A razane ta yi furucin kamin ta ƙarasa gaban Ulfah da ke kwance ƙasa lame-lame tana murje-murje da ihu kamar bata san inda take ba, jikinta har ya sale.
Har ta ɗaga ta tasheta sai kuma ta saketa ta fita a firgice tana kiran Ezzah.
Karo suka yi ita da Ezzah duk ta haɗa uban gumi.
“Mama Teema ga ni”
“Je ki Kitchen ki kama ƴar'uwarki yi sauri”
Ita kuma ta juya da sauri ta koma ɗakinta dan kiran Hilal.
KALSOOM POV.
tana zaune falo Hilal ya shigo bakinsa ƙunshe da murmushi da kuma sallama a lokaci ɗaya. Itama da murmushin ta amsa masa tana ƙara miƙarda ƙafafunta. Kusa da ita ya zauna daman tana zaune ne saman carpet ya kai hannu ya shafa ƙananan kitson da ke kanta yana murmushi.
“A bani canji na na kitso”
“Ba wani canji mai kitson ma ta ce sai an ƙaro”
Dariya yayi ya kai hannu ya shafa cikinta.
“Sai kice mata ai ke mijinki bawan Allah ne, ba mai kuɗi ba ne”
“Ba wani nan, ni sai ka ƙaramin”
“Baki da matsala yarinya ko nawa kike so za a ba ki, ƙuɗin da na ke faɗa miki ina jirajiya sun fito”
Ta zaro ido.
“Da gaske Alhamdulillahi”
Ya lanƙaci hancinta.
“Yes”
“Allah yasa musu albarka”
“Amin mi kike so a siya miki?”
“Ka fara cirewa Hajiya nata, sannan mu sai kuma ƴaƴanka, kai ai ko baka samu ba, ba matsala”
“Sai dai na ɗauki na ki”
“Ba matsala ai daman ni bana siyen komai yanzu”
“Ko da kin haihu?”
“Hilal anya zan haihu?”
“Haba ki daina wannan maganar mana, ke da Teema maganar haihuwar nan na ku ya ishe ni”
“Ƙara ita ai bata yi cikin ba, ni kuwa shekara har da wata huɗu ban haihuwa ba, cikin nan ya ishe ji nake kamar na cire shi na aje”
“Zaki haihu inshallah, tun da an bincika babu wata matsala”
“Allah yasa”
“Amin. Zaki haifa min Baby girl mai kama da ke”
“Baby Boy dai zan haifa mai kama da kai”
Bakinshi ya kai zai yi kissing ɗinta sai wayarsa ta yi ringing, kawar da fuskarta ta yi dan ta bashi damar picking ɗin wayarsa.
“Hello...”
Ya miƙe tsaye da sauri.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, gani nan zuwa”
“Miya faru? ”
Kalsoom ta tambaya a firgice.
“Wai Ezzah ne da Ulfah suka yi faɗa shine Ezzah ta watsa mata miya”
“Subhanallah miya haɗa su haka, ko na ɗauko hijab ɗina muje tare?”
“A'a zauna duk yadda aka yi zan kira ki”
Ya fice a firgice. Daker ta unƙura ta miƙe tsaye da tulelen cikinta.
Yana isa ya ɗauke ta suka yi asibiti tare da Teema, Emergency ya wuce da ita surgical Ward, wata Dr Khadija ce ta shiga bata taimakon gaggawa, dan Dr Hilal tsaye kawai yayi yana kallo saboda jikinsa duk ya mutu ko da suka kawo ta asibitin ma ta suma.
AMIRA POV.
Tun da suka kamo hanyar sokoto take ta aikinki kuka, har suka iso sokoto idonta ya kumbura sosai. Direban na yin horn a bakin gate ɗin gidansu, ta jita cikin wani irin yanayi marar misaltuwa, wani sabon kuka ne ya sake rufeta, musamman lokacin da ta ji muryar mai gadin su yana tambayar wa suke nema.
“Amira na kawo ka min magana da iyayenta zan danƙata hannun Mahaifinta ko mahaifiyarta”
“Amira...!”
Mai gadin ya daki ƙirji. Kamin Direban ya sauke gilashin motarsa ya hango Amirar ce da gaske. Jiki na rawa ya wangale musu gate sannan ya shiga cikin gida da gudu.
Sai ga Mahaifiyarta da duka ƙanenta sun fito har da Baban yayanta. Duk motar suka nufa. Ammy ce ta fara buɗe motar sai ga Amira ta fito daga ciki tana kuka, suka rumgume juna, ƙanenta kuma suka daka tsalle suka yi kanta, Big bro ɓata ne ya tsaya a gurin ya dake yana kallon ikon Allah.
“Ke ce Mahaifiyarta?”
Ammy bata iya amsawa ba sai kuka take, Babban yayansu ne ya amsa da.
“Eh ita ce, waye kai?”
Ya fiddo id cart ɗinsa ya nuna masa,sannan ya miƙa ma Ammy waya.
“Zaki yi magana da Ogan mu”
Cikin muryar kuka Ammy ta ce
“Hello”
“Ke ce Mahaifiyar Amira?”
“Eh nice”
“Kina magana da Major Abdallah Ahmad Mai-doki, da ga rumdunar bada tsoro ta Kasa wato Nigerian Army, da fatar ƴar ki ta shiga hannun ki”
“Ta shigo na goɗe muku”
Daga hakan ɗireban ya janye wayarsa ya buɗe motarsa.
“Wait...”
Big bro nata ya faɗa sannan ya ƙaraso kusa da shi.
“Ina kuka haɗu da ita?”
“Ba ni da wani abun da zan ce ita zata muku bayanin komai da bakinta”
Ya shige motarsa ba tare da ya tsaya jiran abunda zai ƙara tambayarsa ba ya juya a guje ya bar gidan. Sai da Ammy da Amira suka ci kukan su sosai a gurin sannan suka shiga cikin giɗan still suna kuka ita da ƴarta.
NAMRA POV.
“Miya haɗa ki da Yasmin?”
Anty Amarya ta tambaya.
“Ba komai saboda kawai na ƙi amincewa ta maka Uzair kotu ne”
“Kotu a wane dalili?”
A nan Namra ta labarta mata yadda suka yi da Yasmin.
“Karki yarda da ta sa sake jefa ki cikin halin da mahaifin ki zai tsane ki”
“Nima ba zan yarda ba Anty idan munje lahira Allah zai mana hukunci ai”
“Wannan shi ya fi, kin samu kin dawo gida kuma za su kawo miki wani ruɗani, qaya sani ko da mijinta aka haɗa kai ta aikata miki haka”
“Ƙoma ba da shi ba ne babu ta yadda zan yarda ta kai mijinta kotu saboda ni”
“Hakan ya yi ki karya kije ki gaishe da mahaifinki, breakfast ɗin ki na nan dinning”
“To na gode”
Tare suka fito da Anty, suka zauna dinning sai tattauna maganar suke, bayan ta gama karyawa ta koma ɗakin Anty ta ɗauki Hijab ta saka ta nufi part ɗin Abbah.
“Assalamu alaikum”
Ta faɗa yayinda ƙafafunta duka biyu suka tsunduma cikin falon Abbah. Abbah dake dinning area ya ɗago ya kalleta idonsa sanye da farin gilashi fuskarsa kuma ɗauke da murmushi.
“Mamana”
“Na'am Abbah ina kwana”
Ta duƙa har ƙasa ta gaishe shi tare da Hajiya Barau dake ƙoƙarin barin dinning ɗin, kamar zata fasa ihu tace wayyo haka ta bar falon. Sai Abbah ya nunawa Namra kujerar da ke kusa da shi.
“Zo nan ki zauna Mamana”
Ta zauna cikin wani irin jindaɗi marar misaltuwa.
“Kin tashi lafiya, kin karya ko?”
“Na karya”
“Mamana ina son na tunatar da ke akan rayuwa. Ki riƙa haƙuri da abunda ya same ki, kar hakan ya saka ki sakewa ko kuma wani tunani, ko wane bawa da irin ƙaddararsa, dukan abunda ya faru ga bawa zai zamo masa darasi ne ko kuma izna ko wata hanya ta samun cigaban rayuwa, ko da kuwa abun nan mai daɗi ne ko akasin haka, dan haka bana son ki saka damuwa a ranku ni dai na yafe miki, kuma ina son idan kin ɗan hutu kin samu sawaba sai kuma ayi maganar karatu, ina tunanin idan kika koma makaranta sake fi sakewa ki manta da komai”
“Na gode sosai Abbah Allah ya saka maka da alheri, kamin abunda ban taɓa mafarkin zaka min ba, ni kuma na maka alƙawarin va zan sake tsallake zaɓinka ba har a bada ko da kuwa a tufafi ne”
“Allah ya miƙe albarka, ni zanje na shirya akwai inda zan je kwana biyu nan ban samu na fita ba”
Ya miƙe tsaye yana faɗar hakan, ita ta miƙe tsaye.
“Tau Abbah Allah ya tsare”
“Amin”
Ya nufi hanyar da zata sadashi da bedroom ɗinsa, ita kuma ta juya ta fice zuciyarta cike da farinciki.
Ko da ta dawo part ɗin Anty ta tararda su Maryam sun dawo, ga manyan ledoji a gabansu amman sun riƙe baki sai mamaki suke, da alama akwai abunda ya faru.
“Lafiya?”
Maryam ta riƙo hannunta.
“Ke ƴar gidan Abbah wai Amira ta dawo”
“Amira kuma? Daman tun tafiyar da ta yi bata dawo ba sai yanzu?”
“Wallahi sai yanzu, kuma jiya ita ma ta dawo kamar ke”
“Amman kun ji wani abu game da ita?”
“A'a nima Iklima ce take faɗa min ta dawo”
Anty Amarya ta ce
“Allah ya kyauta”
Duk suka amsa da Amin.
UZAIR POV.
Yana shiga bedroom ɗinsa ya fito ya nufi na Yasmin dan yana son ya bincika ko da akwai sauran abunda ta boye, jikinsa na bashi ba saƙon wasiƙar ne kawai ba. Bincike ya fara mata cikin durowoyin ɗakinta kama ya koma gurin wasu takardu da suke gefen gadonta, be samu abunda yake so ba, sai kaiwa ya juya ya fita ya nufi wata ƴar ƙaramar durowarta da take aje takardun aikinta da littafanta duk ya bi ya watsar sai bincike yake mata. Wani abu ya ji ya tsoki tsararsa, kamar an soma masa mashi a kunkuru, tun yana juriya da riƙe kunkurun nasa har ya ji abun ya ƙara sukarsa da wani mugun zugi, wata zarananniyar ƙara ya saki yana jin abun masa ƙasa cikin ƙashin ƙafafunsa, ihu kawai yake yana mirgina, abun ba kyau maza a ƙasa😖
Ta faɗa tana matsar bakinta. Daman ta saba yi mata irin wannan horon a duk lokacin da ta yi mata ba daidai ba. Ta buge mata hannu.
“Ba zaki wuce ba sai na yi ƙwallo da ke?”
Ulfah ta sa kuka.
“Mama Teema Wallahi ba da ni ba”
“Ai ba da ke ba ita kaɗai, ki ki wuce ki gyara min kitchen”
“Tau”
Ta wuce da gudu idonta cike da ƙwalla. Ezzah kuma ta tashi tana kuka ta nufi gurin da ta saba tsayawa kama kunne ta kama kunnenta.
Juyawa Teema ta yi ta koma cikin falon, har ta zauna sai kuma ta miƙe tsaye ta nufi bedroom ɗinta tana ta saƙe-saƙe a ranta. Wani irin ihu ta ji da muryar Ulfah ba shiri ta zaɓura ta fito daga bedroom ɗin a firgice ta nufi kitchen.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Na shiga uku uban waya aike ki taɓa miya?”
A razane ta yi furucin kamin ta ƙarasa gaban Ulfah da ke kwance ƙasa lame-lame tana murje-murje da ihu kamar bata san inda take ba, jikinta har ya sale.
Har ta ɗaga ta tasheta sai kuma ta saketa ta fita a firgice tana kiran Ezzah.
Karo suka yi ita da Ezzah duk ta haɗa uban gumi.
“Mama Teema ga ni”
“Je ki Kitchen ki kama ƴar'uwarki yi sauri”
Ita kuma ta juya da sauri ta koma ɗakinta dan kiran Hilal.
KALSOOM POV.
tana zaune falo Hilal ya shigo bakinsa ƙunshe da murmushi da kuma sallama a lokaci ɗaya. Itama da murmushin ta amsa masa tana ƙara miƙarda ƙafafunta. Kusa da ita ya zauna daman tana zaune ne saman carpet ya kai hannu ya shafa ƙananan kitson da ke kanta yana murmushi.
“A bani canji na na kitso”
“Ba wani canji mai kitson ma ta ce sai an ƙaro”
Dariya yayi ya kai hannu ya shafa cikinta.
“Sai kice mata ai ke mijinki bawan Allah ne, ba mai kuɗi ba ne”
“Ba wani nan, ni sai ka ƙaramin”
“Baki da matsala yarinya ko nawa kike so za a ba ki, ƙuɗin da na ke faɗa miki ina jirajiya sun fito”
Ta zaro ido.
“Da gaske Alhamdulillahi”
Ya lanƙaci hancinta.
“Yes”
“Allah yasa musu albarka”
“Amin mi kike so a siya miki?”
“Ka fara cirewa Hajiya nata, sannan mu sai kuma ƴaƴanka, kai ai ko baka samu ba, ba matsala”
“Sai dai na ɗauki na ki”
“Ba matsala ai daman ni bana siyen komai yanzu”
“Ko da kin haihu?”
“Hilal anya zan haihu?”
“Haba ki daina wannan maganar mana, ke da Teema maganar haihuwar nan na ku ya ishe ni”
“Ƙara ita ai bata yi cikin ba, ni kuwa shekara har da wata huɗu ban haihuwa ba, cikin nan ya ishe ji nake kamar na cire shi na aje”
“Zaki haihu inshallah, tun da an bincika babu wata matsala”
“Allah yasa”
“Amin. Zaki haifa min Baby girl mai kama da ke”
“Baby Boy dai zan haifa mai kama da kai”
Bakinshi ya kai zai yi kissing ɗinta sai wayarsa ta yi ringing, kawar da fuskarta ta yi dan ta bashi damar picking ɗin wayarsa.
“Hello...”
Ya miƙe tsaye da sauri.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, gani nan zuwa”
“Miya faru? ”
Kalsoom ta tambaya a firgice.
“Wai Ezzah ne da Ulfah suka yi faɗa shine Ezzah ta watsa mata miya”
“Subhanallah miya haɗa su haka, ko na ɗauko hijab ɗina muje tare?”
“A'a zauna duk yadda aka yi zan kira ki”
Ya fice a firgice. Daker ta unƙura ta miƙe tsaye da tulelen cikinta.
Yana isa ya ɗauke ta suka yi asibiti tare da Teema, Emergency ya wuce da ita surgical Ward, wata Dr Khadija ce ta shiga bata taimakon gaggawa, dan Dr Hilal tsaye kawai yayi yana kallo saboda jikinsa duk ya mutu ko da suka kawo ta asibitin ma ta suma.
AMIRA POV.
Tun da suka kamo hanyar sokoto take ta aikinki kuka, har suka iso sokoto idonta ya kumbura sosai. Direban na yin horn a bakin gate ɗin gidansu, ta jita cikin wani irin yanayi marar misaltuwa, wani sabon kuka ne ya sake rufeta, musamman lokacin da ta ji muryar mai gadin su yana tambayar wa suke nema.
“Amira na kawo ka min magana da iyayenta zan danƙata hannun Mahaifinta ko mahaifiyarta”
“Amira...!”
Mai gadin ya daki ƙirji. Kamin Direban ya sauke gilashin motarsa ya hango Amirar ce da gaske. Jiki na rawa ya wangale musu gate sannan ya shiga cikin gida da gudu.
Sai ga Mahaifiyarta da duka ƙanenta sun fito har da Baban yayanta. Duk motar suka nufa. Ammy ce ta fara buɗe motar sai ga Amira ta fito daga ciki tana kuka, suka rumgume juna, ƙanenta kuma suka daka tsalle suka yi kanta, Big bro ɓata ne ya tsaya a gurin ya dake yana kallon ikon Allah.
“Ke ce Mahaifiyarta?”
Ammy bata iya amsawa ba sai kuka take, Babban yayansu ne ya amsa da.
“Eh ita ce, waye kai?”
Ya fiddo id cart ɗinsa ya nuna masa,sannan ya miƙa ma Ammy waya.
“Zaki yi magana da Ogan mu”
Cikin muryar kuka Ammy ta ce
“Hello”
“Ke ce Mahaifiyar Amira?”
“Eh nice”
“Kina magana da Major Abdallah Ahmad Mai-doki, da ga rumdunar bada tsoro ta Kasa wato Nigerian Army, da fatar ƴar ki ta shiga hannun ki”
“Ta shigo na goɗe muku”
Daga hakan ɗireban ya janye wayarsa ya buɗe motarsa.
“Wait...”
Big bro nata ya faɗa sannan ya ƙaraso kusa da shi.
“Ina kuka haɗu da ita?”
“Ba ni da wani abun da zan ce ita zata muku bayanin komai da bakinta”
Ya shige motarsa ba tare da ya tsaya jiran abunda zai ƙara tambayarsa ba ya juya a guje ya bar gidan. Sai da Ammy da Amira suka ci kukan su sosai a gurin sannan suka shiga cikin giɗan still suna kuka ita da ƴarta.
NAMRA POV.
“Miya haɗa ki da Yasmin?”
Anty Amarya ta tambaya.
“Ba komai saboda kawai na ƙi amincewa ta maka Uzair kotu ne”
“Kotu a wane dalili?”
A nan Namra ta labarta mata yadda suka yi da Yasmin.
“Karki yarda da ta sa sake jefa ki cikin halin da mahaifin ki zai tsane ki”
“Nima ba zan yarda ba Anty idan munje lahira Allah zai mana hukunci ai”
“Wannan shi ya fi, kin samu kin dawo gida kuma za su kawo miki wani ruɗani, qaya sani ko da mijinta aka haɗa kai ta aikata miki haka”
“Ƙoma ba da shi ba ne babu ta yadda zan yarda ta kai mijinta kotu saboda ni”
“Hakan ya yi ki karya kije ki gaishe da mahaifinki, breakfast ɗin ki na nan dinning”
“To na gode”
Tare suka fito da Anty, suka zauna dinning sai tattauna maganar suke, bayan ta gama karyawa ta koma ɗakin Anty ta ɗauki Hijab ta saka ta nufi part ɗin Abbah.
“Assalamu alaikum”
Ta faɗa yayinda ƙafafunta duka biyu suka tsunduma cikin falon Abbah. Abbah dake dinning area ya ɗago ya kalleta idonsa sanye da farin gilashi fuskarsa kuma ɗauke da murmushi.
“Mamana”
“Na'am Abbah ina kwana”
Ta duƙa har ƙasa ta gaishe shi tare da Hajiya Barau dake ƙoƙarin barin dinning ɗin, kamar zata fasa ihu tace wayyo haka ta bar falon. Sai Abbah ya nunawa Namra kujerar da ke kusa da shi.
“Zo nan ki zauna Mamana”
Ta zauna cikin wani irin jindaɗi marar misaltuwa.
“Kin tashi lafiya, kin karya ko?”
“Na karya”
“Mamana ina son na tunatar da ke akan rayuwa. Ki riƙa haƙuri da abunda ya same ki, kar hakan ya saka ki sakewa ko kuma wani tunani, ko wane bawa da irin ƙaddararsa, dukan abunda ya faru ga bawa zai zamo masa darasi ne ko kuma izna ko wata hanya ta samun cigaban rayuwa, ko da kuwa abun nan mai daɗi ne ko akasin haka, dan haka bana son ki saka damuwa a ranku ni dai na yafe miki, kuma ina son idan kin ɗan hutu kin samu sawaba sai kuma ayi maganar karatu, ina tunanin idan kika koma makaranta sake fi sakewa ki manta da komai”
“Na gode sosai Abbah Allah ya saka maka da alheri, kamin abunda ban taɓa mafarkin zaka min ba, ni kuma na maka alƙawarin va zan sake tsallake zaɓinka ba har a bada ko da kuwa a tufafi ne”
“Allah ya miƙe albarka, ni zanje na shirya akwai inda zan je kwana biyu nan ban samu na fita ba”
Ya miƙe tsaye yana faɗar hakan, ita ta miƙe tsaye.
“Tau Abbah Allah ya tsare”
“Amin”
Ya nufi hanyar da zata sadashi da bedroom ɗinsa, ita kuma ta juya ta fice zuciyarta cike da farinciki.
Ko da ta dawo part ɗin Anty ta tararda su Maryam sun dawo, ga manyan ledoji a gabansu amman sun riƙe baki sai mamaki suke, da alama akwai abunda ya faru.
“Lafiya?”
Maryam ta riƙo hannunta.
“Ke ƴar gidan Abbah wai Amira ta dawo”
“Amira kuma? Daman tun tafiyar da ta yi bata dawo ba sai yanzu?”
“Wallahi sai yanzu, kuma jiya ita ma ta dawo kamar ke”
“Amman kun ji wani abu game da ita?”
“A'a nima Iklima ce take faɗa min ta dawo”
Anty Amarya ta ce
“Allah ya kyauta”
Duk suka amsa da Amin.
UZAIR POV.
Yana shiga bedroom ɗinsa ya fito ya nufi na Yasmin dan yana son ya bincika ko da akwai sauran abunda ta boye, jikinsa na bashi ba saƙon wasiƙar ne kawai ba. Bincike ya fara mata cikin durowoyin ɗakinta kama ya koma gurin wasu takardu da suke gefen gadonta, be samu abunda yake so ba, sai kaiwa ya juya ya fita ya nufi wata ƴar ƙaramar durowarta da take aje takardun aikinta da littafanta duk ya bi ya watsar sai bincike yake mata. Wani abu ya ji ya tsoki tsararsa, kamar an soma masa mashi a kunkuru, tun yana juriya da riƙe kunkurun nasa har ya ji abun ya ƙara sukarsa da wani mugun zugi, wata zarananniyar ƙara ya saki yana jin abun masa ƙasa cikin ƙashin ƙafafunsa, ihu kawai yake yana mirgina, abun ba kyau maza a ƙasa😖