← Book details Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 99 OF 160

Sashe 99

Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayan duk angaggaisa dady yayi bayani sosai tare da fad'a masu cewa shi yana ganin atuntub'i magabatansa kawai aji ba'asi idan har abunda yafad'a ta tabbata shikenan sai anemi maslaha aciki, idan zasu sa yadawo ya d'auki matarsa da d'ansa sukoma tacan qasar tareni walillahil hamd, idan kuma sawaqe mata zaiyi shikenan, anan umma takafe kai da qasa tace bata amince da hakan ba, Babu yanda za'ayi su iskesu bayan su yakamata ace sunyi hakan, kuma koma meye suna sane amma suka share saboda basa qaunarta don haka ita kawai aje kotu araba auren faqat shi yafi sauqi, don ita dama bata shirya sake rabuwa da 'yarta ba akaro na biyu. Nan fa rigima takucce tsakaninta da dady tafad'i yafad'i saboda yanda tad'au zafi, anan Dr yacewa umma a musulunce bazai yuyu araba auren ba har sai in akwai magabatansa aciki sunsan da maganar don haka tayi haquri aje can d'in, nanma kasa fahimtarsa tayi had'e da fashewa da kuka tana fad'in, bazasu fahimci yanda abun yake ba don ALLAH subar mata 'yarta,

Hakan yasa Rashida da tun d'azu batace komai ba ta d'aga kai tana kallon yanda mahaifiyarta take kuka tacewa dady don ALLAH indai donta zasuje kada sutafi, tafiso abar zancen domin zuwan nasu ba lallaine yayi wani amfaniba tunda baza'a iya tirsasashi dawoba, aslalima yariga daya fad'awa duniya cewa baisan komai ba game da ahalinsa da iyayensa to meye amfanin cewa sai angamsar da duniya cewa yana dasu tahanyar tirsasa masa abunda bayada muradi ko qoqarin cewa sai anje kotu domin araba auren, Saida tashare qwalla sannan taci gaba da cewa ita tana ganin yin hakan zai iya zama qalu bale agaresa ga wud'anda basu san gaskiyar al'amari ba tunda shi yanzu yazama wani shahararre da aka sani awannan lokacin, za'a iyayin amfani da wannan damar ayi qoqarin tab'a mutuncin d'ansu kuma masu sheganta mata shi su samu qwarin guiwa da wata damar cigaba da walaqantasa had'e da tozartasa, koba komai ita yanzu batada wani sauran buri akansa amma akwai mafarkai da dama da d'anta kedasu akansa don ALLAH kada hakan yazamo mafarin rushewarsu.

Murmushi dady yayi irin nasu na manya domin gaba d'aya kalamanta sun gama bayyanar da cewa har yanzu akwai sauran soyayyar mijinta aranta, koma meye b'acin rai yasa takasa iya jure abunda yayi kuma yagamsu da maganganunta saboda tarin hujjojin da keciki, dama shi babban burinsa amincewar yarinyar amma tunda tabuqaci ayi hakan shikenan ALLAH yasanya alkhairi, nan yanuna mata cewa shikenan baza'aje ba matuqar hakn zai faranta mata rai sannan suka koma gida.

Akan sa'insar da umma tayi dashi saida yayi kwana biyu yana fushi da ita duk da bawai har azuciyarsa bane, kawai yayine don yanuna mata kuskurenta kuma tabashi haquri suka daidaita, tun lokacin dady ya d'auki alwashin saka Nuraddeen acikin addu'o'in sa akan ALLAH ya yaye masa abunda ke kansa ya dawo da hankalinsa ga iyalinsa kodon tarin d'imbin qaunar da take yimasa.

••• ••• •••
Yaya hawwa kuwa kullum cikin addu'a take da kuka ALLAH yadawo mata da d'anta agareta, kullum cikin kiran sunansa take tana istigfari akn abunda ta aikata, baya da haka bata aikin komai sai kuka, abinci ma sai Inna Bilkisu tayi da gaske takeci, tsananin rad'ad'in da takeji akan rashin d'anta har ji take yana neman sa lumfashinta ya d'auke, sai yanzu takejin rashin kyautawarta nasa a salwantar da rayuwar 'yar mutane ashe haka akejin zafi alokacin da aka raba iyaye da d'ansu ko masoyi da masoyinsa, tayi dana sani sosai tare da nadamar abunda ta aikata.

Baffa ma gaba d'aya yamiqa lamurransa ga ALLAH yanaci gaba da addu'a ALLAH ya karkato masa da hankalin yaronsa izuwa garesa yadawo gida, don shima yasamu labarin firar da akayi dashi da abunda yace, Wanda hakn yasashi komawa can wajen shuwa gabannin da suka turasu yace sutaimaka abashi lambar da zai iya samun d'ansa yana son magana dashi, ai kuwa cikin sa'a saiga wani daga cikin wud'anda sukayi karatu yanada contact dashi Nuraddeen d'in aka samu lambarsa a hannunsa donsu cewa sukayi basada ita,

Cike da farinciki baffa ya amshi lambar wayar yaje da ita yasa kud'i masu yawa yawa yakirasa,

Tajima tana ringin kafin ad'aga cikin wata iriyar miskilalliyar murya aka amsa sallamar, muryar da Nuraddeen dake kwance yaji tasashi miqewa zaune yana qoqarin tunano wani abun amma yakasa, shikuwa Baffa sai fad'in yake Nuraddeen meyake faruwa dakai?, Kana lafiya?, Kayi magana mana idan kaine, meyasa zaka zab'i yin bauta awata qasar bayan qasarka data taimaka maka?, shin I tarbiyarka tatafine har ka I manatawa damu iyayenka?, don ALLAH kadawo hakanan kaga mahaifiyarka kuma kayi qoqarin gano inda matarka take, jikina nafad'a mani cewa tana raye aduk inda take, sarawa kansa ya shigayi yana son tunano muryar amma hakan tafaskara saboda wani juyawa da ciwo da kansa keyi, cikin qarfin hali yace, bab..kafin ya qarasa yasaki wata irin qara tare da buga wayar ajikin bango ta watse saidai baffa yaji tayi d'if, yanata faman hello hello daga nan bai qara jinsa ba yasake kiran lambar yafi aqirga amma sai yajita akashe hakan yasa yahaqura yaci gaba da yimasa addu'a kuma yana qoqarin sake gwada kiran lambar akoda yaushe amma kashe

A b'angaren Nuraddeen kuwa nan take alokacin ciwon kai mai tsanani ya rufesa yadafe kan da hannuwa yanata juye juye daga tsayen da yake cikin d'akin saiga wani abokinsa d'an can qasar yazo gidan, shiya taimaka masa ya d'aukesa yayi asibiti dashi, bayan ya farfad'o yafara qoqarin tunano abunda yafaru da muryar da har lokacin sautin amonta yakeji akunnuwansa amma yakasa tunowa, hakan yasa da kansa yasa akayi masa allurar bacci don da kansa yanzu yafara rage shan barasar da yakeyi gaba d'aya, tun daga lokacin yakasa komawa yanda yake saboda qarar sautin baffa dake damunsa a kunnuwa wanda yaja gaba d'aya yanzu bayason abunda zai had'asa da waya balle d'aga kira daga ko Ina, hakn yasama gaba d'aya bai komabi takan wayar tasa data tarwatseba.

••• ••• •••
Haka rayuwa taci gaba da tafiya har zuwa lokacin da little yagama secondary, sau da dama yakan so yayi zancen mahaifinsa da mahaifiyar tasa amma idan yatuna yanayin da take shiga nadamuwa akan haka da alqawarin da yayi mata na bazai koma yimata zancensa ba sai yafasa, ana qoqarin nema masa makarantar da zaici gaba da ita wato jami'a yahad'u da wata kyakkyawar yarinya da ALLAH ya jarabceta da mugun sonsa Mai suna *BATOOL*, 'yace ga yayan mahaifiyar hajia nafeesa dake can garin kano wato mahaifar iyayensa, sun had'une sanadiyar hutun da take zuwa nan gidan dady wajen 'yar uwar tata da take matsayin abokiyar wasanta, tunda ALLAH yad'ora idanuwanta akansa taji duk duniya babu wanda takeso sama dashi, wani irin so takeyi masa da batasan iya adadinsa ba wanda hakan yahaifar mata da yawan zuwa hutu garin saboda shi, tun tana b'oye son da take yimasa har takasa haqura ta bayyana masa, aranar kwana yayi yana juye juye don bako shakka bazai yi qarya ba shima yana sonta, saidai tunani matsayinta ga wacce duk duniya babu macen daya tsana sama da ita saboda yanda take amfani da halshenta wajen cutar dashi da mahaifiyarsa harma da kakarsa yasa yakejin bazai iya soyayya da itaba don gudun kada allura ta tono masa bakin galma...

*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎

_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*

_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋

_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞

*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖

*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️

Page___73💎

Ganin abun zai zame masa damuwa yasa ya miqe yaje ya d'auro arwala ya fara nafilfili yana mai addu'ar ALLAH kazab'a masa abun duk da yafi zama alkhairai arayuwarsa.

Tun daga lokacin yad'an fara d'ad'd'aurewa batool fuska duk da kuwa tarin d'imbin soyayyar da yake yimata atunaninsa hakan shine mafita amma ako yaushe soyayyarta sai qara nitso takeyi acikin zuciyarsa, musamman yanda yaga tana faman bibiyarsa, sannu ahankali batare daya ankara ba yafara bata damar da bai tab'a tsammani ba azuciyarsa, gashi tuni angama shire shiren wucewarsa jami'a wato BUK dake nan cikin kano inda Dr nura ya cikashe masa fannin computer science bisa shawarar mahaifiyarsa da Fatima a lokacin yanada shekaru ashirin da d'aya aduniya, wasa wasa shaquwa mai tsanani tashiga tsakaninsa da batool da sati d'aya yarage mata takoma gida can kano don hutunsu yaqare.

Tunda umma tafahimci alaqar dake tsakanin little da batool ta zaunar dashi tanuna masa cewa yafita hanyar yarinyar kodon su tsira da mutuncinsu tunda yasan Babu wata jituwa tsakaninsu da ita Kuma yasan koba komai yanzu karatune agabansa ba zancen aure ba don haka ya fad'ama yarinyar gaskiya, amma da yake yariga ya kurb'i giyar soyayya duk da qananun shekarunsa sai yanuna mata cewa shifa yana sonta kuma itama tana sonsa don haka shi baidamu da duk abunda hajia nafeesa zatayi ba domin yariga da tunfarko kafin sufara soyayya yaba ALLAH zab'i akan yazab'a masa duk abunda yafi zama alkahiri tsakaninsa da batool, don haka tunda har yaji ALLAH naqara samasa sonta kuma har suka fara soyayya to yatabbata akwai alkhairi tsakaninsu kuma babu abunda hajia nafeesa zata iya sai abunda ALLAH yaso, duk iya qoqarin da tayi wajen lurar dashi qin fahimta yayi don haka saita sanar da mahaifiyarsa tun kan abu yayi nisa.
Chapter 99 · 0% Book details