Sashe 158
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A gajiye Namra ta miƙe ta shiga wanka ta shirya cikin lace ɗin sai suka gyara mata fuskarta, ana cikin ɗara mata ɗankwali wayar Namra ta yi ringing.
Tana ganin Number Abdool ta yi dariya.
“Ango ango”
“Maryam ya gajiyar biki? Ina Amaryata? Na kira wayarta ta ƙi ta ɗaga ki ce ina gaidata kuma ki ɗaukar min pictures ɗinta”
“An gama ranka ya daɗe”
Ya sauke wayar tana dariya tare da amsa sallamar Gwaggo Ramatu.
“Ku fito ga motoci can an zo da su, Maryam ke kaɗai kin isa ni da Talatu zamu je sai a samu wasu cikin ƙannen Anty Amarya su biyu kuma suje tun da ance mutum biyar sun isa”
Raihanatu ta mike tsaye tana kare ɗankwali.
“Haba Baba Ramatu wane irin Maryam kuma ita da take da aure, ai ƙara dai ki ce ni ko zan samu ɗan saurayi da zai ɗauke cikin ƙannen Yarima”
Sai duk suka bushe da dariya Gwaggo Ramatu ta ce
“To shirya har ke aje da ke”
Motocin dake waje guda biyu sun kusan awa ɗaya sannan Namra ta fito tare da Gwaggo Ramatu da su Maryam da Raihanatu suka shiga motocin.
A tunaninsu za a wace ne gidan sarkin kai tsaye sai suka ga ya kai su gidan Ummi. Kunya sosai Namra ta samu kanta da ji lokacin da motar ta faka a bakin ƙofar shiga falon Ummi. Meesha da Fauza suka fito da wayoyinsu a hannu suka ɗaukarta video, Amal kuma ta zo da gudu ta rumgume ta.
Sam Amal bata gane wace Namra ba, sai dai ita Namra ta gane ta tun a wayar Abdool da take kallon hotunan family ɗin ƴan gidansu. Cike suka tarar da gidan da mutane tana saka ƙafarta cikin falon aka ɗauki guɗa. Ɗakin Ummi aka wuce da ita yayinda su Maryam da Gwaggo suka tsaya a waje a falo suna gaisawa da jama'ah dan basa iya tantance Ummi balle ma bata falon. Namra na shiga Ummi ta shigo sai ta yi saurin yin ƙasa tana gaishe da Ummi. Domin sarai ta san ita mahaifiyar Abdool ga kamanin Abdool nan xube a fuskarta kuma tana ganin ƴadda yake koɗa mahaifiyar ta shi a instagram. Da Murmushi Ummi ta zauna saman gado tana dafa Namra.
“Tashi Tashi Ƴata Allah yayi miki albarka”
Sai Namra ta ɗago sai dai bata yarda ta koma saman gadon ba sai ta zauna ƙasa fuskarka rufe da mayafinta.
Amal ce ta turo ƙofar ɗakin ta shigo cike da zumuɗin ita ƙanwar ango.
“Ummi kin ga fuskarta? Mu bata buɗe mana ba”
“Ai zata buɗe muku har sai kun gaji da ganinta”
“Ni dai ba zan iya haƙuri ba”
Ta faɗa a shagwaɓe. Ummi ta miƙe.tsaye tana gyaɗa kai ta nufi wata dorowa ta buɗe ta ɗauko wasu robobi guda huɗu ta dawo ta zauna.
“Ungo wannan shanye duka”
Hannu biyu Namra tasa ta karɓa ta kafa kai ta shanye abunda yake ciki tas sannan ta sake amsar na biyu ta shanye a na ukun ma shanyewa ta yi sai a huɗu ne Ummi tace karta shanye ta raga. A nan Amal ta samu damar ganin fuskarta har ta yi mata hoto da wayar Ummi.
Bayan Namra ta gama sha Ummi tasa Amal ta ɗauke robobin ta fitar, sai mai Makeup ta shigo da kit ɗinta ta yi zaman dishin a gaban Ummi tana miƙa mata gaisuwa.
Meesha ce ta shigo ɗakin ɗauke da wani koren lace ta aje saman gado.
“Ummi ga shi”
Ummi ta kalli Namra tana nuna mata wani ƙaramin ɗaki dake gefen bathroom ta ce
“Ƴata shiga can ki shirya da wannan kayan”
Meesha ce ta riƙa ta sai suka nufi gurin tare Amal na gaba tana cigaba da leƙen fuskarta.
“Ummi hancinta dogo ne.. Kuma tana da manyan ido.. Fuskarta ma mai D ce”
Ummi ta riƙe baki tana kallon ikon Allah, gulmar mutun a gaban idonshi, wannan ƙulalaici ma Amal har ina!
Bayan ta saka lace ɗin ta fito sai duka suka fita suka barta da mai makeup ɗin, ta zauna saman kujera Mai Makeup ta fara mata fentin fuska amman mai ma'ana, bayan ta gama ta ɗaura mata ɗankwali. Ita kanta wacce ta yi mata kwaliyar sai da ta ɗauke ta a hoto saboda kyau da tayi. Three later Ummi da Fauza da Meesha da Amal suka dawo ɗakin
“Wowwwwwwwwwww”
Shine abunda duk suka faɗa ban da Ummi da ke murmushi. Ɗaukarta suka shiga yi hoto suna selfie. Farar Alkyaba Ummi ta ɗauko miƙawa mai Makeup ɗin ta saka mata. Sannan ta ɗauko fararen takalmi ta aje mata, sannan ta ɗauko akwatin turarenta ta buɗe sisters ɗin Abdool suka shiga fesa mata. Ummi da kanta ta kamo hannunta ta saka mata awarwaro, a ɗayan hannun kuma ta saka mata agogo.
Sannan ta miƙe tsaye, yayinda Namra take ƙasa risine ta saka mata sarka, sai ta miƙawa mai makeup ɗin ta manna mata ƴan kunne.
“To ku fita ku bamu guri”
Kamar umarni suke jira duk suka fita daga ɗakin aka bar Ummi daga ita sai Namra. Ummi ta kama hannayen Namra biyu ta riƙe.
“Ƴata ke tauraruwace, yanzu kin shigo cikin wani sabon shafi, ki haƙuri da duk abunda zaki ji, ba kowa ne zai faɗa miki magana ki mayar masa ba wanna ba tarbiya ba, ki zama mai riƙe sirrin mijinki da iyalansa, idan yayi miki ba dai-dai ba ki fara kawo ƙararsa a guna kamin ki kai ko ina.
Sannan yanzu zaku je gidan Mai Martaba ne wato mahaifin Abdallah, zaki gaishe da shi da iyalinsa, idan kin shiga a tsakiyar falon zaki zauna, karki raɓi kujera, idan kuma kika fito Amal zata ɗauki takalmin ta juyo miki da su ki saka, karki yarda idonki ya haɗu da na matan mai martaba balle ma mai martaba da kansa, karki yarda ki ci abunda za a baki za a miki kallon rashin kunya ko marar tarbiya.
Da misalin ƙarfe tara zaku fita gurin walimar cin abinci da Mai martaba ya shirya muku, Sai dai kamin kuje gurin walimar uwargidan Mai Martaba nasan zata nemi canja miki tufafi, zata aiko barorinta su canja miki kaya, karki yarda su canja miki komai, zan bawa Meesha da Fauza kayan da zaki canja anjima kuma kai makeup zata iso ƙarfe bakwai ta gyara miki fuska. Sai dai karki yarda lokacin Sallah yayi baki yi ba, Allah ya miki albarka”
“Na gode Mama na gode”
Ummi taɓshafa kanta tana murmushi sai ta miƙe tsaye ta fita. Bayan few minutes gwaggo da Maryam suka shigo suka riƙa Namra suka fita tare.
Mashallah shine abunda duk wanda ya kalli fuskar Namra da tufafinta yake faɗa.
Motar da Namra ta shiga daban ita kaɗai ake driving su kuma suka shiga wasu motocin.
Suna isa Faɗar Mai Martaba, aka ɗauki busa ana zuba musu kirari, sai barori suka sheƙo da gudu suna guda aka shimfiɗawa Namra carpet mai sunan Masarautar, sai wani ƙaton mutum cikin kayan dogarai yazo ya buɗewa Namra mota.
Hasbunallahu Namra ta karanta a zuciyarta sannan ta saka ƙafarta ta sauko daga cikin motar. Sai barorin suka rufa mata baya, wasu kuma suka wuce gurin tawagar da suka zo tare da Namra aka musu iso zuwa cikin gida.
Cike da hankali da natsuwa Namra take takawa barori suna take mata baya har suka isa gaban wata ƙatuwar ƙofa. Bakin ƙofar barorin suka tsaya sai Dogarai suka wangale mata ƙofar suka bakin ƙofar suna zuba mata kirari.
“shiga da ƙafar dama yar gidan girma, ƴar da tafi ko wace mace sa'ah a duniya, an gaishe ki gimbiya matar yarima, Allah ya ƙara miki lafiya da nisan kwana”
Kunna kai ta yi cikin faɗar, tana wuce carpet na farko ta cire takalminta saboda ta ga jerin takalmi a gurin. Wani irin maryaba da girma ta ji ya kamata musamman ta ta risina gaban mai martaba tana gaishe shi.
“Sarki ya amsa kuma ya gaishe ki”
Shine abunda mafadawan suke faɗi, sannan mai martaba yayi musu hannu suka tashi suka bar shi da Namra. Nasiha sosai yayi mata akan rayuwa da kuma zaman aure sai kuma kan haƙuri da iya kula da mutane.
Sai da Mai Martaba ya tabbatar Nasihar ta shiga jikinta sannan ya sallame dan ta shiga cikin gida ta gaishe da matansa.
ASIM POV.
Tun bayan da ya saka ƙarin aure a gabansa be waiwayi kowa ba, duk da da irin kuka da magiyar da Mardiya ta riƙa masa akan karka ya ƙara auren. Sai dai be ji ba sai da ya auro ƴar manyan mutane wato Balkisu.
An kashe dukiya sosai gurin auren daga duka ɓangarorin guda biyu, domin ko gidan da ya sakata mai tsada ne sosai.
Gida ne mai part biyu a ɗayan part ɗin ya saka Mardiya ta ƴar tabarmarta ta shinfiɗa saboda bata katifa kuma malamin da suka je gurinsa ya faɗa musu karta yarda ta saka katifa ko gado a gidan, abun shinfiɗa kawai zata je da shi sai kayan abinci.
Haka ta riƙa zama har tsawon wata tara duk wanda ya leƙa part ɗinta sai ya sha mamakin ganin babu komai a ciki, part ɗin Balkisu kam Aljannar duniya. Wannan matsalar ta damu Mardiya sosai har ta kai bata da wani sukuni a rayuwarta, ga mafarkin wutar da take bata daina ba, sau da dama zata zauna ta yi da kuka, wani lokaci kuma ko da tana cikin mutane zaka ganta ta koma wata iri kamar wacce aka ɗauki tunanin duniya aka ɗora mata. Ita da tayi aure dan jindaɗi abu ya zame mata ɗan zane, ta san matsalar daga gareta ne saboda yawan mafarkin wutar da take kuma gashi ita Balkisu wutar ba kama ta ko da sau ɗaya.
Ba ko wace ranar girkinta ba ne Asim yake kwana part ɗinta saboda bata da katifa balle kuma gado, sai a lokacin da yaji yana buƙatarta. Yau ma part ɗin Balkisu ya kwana, bayan yayi wanka ya shirya ya leƙo part ɗinta suka gaisa, duk ta yi wani zurun-zurun gwanin tausayi kamar marar lafiya, bayan sun gaisa ya dawo part ɗin Balkisu da yi mata sallama, sai ya samu tana tsaye jikin ƙofa tana jiranshi.
“Sai ina?”
Ta faɗa ta wani langaɓar da wuya tana kaɗa jiki, kamar wata tsohuwar karuwa.
Tana ganin Number Abdool ta yi dariya.
“Ango ango”
“Maryam ya gajiyar biki? Ina Amaryata? Na kira wayarta ta ƙi ta ɗaga ki ce ina gaidata kuma ki ɗaukar min pictures ɗinta”
“An gama ranka ya daɗe”
Ya sauke wayar tana dariya tare da amsa sallamar Gwaggo Ramatu.
“Ku fito ga motoci can an zo da su, Maryam ke kaɗai kin isa ni da Talatu zamu je sai a samu wasu cikin ƙannen Anty Amarya su biyu kuma suje tun da ance mutum biyar sun isa”
Raihanatu ta mike tsaye tana kare ɗankwali.
“Haba Baba Ramatu wane irin Maryam kuma ita da take da aure, ai ƙara dai ki ce ni ko zan samu ɗan saurayi da zai ɗauke cikin ƙannen Yarima”
Sai duk suka bushe da dariya Gwaggo Ramatu ta ce
“To shirya har ke aje da ke”
Motocin dake waje guda biyu sun kusan awa ɗaya sannan Namra ta fito tare da Gwaggo Ramatu da su Maryam da Raihanatu suka shiga motocin.
A tunaninsu za a wace ne gidan sarkin kai tsaye sai suka ga ya kai su gidan Ummi. Kunya sosai Namra ta samu kanta da ji lokacin da motar ta faka a bakin ƙofar shiga falon Ummi. Meesha da Fauza suka fito da wayoyinsu a hannu suka ɗaukarta video, Amal kuma ta zo da gudu ta rumgume ta.
Sam Amal bata gane wace Namra ba, sai dai ita Namra ta gane ta tun a wayar Abdool da take kallon hotunan family ɗin ƴan gidansu. Cike suka tarar da gidan da mutane tana saka ƙafarta cikin falon aka ɗauki guɗa. Ɗakin Ummi aka wuce da ita yayinda su Maryam da Gwaggo suka tsaya a waje a falo suna gaisawa da jama'ah dan basa iya tantance Ummi balle ma bata falon. Namra na shiga Ummi ta shigo sai ta yi saurin yin ƙasa tana gaishe da Ummi. Domin sarai ta san ita mahaifiyar Abdool ga kamanin Abdool nan xube a fuskarta kuma tana ganin ƴadda yake koɗa mahaifiyar ta shi a instagram. Da Murmushi Ummi ta zauna saman gado tana dafa Namra.
“Tashi Tashi Ƴata Allah yayi miki albarka”
Sai Namra ta ɗago sai dai bata yarda ta koma saman gadon ba sai ta zauna ƙasa fuskarka rufe da mayafinta.
Amal ce ta turo ƙofar ɗakin ta shigo cike da zumuɗin ita ƙanwar ango.
“Ummi kin ga fuskarta? Mu bata buɗe mana ba”
“Ai zata buɗe muku har sai kun gaji da ganinta”
“Ni dai ba zan iya haƙuri ba”
Ta faɗa a shagwaɓe. Ummi ta miƙe.tsaye tana gyaɗa kai ta nufi wata dorowa ta buɗe ta ɗauko wasu robobi guda huɗu ta dawo ta zauna.
“Ungo wannan shanye duka”
Hannu biyu Namra tasa ta karɓa ta kafa kai ta shanye abunda yake ciki tas sannan ta sake amsar na biyu ta shanye a na ukun ma shanyewa ta yi sai a huɗu ne Ummi tace karta shanye ta raga. A nan Amal ta samu damar ganin fuskarta har ta yi mata hoto da wayar Ummi.
Bayan Namra ta gama sha Ummi tasa Amal ta ɗauke robobin ta fitar, sai mai Makeup ta shigo da kit ɗinta ta yi zaman dishin a gaban Ummi tana miƙa mata gaisuwa.
Meesha ce ta shigo ɗakin ɗauke da wani koren lace ta aje saman gado.
“Ummi ga shi”
Ummi ta kalli Namra tana nuna mata wani ƙaramin ɗaki dake gefen bathroom ta ce
“Ƴata shiga can ki shirya da wannan kayan”
Meesha ce ta riƙa ta sai suka nufi gurin tare Amal na gaba tana cigaba da leƙen fuskarta.
“Ummi hancinta dogo ne.. Kuma tana da manyan ido.. Fuskarta ma mai D ce”
Ummi ta riƙe baki tana kallon ikon Allah, gulmar mutun a gaban idonshi, wannan ƙulalaici ma Amal har ina!
Bayan ta saka lace ɗin ta fito sai duka suka fita suka barta da mai makeup ɗin, ta zauna saman kujera Mai Makeup ta fara mata fentin fuska amman mai ma'ana, bayan ta gama ta ɗaura mata ɗankwali. Ita kanta wacce ta yi mata kwaliyar sai da ta ɗauke ta a hoto saboda kyau da tayi. Three later Ummi da Fauza da Meesha da Amal suka dawo ɗakin
“Wowwwwwwwwwww”
Shine abunda duk suka faɗa ban da Ummi da ke murmushi. Ɗaukarta suka shiga yi hoto suna selfie. Farar Alkyaba Ummi ta ɗauko miƙawa mai Makeup ɗin ta saka mata. Sannan ta ɗauko fararen takalmi ta aje mata, sannan ta ɗauko akwatin turarenta ta buɗe sisters ɗin Abdool suka shiga fesa mata. Ummi da kanta ta kamo hannunta ta saka mata awarwaro, a ɗayan hannun kuma ta saka mata agogo.
Sannan ta miƙe tsaye, yayinda Namra take ƙasa risine ta saka mata sarka, sai ta miƙawa mai makeup ɗin ta manna mata ƴan kunne.
“To ku fita ku bamu guri”
Kamar umarni suke jira duk suka fita daga ɗakin aka bar Ummi daga ita sai Namra. Ummi ta kama hannayen Namra biyu ta riƙe.
“Ƴata ke tauraruwace, yanzu kin shigo cikin wani sabon shafi, ki haƙuri da duk abunda zaki ji, ba kowa ne zai faɗa miki magana ki mayar masa ba wanna ba tarbiya ba, ki zama mai riƙe sirrin mijinki da iyalansa, idan yayi miki ba dai-dai ba ki fara kawo ƙararsa a guna kamin ki kai ko ina.
Sannan yanzu zaku je gidan Mai Martaba ne wato mahaifin Abdallah, zaki gaishe da shi da iyalinsa, idan kin shiga a tsakiyar falon zaki zauna, karki raɓi kujera, idan kuma kika fito Amal zata ɗauki takalmin ta juyo miki da su ki saka, karki yarda idonki ya haɗu da na matan mai martaba balle ma mai martaba da kansa, karki yarda ki ci abunda za a baki za a miki kallon rashin kunya ko marar tarbiya.
Da misalin ƙarfe tara zaku fita gurin walimar cin abinci da Mai martaba ya shirya muku, Sai dai kamin kuje gurin walimar uwargidan Mai Martaba nasan zata nemi canja miki tufafi, zata aiko barorinta su canja miki kaya, karki yarda su canja miki komai, zan bawa Meesha da Fauza kayan da zaki canja anjima kuma kai makeup zata iso ƙarfe bakwai ta gyara miki fuska. Sai dai karki yarda lokacin Sallah yayi baki yi ba, Allah ya miki albarka”
“Na gode Mama na gode”
Ummi taɓshafa kanta tana murmushi sai ta miƙe tsaye ta fita. Bayan few minutes gwaggo da Maryam suka shigo suka riƙa Namra suka fita tare.
Mashallah shine abunda duk wanda ya kalli fuskar Namra da tufafinta yake faɗa.
Motar da Namra ta shiga daban ita kaɗai ake driving su kuma suka shiga wasu motocin.
Suna isa Faɗar Mai Martaba, aka ɗauki busa ana zuba musu kirari, sai barori suka sheƙo da gudu suna guda aka shimfiɗawa Namra carpet mai sunan Masarautar, sai wani ƙaton mutum cikin kayan dogarai yazo ya buɗewa Namra mota.
Hasbunallahu Namra ta karanta a zuciyarta sannan ta saka ƙafarta ta sauko daga cikin motar. Sai barorin suka rufa mata baya, wasu kuma suka wuce gurin tawagar da suka zo tare da Namra aka musu iso zuwa cikin gida.
Cike da hankali da natsuwa Namra take takawa barori suna take mata baya har suka isa gaban wata ƙatuwar ƙofa. Bakin ƙofar barorin suka tsaya sai Dogarai suka wangale mata ƙofar suka bakin ƙofar suna zuba mata kirari.
“shiga da ƙafar dama yar gidan girma, ƴar da tafi ko wace mace sa'ah a duniya, an gaishe ki gimbiya matar yarima, Allah ya ƙara miki lafiya da nisan kwana”
Kunna kai ta yi cikin faɗar, tana wuce carpet na farko ta cire takalminta saboda ta ga jerin takalmi a gurin. Wani irin maryaba da girma ta ji ya kamata musamman ta ta risina gaban mai martaba tana gaishe shi.
“Sarki ya amsa kuma ya gaishe ki”
Shine abunda mafadawan suke faɗi, sannan mai martaba yayi musu hannu suka tashi suka bar shi da Namra. Nasiha sosai yayi mata akan rayuwa da kuma zaman aure sai kuma kan haƙuri da iya kula da mutane.
Sai da Mai Martaba ya tabbatar Nasihar ta shiga jikinta sannan ya sallame dan ta shiga cikin gida ta gaishe da matansa.
ASIM POV.
Tun bayan da ya saka ƙarin aure a gabansa be waiwayi kowa ba, duk da da irin kuka da magiyar da Mardiya ta riƙa masa akan karka ya ƙara auren. Sai dai be ji ba sai da ya auro ƴar manyan mutane wato Balkisu.
An kashe dukiya sosai gurin auren daga duka ɓangarorin guda biyu, domin ko gidan da ya sakata mai tsada ne sosai.
Gida ne mai part biyu a ɗayan part ɗin ya saka Mardiya ta ƴar tabarmarta ta shinfiɗa saboda bata katifa kuma malamin da suka je gurinsa ya faɗa musu karta yarda ta saka katifa ko gado a gidan, abun shinfiɗa kawai zata je da shi sai kayan abinci.
Haka ta riƙa zama har tsawon wata tara duk wanda ya leƙa part ɗinta sai ya sha mamakin ganin babu komai a ciki, part ɗin Balkisu kam Aljannar duniya. Wannan matsalar ta damu Mardiya sosai har ta kai bata da wani sukuni a rayuwarta, ga mafarkin wutar da take bata daina ba, sau da dama zata zauna ta yi da kuka, wani lokaci kuma ko da tana cikin mutane zaka ganta ta koma wata iri kamar wacce aka ɗauki tunanin duniya aka ɗora mata. Ita da tayi aure dan jindaɗi abu ya zame mata ɗan zane, ta san matsalar daga gareta ne saboda yawan mafarkin wutar da take kuma gashi ita Balkisu wutar ba kama ta ko da sau ɗaya.
Ba ko wace ranar girkinta ba ne Asim yake kwana part ɗinta saboda bata da katifa balle kuma gado, sai a lokacin da yaji yana buƙatarta. Yau ma part ɗin Balkisu ya kwana, bayan yayi wanka ya shirya ya leƙo part ɗinta suka gaisa, duk ta yi wani zurun-zurun gwanin tausayi kamar marar lafiya, bayan sun gaisa ya dawo part ɗin Balkisu da yi mata sallama, sai ya samu tana tsaye jikin ƙofa tana jiranshi.
“Sai ina?”
Ta faɗa ta wani langaɓar da wuya tana kaɗa jiki, kamar wata tsohuwar karuwa.