Sashe 149
Zagon Kasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta faɗa tana kallon sabuwar motar da aka buɗewa gate ta kunna kai a harabar gidan. A gurin da aka tanada dan faka motoci, aka nufa da motar kasancewarta mai baƙin gilashi baka iya hango wanda yake cikin motar. Ya ɗauki daƙiƙa goma sha biyar zuwa ashirin kamin ya fito daga cikin motar. Gaban Namra yayi mugun faɗuwa hango Abdool daya fito daga cikin motar sanye da farin yadi fuskarsa sai sheƙi take..
[7/18, 8:14 PM] Khadeeja Candy♥: *85*
Bayan Abdool ya fita Namra ta koma cikin falon Abbah, har lokacin tana jiyo shessehakar kukan Anty. Hannu ta kai ta tura ƙofar ɗakin Abbah ta tsaya daga bakin ƙofa tana hawaye. Bata san abunda Abbah yayi ba ko yace, sai dai tasan yadda ransa ya ɓace hakan nan dole sai wani abu ya faru.
Kallo ɗaya Abbah yayi mata ya ɗauke kai, ya zauna saman kujera yana kallon Anty Amarya.
“Dan Allah ki tashi ki ba ni guri ni bana son hayani”
Unƙurawa Anty ta yi ta tashi tana cigaba da kuka ta fito sai Namra ta riƙa ta suka nufi part ɗinta.
Saman kujera ta zauna tana kuka, Namra ta zauna kusa da ita ta kama hannunta ta riƙe.
“Anty mi Abbah yayi? Miyasa kuke kuka?”
“Yace Hajiya ta tafi ta bar masa gidansa, nayi nayi da shi amman ya ƙi, taya zai tura mace mai ƴaƴa da ƴawa kuma uwargidansa ya ce ta bar masa gida? Wannan sam be dace ba, komai ta aikata aiko ƙyaleta yayi ya barta da kunyarta, gaskiya dai ta riga ta bayyana babu abunda zata koma yi, amman yanzu ai ƴaƴanta ba za su ji daɗi ba”
“Ya sake ta ne?”
“Be sake ta amman ya ce da tafi duk inda zata je sai ya nemeta”
“Idan ya huce zai maida ta Anty, kowa dole ne yaji baƙinciki ace da matarsa za a haɗa kai a cuci iyalansa”
“Nasan abunda ta yi bata kyauta ba, amman ki duba ki ga halin da yaron nan yake wannan kawai ya isaahe ta ishara, ita sai ya zuba mata ido ko dan ƴaƴanta, wani lokacin mahaifinki yana rufe ido ya aikata abu kamar bai san kowa ba sai kansa”
“Zai dawo da ita, kawai ki bashi lokaci”
“Allah yasa”
“Amin. Abdallah ya zo”
Anty ta share hawayenta tana faɗin.
“Yaushe?”
“Yanzu ya tafi amman yace zai dawo”
“Na manta kin kaiwa Lamido abinci?”
Namra ta miƙe tsaye da sauri dan ita ta manta da shi gaba ɗaya.
Kitchen ta shiga ta haɗa masa fruits da drinks, ta dauƙa nufi waje. Zaune ta same shi cikin ɗakin hannunshi a bakinsa kamar mai nazari.
“Sorry mun cinye abincin rana amman yanzu xan girka maku wani”
Janye hannunsa yayi yana murmushi ya karɓi turen ya aje yana faɗin.
“Kin manta da direban ki saboda sahibin ki ya zo”
Wani kallo tayi masa mai cike da mamaki.
“Kai da Abdallah duk matsayin ku ɗaya a gare ni”
“Ba ɗaya ba ne, Shi ɗan masu kuɗi ne”
“Kai kuma ɗan talakawa”
“Shi ɗan sarauta ne”
“Kai kuma ɗan bayi”
“Yana da matsayi a zuciyarki”
“Kai kuma baka da shi. Na gode”
Tana miƙewa tsaye shi ma ta miƙe yana ƙokarin shan gabanta.
“Am sorry ban yi dan na ɓata ran ki ba, kawai ina ganin ba zan taɓa taka matsayin da Abdallah ya taka a zuciyarki ba ne, daga yau zan sauka a matsayin masoyinki, daga yau ni yayanki ne”
Ya faɗa cikin muryarsa marar daɗi, kallonsa kawai ta yi ta ɗauke kai, ta fice. Tana fitowa ta hango Abdool tsaye tare da Abbah suna magana, yadda Abbah yake watsar haƙora zaka rantse da Allah ba shi ya gama yi ma Hajiya Barau faɗa ba. Har zata wuce Abbah ya kira ta
“Mamana”
Sai ta ƙarasa gurin cikin ladabi.
“Ba ki ga ɗa na bane? Ko baki iya gaisuwa ba”
Ɗan risina tayi ta gaishe da Abdool suna haɗa ido ya kanne mata ido ɗaya ƴana murmushin gefen baki.
“Mun samu ku lafiya”
“Lafiya ƙalau”
“Je ki shirya zaki zaka shi wani guri”
Abbah ya faɗa, har ta buɗe baki ta yi magana sai kuma ta yi shiru ta amsa da to kawai ta nufi part ɗin Anty.
Ya kusan awa ɗaya yana jiranta sannan ta fito cikin ƙaton hijab, a lokacin Lamido na jikin window yana kallonsu, a front seat ta shiga sannan yayi ma motar key suka fita.
AMIRA POV.
Tun tana kuka hawaye na mata zuba har hawaye suka daina kukan kawai take ba hawaye. Gashi tun da suka dawo gida Mahaifinta be ce da ita uffan ba, Ammy xw kawai take bata magana.
Tashi ta yi ta nufi ɗakinta, tana shiga ta maida ƙofa ta rufe. Haƙiƙa ta yi rashin abubuwa da yawa, ta rasa mutuncinta ta rasa martabarta ta rasa wanda take so yanzu me ya rage mata?
Ta ci amanar ƙawarta dole ita taga ba daidai ba, tabbas hassada bata haifar mata da komai ba sai nadama da dana sani. Da ace tun farko bata hassadar Namra da bata yarda ta aikata abunda ya kai ta ga halaka ba, da ace ta zauna da ita da zuciya ɗaya da duk wannan be faru da ita ba.
Yanzu gashi daga ita har Uzair babu wanda yake cikin rayuwar jindaɗi, Allah ya jarrabeta da son Abdool idan ta tuna shi har ji take kamar zuciyarta zata rabe biyu.
Bugar ƙofar ɗakinta Ammy tayi dan tana tsoron kar ƴarta ta saje shiga cikin halin da ta shiga a baya, musamman yanzu da take ganin duniya ta juya mata baya.
“Amira an kira wayarki”
Miƙewa tayi tsaye taje ta buɗe ƙofar da idonta da suka kumbura sosai suka ƴi ja kamar an zuba mata barkono a ciki. Hannu Ammy ta kai ta shafa fuskarta.
“Amira karki sa ranki a damuwa, dan adam be isa ya wuce ƙaddararsa ba, Allah ya rubuto haka zai faru da ke babu yadda zaki yi, dan Allah kar zuciyarki ta sake tunanin guduwa ki bar mu”
“Idan ma na gudu ina zanje? Ko wace mace bata da daraja sai a gurare biyu, gidan iyayenta ko gidan mijinta, guduwa da na yi a wacan karon yasa na gane iyaye suna da muhimmanci sosai a rayuwa, rashin zaman mace a gaban iyayenta yana karyarda darajarta, wannan ne ya hana Abdool da family sa su kalle ni da daraja da ace ina a gidan iyayena xauna wata ƙila da zai iya aurena”
“Wanene Abdool kuma?”
“Shine mutumen da ya hana zuciya sukuni, Allah yayi min jarawata ta nan ne, ina son shi, shi kuma yana son wata”
Komawa ta yi ta zauna, Ammy ta zauna kusa da ita tana kallon ƴarta cike da damuwa. A nan Amira ta faɗawa Ammy komai a zaman da tayi da Abdool da kuma wanda ta yi kamin da haɗu da shi da yadda ta sadaukarda kanta gareshi.
“Kin sadaukarka da kanki gurin da bashi da amfani, kin salwantar da rayuwarki gurin da ba a san darajar rai ba, kin yi sadaukarwar da ba zaki taɓa cin ribarta ba, kin yi kuskuren da ba zaki iya gyarawa ba, kuma ina tsoron kar ɗaya daga cikin ƴaran mutumen nan ya farauci rayuwarki, kin yi kuakuren ba rin zuciyarki ta kamu da son mutum kamar wannan”
“Na sani, amman zuciya bata da laifi babu yadda ta iya, ina son sa Ammy amman shi baya so na, be san hallaci ba”
NAMRA POV..
Ta share hawayen da suka zubo mata cike da tausayin labarin da Abdool ya bata.
“Amman wannan yarinyar ta cancanci komai daga gareka, ya kamata kai ma ka yi mata hallaci, duk wanda ya sadaukarka da ranshi a gareka ya cancanci ko wane irin sakamako daga gareka, da yanzu ta mutu kai ka rayu”
Murmushi yayi yana cigaba da tuƙinsa hankalinsa kwance.
“Ashe ko na cancanci ko wane irin sakamako a daga gareki, dan na daɗe da salwantar da rai na akan ki”
“Kar zuciyarka ta raya maka abunda ba shi bane a Abdallah karka cuci kan ka ka cutar da yarinyar nan”
“Namra baki taɓa tambayar kan ki miyasa Abdool yake son ki ba? Baki taɓa wannan tunanin ba? Ko dan ban taɓa furta miki ina son ki ba?”
“Babu so agaban Namra a yanzu balle har ta yi tunanin dalilin na ka son, kar zuciyarka ta yaudareka a yanzu Abdool ban shiryawa irin wacan rayuwar ba”
“Ashe ke ba mumuna bace Namra, har yanzu kina da sauran cikon imani a zuciyarki tun da baki yarda da ƙaddara ba. Miyasa zuciyarki take ta nuna miki Asim kamar Abdool yake, dan me kike tunanin irin rayuwar da kikayi a gidan Asim irinta zaki yi a gidan Abdool? Mahaifiyata bata da buri a yanzu wanda ya wuce na maganar aurena da ke, ina da ayukan yi da yawa Namra amman na danne su na tako garin nan saboda ke kawai”
Hannu ya kai ya canja fm zuwa wata sannan ya ce
“Wata kila zuciyarki wani take so ba ni ba, na lura Lamido na da matsayi a zuciyarki sama da ni”
Kalamansa da fakin ɗinsa sun rikita ta a lokaci ɗaya, ya faɗa mata abunda yau ma Lamido ya faɗa mata, dan me suke ƙoƙarin saka ta cikin matsalar da bata daɗe da fita ba?
“Miya kawo mu nan?”
A fili ta tambaya tana kallonsa, ba tare daya kalleta ba ya sauke wayar kunnensa yace
“Zaku gaisa da yarinyar ne”
“Nan gidan su Amira ne”
“Ita ma yarinyar sunanta Amira”
Kamin ta ƙara wata magana sai ga Amira ta fito da gudu daga cikin gidan ta nufo motarsu. Buɗe motar Abdool yayi ya fita sai tazo gabansa ta durƙusa ta riƙe ƙafafunsa ta tada kanta sama ta kalleshi. Shi ma kallonta yake kamin ya janye ƙafafunsa ya nuna mata front seat. Bata fahimci mi yake nufi ba, ta shiga ko kuma ta buɗe ta gani, sai dai bata tambayeshi ba ta tashi tsaye ta nufi motar ta buɗe. Ganin Namra yasa ta murmushi da hawaye a lokaci ɗaya.
“Itace?”
“Itace”
Ya amsa mata kai tsaye. Sai ta ƙara faɗaɗa murmiahinta.
[7/18, 8:14 PM] Khadeeja Candy♥: *85*
Bayan Abdool ya fita Namra ta koma cikin falon Abbah, har lokacin tana jiyo shessehakar kukan Anty. Hannu ta kai ta tura ƙofar ɗakin Abbah ta tsaya daga bakin ƙofa tana hawaye. Bata san abunda Abbah yayi ba ko yace, sai dai tasan yadda ransa ya ɓace hakan nan dole sai wani abu ya faru.
Kallo ɗaya Abbah yayi mata ya ɗauke kai, ya zauna saman kujera yana kallon Anty Amarya.
“Dan Allah ki tashi ki ba ni guri ni bana son hayani”
Unƙurawa Anty ta yi ta tashi tana cigaba da kuka ta fito sai Namra ta riƙa ta suka nufi part ɗinta.
Saman kujera ta zauna tana kuka, Namra ta zauna kusa da ita ta kama hannunta ta riƙe.
“Anty mi Abbah yayi? Miyasa kuke kuka?”
“Yace Hajiya ta tafi ta bar masa gidansa, nayi nayi da shi amman ya ƙi, taya zai tura mace mai ƴaƴa da ƴawa kuma uwargidansa ya ce ta bar masa gida? Wannan sam be dace ba, komai ta aikata aiko ƙyaleta yayi ya barta da kunyarta, gaskiya dai ta riga ta bayyana babu abunda zata koma yi, amman yanzu ai ƴaƴanta ba za su ji daɗi ba”
“Ya sake ta ne?”
“Be sake ta amman ya ce da tafi duk inda zata je sai ya nemeta”
“Idan ya huce zai maida ta Anty, kowa dole ne yaji baƙinciki ace da matarsa za a haɗa kai a cuci iyalansa”
“Nasan abunda ta yi bata kyauta ba, amman ki duba ki ga halin da yaron nan yake wannan kawai ya isaahe ta ishara, ita sai ya zuba mata ido ko dan ƴaƴanta, wani lokacin mahaifinki yana rufe ido ya aikata abu kamar bai san kowa ba sai kansa”
“Zai dawo da ita, kawai ki bashi lokaci”
“Allah yasa”
“Amin. Abdallah ya zo”
Anty ta share hawayenta tana faɗin.
“Yaushe?”
“Yanzu ya tafi amman yace zai dawo”
“Na manta kin kaiwa Lamido abinci?”
Namra ta miƙe tsaye da sauri dan ita ta manta da shi gaba ɗaya.
Kitchen ta shiga ta haɗa masa fruits da drinks, ta dauƙa nufi waje. Zaune ta same shi cikin ɗakin hannunshi a bakinsa kamar mai nazari.
“Sorry mun cinye abincin rana amman yanzu xan girka maku wani”
Janye hannunsa yayi yana murmushi ya karɓi turen ya aje yana faɗin.
“Kin manta da direban ki saboda sahibin ki ya zo”
Wani kallo tayi masa mai cike da mamaki.
“Kai da Abdallah duk matsayin ku ɗaya a gare ni”
“Ba ɗaya ba ne, Shi ɗan masu kuɗi ne”
“Kai kuma ɗan talakawa”
“Shi ɗan sarauta ne”
“Kai kuma ɗan bayi”
“Yana da matsayi a zuciyarki”
“Kai kuma baka da shi. Na gode”
Tana miƙewa tsaye shi ma ta miƙe yana ƙokarin shan gabanta.
“Am sorry ban yi dan na ɓata ran ki ba, kawai ina ganin ba zan taɓa taka matsayin da Abdallah ya taka a zuciyarki ba ne, daga yau zan sauka a matsayin masoyinki, daga yau ni yayanki ne”
Ya faɗa cikin muryarsa marar daɗi, kallonsa kawai ta yi ta ɗauke kai, ta fice. Tana fitowa ta hango Abdool tsaye tare da Abbah suna magana, yadda Abbah yake watsar haƙora zaka rantse da Allah ba shi ya gama yi ma Hajiya Barau faɗa ba. Har zata wuce Abbah ya kira ta
“Mamana”
Sai ta ƙarasa gurin cikin ladabi.
“Ba ki ga ɗa na bane? Ko baki iya gaisuwa ba”
Ɗan risina tayi ta gaishe da Abdool suna haɗa ido ya kanne mata ido ɗaya ƴana murmushin gefen baki.
“Mun samu ku lafiya”
“Lafiya ƙalau”
“Je ki shirya zaki zaka shi wani guri”
Abbah ya faɗa, har ta buɗe baki ta yi magana sai kuma ta yi shiru ta amsa da to kawai ta nufi part ɗin Anty.
Ya kusan awa ɗaya yana jiranta sannan ta fito cikin ƙaton hijab, a lokacin Lamido na jikin window yana kallonsu, a front seat ta shiga sannan yayi ma motar key suka fita.
AMIRA POV.
Tun tana kuka hawaye na mata zuba har hawaye suka daina kukan kawai take ba hawaye. Gashi tun da suka dawo gida Mahaifinta be ce da ita uffan ba, Ammy xw kawai take bata magana.
Tashi ta yi ta nufi ɗakinta, tana shiga ta maida ƙofa ta rufe. Haƙiƙa ta yi rashin abubuwa da yawa, ta rasa mutuncinta ta rasa martabarta ta rasa wanda take so yanzu me ya rage mata?
Ta ci amanar ƙawarta dole ita taga ba daidai ba, tabbas hassada bata haifar mata da komai ba sai nadama da dana sani. Da ace tun farko bata hassadar Namra da bata yarda ta aikata abunda ya kai ta ga halaka ba, da ace ta zauna da ita da zuciya ɗaya da duk wannan be faru da ita ba.
Yanzu gashi daga ita har Uzair babu wanda yake cikin rayuwar jindaɗi, Allah ya jarrabeta da son Abdool idan ta tuna shi har ji take kamar zuciyarta zata rabe biyu.
Bugar ƙofar ɗakinta Ammy tayi dan tana tsoron kar ƴarta ta saje shiga cikin halin da ta shiga a baya, musamman yanzu da take ganin duniya ta juya mata baya.
“Amira an kira wayarki”
Miƙewa tayi tsaye taje ta buɗe ƙofar da idonta da suka kumbura sosai suka ƴi ja kamar an zuba mata barkono a ciki. Hannu Ammy ta kai ta shafa fuskarta.
“Amira karki sa ranki a damuwa, dan adam be isa ya wuce ƙaddararsa ba, Allah ya rubuto haka zai faru da ke babu yadda zaki yi, dan Allah kar zuciyarki ta sake tunanin guduwa ki bar mu”
“Idan ma na gudu ina zanje? Ko wace mace bata da daraja sai a gurare biyu, gidan iyayenta ko gidan mijinta, guduwa da na yi a wacan karon yasa na gane iyaye suna da muhimmanci sosai a rayuwa, rashin zaman mace a gaban iyayenta yana karyarda darajarta, wannan ne ya hana Abdool da family sa su kalle ni da daraja da ace ina a gidan iyayena xauna wata ƙila da zai iya aurena”
“Wanene Abdool kuma?”
“Shine mutumen da ya hana zuciya sukuni, Allah yayi min jarawata ta nan ne, ina son shi, shi kuma yana son wata”
Komawa ta yi ta zauna, Ammy ta zauna kusa da ita tana kallon ƴarta cike da damuwa. A nan Amira ta faɗawa Ammy komai a zaman da tayi da Abdool da kuma wanda ta yi kamin da haɗu da shi da yadda ta sadaukarda kanta gareshi.
“Kin sadaukarka da kanki gurin da bashi da amfani, kin salwantar da rayuwarki gurin da ba a san darajar rai ba, kin yi sadaukarwar da ba zaki taɓa cin ribarta ba, kin yi kuskuren da ba zaki iya gyarawa ba, kuma ina tsoron kar ɗaya daga cikin ƴaran mutumen nan ya farauci rayuwarki, kin yi kuakuren ba rin zuciyarki ta kamu da son mutum kamar wannan”
“Na sani, amman zuciya bata da laifi babu yadda ta iya, ina son sa Ammy amman shi baya so na, be san hallaci ba”
NAMRA POV..
Ta share hawayen da suka zubo mata cike da tausayin labarin da Abdool ya bata.
“Amman wannan yarinyar ta cancanci komai daga gareka, ya kamata kai ma ka yi mata hallaci, duk wanda ya sadaukarka da ranshi a gareka ya cancanci ko wane irin sakamako daga gareka, da yanzu ta mutu kai ka rayu”
Murmushi yayi yana cigaba da tuƙinsa hankalinsa kwance.
“Ashe ko na cancanci ko wane irin sakamako a daga gareki, dan na daɗe da salwantar da rai na akan ki”
“Kar zuciyarka ta raya maka abunda ba shi bane a Abdallah karka cuci kan ka ka cutar da yarinyar nan”
“Namra baki taɓa tambayar kan ki miyasa Abdool yake son ki ba? Baki taɓa wannan tunanin ba? Ko dan ban taɓa furta miki ina son ki ba?”
“Babu so agaban Namra a yanzu balle har ta yi tunanin dalilin na ka son, kar zuciyarka ta yaudareka a yanzu Abdool ban shiryawa irin wacan rayuwar ba”
“Ashe ke ba mumuna bace Namra, har yanzu kina da sauran cikon imani a zuciyarki tun da baki yarda da ƙaddara ba. Miyasa zuciyarki take ta nuna miki Asim kamar Abdool yake, dan me kike tunanin irin rayuwar da kikayi a gidan Asim irinta zaki yi a gidan Abdool? Mahaifiyata bata da buri a yanzu wanda ya wuce na maganar aurena da ke, ina da ayukan yi da yawa Namra amman na danne su na tako garin nan saboda ke kawai”
Hannu ya kai ya canja fm zuwa wata sannan ya ce
“Wata kila zuciyarki wani take so ba ni ba, na lura Lamido na da matsayi a zuciyarki sama da ni”
Kalamansa da fakin ɗinsa sun rikita ta a lokaci ɗaya, ya faɗa mata abunda yau ma Lamido ya faɗa mata, dan me suke ƙoƙarin saka ta cikin matsalar da bata daɗe da fita ba?
“Miya kawo mu nan?”
A fili ta tambaya tana kallonsa, ba tare daya kalleta ba ya sauke wayar kunnensa yace
“Zaku gaisa da yarinyar ne”
“Nan gidan su Amira ne”
“Ita ma yarinyar sunanta Amira”
Kamin ta ƙara wata magana sai ga Amira ta fito da gudu daga cikin gidan ta nufo motarsu. Buɗe motar Abdool yayi ya fita sai tazo gabansa ta durƙusa ta riƙe ƙafafunsa ta tada kanta sama ta kalleshi. Shi ma kallonta yake kamin ya janye ƙafafunsa ya nuna mata front seat. Bata fahimci mi yake nufi ba, ta shiga ko kuma ta buɗe ta gani, sai dai bata tambayeshi ba ta tashi tsaye ta nufi motar ta buɗe. Ganin Namra yasa ta murmushi da hawaye a lokaci ɗaya.
“Itace?”
“Itace”
Ya amsa mata kai tsaye. Sai ta ƙara faɗaɗa murmiahinta.