Sashe 41
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ba komai, nima bana jindaɗin ne, amman zan daure a haka naje”
“Yauwa na gode sosai, kin ce dai yana aiki sosai ko?”
“Sosai Wallahi kamar yan kan wuƙa, duk yadda mu kayi zan faɗa miki”
“Okay na gode”
Rashida na kashe wayar Asmee ta fashe da kuka.
‘Allah kasa ba gaske bane Allah, idan har da gaske ne ya ci amanata, tun da yasan yana da shi kuma ya nemi ya kwana da ni, Wallahi dana sani ni dama ban je gunsa neman magani ba, mugun Malami kawai’
Abunda take ta tunani a zuciyarta kenan, a fili kam kuka kawai take, kamar ta cire idonta.
_________________________________________
Kuyi Haƙuri da wannan idan Allah ya bani iko zan kara muku wani anjima.
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY 😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
Godiya marar iyaka gareki Daughter, na gode na gode I really did not expect this awesome surprise from your side
Allah ya kara arziki 😘
*PAGE - 31*
NOT EDITED ⚠️
Ƴan seconds ya rage wayar ta fara ringing sai kawai ta kashe, tana tunanin yadda za fallasawa kanta asiri idan har ta yarda ta faɗa masa danuwarta, ba duka ɗan'uwane yake taimako dan Allah ba, ballanta shi data san dole ne ya faɗawa Hajiya Barau, ita kuma fitar da maganar zata yi, sai a fara cewa tana roƙon dangi.
Juyowa tayi ta nufo gurin da Hajara take zaune, ita ma ta zauna tana miƙa mata wayar.
“Har kin kira?”
“A'a ban kira ba na fasa ne”
Ta faɗa tana murmushi, isowar Mama yasa ta sadda kanta ƙasa tana watsa da yatsun hannunta.
“Wai gida za mu koma yanzu”
Daga Hajara har Namra kallonta suka yi
“Gida kuma? Ina ba dai sokoto ba ko?”
Namra ta tambaya cike da mamaki.
“Can fa, wai so nake muje yanzu kamin yamma mun isa sai da gobe kuma mu juyo”
“Amman zuwa lafiya ne?”
Mama ta ɗan yi shiru kamar mai tunanin abunda zata ce mata.
“A'a wai kuɗi zan je na ranto idan har Allah yasa an samu sai a siye maganin da likita ya rubuta ta, tun da naga alamun sauƙi a jikinsa amman kumburin nan na kansa yana bani tsoro. Kuma ina son naje na ɗauko wasu tufafin gashi mai son Hajara shi ma ya damu yaushe za mu dawo”
Namra ta sauke ajiyar zuciya cike da tausayawa, ji take kamar ace tana da mafitar su ta ɗauka ta bada, ba sai taje neman rance ba.
“Amman Mama da zaki yi haƙuri har gobe, saboda yanzu rana yayi sosai, kuma zaku iya zuwa ku tarar da jira a tasha, ƙara ki haƙura har da safe sai ki tafi, amman tafiyar dare ba kyau, musamman lokacin nan na muke cikin matsalar tsaro”
Mama ta ɗan yi shiru, tana nazarin maganganun Namra.
“Nima haka nake gani, ƙara na haƙura har zuwa goben”
Ta faɗa daga tsayen da take tana gyara ɗaurin zanenta, sai kuma ta juya ta koma dan faɗawa Asim zancen canjin tafiyar.
Sai da wuce sannan Hajara ta kalli Namra tace
“Tafiya yanzu sai kace waɗanda aka kora daga gari”
“Nima ai shi na gani, ƙara dai a haƙura har da safe, yau da gobe a duk ɗaya ne wajen Allah”
Namra ta faɗa tana ƙoƙarin tashi
“Lallai kam, nima bana son tafiya irin wannan”
Murmushi kawai tayi ta nufi ward ɗin da nufin ƙara tausasa Mama ta haƙura da tafiyar har gobe.
A bakin ƙofar ta tsaya cak! Tana sauraren muryar Mama da kunnuwanta suke sato mata.
“Na ce amman ai dubu ɗari sun isa ko? Kar mu karɓo kuɗin duka ya zama ba muna da komai gurin mai dashen”
“A'a Mama ki karɓo gaba ɗaya, kin san dole ne mu siye abinci, kuma wata ƙila ba wannan maganin kawai za a siya ba”
“Amman Ibrahim idan muka karɓi kuɗin duka mun fita daga adashen kenan fa, abinci idan har taga babu shi ai dole ta faɗa ma iyayen nata, ni ina mamakin ace ƴarka ta yi wuta irin haka ka kasa taimaka mata, anya wai ƴar su ce tagaske kuwa? Ni bana ganin a kashe kuɗi dika fa”
“Haba Mama lafiya na kama da me? Idan har Allah yasa na ji sauƙi, ai sai a samo wasu a ake shiga kuma”
“Ina za'a samu wasu Ibrahim? Kana ganin yadda suka juya maka baya, Wallahi bana tunanin zaka samu wani abu a auren nan, duba kaga ko fa ƴar garar nan da ake ba su maka ba, yanzu dubi halin da kake ciki ai ko basu fitar da kai waje ba, sa maka iya ƙoƙarin su amman suja ƙyale ka”
Wani dogon numfashi Asim.yaja ya sauke zuciyarsa cike da jin zafin abunda iyayen Namra suka masa.
“Allah dai ya bani lafiya, idan kiɗa ya canja rawa ma dole ta canja, idan su yi dan Allah ba sa yi dan ƴar su”
Kamar an jefar da gilass a ƙasa ya tarwatse haka taji a zuciyarta, lokacin da maganganun Asim suka daki dodon kunnenta.
Da sauri tayi baya tana maida numfashi, tare da haɗiye yawu a lokaci ɗaya. Wani irin mamaki take tana girgiza kai, kamin tayi haramar barin gurin.
Da sauri-sauri take tafiya kamar zata haɗa da gudu, ji take kamar tayi tsalle ta ganta a wani wajen, ta kasa yarda da kunnuwanta sun ji abunda Asim da Mahaifiyarsa suke faɗa.
Ta tari mai Napep tana haƙi kamar wanda aka janye wa numfashi.
“Nasarawa zaka kai”
“To ɗari da Hansi, kuma sai na bi ta Yarima Estate na sauke wannan matar”
Kai kawai Namra ɗaga masa, ta shiga Napep ɗin ba dan hankalinta yana jikinta ba. Yarinyar dake kusa da ita taja wani dogon tsaki, tana matsawa can gefe irin tana ƙyaƙyamin Namra ɗin nan.
“Mtswww ni dama zaka sauke ta, ta nemi wani sai na biya ka kuɗin duka”
“A a haƙura dai zaki yi Hajiya, ai da kamin a ɗauke ta kika ce haka, amman yanzu na riga na ɗauko ta kyayi wannan maganar kuma”
Mai Napep ɗin ya faɗa, yana mai cigaba da tuƙinsa. Sai a lokacin Namra ta kalle ta da kyau.
“A'a ka sauke ni mana ka kaita ita kaɗai saboda ni ba mutum bace, ko kuma Napep ɗin ta gidan ku ce, idan har kin isa miyasa ba'a siya miki mota ba? Ko kuma ayi miki direba na ki na kan ki? Wallahi ƙaryar arziki kike tun da har kika iya shigo Napep”
Ƙasa-ƙasa ta kalli Namra tana wani yamutsa fuska, ita har ga Allah ƙyaƙƙyamin Namra take. Wayarta dake jaka tayi ringing, tayi saurin fidɗo purse ɗin dake cikin jakar ta cire wayar tare da yin picking ta kara a kunne.
“Hello Dude”
Ta ɗan yi shiru kamin ta sake cewa.
“Ni na baro motar can, Ummy ce na faɗa mata, wai bata turo direba tun da ban faɗa mata zan fita ba”
“Eh ina kam Napep n kusa isa, okay bye safe trip Dude”
Ta kashe wayar kamar ta fasa kuka, kamin a isa Estate ɗin nasu har ta tsawala.
Har bakin gate ɗin gidansu ya sauke ta, ta ciro 1k ta miƙa masa, bata tsaya karɓar canji ba ta nufi gidan, da sojoji suke gadi, da sauri suka buɗe mata gate shige cikin, sai ƙyaƙƙyamin kanta take.
Kai kawai mai Napep ɗin ya kaɗa ya wuce da Namra Nasarawa road.
A ƙofar gidan su Mardiya tace a sauke ta, ta ciro ɗari biyu ta miƙa masa ya karɓa ya bata canji sannan ta juya ta nufi cikin gidan, zuciyarta na dawo da maganganun da kunnuwanta suka joyo mata.
A zauren gidan ta tsaya, ta jingina da ginin gurin ta lumshe.
‘Miyasa Asim yake ƙoƙarin ɓoye min sirrin sa? Me suke shiryawa shi da mahaifiyarsa? Kar zancen Anty ya zama gaskiya, kar dai ace rayuwar Asim ta canja, da biyu ya aure ni kenan? Soyayyar daya nuna min a baya ta ƙarya ce?’
Hawaye ya silalo daga idonta, dake lumshe, sai kuma ta girgiza kai tana cigaba da zancen zuci.
‘Amman ya so ni a baya kuma so na gaskiya, miyasa yanzu zai canja? Na juyawa kowa baya saboda shi, ba zai min haka ba, what if i choose the wrong person? No no no it's Asim mutumen da yake son ki so na haƙiƙa mutumen da yace min miki ba dukiyarki ce a gabansa ba’
Ta buɗe ido tana share hawayenta.
“Amman mi yake nufi da idan ba suyi dan Allah sa yi dan ni? Me yake nufi da idan rawa ta canja, Allah ka fahimtar da ni, Allah ka amintar da ni, Allah kar ka saka zancen Anty ya zama gaskiya, Allah kar kasa Asim ya zama cikin mutanen da za su min Zagon Ƙasa, Allah kar kasa ayi ma auren nan na mu dariya”
A fili tayi furucin tana kuka, zuciyarta a karye, tana ji a jikinta ranar nadamar ta tana daf ta ita.
Ganin wata zata fito daga cikin gidan yasa tayi saurin ɓoye kukanta.
“Namra ce a nan tsaye?”
“Eh yanzu na shigo ina wuni?”
“Ya jikin mai gidan na ki?”
“Da sauƙi sosai”
“Allah ya ƙara sauke, har yanzu dai ba mu samu mun koma mu ƙara dubashi ba”
“Ba komai ai, kuna ta sana'ah ba zama”
“Ba zama fa Allah dai ya ɗauƙe Wahala”
“Amin”
Namra ta kunna kai cikin gidan, ita kuma ta fice tana gyara hijabinta.
HILAL POV.
Yau one day da gwajin da ya kai ayi ma Rashida, dan haka yana buƙatar karɓo result ɗin dan tabbatar da zarginsa, duk da alamu sun nuna cikin ne amman ya fi son ya ƙara tabbatarwa.
Lokacin daya gama duba Patients ɗinsa sai ya nufi lab dan karɓar sakamakon.
To his surprise ba abunda yake zato ba kawai ya gani, a cikin result ɗin akwai symptom ɗin HIV. Haka ya riƙa karanta result ɗin ba daɗi, but still abu ɗaya yake gani da biyu yake gani.
Ciki da kuma symptom.
Ƙoƙarin ɓoye damuwarsa yayi, kar mutanen da suke gurin su zargi wani abu. Cikin rashin kuzari ya dawo office ɗinsa, har ya zauna sai kuma ya tashi tsaye, sai karanta takardar yake numfashinsa na yawo, wani zafi ya riƙa jin yana masa yawo tun daga cikin cikinsa zuwa ƙwaƙwalwarsa.
“Ko dai mistake suka yi? How could this happen?”
“Yauwa na gode sosai, kin ce dai yana aiki sosai ko?”
“Sosai Wallahi kamar yan kan wuƙa, duk yadda mu kayi zan faɗa miki”
“Okay na gode”
Rashida na kashe wayar Asmee ta fashe da kuka.
‘Allah kasa ba gaske bane Allah, idan har da gaske ne ya ci amanata, tun da yasan yana da shi kuma ya nemi ya kwana da ni, Wallahi dana sani ni dama ban je gunsa neman magani ba, mugun Malami kawai’
Abunda take ta tunani a zuciyarta kenan, a fili kam kuka kawai take, kamar ta cire idonta.
_________________________________________
Kuyi Haƙuri da wannan idan Allah ya bani iko zan kara muku wani anjima.
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY 😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
Godiya marar iyaka gareki Daughter, na gode na gode I really did not expect this awesome surprise from your side
Allah ya kara arziki 😘
*PAGE - 31*
NOT EDITED ⚠️
Ƴan seconds ya rage wayar ta fara ringing sai kawai ta kashe, tana tunanin yadda za fallasawa kanta asiri idan har ta yarda ta faɗa masa danuwarta, ba duka ɗan'uwane yake taimako dan Allah ba, ballanta shi data san dole ne ya faɗawa Hajiya Barau, ita kuma fitar da maganar zata yi, sai a fara cewa tana roƙon dangi.
Juyowa tayi ta nufo gurin da Hajara take zaune, ita ma ta zauna tana miƙa mata wayar.
“Har kin kira?”
“A'a ban kira ba na fasa ne”
Ta faɗa tana murmushi, isowar Mama yasa ta sadda kanta ƙasa tana watsa da yatsun hannunta.
“Wai gida za mu koma yanzu”
Daga Hajara har Namra kallonta suka yi
“Gida kuma? Ina ba dai sokoto ba ko?”
Namra ta tambaya cike da mamaki.
“Can fa, wai so nake muje yanzu kamin yamma mun isa sai da gobe kuma mu juyo”
“Amman zuwa lafiya ne?”
Mama ta ɗan yi shiru kamar mai tunanin abunda zata ce mata.
“A'a wai kuɗi zan je na ranto idan har Allah yasa an samu sai a siye maganin da likita ya rubuta ta, tun da naga alamun sauƙi a jikinsa amman kumburin nan na kansa yana bani tsoro. Kuma ina son naje na ɗauko wasu tufafin gashi mai son Hajara shi ma ya damu yaushe za mu dawo”
Namra ta sauke ajiyar zuciya cike da tausayawa, ji take kamar ace tana da mafitar su ta ɗauka ta bada, ba sai taje neman rance ba.
“Amman Mama da zaki yi haƙuri har gobe, saboda yanzu rana yayi sosai, kuma zaku iya zuwa ku tarar da jira a tasha, ƙara ki haƙura har da safe sai ki tafi, amman tafiyar dare ba kyau, musamman lokacin nan na muke cikin matsalar tsaro”
Mama ta ɗan yi shiru, tana nazarin maganganun Namra.
“Nima haka nake gani, ƙara na haƙura har zuwa goben”
Ta faɗa daga tsayen da take tana gyara ɗaurin zanenta, sai kuma ta juya ta koma dan faɗawa Asim zancen canjin tafiyar.
Sai da wuce sannan Hajara ta kalli Namra tace
“Tafiya yanzu sai kace waɗanda aka kora daga gari”
“Nima ai shi na gani, ƙara dai a haƙura har da safe, yau da gobe a duk ɗaya ne wajen Allah”
Namra ta faɗa tana ƙoƙarin tashi
“Lallai kam, nima bana son tafiya irin wannan”
Murmushi kawai tayi ta nufi ward ɗin da nufin ƙara tausasa Mama ta haƙura da tafiyar har gobe.
A bakin ƙofar ta tsaya cak! Tana sauraren muryar Mama da kunnuwanta suke sato mata.
“Na ce amman ai dubu ɗari sun isa ko? Kar mu karɓo kuɗin duka ya zama ba muna da komai gurin mai dashen”
“A'a Mama ki karɓo gaba ɗaya, kin san dole ne mu siye abinci, kuma wata ƙila ba wannan maganin kawai za a siya ba”
“Amman Ibrahim idan muka karɓi kuɗin duka mun fita daga adashen kenan fa, abinci idan har taga babu shi ai dole ta faɗa ma iyayen nata, ni ina mamakin ace ƴarka ta yi wuta irin haka ka kasa taimaka mata, anya wai ƴar su ce tagaske kuwa? Ni bana ganin a kashe kuɗi dika fa”
“Haba Mama lafiya na kama da me? Idan har Allah yasa na ji sauƙi, ai sai a samo wasu a ake shiga kuma”
“Ina za'a samu wasu Ibrahim? Kana ganin yadda suka juya maka baya, Wallahi bana tunanin zaka samu wani abu a auren nan, duba kaga ko fa ƴar garar nan da ake ba su maka ba, yanzu dubi halin da kake ciki ai ko basu fitar da kai waje ba, sa maka iya ƙoƙarin su amman suja ƙyale ka”
Wani dogon numfashi Asim.yaja ya sauke zuciyarsa cike da jin zafin abunda iyayen Namra suka masa.
“Allah dai ya bani lafiya, idan kiɗa ya canja rawa ma dole ta canja, idan su yi dan Allah ba sa yi dan ƴar su”
Kamar an jefar da gilass a ƙasa ya tarwatse haka taji a zuciyarta, lokacin da maganganun Asim suka daki dodon kunnenta.
Da sauri tayi baya tana maida numfashi, tare da haɗiye yawu a lokaci ɗaya. Wani irin mamaki take tana girgiza kai, kamin tayi haramar barin gurin.
Da sauri-sauri take tafiya kamar zata haɗa da gudu, ji take kamar tayi tsalle ta ganta a wani wajen, ta kasa yarda da kunnuwanta sun ji abunda Asim da Mahaifiyarsa suke faɗa.
Ta tari mai Napep tana haƙi kamar wanda aka janye wa numfashi.
“Nasarawa zaka kai”
“To ɗari da Hansi, kuma sai na bi ta Yarima Estate na sauke wannan matar”
Kai kawai Namra ɗaga masa, ta shiga Napep ɗin ba dan hankalinta yana jikinta ba. Yarinyar dake kusa da ita taja wani dogon tsaki, tana matsawa can gefe irin tana ƙyaƙyamin Namra ɗin nan.
“Mtswww ni dama zaka sauke ta, ta nemi wani sai na biya ka kuɗin duka”
“A a haƙura dai zaki yi Hajiya, ai da kamin a ɗauke ta kika ce haka, amman yanzu na riga na ɗauko ta kyayi wannan maganar kuma”
Mai Napep ɗin ya faɗa, yana mai cigaba da tuƙinsa. Sai a lokacin Namra ta kalle ta da kyau.
“A'a ka sauke ni mana ka kaita ita kaɗai saboda ni ba mutum bace, ko kuma Napep ɗin ta gidan ku ce, idan har kin isa miyasa ba'a siya miki mota ba? Ko kuma ayi miki direba na ki na kan ki? Wallahi ƙaryar arziki kike tun da har kika iya shigo Napep”
Ƙasa-ƙasa ta kalli Namra tana wani yamutsa fuska, ita har ga Allah ƙyaƙƙyamin Namra take. Wayarta dake jaka tayi ringing, tayi saurin fidɗo purse ɗin dake cikin jakar ta cire wayar tare da yin picking ta kara a kunne.
“Hello Dude”
Ta ɗan yi shiru kamin ta sake cewa.
“Ni na baro motar can, Ummy ce na faɗa mata, wai bata turo direba tun da ban faɗa mata zan fita ba”
“Eh ina kam Napep n kusa isa, okay bye safe trip Dude”
Ta kashe wayar kamar ta fasa kuka, kamin a isa Estate ɗin nasu har ta tsawala.
Har bakin gate ɗin gidansu ya sauke ta, ta ciro 1k ta miƙa masa, bata tsaya karɓar canji ba ta nufi gidan, da sojoji suke gadi, da sauri suka buɗe mata gate shige cikin, sai ƙyaƙƙyamin kanta take.
Kai kawai mai Napep ɗin ya kaɗa ya wuce da Namra Nasarawa road.
A ƙofar gidan su Mardiya tace a sauke ta, ta ciro ɗari biyu ta miƙa masa ya karɓa ya bata canji sannan ta juya ta nufi cikin gidan, zuciyarta na dawo da maganganun da kunnuwanta suka joyo mata.
A zauren gidan ta tsaya, ta jingina da ginin gurin ta lumshe.
‘Miyasa Asim yake ƙoƙarin ɓoye min sirrin sa? Me suke shiryawa shi da mahaifiyarsa? Kar zancen Anty ya zama gaskiya, kar dai ace rayuwar Asim ta canja, da biyu ya aure ni kenan? Soyayyar daya nuna min a baya ta ƙarya ce?’
Hawaye ya silalo daga idonta, dake lumshe, sai kuma ta girgiza kai tana cigaba da zancen zuci.
‘Amman ya so ni a baya kuma so na gaskiya, miyasa yanzu zai canja? Na juyawa kowa baya saboda shi, ba zai min haka ba, what if i choose the wrong person? No no no it's Asim mutumen da yake son ki so na haƙiƙa mutumen da yace min miki ba dukiyarki ce a gabansa ba’
Ta buɗe ido tana share hawayenta.
“Amman mi yake nufi da idan ba suyi dan Allah sa yi dan ni? Me yake nufi da idan rawa ta canja, Allah ka fahimtar da ni, Allah ka amintar da ni, Allah kar ka saka zancen Anty ya zama gaskiya, Allah kar kasa Asim ya zama cikin mutanen da za su min Zagon Ƙasa, Allah kar kasa ayi ma auren nan na mu dariya”
A fili tayi furucin tana kuka, zuciyarta a karye, tana ji a jikinta ranar nadamar ta tana daf ta ita.
Ganin wata zata fito daga cikin gidan yasa tayi saurin ɓoye kukanta.
“Namra ce a nan tsaye?”
“Eh yanzu na shigo ina wuni?”
“Ya jikin mai gidan na ki?”
“Da sauƙi sosai”
“Allah ya ƙara sauke, har yanzu dai ba mu samu mun koma mu ƙara dubashi ba”
“Ba komai ai, kuna ta sana'ah ba zama”
“Ba zama fa Allah dai ya ɗauƙe Wahala”
“Amin”
Namra ta kunna kai cikin gidan, ita kuma ta fice tana gyara hijabinta.
HILAL POV.
Yau one day da gwajin da ya kai ayi ma Rashida, dan haka yana buƙatar karɓo result ɗin dan tabbatar da zarginsa, duk da alamu sun nuna cikin ne amman ya fi son ya ƙara tabbatarwa.
Lokacin daya gama duba Patients ɗinsa sai ya nufi lab dan karɓar sakamakon.
To his surprise ba abunda yake zato ba kawai ya gani, a cikin result ɗin akwai symptom ɗin HIV. Haka ya riƙa karanta result ɗin ba daɗi, but still abu ɗaya yake gani da biyu yake gani.
Ciki da kuma symptom.
Ƙoƙarin ɓoye damuwarsa yayi, kar mutanen da suke gurin su zargi wani abu. Cikin rashin kuzari ya dawo office ɗinsa, har ya zauna sai kuma ya tashi tsaye, sai karanta takardar yake numfashinsa na yawo, wani zafi ya riƙa jin yana masa yawo tun daga cikin cikinsa zuwa ƙwaƙwalwarsa.
“Ko dai mistake suka yi? How could this happen?”