Sashe 56
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tunsu Dr na rarrashinta har sungaji sun dangana, Fatima kuwa duk da haka haka take tasata agaba tasa tayi mata wankan jego duk da dai ba irin na al'ada take yimataba saboda matsalar hawan jinin da tayi fama dashi amma dai takan sa tayi wanka da ruwa masu d'imi sosai da taimakonta, kuma tana tirsasata taci abinci maikyau sosai saboda yaron yasamu isashhin ruwan nono duk da yanzu saidai a matsa mashi nonon a fida saboda gaba d'aya likitoci basa bari aganshi, ganin yanda su Dr suka damu da yanayin da take ciki yasa tarage nuna damuwarta agabansu amma idan tana itad'ai batada wani aikin daya wuce kuka da tunani.
Tashin hankalin da suke ciki na rashin lafiyar yaron yasa gaba d'aya su Dr suka manta da batun tambayar ko ita waye balle har su nemi maida ita wajen iyayenta, sun ajiye wannan har sai lokacin da yaron yasamu lafiya ita kuma tasamu natsuwar da zata basu cikakken labarinta da kuma dalilin daya rabota da gida...
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[8/17, 10:19] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___42💎
Ganin yanda hankalin Rashida yatashi sosai akan rashin lafiyar jaririnta yasa Dr nura yanke shawarar d'aukesa daga wannan asibitin zuwa federal hospital dake nan cikin garin borno saboda sunada qwararrin likitoci sosai, kasancewar duk irin aikin da yakeyine kuma akwai sanayya sosai tsakaninsa da likitocin yasa babu wata wahala aka basu takardar transfer izuwa federal hospital d'in.
Nana take suka fara yimasa sabbin gwaje gwajen saboda gano haqiqanin abunda ke damunsa, yanayin yanda yaron keshan wahala tamkar ransa zai fita ya matuqar tayarwa da likitocin hankali don koda akazo dashi asibitin lumfashinsa nafitane da taimakon oxygen d'in da aka ska masa, tsawon sati biyu sukayi a asibitin Amma al'amarin jaririn jiya iyau kuma sun kasa gane takamammiyar matsalar yaron don ko motsi yadena yi lumfashinsa kawai ne kefita, tun Rashida nakuka had'e da tsammanin tashinsa har takai ga cire rai, gaba d'aya yanzu ta dangana tare da cire ran yaronta zai tashi, kullum addu'arta d'aya ALLAH ya sassauta masa zafin ciwo saboda bayada alhakin kowa inba nata na haihuwar da tayi masa ba, ita kuma tayafe masa duniya da lahira, ahalin yanzu tafison idan ba Mai tsawon rai bane ALLAH ya karb'i abunsa da gaggawa akan wannan wahalar da yake sha, ta saki jikinta sosai tamaida al-amarin gaba d'aya ga ALLAH, asibitin ma tadena zuwa Fatima ce ke zuwa sai kuma Dr nura, kullum tana zaunenta gida tana ragema Fatima aikace aikace da girki ita da sabuwar mai aikin da Fatima tasamu, iyakarta idan ana buqatar nono ta tatsawa yaron a fida taci gaba da al-amurranta, tanajin damuwar amma dole ta tirsasawa kanta fidda ita saboda batasan tsarin da ALLAH yayi mata akan yaron ba, idan abunnya taso mata saita zauna ta kwatanta soyayyar da takeyiwa mahaifinsa amma ALLAH ya tsaro rabiwarsu duk da dai ako yaushe tana fatar sake had'uwa dashi nan kusa ba nesa ba,
Yau tunda safe ta tashi cikin wani irin kad'aici da shauqin son ganin habibynta ab'angare d'aya kuwa tausayin halin da yake cikine kwance azuciyarta, zaunawa tayi tayi kukanta mai isarta kafin tamiqe da sauri taje toilet ta wanko fuskarta jin motsin Dr nura da Fatima naqoqarin fitowa daga part d'insa zuwa nata zasuje asibiti, cikin jin kunya take takowa izuwa inda suke kanta sunkuye a qasa,
"A'a maman baby muna qoqarin qarasowa inda kike sai gashi munyi karo dake, hop kin tashi lafiya." Fatima tafad'a had'e da qarasowa tarungumota ajiki,
"Lafiya klw aunty Ina kwana?"
"Lafiya klw ya qarfin jikin naki?"
"Alhamdulillah, Ina kwana uncle." Rashida tafad'a had'e da d'ago kai tana kallonsa.
Murmushi yayi had'e da d'agowa daga dannar wayar da yakeyi kafin yace. "Lafiya klw Rashida kin tashi lafiya?"
"Lafiya klw uncle." Shiru yabiyo bayan gaisuwar taau kafin ya kad'a wayarsa a aljihunsa nagaba yana cewa.
"Yadai?, Rashida ko akwai wata matsala?"
"Eh uncle." Tafad'a hawaye na zubo mata daga cikin idanuwa,
"Subhanallahi! To kuzo mu koma ciki" yafad'a tare da nufar falon dake cikin sashen nasa, da sauri tace.
"A'a uncle tunda fita zakuyi kubari idan kundawo zamuyi magana."
"Ina ai bazai yuyu ba, dama sayayyar kayanki dana baby ne nake son muje daga nan sai muwuce asibiti, Amma yanzu kawai mubar zancen sayayyar har zuwa gobe, kuzo mushiga daga ciki." Hannunta Fatima takamo had'e dasa d'ayan hannunta tana goge mata hawayen dake kwance afuskarta, murmushin qarfin hali tayi mata tana mamakin cewa wai zasuje yomata sayayyar kaya ita da jaririnta, yaron da ba'ada tabbacin zai rayu kuma bayan haka satin daya wuce fa suka sassayo mata kayan sawarta daau hijabi da takalma da ita har yaron to idan ba b'arnar kud'i ba meye nacewa yanzu kuma zasu je sawo masu wasu kayan?,
Har suka isa falonsa Rashida batasan sun isoba tanacan tana jefama kanta tambayoyin da batada amsarsu,
"Zauna." Taji Fatima tafad'a tana qoqarin zaunar da ita akan kujera, kafin itama tanemi waje kusa da Dr tazauna.
Cire madubin idonsa yayi ya ajiye agefe sannan ya shafa fuskarsa yana fad'in. "Ina jinki Rashida meke faruwa."
Tajima tana wasa da yatsun hannuwanta kafin can tasamu tace. "Dama Ina son sanar daku ko wacece ni, saboda Ina son nakoma hannun iyayena da kuma mijina, kuyi haquri bana Rena irin taimakonda kulawar da kuka bani bane, kawai Ina aunayanayin da suke acikine, wanda jikina nabani cewa akwai matsala atare dasu, kamar yanda kuka sani sunana Rashida, ni haifaffiyar kano ce, nikad'ai nake ga iyayena, banida wa ko ya banida qane ko qanwa, muna zaune awani qauye da ake kira yarimawa, nayi aure da mijina dake tsananin sona awani gari da ake cema bebeji saidai nahad'u da matsalar rashin so da qauna daga uwar mijina, qarara tanunawa duniya bata sona bata qaunata, bansan cikakken dalilinta nayin haka ba inba kasancewata bare acikinsu ba, ko kad'an bata qaunata ita da wasu danginsa wanda adalilin hakanne suka nemi salwantar mani da rayuwa har nafad'a ayanayin da kuka tsinceni, namatuqar tsorata da al-amarinta wanda har nakai bana son tuna garin da duk wani abu daya shafesa, bana fata ko burin daidai da rana d'aya yarona ya kusanci koda inuwar garince saboda tsoron kada shima acutar mani dashi ko anemi salwantar mani da rayuwarsa, amma d'imbin soyayyar da nakewa mahaifinsa bazata barni nayi hakan ba, tsananin qaunar iyayena bazata barni in Amin da zuciyata dake raya mani innesanta dasu ba, naroqeku da kusake taimaka mani akaro na biyu ku hannuntani awajensu, inada yaqini akan dukkaninsu basa cikin kwanciyar hankali da walwala akan b'atarnan tawa, nasan kunyi mani abubuwa da yawa da bazan biyaku ba Amma zanso kusake taimakona awannan karon don Allah."
Taqarasa maganar had'e da duqewa gabansu tahad'a hannuwa tana kuka, duk da dai a dunqule tabasu labarin hakan bai hanasu fahimtar matsalar tata daga wajen mahaifiyar mijinta bane, ita tayi mata wannan aikin da Babu ko shakka asirine amma sai ALLAH ya kubutar da ita, d'agota Fatima tayi idanuwanta cike tab da hawaye tace.
"Kiyi haquri Rashida in Sha ALLAH sai ALLAH ya isar maki akan zaluntarki da akayi, tacutar dake tahanyar rabakinda masoyinki wanda afarko na munana masa zato, sannan ta rab'a iyayenki dake tajefasu cikin tashin hankali, in Sha ALLAH, saita tozarta kamar yanda ta tozarta soyayyar dake tsakaninki da mijinki. Kiyi shiru ki kwantar da hankalinki zamu maidaki agaban iyayenki amma don ALLAH kiyi haquri har yaronki ya samu lafiya, ahaka babu inda za'a iya tafiya dashi don haka mubar zancen komawarki har mugaabunda ALLAH zaiyi kinji."
Tafad'a tana d'an bubbuga kafad'arta.
Dr. Nura kuwa d'aukar glass d'in idonsa yasa sannan yace.
"An zalunceki matuqa amma kiyi haquri hakan na rubuce ne a cikin qundin qaddarar rayuwarki, ALLAH yakan jarabci mumini don ya gwada imaninsa, in Sha ALLAH komai zai daidaita, Amma kamar yanda Fatima tace, a matsayinki na uwa kitausayawa yaronki har zuwa lokacin da zai samu sauqi ni kuma zanjena shaidawa iyayenki da mijinki cewa kina hannuna cikin qoshin lafiya saboda hankalinsu ya kwanta kinji ko?"
"Shikenan uncle duk yanda kuka ce, nagode sosai, ALLAH ya saka maku da alkhairi ya arzuttaku da 'ya'yaye masu albaka."
"Amin mman baby don ALLAH kiyi haquri ki kwantar da hankalinki, SANNU SANNU Bata hana zuwa...in ALLAH yaso yaronki zai tashi kuma ki koma hannun iyayenki lafiya."
Fatima tafad'a tana cirota daga duqen da take, yayinda al'ajabin hali irin na Yaya hawwa yasa Dr yakasa motsawa daga inda yake zaune, Anya kuwamatar nan nada imani da zata I salwantar da rayuwar d'anta a irin wannan yanayi na tsohon cikin da suka ganta?, Anya kuwa ita tahaifesa da batayi tunanin halin da zai iya shigaba ta rabasa da jininsa da kuma matarsa da yake matuqar qauna?.
Wud'annan tambayoyin yashiga jerowa kansa yana mai ALLAH yawadarai da iyaye masu tunani da kuma hali irin nata.
••• ••• •••
A b'angaren su Yaya hawwa kuwa tuni aka saki muneera bayan ta amsa masu dukkanin tambayoyin dasukayi mata Wanda ac suka sake samun haske akan bincikensu, sun fahimci batada wani laifi ko sa hannu a b'atan Rashida don haka randa suka cikasati d'aya da kamawa aka saki muneera, tsalle da farinciki ba'a magana awajenta, da zata tafi takalli blessin wacce itace tayi mata mummunan duka kafin afara yimata tambayoyin tace.
"Mai kaki baki jiba." Juyowa blessing tayi fuskarta sake tana fad'in. "Maneera ya akayi?karkaji komai kaje ka sira?" Dashe baki muneera tayi tana susar kanta yadda kukasan maiqeya fuska duk tabi ta kumbure, ijiyarta d'aya tarufe saboda matsanancin dukan da tasha ga lab'b'anta sunyi sutu sutu kamar anjika ganda tace
Tashin hankalin da suke ciki na rashin lafiyar yaron yasa gaba d'aya su Dr suka manta da batun tambayar ko ita waye balle har su nemi maida ita wajen iyayenta, sun ajiye wannan har sai lokacin da yaron yasamu lafiya ita kuma tasamu natsuwar da zata basu cikakken labarinta da kuma dalilin daya rabota da gida...
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[8/17, 10:19] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___42💎
Ganin yanda hankalin Rashida yatashi sosai akan rashin lafiyar jaririnta yasa Dr nura yanke shawarar d'aukesa daga wannan asibitin zuwa federal hospital dake nan cikin garin borno saboda sunada qwararrin likitoci sosai, kasancewar duk irin aikin da yakeyine kuma akwai sanayya sosai tsakaninsa da likitocin yasa babu wata wahala aka basu takardar transfer izuwa federal hospital d'in.
Nana take suka fara yimasa sabbin gwaje gwajen saboda gano haqiqanin abunda ke damunsa, yanayin yanda yaron keshan wahala tamkar ransa zai fita ya matuqar tayarwa da likitocin hankali don koda akazo dashi asibitin lumfashinsa nafitane da taimakon oxygen d'in da aka ska masa, tsawon sati biyu sukayi a asibitin Amma al'amarin jaririn jiya iyau kuma sun kasa gane takamammiyar matsalar yaron don ko motsi yadena yi lumfashinsa kawai ne kefita, tun Rashida nakuka had'e da tsammanin tashinsa har takai ga cire rai, gaba d'aya yanzu ta dangana tare da cire ran yaronta zai tashi, kullum addu'arta d'aya ALLAH ya sassauta masa zafin ciwo saboda bayada alhakin kowa inba nata na haihuwar da tayi masa ba, ita kuma tayafe masa duniya da lahira, ahalin yanzu tafison idan ba Mai tsawon rai bane ALLAH ya karb'i abunsa da gaggawa akan wannan wahalar da yake sha, ta saki jikinta sosai tamaida al-amarin gaba d'aya ga ALLAH, asibitin ma tadena zuwa Fatima ce ke zuwa sai kuma Dr nura, kullum tana zaunenta gida tana ragema Fatima aikace aikace da girki ita da sabuwar mai aikin da Fatima tasamu, iyakarta idan ana buqatar nono ta tatsawa yaron a fida taci gaba da al-amurranta, tanajin damuwar amma dole ta tirsasawa kanta fidda ita saboda batasan tsarin da ALLAH yayi mata akan yaron ba, idan abunnya taso mata saita zauna ta kwatanta soyayyar da takeyiwa mahaifinsa amma ALLAH ya tsaro rabiwarsu duk da dai ako yaushe tana fatar sake had'uwa dashi nan kusa ba nesa ba,
Yau tunda safe ta tashi cikin wani irin kad'aici da shauqin son ganin habibynta ab'angare d'aya kuwa tausayin halin da yake cikine kwance azuciyarta, zaunawa tayi tayi kukanta mai isarta kafin tamiqe da sauri taje toilet ta wanko fuskarta jin motsin Dr nura da Fatima naqoqarin fitowa daga part d'insa zuwa nata zasuje asibiti, cikin jin kunya take takowa izuwa inda suke kanta sunkuye a qasa,
"A'a maman baby muna qoqarin qarasowa inda kike sai gashi munyi karo dake, hop kin tashi lafiya." Fatima tafad'a had'e da qarasowa tarungumota ajiki,
"Lafiya klw aunty Ina kwana?"
"Lafiya klw ya qarfin jikin naki?"
"Alhamdulillah, Ina kwana uncle." Rashida tafad'a had'e da d'ago kai tana kallonsa.
Murmushi yayi had'e da d'agowa daga dannar wayar da yakeyi kafin yace. "Lafiya klw Rashida kin tashi lafiya?"
"Lafiya klw uncle." Shiru yabiyo bayan gaisuwar taau kafin ya kad'a wayarsa a aljihunsa nagaba yana cewa.
"Yadai?, Rashida ko akwai wata matsala?"
"Eh uncle." Tafad'a hawaye na zubo mata daga cikin idanuwa,
"Subhanallahi! To kuzo mu koma ciki" yafad'a tare da nufar falon dake cikin sashen nasa, da sauri tace.
"A'a uncle tunda fita zakuyi kubari idan kundawo zamuyi magana."
"Ina ai bazai yuyu ba, dama sayayyar kayanki dana baby ne nake son muje daga nan sai muwuce asibiti, Amma yanzu kawai mubar zancen sayayyar har zuwa gobe, kuzo mushiga daga ciki." Hannunta Fatima takamo had'e dasa d'ayan hannunta tana goge mata hawayen dake kwance afuskarta, murmushin qarfin hali tayi mata tana mamakin cewa wai zasuje yomata sayayyar kaya ita da jaririnta, yaron da ba'ada tabbacin zai rayu kuma bayan haka satin daya wuce fa suka sassayo mata kayan sawarta daau hijabi da takalma da ita har yaron to idan ba b'arnar kud'i ba meye nacewa yanzu kuma zasu je sawo masu wasu kayan?,
Har suka isa falonsa Rashida batasan sun isoba tanacan tana jefama kanta tambayoyin da batada amsarsu,
"Zauna." Taji Fatima tafad'a tana qoqarin zaunar da ita akan kujera, kafin itama tanemi waje kusa da Dr tazauna.
Cire madubin idonsa yayi ya ajiye agefe sannan ya shafa fuskarsa yana fad'in. "Ina jinki Rashida meke faruwa."
Tajima tana wasa da yatsun hannuwanta kafin can tasamu tace. "Dama Ina son sanar daku ko wacece ni, saboda Ina son nakoma hannun iyayena da kuma mijina, kuyi haquri bana Rena irin taimakonda kulawar da kuka bani bane, kawai Ina aunayanayin da suke acikine, wanda jikina nabani cewa akwai matsala atare dasu, kamar yanda kuka sani sunana Rashida, ni haifaffiyar kano ce, nikad'ai nake ga iyayena, banida wa ko ya banida qane ko qanwa, muna zaune awani qauye da ake kira yarimawa, nayi aure da mijina dake tsananin sona awani gari da ake cema bebeji saidai nahad'u da matsalar rashin so da qauna daga uwar mijina, qarara tanunawa duniya bata sona bata qaunata, bansan cikakken dalilinta nayin haka ba inba kasancewata bare acikinsu ba, ko kad'an bata qaunata ita da wasu danginsa wanda adalilin hakanne suka nemi salwantar mani da rayuwa har nafad'a ayanayin da kuka tsinceni, namatuqar tsorata da al-amarinta wanda har nakai bana son tuna garin da duk wani abu daya shafesa, bana fata ko burin daidai da rana d'aya yarona ya kusanci koda inuwar garince saboda tsoron kada shima acutar mani dashi ko anemi salwantar mani da rayuwarsa, amma d'imbin soyayyar da nakewa mahaifinsa bazata barni nayi hakan ba, tsananin qaunar iyayena bazata barni in Amin da zuciyata dake raya mani innesanta dasu ba, naroqeku da kusake taimaka mani akaro na biyu ku hannuntani awajensu, inada yaqini akan dukkaninsu basa cikin kwanciyar hankali da walwala akan b'atarnan tawa, nasan kunyi mani abubuwa da yawa da bazan biyaku ba Amma zanso kusake taimakona awannan karon don Allah."
Taqarasa maganar had'e da duqewa gabansu tahad'a hannuwa tana kuka, duk da dai a dunqule tabasu labarin hakan bai hanasu fahimtar matsalar tata daga wajen mahaifiyar mijinta bane, ita tayi mata wannan aikin da Babu ko shakka asirine amma sai ALLAH ya kubutar da ita, d'agota Fatima tayi idanuwanta cike tab da hawaye tace.
"Kiyi haquri Rashida in Sha ALLAH sai ALLAH ya isar maki akan zaluntarki da akayi, tacutar dake tahanyar rabakinda masoyinki wanda afarko na munana masa zato, sannan ta rab'a iyayenki dake tajefasu cikin tashin hankali, in Sha ALLAH, saita tozarta kamar yanda ta tozarta soyayyar dake tsakaninki da mijinki. Kiyi shiru ki kwantar da hankalinki zamu maidaki agaban iyayenki amma don ALLAH kiyi haquri har yaronki ya samu lafiya, ahaka babu inda za'a iya tafiya dashi don haka mubar zancen komawarki har mugaabunda ALLAH zaiyi kinji."
Tafad'a tana d'an bubbuga kafad'arta.
Dr. Nura kuwa d'aukar glass d'in idonsa yasa sannan yace.
"An zalunceki matuqa amma kiyi haquri hakan na rubuce ne a cikin qundin qaddarar rayuwarki, ALLAH yakan jarabci mumini don ya gwada imaninsa, in Sha ALLAH komai zai daidaita, Amma kamar yanda Fatima tace, a matsayinki na uwa kitausayawa yaronki har zuwa lokacin da zai samu sauqi ni kuma zanjena shaidawa iyayenki da mijinki cewa kina hannuna cikin qoshin lafiya saboda hankalinsu ya kwanta kinji ko?"
"Shikenan uncle duk yanda kuka ce, nagode sosai, ALLAH ya saka maku da alkhairi ya arzuttaku da 'ya'yaye masu albaka."
"Amin mman baby don ALLAH kiyi haquri ki kwantar da hankalinki, SANNU SANNU Bata hana zuwa...in ALLAH yaso yaronki zai tashi kuma ki koma hannun iyayenki lafiya."
Fatima tafad'a tana cirota daga duqen da take, yayinda al'ajabin hali irin na Yaya hawwa yasa Dr yakasa motsawa daga inda yake zaune, Anya kuwamatar nan nada imani da zata I salwantar da rayuwar d'anta a irin wannan yanayi na tsohon cikin da suka ganta?, Anya kuwa ita tahaifesa da batayi tunanin halin da zai iya shigaba ta rabasa da jininsa da kuma matarsa da yake matuqar qauna?.
Wud'annan tambayoyin yashiga jerowa kansa yana mai ALLAH yawadarai da iyaye masu tunani da kuma hali irin nata.
••• ••• •••
A b'angaren su Yaya hawwa kuwa tuni aka saki muneera bayan ta amsa masu dukkanin tambayoyin dasukayi mata Wanda ac suka sake samun haske akan bincikensu, sun fahimci batada wani laifi ko sa hannu a b'atan Rashida don haka randa suka cikasati d'aya da kamawa aka saki muneera, tsalle da farinciki ba'a magana awajenta, da zata tafi takalli blessin wacce itace tayi mata mummunan duka kafin afara yimata tambayoyin tace.
"Mai kaki baki jiba." Juyowa blessing tayi fuskarta sake tana fad'in. "Maneera ya akayi?karkaji komai kaje ka sira?" Dashe baki muneera tayi tana susar kanta yadda kukasan maiqeya fuska duk tabi ta kumbure, ijiyarta d'aya tarufe saboda matsanancin dukan da tasha ga lab'b'anta sunyi sutu sutu kamar anjika ganda tace