Sashe 70
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Basu suka gyara ba sai kusan qarfe d'aya na rana saboda wasu 'yan abubuwa da Nuraddeen ya tsayayi, shidai Nuraddeen sai binta yakeyi da kallo yana jimamin abunda zata riska idan sunje, Saida yayi mata nasiha sosai akan rayuwa da kuma muhimmancin yadda da qaddara mai kyau ko marar kyau, sannan ya tabbatar mata da cewa sauran maganin little Nuraddeen na cikon wata d'aya daya rage in Sha ALLAH zai karb'a sai ya kaimata idan lokacin yayi tana tayi masa godiya harda 'yar qwallarta, haka ma Fatima tayi mata godiya sosai suka rungume juna kafin suwuce su d'auki hanyar zuwa kano tana murna tana qarawa.
••• ••• •••
A b'angaren su umma kuwa Saida suka kwashe kwana uku suna yawo acikin borno kafin baba yagano Wanda yake nema, haka suke buge yini suna yawon tambayarsa in kuma dare yayi sai suje asibiti su shige cikin majinyata su kwanta da safe kuma su sake fita nemansa har ALLAH yasa suka ganesa, hannu biyu mutumen ya karb'esu bayan baba yayi masa bayanin dalilinsu na zuwa garin saida, sosi ya jajanta masa tare da yimasa addu'ar ALLAH ya bayyana masa inda 'yarsa take, nan yabasu wajen da zasu zauna acikin gidansa acan baya inda d'akunan masu aikin gidan suke sannan yace suyi haquri zai sama masu abunyi nan da kwana biyu, bayan kwana biyu ya tambayi baba in zai iya zaman tsaron wani sabon shagonsa daya bud'e zai dinga biyansa albashi duk wata dubu goma idan ya amince bisa amana da Kuma yardar daya yimasa, nan take ya amince har yana duqawa had'e da yimasa godiya, ita kuma umma d'aya daga cikin matan alhajin taroqa ta dinga yimata aiki duk wata zata biyata dubu hud'u, daga alhajin har baba basuso hakan ba amma nan take umma ta amince da zatayi aikin, acewarta hakan zai d'an d'auke mata hankali da ace tayi zaune ita kad'ai bata komai sai aikin tunanin b'atan 'yarta. Babu yanda suka iya tunda ta amsa zatayi, ajiyar zuciya alhajin yayi kafin ya kalli matar tasa bayan sun wuce yace.
"Hajia nafeesa don ALLAH kada kiyiwa baiwar ALLAHn nan abunda kika saba yiwa sauran masu aikinki, mutanene masu kirki da daraja agarena don haka kada kiwatsamun qasa tahanyar tozartar dasu don suna aiki aqarqashinki, zamane zamuyi dasu nad'an wani lokaci kafin su koma inda suka fito, saboda haka Ina roqonki daki mutuntasu don girman ALLAH kinji ko."
Saida ta yatsina fuska sannan ta mere baki had'e da kallon gefe tace.
"Naji.."
Hajiya nafeesa itace matarsa ta biyu, matada kirki ko kad'an ga son walaqanta mutane matuqar suka amsa sunan talauci atttare dasu kuma suka zamo qarqashinta, shiyasa yaja mata kunne tun kafin aje ko Ina saboda shi mutumne mai dattako, yau itace rana ta uku da umma tafara aiki a sashenta, Babu ruwanta da shiga sha'aninta iya karta tayi abunda tasata ta koma sashenta, kamar kullum yau umma tagama gyaggyara kitchen bayan aikin da tayi saiga baqi hajia nafeesa tayi, sai da aka kwashi mintuna uku sannan ta d'ibi ruwa da lemuna ta kaimasu a falo tare da russunawa ta gaishesu sannan ta koma kitchen, sake kirawota tayi had'e da cewa.
"Umma jeki ki kawo masu fruit"
Saida taje kitchen tabud'e fridge d'in taga babu komai sun qare sannan tadawo taduqa tare da cewa.
"Hajia ba'a samu kawo wasu ba, Kuma naciki sun qare."
Batare da hajia nafeesa ta damuba taje d'aki tad'auko dubu uku tadawo falon tare da jefowa umma kud'in tace.
"Jeki kicewa driver nace ya kaikai inda aka siyo mana kisawomun, kiyi sauri Ina jira yanzu yanzu kinji ko."
"To hajia." umma tafad'a tare da d'aukar kud'in tabar falon.
Tafe suke ita da drivern har suka kai daidai wajen da zata siyo fruit d'in yayi parking acan gefen titin yana nuna mata tsallake inda suke yace
"Umma ki tsallaka acan kice daga gidan alhaji aka turoki, zasu had'a maku duk abunda suka san ana buqata."
"To"
Umma ta and masa tare da bud'e marfin motar tafito tana waige waigen gefe gefe don tasamu ta tsallaka.
A daidai lokacin motarsu Dr nura tazo wucewa yana sauri ganin har qarfe d'aya na rana yayi saboda bayason suyi dare ahanya gashi ko cikin garin basu fita ba......
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___53💎
Umma na tsallakowa a dai dai tsakiyar titin Dr. Nura na kawowa da sauri ya sakar mata oda yana qoqarin juya starring nasa wanda kad'an ya rage ya bugeta, daga Fatima har Rashida runtse idanuwa sukayi had'e da dafe kai suna fad'in. "Innalillahi wa'inna ilaihirrajiuun."
Ita kuma umma tsabar tsoro duqewa wajen tayi jikinta na rawa, gefe yayi parking had'e da fitowa ganin takasa motsawa daga duqen da take a tsakiyar titin ya nufi wajenta. Kafin ya isa har drivern da sukazo tare yazo ya jayeta ya nufi wajen motar yana masifa da ita,
"Umma kar kizo ki jazamun bala'i, duka duka yau kwanana uku da d'auka aiki agidannan kizo kisa akoreni, fisabillahi idan kinsan bazaki iya tsallakawa ba ai saiki fad'amun, gashi yanzu da kinja mani fitina." Maganar yakeyi kamar zai doketa saboda tsananin takaici, ganin babu abunda yasamu matar yasa Dr nura juyawa yakoma wajen motarsa yana girgiza kai had'e da fad'in ALLAH ya sawaqe, kallon Fatima yayi dake faman jijjiga little Nuraddeen dake kuka saboda tsoron qararsu da yaji ta tadashi daga baccin da yakeyi yace
"Bari na tsallaka nabawa matar can haquri duk da dai naga bataji ciwo ba."
"Haba saurifa mukeyi, tunda ALLAH ya kare kuma ba laifinka bane kawai mutafi ALLAH ya tsare gaba."
"Amin ya amsa yana qoqarin bud'e marfin motar ya shiga sai yaga drivern ya iso wajen masu fruit d'in, fasa shiga yayi ya nufi wajensa ya bashi hannu suka gaisa sannan ya amsa gaisuwar da masu fruit d'in keyi masa dake nuna sun sanshi,
"Amm..don ALLAH kabawa matar can da muka kusan samun tsotsayi da ita haquri, sauri nakeyi amma tunda ALLAH ya tsare naga dacewar nayi maka magana tunda tare kuke kabata haquri."
"Babu komai ranka ya dad'e, ALLAH ya tsare gaba kuma ya kaiku lafiya."
"Amin." Yafad'a tare da miqa masa hannu suka sake gaisawa sanna ya juya yashiga motar ya tayar suka kama hanya shi kuma drivern ya amshi fruits d'in ya tsallaka inda ya ajiye motar tasu, ta glass Dr nura ke kallonsa lokacin daya biyo bayansa don yayi utorn yace da Fatima.
"Matar wai kinsan wani abun, ashema motar gidace, sai yanzu na hango lambar dady dake jiki, kingasu nan sun biyo bayan mu."
"Allah sarki, to ko waye waccan matar?, Inaga dai sabon drive ne dady ya samu, Amma shima bayada mutunci, don me sunzo a mota bazai iya tsallakawa yayi parking acan ba sai dai ya tsaya acan tsallake kuma ya turo matar mutane a wannan babban titi hakan shi bazai iya fitowa ba sai ita."
"Iskanci samarin yanzune, Amma zanyi magana da dad a dinga tsawatar dasu akan tsofaffin mutane, inaga d'aya daga cikin masu aikine hajiya nafeesa ta turo kinsan halinta."
"Zata iya yuyuwa gaskiya, ALLAH ya kyauta." A daidai lokacin da suka tsaya a bakin junction suna jiran traffic tabasu hannu drivern yazo saiti dasu Dr nura ya juyo ya kallesa yana fad'in.
"Kin gashi ko?" Fatima tajuya ta kalli drivern daya qore sautin kid'an motar yana kad'a kai, dai dai lokacin itama rashida ta d'ago kai ta gefenta tana kallon motar da taji suna fira akai, motace mai kyan gaske don zata iya cewa takusa kyn ta Dr.nura ko kuma suzo d'ai, matar dake ciki tajuyar da kanta can gefe take kallo da jikinta yabata kmar ta santa kota tab'a ganinta awani wajen amma rashin juyo fuskarta da tayi yasa takasa tantance haka, tan wannan tunanin ne little Nuraddeen ya tsanyara kukan da ya maido hankalinta agaresa tare da qoqarin turasa cikin mayafinta don tabashi nono, a lokacin ita kuma umma tajuyo fuskarta ta b'angaren tana qarewa yanayin kyawon garin da yanda motocin suka tsaitsaya suna jiran abasu hannu suwuce amma kasancewar glass d'in motar tasu Dr nura tinted ne yasa takasa hango 'yar tata dake ciki tana kicaniyar bawa little Nuraddeen har traffic d'in tabasu hannu, jin motarsu tafara tafiya yasa Rashida d'agowa tare da maida kallonta wajen amma sai taga wayam tuni har motar tajuya ta d'ayan hannun takoma baya sukuma suka miqe hanyarsu tabarin cikin garin.
••• ••• •••
Baffa ya matuqar tsorata da abunda yaji inspector najida tace Nuraddeen ya aikata, sukayita bata haquri shida baffa, daqyar suka samu tabasu belinsa saboda yanda ranta ya matuqar b'aci kafin tace.
"Baba kaja masa kunne don idan ya sake maimaita hakan zamu kaishi a hukuntashi ne saboda babban laifine civilian yasa hannu ya bugi kowane irin kaki, don haka kajamasa kunne, kawai na qyalesa ne albarkacinka daya sai mun ganar dashi kuskurensa"
"To 'yata nagode nagode sosai."
Kallon Nuraddeen da duk yafita hayyacinsa yayi had'e da cewa "tashi muje."
"Babu inda zanje baffa matuqar innarmu na wannan wajen." Nuraddeen yabashi amsa had'e da d'agowa yana kallonsa da ijiyarsa da aka bubbuge ta kumbure.
Cike da mamaki suka bishi da kallo kafin baffa Usman yace. "Haba Nuraddeen, kayi haquri, zamu d'auke mahaifiyarka anan amma kasan komai sai anshirya, kabi komai ahankali insha ALLAH zamu fidda ita nan kuma zata samu lafiya, yanzu haka muna tattaunawa akan maganar ne inspector najida ta kirawomu, kayi haquri ka taso muje kaji ko."
"Baffa bazan iya ba." Yafad'a tare da miqewa zai koma cikin cell d'in baffa ya bishi da kallo, saurin dakatar dashi baffa Usman yayi had'e da cewa.
"Dawo Nuraddeen za'a fiddo da ita kaji!"
Baffa zaiyi magana baffa Usman ya dakatar dashi had'e da cewa "a'a ya kabarshi, inspector najida ya za'ayi kubamu ita." Baffa Usman ya qarasa maganar yana kallonta.
"Bayada matsala baba, dama Bata qarqashin kulawarmu don haka zaku iya zuwa ku d'auketa ko yaushe, Amma d'aukarta akwai had'ari sosai saboda yanayin da take ciki bai kamata ace an d'auketa ankaita cikin mutane ba, wannan kawai shine matsalar."
••• ••• •••
A b'angaren su umma kuwa Saida suka kwashe kwana uku suna yawo acikin borno kafin baba yagano Wanda yake nema, haka suke buge yini suna yawon tambayarsa in kuma dare yayi sai suje asibiti su shige cikin majinyata su kwanta da safe kuma su sake fita nemansa har ALLAH yasa suka ganesa, hannu biyu mutumen ya karb'esu bayan baba yayi masa bayanin dalilinsu na zuwa garin saida, sosi ya jajanta masa tare da yimasa addu'ar ALLAH ya bayyana masa inda 'yarsa take, nan yabasu wajen da zasu zauna acikin gidansa acan baya inda d'akunan masu aikin gidan suke sannan yace suyi haquri zai sama masu abunyi nan da kwana biyu, bayan kwana biyu ya tambayi baba in zai iya zaman tsaron wani sabon shagonsa daya bud'e zai dinga biyansa albashi duk wata dubu goma idan ya amince bisa amana da Kuma yardar daya yimasa, nan take ya amince har yana duqawa had'e da yimasa godiya, ita kuma umma d'aya daga cikin matan alhajin taroqa ta dinga yimata aiki duk wata zata biyata dubu hud'u, daga alhajin har baba basuso hakan ba amma nan take umma ta amince da zatayi aikin, acewarta hakan zai d'an d'auke mata hankali da ace tayi zaune ita kad'ai bata komai sai aikin tunanin b'atan 'yarta. Babu yanda suka iya tunda ta amsa zatayi, ajiyar zuciya alhajin yayi kafin ya kalli matar tasa bayan sun wuce yace.
"Hajia nafeesa don ALLAH kada kiyiwa baiwar ALLAHn nan abunda kika saba yiwa sauran masu aikinki, mutanene masu kirki da daraja agarena don haka kada kiwatsamun qasa tahanyar tozartar dasu don suna aiki aqarqashinki, zamane zamuyi dasu nad'an wani lokaci kafin su koma inda suka fito, saboda haka Ina roqonki daki mutuntasu don girman ALLAH kinji ko."
Saida ta yatsina fuska sannan ta mere baki had'e da kallon gefe tace.
"Naji.."
Hajiya nafeesa itace matarsa ta biyu, matada kirki ko kad'an ga son walaqanta mutane matuqar suka amsa sunan talauci atttare dasu kuma suka zamo qarqashinta, shiyasa yaja mata kunne tun kafin aje ko Ina saboda shi mutumne mai dattako, yau itace rana ta uku da umma tafara aiki a sashenta, Babu ruwanta da shiga sha'aninta iya karta tayi abunda tasata ta koma sashenta, kamar kullum yau umma tagama gyaggyara kitchen bayan aikin da tayi saiga baqi hajia nafeesa tayi, sai da aka kwashi mintuna uku sannan ta d'ibi ruwa da lemuna ta kaimasu a falo tare da russunawa ta gaishesu sannan ta koma kitchen, sake kirawota tayi had'e da cewa.
"Umma jeki ki kawo masu fruit"
Saida taje kitchen tabud'e fridge d'in taga babu komai sun qare sannan tadawo taduqa tare da cewa.
"Hajia ba'a samu kawo wasu ba, Kuma naciki sun qare."
Batare da hajia nafeesa ta damuba taje d'aki tad'auko dubu uku tadawo falon tare da jefowa umma kud'in tace.
"Jeki kicewa driver nace ya kaikai inda aka siyo mana kisawomun, kiyi sauri Ina jira yanzu yanzu kinji ko."
"To hajia." umma tafad'a tare da d'aukar kud'in tabar falon.
Tafe suke ita da drivern har suka kai daidai wajen da zata siyo fruit d'in yayi parking acan gefen titin yana nuna mata tsallake inda suke yace
"Umma ki tsallaka acan kice daga gidan alhaji aka turoki, zasu had'a maku duk abunda suka san ana buqata."
"To"
Umma ta and masa tare da bud'e marfin motar tafito tana waige waigen gefe gefe don tasamu ta tsallaka.
A daidai lokacin motarsu Dr nura tazo wucewa yana sauri ganin har qarfe d'aya na rana yayi saboda bayason suyi dare ahanya gashi ko cikin garin basu fita ba......
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___53💎
Umma na tsallakowa a dai dai tsakiyar titin Dr. Nura na kawowa da sauri ya sakar mata oda yana qoqarin juya starring nasa wanda kad'an ya rage ya bugeta, daga Fatima har Rashida runtse idanuwa sukayi had'e da dafe kai suna fad'in. "Innalillahi wa'inna ilaihirrajiuun."
Ita kuma umma tsabar tsoro duqewa wajen tayi jikinta na rawa, gefe yayi parking had'e da fitowa ganin takasa motsawa daga duqen da take a tsakiyar titin ya nufi wajenta. Kafin ya isa har drivern da sukazo tare yazo ya jayeta ya nufi wajen motar yana masifa da ita,
"Umma kar kizo ki jazamun bala'i, duka duka yau kwanana uku da d'auka aiki agidannan kizo kisa akoreni, fisabillahi idan kinsan bazaki iya tsallakawa ba ai saiki fad'amun, gashi yanzu da kinja mani fitina." Maganar yakeyi kamar zai doketa saboda tsananin takaici, ganin babu abunda yasamu matar yasa Dr nura juyawa yakoma wajen motarsa yana girgiza kai had'e da fad'in ALLAH ya sawaqe, kallon Fatima yayi dake faman jijjiga little Nuraddeen dake kuka saboda tsoron qararsu da yaji ta tadashi daga baccin da yakeyi yace
"Bari na tsallaka nabawa matar can haquri duk da dai naga bataji ciwo ba."
"Haba saurifa mukeyi, tunda ALLAH ya kare kuma ba laifinka bane kawai mutafi ALLAH ya tsare gaba."
"Amin ya amsa yana qoqarin bud'e marfin motar ya shiga sai yaga drivern ya iso wajen masu fruit d'in, fasa shiga yayi ya nufi wajensa ya bashi hannu suka gaisa sannan ya amsa gaisuwar da masu fruit d'in keyi masa dake nuna sun sanshi,
"Amm..don ALLAH kabawa matar can da muka kusan samun tsotsayi da ita haquri, sauri nakeyi amma tunda ALLAH ya tsare naga dacewar nayi maka magana tunda tare kuke kabata haquri."
"Babu komai ranka ya dad'e, ALLAH ya tsare gaba kuma ya kaiku lafiya."
"Amin." Yafad'a tare da miqa masa hannu suka sake gaisawa sanna ya juya yashiga motar ya tayar suka kama hanya shi kuma drivern ya amshi fruits d'in ya tsallaka inda ya ajiye motar tasu, ta glass Dr nura ke kallonsa lokacin daya biyo bayansa don yayi utorn yace da Fatima.
"Matar wai kinsan wani abun, ashema motar gidace, sai yanzu na hango lambar dady dake jiki, kingasu nan sun biyo bayan mu."
"Allah sarki, to ko waye waccan matar?, Inaga dai sabon drive ne dady ya samu, Amma shima bayada mutunci, don me sunzo a mota bazai iya tsallakawa yayi parking acan ba sai dai ya tsaya acan tsallake kuma ya turo matar mutane a wannan babban titi hakan shi bazai iya fitowa ba sai ita."
"Iskanci samarin yanzune, Amma zanyi magana da dad a dinga tsawatar dasu akan tsofaffin mutane, inaga d'aya daga cikin masu aikine hajiya nafeesa ta turo kinsan halinta."
"Zata iya yuyuwa gaskiya, ALLAH ya kyauta." A daidai lokacin da suka tsaya a bakin junction suna jiran traffic tabasu hannu drivern yazo saiti dasu Dr nura ya juyo ya kallesa yana fad'in.
"Kin gashi ko?" Fatima tajuya ta kalli drivern daya qore sautin kid'an motar yana kad'a kai, dai dai lokacin itama rashida ta d'ago kai ta gefenta tana kallon motar da taji suna fira akai, motace mai kyan gaske don zata iya cewa takusa kyn ta Dr.nura ko kuma suzo d'ai, matar dake ciki tajuyar da kanta can gefe take kallo da jikinta yabata kmar ta santa kota tab'a ganinta awani wajen amma rashin juyo fuskarta da tayi yasa takasa tantance haka, tan wannan tunanin ne little Nuraddeen ya tsanyara kukan da ya maido hankalinta agaresa tare da qoqarin turasa cikin mayafinta don tabashi nono, a lokacin ita kuma umma tajuyo fuskarta ta b'angaren tana qarewa yanayin kyawon garin da yanda motocin suka tsaitsaya suna jiran abasu hannu suwuce amma kasancewar glass d'in motar tasu Dr nura tinted ne yasa takasa hango 'yar tata dake ciki tana kicaniyar bawa little Nuraddeen har traffic d'in tabasu hannu, jin motarsu tafara tafiya yasa Rashida d'agowa tare da maida kallonta wajen amma sai taga wayam tuni har motar tajuya ta d'ayan hannun takoma baya sukuma suka miqe hanyarsu tabarin cikin garin.
••• ••• •••
Baffa ya matuqar tsorata da abunda yaji inspector najida tace Nuraddeen ya aikata, sukayita bata haquri shida baffa, daqyar suka samu tabasu belinsa saboda yanda ranta ya matuqar b'aci kafin tace.
"Baba kaja masa kunne don idan ya sake maimaita hakan zamu kaishi a hukuntashi ne saboda babban laifine civilian yasa hannu ya bugi kowane irin kaki, don haka kajamasa kunne, kawai na qyalesa ne albarkacinka daya sai mun ganar dashi kuskurensa"
"To 'yata nagode nagode sosai."
Kallon Nuraddeen da duk yafita hayyacinsa yayi had'e da cewa "tashi muje."
"Babu inda zanje baffa matuqar innarmu na wannan wajen." Nuraddeen yabashi amsa had'e da d'agowa yana kallonsa da ijiyarsa da aka bubbuge ta kumbure.
Cike da mamaki suka bishi da kallo kafin baffa Usman yace. "Haba Nuraddeen, kayi haquri, zamu d'auke mahaifiyarka anan amma kasan komai sai anshirya, kabi komai ahankali insha ALLAH zamu fidda ita nan kuma zata samu lafiya, yanzu haka muna tattaunawa akan maganar ne inspector najida ta kirawomu, kayi haquri ka taso muje kaji ko."
"Baffa bazan iya ba." Yafad'a tare da miqewa zai koma cikin cell d'in baffa ya bishi da kallo, saurin dakatar dashi baffa Usman yayi had'e da cewa.
"Dawo Nuraddeen za'a fiddo da ita kaji!"
Baffa zaiyi magana baffa Usman ya dakatar dashi had'e da cewa "a'a ya kabarshi, inspector najida ya za'ayi kubamu ita." Baffa Usman ya qarasa maganar yana kallonta.
"Bayada matsala baba, dama Bata qarqashin kulawarmu don haka zaku iya zuwa ku d'auketa ko yaushe, Amma d'aukarta akwai had'ari sosai saboda yanayin da take ciki bai kamata ace an d'auketa ankaita cikin mutane ba, wannan kawai shine matsalar."