Sashe 52
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kam buhun uban nan, Bilki me nake shirin gani anan?, So kikeyi shi kuma yaron nawa bayan halin da yake ciki ki hallaka mani shi ta hanyar asirce manishi sai yanda kikayi dashi don mugunta?, To wallahi jinina yafi qarfinki munafukar banza munafukar wofi, hadda wani d'auko abu kina bashi abaki, kai Kuma sakaran banza da bakasan inda duniya tayi ba kasaki baki kana sha."
Yaya hawwa taqarasa fad'a tare da jawo hannunsa zatabar falon dashi tana cika tana batsewa, cike da tausayin mugun halin da ALLAH yayi mata yajarab tawar rayuwa dashi Inna Bilkisu ke kallonta kafin tace. "Dakata Yaya hawwa, kiji tsoron ALLAH, kiji tsoron ALLAH kitausayawa yaron nan halin da yake ciki, a matsayinmu na iyaye bamu kad'aine ALLAH ke hukunta 'ya'yanmu akan haqqoqan muba idan suka danne, hatta mu kanmu ubangiji na kamamu da haqqoqansu kuma yayi mana hukunci mai tsauri idan muka taushe masusu, su amana ne agaremu kuma ALLAH zai tambayemu, Nuraddeen d'anane duniya da lahira tunda nake auren qanen mahaifinsa, don haka banga ribar da zan samu ba idan nacutar dashi, dama haka rayuwa take idan kana abu sai kayi tsammanin kowa ma yanayi, kitaka sannu haqqin d'anki kad'ai ya isheki aduniya balle na sauran rayukan da basuji basu gani ba, agidannan Banda darajar mijina da yayansa da kike ci saita haihuwa da kikayi badon haka ba da saina koya maki darasin rayuwa, amma ko yanzu muje zuwa da sannu duniya zata koya maki."
Rab'awa tagefensu tayi tawuce bayan ta d'auko kwanon abincin data kawo masa tare da furar da Yaya hawwa ta b'arara,
"Kagani ko shashashan banza da wofi, bakasan mai sonka ba, dubi yanda tayi tsaye ta cimun mutunci agabanka amma ka kasa cewa uffan saboda tariga data gama da kai, dallah wuce mutafi samna sakaran banza, biye yake da ita kamar hoto har suka fito sashen tana rafka uwar masifa da zagezage, daidai bakin qofa taci karo da fadeela Inna taturota tagyara inda furar tazube, hannu tasa ta bangajeta gefe da kad'an tafad'e da sauri Nuraddeen yariqe mata hannu.
"Gidan ubanwa zakijene" Yaya hawwa tafad'a tana watsa mata wani mugun kallo,
"Inna ce tace nazo nagoge inda fura ta zube.."
"To ahalin kicifaffi anyo gadon ashibilanci da iyayi maza kiwuce kibar nan kafin in makeki, shegu d'iyan bani na iya.."
Da sauri fadeela tabar wajen tun kafin tarufe baki ita kuma tajawo gambun qofar tarufe har lokacin tana riqe da hannunsa kamar wani qaramin yaro,
'Daki tashiga dashi ta zaunar saman gefen gado ta jawo wani kwano da dambu aciki sannan ta d'ebo ruwa ga kofi ta ajiye agabansa,
"Maza kaci kada yunwa ta illataka, yanzu haka duk inda ta tafi tana can hankalinta kwance tabarmu da tashin hankali anan." 'Doga kansa yayi yana kallon mahaifiyar tasa had'e da cewa.
"Kamarya duk inda tatafi innar mu, taya Rashida zata bar gidannan da tsohon cikinta haihuwa ko yau ko gobe?."
"Eh mana, ai haka na iya yuyuwa idan taji tagaji da zama dakai, to don ta tayar maka da hankali tunda taga kana sonta, ya kamata kiyi tunani anya ba guduwarta tayi ba tunda auren naku na had'ine?." Murmushin da yafi kuka ciwo yayi kafin yace.
"Innar mu kenan! Ai aurena da Rashida ba had'in iyaye bane balle tagudu tabarni, ni naganta da kaina nace Ina sonta kuma itama ba tilastata akayi sai ta aureni ba, ita da kanta taji tana sona kuma ta amsa mani, kinga batun guduwa anan ga masoyan da sukaji sun amince da juna ai bata taso ba, Rashida inada tabbaci akan d'auketa akayi amma su waye? Meyasa? Duka ban sani ba, tsorona d'aya aduniya kada ace mahaifiyata nada sa hannu aciki, Ina addu'a kar ALLAH yasa tsanar da kike yimata bata Kai mizanin da Zaki iya salwantar da rayuwarta ba."
Hannuwanta yariqo had'e da durqushewa agabanta sannan yaci gaba da cewa, "innar mu duk duniya banida maccen da takai matsayinki araina domin ke kika haifeni, kikayi d'awainiya dani tun Ina cikin cikinki har zuwa girmana amma duk da haka farincikina da kwanciyar hankali na suna tattarene a hannun matata Rashida, don ALLAH idan kinada masaniya akan inda take don ALLAH innar mu kisanar dani kafin nakoma marar amfani adoron duniya."
Wani banzan kallo tayi masa kafin a hasale tace. "Tashi fita kabani waje tunda naga kai bakasan abunda kakeyi ba." Tsom ya tashi ya miqe jikinsa ba k'wari ko kad'an ya koma sashensa, bai jima da shiga ba yafito sanye da wasu kaya yamiqi hanyar fita gidan.
"Ina zaka?" Yaji muryar Yaya hawwa tana fad'a cike da gadara, batare daya juyo ba yace.
"Zantafi nemo farincikina." Bai tsaya sauraron abunda zatace ba yaci gaba da tafiya, daidai bakin qofar fita gidan yaci karo muneera tashigo aguje da alama wani tajawo sauran k'iris ta bangajesa tawuce, jikinta na rawa tatsaya tana fad'in. "Don ALLAH ya nura kayi haquri" kota kanta baibi ba yawuce abunsa batare dama yasan da ita awajen ba, biyo bayansa tayi tana fad'in, "ya nura, ya nura."
Ko juyowa beyi ba balle ma yakalleta har tasa ran zai tanka mata, hakan yasa tafashewa da kuka had'e da rugawa cikin gida, da sauri Inna ruqayya tafito tana fad'in.
"Ya rasulu manzon ALLAH, muneera keda wa acikin gidannan, fad'amun inji waya tab'aki ne, qara tale baki tayi tana cigaba da rere kukanta wanda nan take yasa hankalin mutanen gida yadawo wajen saboda sanin halin da ake ciki,
"Ke muneera lafiya? Wata tsohuwa data dudduqo daga wancan b'angaren dake cikin gidan tafad'a tana tokare sandarta akusa da ita, "ke fad'amun waya tab'eki ko d'an gidan uban waye inje dashi har iyayen da suka haifesa inci masu mutunci tas, fad'i Ina jinki keda waye?"
Cikin kuka tace, "Inna koba ya nura neba inayi masa magana ya qyaleni ko kallona beyi ba yai tafiyarsa." Kallon dan dazon mutanen gidan dake wajen Inna ruqayya tayi had'e da had'a wasu yawu masu kabrin gaske saboda sanin halin 'yar tata, hannunta tariqo tana fad'in. "To zo muje d'aka kiji kinsan yau yana cikin yanayi marar dad'i."
"Wlh Babu inda zanje ai bani na b'atar masa da mata ba balle yadinga qyaleni yana fushi dani kuma Inna ai haka kukeso tunda kunce bakwa son ya aureni tana cikin gidan."
'Dago kai gaba d'aya mutanen gidan sukayi had'e da maido kallonsu ga inna ruqayya data fara kalle kallen gefenta, tsohuwar dake kusa garetace tace. "Ke muneera kirufa mana asiri gidannan, wannan sheri da kike neman qaqabawa uwarki har ina?"
"Ai wlh basheri bane itama innar tasan gaskiya nafad'a, har magani suka karb'o aka barbad'awa ya nura saboda akarkato zuciyarsa yafara sona muyi aure amma gashinan beyi amfanin komai ba, ni wlh ALLAH bazan yarda ba sai an auramun ya nura." Taqare maganar tana bubbuga qafafuwa tana kuka.
Ana haka saidai mutanen dake wajen suna tafa hannuwa suna sallallami sukaga Yaya hawwa da bawanda ya lura da lokacin data fito tayi tsaye wajen tana kallon sakarci irin na muneera tayo wani irin kukan kura ta damqi wuyan Inna ruqayya tana fad'in
"Buhun uba, d'an nawa zaku kai ayiwa asiri don kuna munafukai algungumai, to wallahi ALLAH baku isa ba yau nafison garin bebeji ya tarwatse ya watse akan wannan rashin mutunci da kuka tafka mani matsiyata da bakusan abun arziqi ba." Taqare maganar tana kaimata naushi a gefen fuska, kokuwa suka shigayi ita da ita cikin sanyin muryar qasaqasa ta yanda baza'a jiba Inna ruqayya ta dinga bata haquri gudun kada suyiwa kawunansu tonon asiri, Amma saboda yanda Yaya hawwa taji zafin abun aranta ko saurarenta batayi taci gaba da tsigarta tana jifarta da miyagun kalamai, cikin b'acin rai da hasala Inna ruqayya tasa hannu biyu biyu ta tureta tana fad'in. "Ke hawwa bari nafad'a maki shuru shurufa ba tsoro bane, sannan shi abun fad'i kowa yana dashi qulle agindinsa saidai idan bai fito bane, karkiga na qyaleki kinemi maidani sakarai agaban mutane Ina d'an naki ba damuwa da rayuwarsa kikayi ba balle har kinuna mani cewa ke uwar sace, naji munkai nura wajen mlamin tsibbu a karkato da zuciyarsa ga muneera, ai nayine don farincikin 'yata, amma kefa? d'an naki kike zuwa kikai wajen bokaye don farin cikin kanki dana wasu, ko kina tunanin ban san cewa ke kika b'atar da yarinyar nan ba da har zakizo kina yimani cin mutunci agaban mutane, to
anyi masa asirin duk abunda kika iya kije kiyi, in shed'anci kike taqama dashi na damaki na shanye Kuma wallahi da sannu zan koya maki hankali, banza ke atunaninki duk wannn walaqancin da kike yimani kinasa ran zan barshine yatafi abanza? Wlh kinsha qarya dama jira nake kigama yaqin ni kuma nakwashe ganimar, kuma tunda kika yimun wannan tozarcin wlh saina tabbatarwa da duniya cewa kece nan kika b'atar da surukarki kika sa ahallaka maki ita don bakya sonta." Inna ruqayya taqare maganar tana shed'a guda guda had'e da gyara d'aurin d'an kwalinta.
"Kan hatta kazak kaza..ni zakiyiwa sharri ruqayya don 'yarki ta tona maki asiri, to baki Isa ba wlh..." Nan suka shiga tonawa kansu asiri mutanen dake wajen nata la'antarsu da miyagun halayensu.
Inna Bilkisu kuwa fashewa tayi da kuka tashige d'aki tana mai tausayawa halin da Rashida keciki, baffa kuwa da tun d'azu suna bakin qofar shigowa tsakar gidan yanata ko kuwar shigowa ciki saboda abunda kunnuwansa suka jiyo masa lokacin da zasu shigo amma baffa Usman yariqesa yace yabari har sai sun gama fad'in komai da zai zamo masu hujja tukuna, kasa haquri yayi ya fizgikke daga riqon da yayi masa jikinsa narawa idanuwnsa na hawaye yashigo yana nuna yaya hawwa da hannu yace....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[8/17, 10:19] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___40💎
Yaya hawwa taqarasa fad'a tare da jawo hannunsa zatabar falon dashi tana cika tana batsewa, cike da tausayin mugun halin da ALLAH yayi mata yajarab tawar rayuwa dashi Inna Bilkisu ke kallonta kafin tace. "Dakata Yaya hawwa, kiji tsoron ALLAH, kiji tsoron ALLAH kitausayawa yaron nan halin da yake ciki, a matsayinmu na iyaye bamu kad'aine ALLAH ke hukunta 'ya'yanmu akan haqqoqan muba idan suka danne, hatta mu kanmu ubangiji na kamamu da haqqoqansu kuma yayi mana hukunci mai tsauri idan muka taushe masusu, su amana ne agaremu kuma ALLAH zai tambayemu, Nuraddeen d'anane duniya da lahira tunda nake auren qanen mahaifinsa, don haka banga ribar da zan samu ba idan nacutar dashi, dama haka rayuwa take idan kana abu sai kayi tsammanin kowa ma yanayi, kitaka sannu haqqin d'anki kad'ai ya isheki aduniya balle na sauran rayukan da basuji basu gani ba, agidannan Banda darajar mijina da yayansa da kike ci saita haihuwa da kikayi badon haka ba da saina koya maki darasin rayuwa, amma ko yanzu muje zuwa da sannu duniya zata koya maki."
Rab'awa tagefensu tayi tawuce bayan ta d'auko kwanon abincin data kawo masa tare da furar da Yaya hawwa ta b'arara,
"Kagani ko shashashan banza da wofi, bakasan mai sonka ba, dubi yanda tayi tsaye ta cimun mutunci agabanka amma ka kasa cewa uffan saboda tariga data gama da kai, dallah wuce mutafi samna sakaran banza, biye yake da ita kamar hoto har suka fito sashen tana rafka uwar masifa da zagezage, daidai bakin qofa taci karo da fadeela Inna taturota tagyara inda furar tazube, hannu tasa ta bangajeta gefe da kad'an tafad'e da sauri Nuraddeen yariqe mata hannu.
"Gidan ubanwa zakijene" Yaya hawwa tafad'a tana watsa mata wani mugun kallo,
"Inna ce tace nazo nagoge inda fura ta zube.."
"To ahalin kicifaffi anyo gadon ashibilanci da iyayi maza kiwuce kibar nan kafin in makeki, shegu d'iyan bani na iya.."
Da sauri fadeela tabar wajen tun kafin tarufe baki ita kuma tajawo gambun qofar tarufe har lokacin tana riqe da hannunsa kamar wani qaramin yaro,
'Daki tashiga dashi ta zaunar saman gefen gado ta jawo wani kwano da dambu aciki sannan ta d'ebo ruwa ga kofi ta ajiye agabansa,
"Maza kaci kada yunwa ta illataka, yanzu haka duk inda ta tafi tana can hankalinta kwance tabarmu da tashin hankali anan." 'Doga kansa yayi yana kallon mahaifiyar tasa had'e da cewa.
"Kamarya duk inda tatafi innar mu, taya Rashida zata bar gidannan da tsohon cikinta haihuwa ko yau ko gobe?."
"Eh mana, ai haka na iya yuyuwa idan taji tagaji da zama dakai, to don ta tayar maka da hankali tunda taga kana sonta, ya kamata kiyi tunani anya ba guduwarta tayi ba tunda auren naku na had'ine?." Murmushin da yafi kuka ciwo yayi kafin yace.
"Innar mu kenan! Ai aurena da Rashida ba had'in iyaye bane balle tagudu tabarni, ni naganta da kaina nace Ina sonta kuma itama ba tilastata akayi sai ta aureni ba, ita da kanta taji tana sona kuma ta amsa mani, kinga batun guduwa anan ga masoyan da sukaji sun amince da juna ai bata taso ba, Rashida inada tabbaci akan d'auketa akayi amma su waye? Meyasa? Duka ban sani ba, tsorona d'aya aduniya kada ace mahaifiyata nada sa hannu aciki, Ina addu'a kar ALLAH yasa tsanar da kike yimata bata Kai mizanin da Zaki iya salwantar da rayuwarta ba."
Hannuwanta yariqo had'e da durqushewa agabanta sannan yaci gaba da cewa, "innar mu duk duniya banida maccen da takai matsayinki araina domin ke kika haifeni, kikayi d'awainiya dani tun Ina cikin cikinki har zuwa girmana amma duk da haka farincikina da kwanciyar hankali na suna tattarene a hannun matata Rashida, don ALLAH idan kinada masaniya akan inda take don ALLAH innar mu kisanar dani kafin nakoma marar amfani adoron duniya."
Wani banzan kallo tayi masa kafin a hasale tace. "Tashi fita kabani waje tunda naga kai bakasan abunda kakeyi ba." Tsom ya tashi ya miqe jikinsa ba k'wari ko kad'an ya koma sashensa, bai jima da shiga ba yafito sanye da wasu kaya yamiqi hanyar fita gidan.
"Ina zaka?" Yaji muryar Yaya hawwa tana fad'a cike da gadara, batare daya juyo ba yace.
"Zantafi nemo farincikina." Bai tsaya sauraron abunda zatace ba yaci gaba da tafiya, daidai bakin qofar fita gidan yaci karo muneera tashigo aguje da alama wani tajawo sauran k'iris ta bangajesa tawuce, jikinta na rawa tatsaya tana fad'in. "Don ALLAH ya nura kayi haquri" kota kanta baibi ba yawuce abunsa batare dama yasan da ita awajen ba, biyo bayansa tayi tana fad'in, "ya nura, ya nura."
Ko juyowa beyi ba balle ma yakalleta har tasa ran zai tanka mata, hakan yasa tafashewa da kuka had'e da rugawa cikin gida, da sauri Inna ruqayya tafito tana fad'in.
"Ya rasulu manzon ALLAH, muneera keda wa acikin gidannan, fad'amun inji waya tab'aki ne, qara tale baki tayi tana cigaba da rere kukanta wanda nan take yasa hankalin mutanen gida yadawo wajen saboda sanin halin da ake ciki,
"Ke muneera lafiya? Wata tsohuwa data dudduqo daga wancan b'angaren dake cikin gidan tafad'a tana tokare sandarta akusa da ita, "ke fad'amun waya tab'eki ko d'an gidan uban waye inje dashi har iyayen da suka haifesa inci masu mutunci tas, fad'i Ina jinki keda waye?"
Cikin kuka tace, "Inna koba ya nura neba inayi masa magana ya qyaleni ko kallona beyi ba yai tafiyarsa." Kallon dan dazon mutanen gidan dake wajen Inna ruqayya tayi had'e da had'a wasu yawu masu kabrin gaske saboda sanin halin 'yar tata, hannunta tariqo tana fad'in. "To zo muje d'aka kiji kinsan yau yana cikin yanayi marar dad'i."
"Wlh Babu inda zanje ai bani na b'atar masa da mata ba balle yadinga qyaleni yana fushi dani kuma Inna ai haka kukeso tunda kunce bakwa son ya aureni tana cikin gidan."
'Dago kai gaba d'aya mutanen gidan sukayi had'e da maido kallonsu ga inna ruqayya data fara kalle kallen gefenta, tsohuwar dake kusa garetace tace. "Ke muneera kirufa mana asiri gidannan, wannan sheri da kike neman qaqabawa uwarki har ina?"
"Ai wlh basheri bane itama innar tasan gaskiya nafad'a, har magani suka karb'o aka barbad'awa ya nura saboda akarkato zuciyarsa yafara sona muyi aure amma gashinan beyi amfanin komai ba, ni wlh ALLAH bazan yarda ba sai an auramun ya nura." Taqare maganar tana bubbuga qafafuwa tana kuka.
Ana haka saidai mutanen dake wajen suna tafa hannuwa suna sallallami sukaga Yaya hawwa da bawanda ya lura da lokacin data fito tayi tsaye wajen tana kallon sakarci irin na muneera tayo wani irin kukan kura ta damqi wuyan Inna ruqayya tana fad'in
"Buhun uba, d'an nawa zaku kai ayiwa asiri don kuna munafukai algungumai, to wallahi ALLAH baku isa ba yau nafison garin bebeji ya tarwatse ya watse akan wannan rashin mutunci da kuka tafka mani matsiyata da bakusan abun arziqi ba." Taqare maganar tana kaimata naushi a gefen fuska, kokuwa suka shigayi ita da ita cikin sanyin muryar qasaqasa ta yanda baza'a jiba Inna ruqayya ta dinga bata haquri gudun kada suyiwa kawunansu tonon asiri, Amma saboda yanda Yaya hawwa taji zafin abun aranta ko saurarenta batayi taci gaba da tsigarta tana jifarta da miyagun kalamai, cikin b'acin rai da hasala Inna ruqayya tasa hannu biyu biyu ta tureta tana fad'in. "Ke hawwa bari nafad'a maki shuru shurufa ba tsoro bane, sannan shi abun fad'i kowa yana dashi qulle agindinsa saidai idan bai fito bane, karkiga na qyaleki kinemi maidani sakarai agaban mutane Ina d'an naki ba damuwa da rayuwarsa kikayi ba balle har kinuna mani cewa ke uwar sace, naji munkai nura wajen mlamin tsibbu a karkato da zuciyarsa ga muneera, ai nayine don farincikin 'yata, amma kefa? d'an naki kike zuwa kikai wajen bokaye don farin cikin kanki dana wasu, ko kina tunanin ban san cewa ke kika b'atar da yarinyar nan ba da har zakizo kina yimani cin mutunci agaban mutane, to
anyi masa asirin duk abunda kika iya kije kiyi, in shed'anci kike taqama dashi na damaki na shanye Kuma wallahi da sannu zan koya maki hankali, banza ke atunaninki duk wannn walaqancin da kike yimani kinasa ran zan barshine yatafi abanza? Wlh kinsha qarya dama jira nake kigama yaqin ni kuma nakwashe ganimar, kuma tunda kika yimun wannan tozarcin wlh saina tabbatarwa da duniya cewa kece nan kika b'atar da surukarki kika sa ahallaka maki ita don bakya sonta." Inna ruqayya taqare maganar tana shed'a guda guda had'e da gyara d'aurin d'an kwalinta.
"Kan hatta kazak kaza..ni zakiyiwa sharri ruqayya don 'yarki ta tona maki asiri, to baki Isa ba wlh..." Nan suka shiga tonawa kansu asiri mutanen dake wajen nata la'antarsu da miyagun halayensu.
Inna Bilkisu kuwa fashewa tayi da kuka tashige d'aki tana mai tausayawa halin da Rashida keciki, baffa kuwa da tun d'azu suna bakin qofar shigowa tsakar gidan yanata ko kuwar shigowa ciki saboda abunda kunnuwansa suka jiyo masa lokacin da zasu shigo amma baffa Usman yariqesa yace yabari har sai sun gama fad'in komai da zai zamo masu hujja tukuna, kasa haquri yayi ya fizgikke daga riqon da yayi masa jikinsa narawa idanuwnsa na hawaye yashigo yana nuna yaya hawwa da hannu yace....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[8/17, 10:19] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___40💎