Sashe 79
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Don ALLAH uncle ku kaini naga ya Nuraddeen, Ina son ganinsa Ina so nahad'u dashi Amma su baffa sunqi amincewa,"
"Kamar ya Rashida?" Dr.nura ya tambayeta cikin rashin sani.
"So sukeyi su raba aurena dashi uncle kuma Ina son mijina, bayada laifi, akan abunda yafaru amma gaba d'aya sun kasa fahimtar hakan! don ALLAH ko sau d'ayane kataimaka akaro nabiyu ka had'ani da mijina kamar yanda kahad'ani da iyayena."
Maganar takeyi tana kuka had'e da game hannayenta waje d'aya,
Alama yayiwa Fatima dasu shiga motar sannan yajuya shima yashiga had'e da tayarwa, hannunta Fatima tariqa tabud'e gambun bayan motar tasata ciki sannan tarufe itama tashiga yaja motar sukabar qofar gidan,
"Ina muka nufa?"
Ya tambayeta adaidai lokacin da suka fito qauyen.
"Bebeji." Tabashi amsa ataqaice tana goge hawayen da suka jiqa mata fuska sharkaf,
Tafiya mai d'an nisa sukayi kafin su iso gaba d'ayansu Babu wanda kecewa wani uffan, tuqi yakeyi da hannu d'aya, hannun d'aya kuma ya azoshi saman tagar qofar yariqe hab'arsa dashi ita kuma Fatima sai faman jujjuya kwalin wayar dake hannunta takeyi wacce dama itace dalilin zuwan nasu saboda kewarta da tayi mata yawa kullum cikin zancenta ita da little yasa Dr yasiyowa Rashida wayar don suriqa gaisawa sai gashi sun tarar da ita cikin wannan halin.
Bini bini take juyowa takalleta cike da tausayi kafin Dr yamiqo mata wayarsa.
"Kamomin Yaya maryam"
Scrolling contact d'insa ta farayi har takai ga lambar Yaya Maryam da yayi saving da Ya Maryam kano takirata.
Bugu d'aya ta d'aga muryarta a hargitse.
"Dr."
"Na'am, anwuni lafiya.?"
"Lafiya klw, yanzu nake zancen kiranka na nemi Rashida sama ko qasa narasa saboda nayi mata fad'a."
"Karki damu tana tare damu, dama shine kiran dana yimaki."
"Tirqashi Amma wannan yarinyar anyi shashasha, shine zata fita fisabillahi bazata fad'amun ba, gaba d'aya duk tabi ta tayarmun da hankali?."
"Kiyi haquri, Bata kyauta ba gaskiya amma yanzun nan zamu dawo tare in Sha ALLAH." Kasancewar akwai cikakkiyar yarda tsakaninsu yasa bata damu sosai ba duk da abun ya b'ata mata rai, asalima gaba d'aya ranta bai kawo mata cewa Rashida zatayi tunanin zuwa tahad'u da Nuraddeen ba balle har ta taka da kanta taje garin nasu,
Koda suka iso angama sallar isha'i suka samu gefen wani shago sukayi parking,
Fitowa tayi cikin motar suma suka biyo bayanta har suka iso inda za'a iya hango gidan,
"Inane gidan Rashida?"
"Wancanne uncle." Tafad'a tana nuna gidan da yatsa.
"To muje ko."
"A'a uncle bazan iya ba, kawai ni shi kad'ai nake son nahad'u dashi."
"Bari to naje nasa ayo mani sallama dashi.," Yafad'a tare da tunkarar gidan.
Tsaye kawai take duk qafafuwanta sunyi sanyi tanaji tamkar basu imata, kallon anguwar takeyi d'aya bayan d'aya,
Kafin tahango Yusuf tafe yanufo inda suke gefen wani tsoho dake saida kalanzir saman d'an teburinsa,
"Lado abani kalanzir na naira ashirin?"
"Ahhh... yusufa d'an gidan yayansa nura, Wai ina yashige ne kwana biyu nadena ganinsa.?"
"Laah...ashe lado bakasan yaje qasar waje ba?"
"Kai yusufa!, Kace wlh."
"Wlh lado da gaske nakeyi."
"Kai ALLAH ban yarda da kaiba, shi nuran d'an mahaukaciya ne da zaibar qasar nan bayan matarsa da tsohon ciki tab'ata, sai kace wanda bedamu da ita ba,"
"To ni kabani kalanzir d'ina kada innar mu tabugeni, ai sai katambyi mutane kaji, yanacan yaje k'aro karatunsa."
"Tirqashi! Amma gaskiya be kyauta ba."
Kukan da Rashida ke qoqarin dannewa ne yaci qarfinta had'e da kucce mata.
Da sauri Yusuf daya miqa hannu zai karb'i kalanzir d'in da lado kemiqo masa suka d'ago kai tare jin kukan da suka jiyo agefensu.
"Yaa rasulu manzon ALLAH, ke baiwar ALLAH lafiya.?"
Lado yafad'a had'e da sakin kalanzir d'in yana kallon Fatima da Rashida dake tsaye hasken k'wan shago na yadosu, da hannu Yusuf ya shiga nuna Rashida don fuskarta bazata tab'a b'oye masa ba aduk inda tashiga, kasa magana yayi sai faman ja da baya yana fad'in.
"Aun..aunt..auntyyy.."
Yaruga aguje yabar wajen had'e da nufar gida yana k'walawa su baffa....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___60💎
Tunda Rashida ta tabbatar da cewa Nuraddeen yabar qasar taji gaba d'aya komai na duniya ya tsaya mata, Babu abunda ke mata dad'i haka kuma babu abunda ke burgeta arayuwar duniya, kallo d'aya zakayi mata kafahimci tsantsar damuwar da take ciki saboda yanda duk tabi ta susuce, batada wani aike sai kuka, na safe daban na rana daban hakama na dare daban, duk tabi tarame tayi baqi, rashin iyayenta namatuqar damunta musamman yanzu da take cikin wani hali marar misaltuwa duk da kuwa Yaya maryam da baffa sunyi qoqarin nuna mata sun sauko daga dokin naqin da suka hau saboda yanda sukaga tana nemanfita hayyacinta sai dai aransu ba haka bane.
Baffa Usman kuwa da baffa basu san abunda kefaruwa ba , gaba d'aya sun maida hankalinsu kocokom ga nemawa Yaya hawwa magani har zuwa lokacin da aka d'ibar masu nazuwa a d'auketa, ranar nayi misalin qarfe sha biyu na rana motar asibitin ta dira abakin qofar gidansu baffa, lokacin suna tsaitsaye da alamu dama suna jiran dakon isowarsune tun d'azu, wasu ma'aikatan lafiyane su biyar da kuma wani mutum yasha suit, da alama shine babbansu, Saida suka gaisa dasu sannan baffa Usman yayi masu jagora zuwa cikin gidan inda Yaya hawwa take ya bud'e masu d'akin,
Cikin qwarewar aikinsu suka shiga cikin d'akin yayainda Yaya hawwa tayi wani irin kukan kura tayo kansu.
Ba qaramar wahala suka shaba kafin su samu damar rirriqeta tana keta wani irin ihu daya karad'e ko ina tana fizge fizge, sai da sukayi da gaske sannan suka sakata cikin mota suma suka shiga.
Wajen motar baffa yatako yana hango ta glass d'in motar yanda jami'an lafiya ke qoqarin yimata allurar da zatasa tayi bacci kafin su isa yasa hannu ya goge k'wallan da suka zubo masa a idanuwansa yana mai addu'ar Allah yabata lafiya, gaban motar ya koma saiti gefen driver inda babbansu yake ya saukar da glass d'in motar yamiqa masa hannu suka sake gaisawa yayi masu godiya sannan motarsu tabar wajen, ahankali dandazon mutanen da suka taru qofar gidan suka fara watsewa cike da tausayin halin da sukaga anfito da Yaya hawwa aciki saboda yanda tayi baqi da rama sosai fiye da tunani, inba wanda yasanta sosai ba bazaka tab'a ganinta kace itace ba.
Adai dai lokacin baffa Ali yadawo daga gona rataye da fartanyarsa a kafad'a yana rera 'yan waqoqinsa, yana hango su baffa Usman ya murtuqe fuska tunkafin ya iso har zai wuce abunsa sai kuma yadawo baya had'e da kallon gungun wasu yara dake tsaye abakin gidan.
"Kai me kukeyi anan naga kun had'e kanu kamar d'iyan awaki?"
"Wlh Yaya hawwa ce akafito da ita za'a kaita asibitin mahaukata abun gwanin tausayi."
Wani yarone daga cikinsu yafad'a hannunsa na tallab'e da kuncinsa.
Batare da baffa Ali yadamu da 'yan uwansa dake wajen ba yayi tsaki had'e da cewa.
"ALLAH yaraka taki gona, ai mun huta da gayyar tsiya kullum ana hanamu bacci ana tsorata iyalinmu da yaranmu,"
Juyowa baffa yayi ransa amatuqar b'ace yace.
"Karka damu Aliyu, SANNU SANNU ai bata hana zuwa...kamar dai yanda hawwa ke girbar abunda tayi haka kaima zaka girbi naka in alkhairi in kuma sharran."
Guntun tsaki yaja batare daya damu da abunda baffa yace masa ba yashige cikin gida yana cigaba da rera 'yan waqoqinsa...
••• ••• •••
Kimanin satinsu Dr nura uku kenan da dawowa kano kawo Rashida, wanda sun jima hakanne sanadiyar Fatima data nace akan suyi zamansu sai qarshen wata saisu koma gaba d'aya tunda dama yakusa d'aukar hutu (annual leave), saidai hakan bazai yuyu ba saboda maganin little Nuraddeen da za'a karb'o masa gashi bayason idan yaje qarshen watan yasake dawowa har sai hutunsa yaqare,
Hakan yasa cikin satin da zasu koma kafin ranar tazo yayi sakko yaje borno ya karb'owa little maganinsa wanda idan yasha shine naqarshe,
Yana isa garin kai tsaye yawuce gidan iyayensa saboda akwai saqon da mahaifiyarsa tace yaje ya karb'owa Fatima na maganin da takesha,
Yana isa yatarar da mahaifinsa shima yadawo lokacin yana zaune kan dining table yana cin abinci, qarasawa yayi bakinsa d'auke da sallama yaje ya d'an russuna gabansa had'e da gaishesa.
Sake da fuska yamiqa masa hannu yana fad'in.
"A'a bokan turawa saukar yaushe?"
"Yanzunnan dady, mun sameku lafiya?"
"Lafiya klw dady, ya kasuwar."
"Kasuwa Alhamdulillah muna nan muna tattab'awa musanmman sabon shagon dana bud'e, abun Masha ALLAH gaskiya."
"ALLAH yaqaro bud'emai albarka, dady ammie fa?"
"Tana ciki, yanzu tabar nan inaga ankirata ne awaya."
Yana rufe baki tana fitowa, babbar mace ce mai cikar zati da kamala, farar mace ce sosai mai yawan fara'a da son mutane, kallo d'aya zakayi mata kafahimci hutu na tattare da ita, da sauri yanufi wajenta had'e da gaishesa, rungumosa tayi ajiki kai kace bashine d'anta nafarin ba suka nufo wajen dadyn tana fad'in.
"Oyoyo mutanen kano ta dabo tumbin giwa yaro koda mekazo anfika, Amma inada tabbaci akan ba'afi yaron nawa ba saidai ayi gogayya dashi ko ba haka ba alhaji?" Taqarasa maganar had'e da jawo kujera ta zaunar da Dr nura.
Dariya sukasa shida dady kafin yace.
"Mezance hajia fareeda tunda kinriga kin fad'a, ai ko ba haka bane ta zauna, uwa da d'anta kome tace akansa ai babu wanda ya isa musa mata." Suka sake sa dariya.
"Son ya hanya da 'yata Ina fatar kuna lafiya?"
"Lafiya klw ammie, tace agaisheki sosai."
"Muna amsawa, injin tana amfani da maganin yanda yakamata? Nasan halinku na 'yan boko baku fiye ba maganin nan namu na gargajiya muhimmanci ba.?"
"Ahh ammie banda Fatima tana kulawa sosai da lokutan shansa yanda yakamata,"
"ALLAH sarki baiwar ALLAH, ALLAH yasa adace, yarinyar nabani tausayi sosai, tanada matauqar juriya da haquri wlh, badon haka ba idan irin 'yan matan nan namu na zamani ne da yanxu tabi ta tayar maka da hankali dama kanta ga abunda Babu mai iya baku sai ALLAH, kuci gaba da haquri, in Sha ALLAH lokaci nazuwa da ijaba zata sauka, muna nan muna yimaku addu'a,"
"Kamar ya Rashida?" Dr.nura ya tambayeta cikin rashin sani.
"So sukeyi su raba aurena dashi uncle kuma Ina son mijina, bayada laifi, akan abunda yafaru amma gaba d'aya sun kasa fahimtar hakan! don ALLAH ko sau d'ayane kataimaka akaro nabiyu ka had'ani da mijina kamar yanda kahad'ani da iyayena."
Maganar takeyi tana kuka had'e da game hannayenta waje d'aya,
Alama yayiwa Fatima dasu shiga motar sannan yajuya shima yashiga had'e da tayarwa, hannunta Fatima tariqa tabud'e gambun bayan motar tasata ciki sannan tarufe itama tashiga yaja motar sukabar qofar gidan,
"Ina muka nufa?"
Ya tambayeta adaidai lokacin da suka fito qauyen.
"Bebeji." Tabashi amsa ataqaice tana goge hawayen da suka jiqa mata fuska sharkaf,
Tafiya mai d'an nisa sukayi kafin su iso gaba d'ayansu Babu wanda kecewa wani uffan, tuqi yakeyi da hannu d'aya, hannun d'aya kuma ya azoshi saman tagar qofar yariqe hab'arsa dashi ita kuma Fatima sai faman jujjuya kwalin wayar dake hannunta takeyi wacce dama itace dalilin zuwan nasu saboda kewarta da tayi mata yawa kullum cikin zancenta ita da little yasa Dr yasiyowa Rashida wayar don suriqa gaisawa sai gashi sun tarar da ita cikin wannan halin.
Bini bini take juyowa takalleta cike da tausayi kafin Dr yamiqo mata wayarsa.
"Kamomin Yaya maryam"
Scrolling contact d'insa ta farayi har takai ga lambar Yaya Maryam da yayi saving da Ya Maryam kano takirata.
Bugu d'aya ta d'aga muryarta a hargitse.
"Dr."
"Na'am, anwuni lafiya.?"
"Lafiya klw, yanzu nake zancen kiranka na nemi Rashida sama ko qasa narasa saboda nayi mata fad'a."
"Karki damu tana tare damu, dama shine kiran dana yimaki."
"Tirqashi Amma wannan yarinyar anyi shashasha, shine zata fita fisabillahi bazata fad'amun ba, gaba d'aya duk tabi ta tayarmun da hankali?."
"Kiyi haquri, Bata kyauta ba gaskiya amma yanzun nan zamu dawo tare in Sha ALLAH." Kasancewar akwai cikakkiyar yarda tsakaninsu yasa bata damu sosai ba duk da abun ya b'ata mata rai, asalima gaba d'aya ranta bai kawo mata cewa Rashida zatayi tunanin zuwa tahad'u da Nuraddeen ba balle har ta taka da kanta taje garin nasu,
Koda suka iso angama sallar isha'i suka samu gefen wani shago sukayi parking,
Fitowa tayi cikin motar suma suka biyo bayanta har suka iso inda za'a iya hango gidan,
"Inane gidan Rashida?"
"Wancanne uncle." Tafad'a tana nuna gidan da yatsa.
"To muje ko."
"A'a uncle bazan iya ba, kawai ni shi kad'ai nake son nahad'u dashi."
"Bari to naje nasa ayo mani sallama dashi.," Yafad'a tare da tunkarar gidan.
Tsaye kawai take duk qafafuwanta sunyi sanyi tanaji tamkar basu imata, kallon anguwar takeyi d'aya bayan d'aya,
Kafin tahango Yusuf tafe yanufo inda suke gefen wani tsoho dake saida kalanzir saman d'an teburinsa,
"Lado abani kalanzir na naira ashirin?"
"Ahhh... yusufa d'an gidan yayansa nura, Wai ina yashige ne kwana biyu nadena ganinsa.?"
"Laah...ashe lado bakasan yaje qasar waje ba?"
"Kai yusufa!, Kace wlh."
"Wlh lado da gaske nakeyi."
"Kai ALLAH ban yarda da kaiba, shi nuran d'an mahaukaciya ne da zaibar qasar nan bayan matarsa da tsohon ciki tab'ata, sai kace wanda bedamu da ita ba,"
"To ni kabani kalanzir d'ina kada innar mu tabugeni, ai sai katambyi mutane kaji, yanacan yaje k'aro karatunsa."
"Tirqashi! Amma gaskiya be kyauta ba."
Kukan da Rashida ke qoqarin dannewa ne yaci qarfinta had'e da kucce mata.
Da sauri Yusuf daya miqa hannu zai karb'i kalanzir d'in da lado kemiqo masa suka d'ago kai tare jin kukan da suka jiyo agefensu.
"Yaa rasulu manzon ALLAH, ke baiwar ALLAH lafiya.?"
Lado yafad'a had'e da sakin kalanzir d'in yana kallon Fatima da Rashida dake tsaye hasken k'wan shago na yadosu, da hannu Yusuf ya shiga nuna Rashida don fuskarta bazata tab'a b'oye masa ba aduk inda tashiga, kasa magana yayi sai faman ja da baya yana fad'in.
"Aun..aunt..auntyyy.."
Yaruga aguje yabar wajen had'e da nufar gida yana k'walawa su baffa....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___60💎
Tunda Rashida ta tabbatar da cewa Nuraddeen yabar qasar taji gaba d'aya komai na duniya ya tsaya mata, Babu abunda ke mata dad'i haka kuma babu abunda ke burgeta arayuwar duniya, kallo d'aya zakayi mata kafahimci tsantsar damuwar da take ciki saboda yanda duk tabi ta susuce, batada wani aike sai kuka, na safe daban na rana daban hakama na dare daban, duk tabi tarame tayi baqi, rashin iyayenta namatuqar damunta musamman yanzu da take cikin wani hali marar misaltuwa duk da kuwa Yaya maryam da baffa sunyi qoqarin nuna mata sun sauko daga dokin naqin da suka hau saboda yanda sukaga tana nemanfita hayyacinta sai dai aransu ba haka bane.
Baffa Usman kuwa da baffa basu san abunda kefaruwa ba , gaba d'aya sun maida hankalinsu kocokom ga nemawa Yaya hawwa magani har zuwa lokacin da aka d'ibar masu nazuwa a d'auketa, ranar nayi misalin qarfe sha biyu na rana motar asibitin ta dira abakin qofar gidansu baffa, lokacin suna tsaitsaye da alamu dama suna jiran dakon isowarsune tun d'azu, wasu ma'aikatan lafiyane su biyar da kuma wani mutum yasha suit, da alama shine babbansu, Saida suka gaisa dasu sannan baffa Usman yayi masu jagora zuwa cikin gidan inda Yaya hawwa take ya bud'e masu d'akin,
Cikin qwarewar aikinsu suka shiga cikin d'akin yayainda Yaya hawwa tayi wani irin kukan kura tayo kansu.
Ba qaramar wahala suka shaba kafin su samu damar rirriqeta tana keta wani irin ihu daya karad'e ko ina tana fizge fizge, sai da sukayi da gaske sannan suka sakata cikin mota suma suka shiga.
Wajen motar baffa yatako yana hango ta glass d'in motar yanda jami'an lafiya ke qoqarin yimata allurar da zatasa tayi bacci kafin su isa yasa hannu ya goge k'wallan da suka zubo masa a idanuwansa yana mai addu'ar Allah yabata lafiya, gaban motar ya koma saiti gefen driver inda babbansu yake ya saukar da glass d'in motar yamiqa masa hannu suka sake gaisawa yayi masu godiya sannan motarsu tabar wajen, ahankali dandazon mutanen da suka taru qofar gidan suka fara watsewa cike da tausayin halin da sukaga anfito da Yaya hawwa aciki saboda yanda tayi baqi da rama sosai fiye da tunani, inba wanda yasanta sosai ba bazaka tab'a ganinta kace itace ba.
Adai dai lokacin baffa Ali yadawo daga gona rataye da fartanyarsa a kafad'a yana rera 'yan waqoqinsa, yana hango su baffa Usman ya murtuqe fuska tunkafin ya iso har zai wuce abunsa sai kuma yadawo baya had'e da kallon gungun wasu yara dake tsaye abakin gidan.
"Kai me kukeyi anan naga kun had'e kanu kamar d'iyan awaki?"
"Wlh Yaya hawwa ce akafito da ita za'a kaita asibitin mahaukata abun gwanin tausayi."
Wani yarone daga cikinsu yafad'a hannunsa na tallab'e da kuncinsa.
Batare da baffa Ali yadamu da 'yan uwansa dake wajen ba yayi tsaki had'e da cewa.
"ALLAH yaraka taki gona, ai mun huta da gayyar tsiya kullum ana hanamu bacci ana tsorata iyalinmu da yaranmu,"
Juyowa baffa yayi ransa amatuqar b'ace yace.
"Karka damu Aliyu, SANNU SANNU ai bata hana zuwa...kamar dai yanda hawwa ke girbar abunda tayi haka kaima zaka girbi naka in alkhairi in kuma sharran."
Guntun tsaki yaja batare daya damu da abunda baffa yace masa ba yashige cikin gida yana cigaba da rera 'yan waqoqinsa...
••• ••• •••
Kimanin satinsu Dr nura uku kenan da dawowa kano kawo Rashida, wanda sun jima hakanne sanadiyar Fatima data nace akan suyi zamansu sai qarshen wata saisu koma gaba d'aya tunda dama yakusa d'aukar hutu (annual leave), saidai hakan bazai yuyu ba saboda maganin little Nuraddeen da za'a karb'o masa gashi bayason idan yaje qarshen watan yasake dawowa har sai hutunsa yaqare,
Hakan yasa cikin satin da zasu koma kafin ranar tazo yayi sakko yaje borno ya karb'owa little maganinsa wanda idan yasha shine naqarshe,
Yana isa garin kai tsaye yawuce gidan iyayensa saboda akwai saqon da mahaifiyarsa tace yaje ya karb'owa Fatima na maganin da takesha,
Yana isa yatarar da mahaifinsa shima yadawo lokacin yana zaune kan dining table yana cin abinci, qarasawa yayi bakinsa d'auke da sallama yaje ya d'an russuna gabansa had'e da gaishesa.
Sake da fuska yamiqa masa hannu yana fad'in.
"A'a bokan turawa saukar yaushe?"
"Yanzunnan dady, mun sameku lafiya?"
"Lafiya klw dady, ya kasuwar."
"Kasuwa Alhamdulillah muna nan muna tattab'awa musanmman sabon shagon dana bud'e, abun Masha ALLAH gaskiya."
"ALLAH yaqaro bud'emai albarka, dady ammie fa?"
"Tana ciki, yanzu tabar nan inaga ankirata ne awaya."
Yana rufe baki tana fitowa, babbar mace ce mai cikar zati da kamala, farar mace ce sosai mai yawan fara'a da son mutane, kallo d'aya zakayi mata kafahimci hutu na tattare da ita, da sauri yanufi wajenta had'e da gaishesa, rungumosa tayi ajiki kai kace bashine d'anta nafarin ba suka nufo wajen dadyn tana fad'in.
"Oyoyo mutanen kano ta dabo tumbin giwa yaro koda mekazo anfika, Amma inada tabbaci akan ba'afi yaron nawa ba saidai ayi gogayya dashi ko ba haka ba alhaji?" Taqarasa maganar had'e da jawo kujera ta zaunar da Dr nura.
Dariya sukasa shida dady kafin yace.
"Mezance hajia fareeda tunda kinriga kin fad'a, ai ko ba haka bane ta zauna, uwa da d'anta kome tace akansa ai babu wanda ya isa musa mata." Suka sake sa dariya.
"Son ya hanya da 'yata Ina fatar kuna lafiya?"
"Lafiya klw ammie, tace agaisheki sosai."
"Muna amsawa, injin tana amfani da maganin yanda yakamata? Nasan halinku na 'yan boko baku fiye ba maganin nan namu na gargajiya muhimmanci ba.?"
"Ahh ammie banda Fatima tana kulawa sosai da lokutan shansa yanda yakamata,"
"ALLAH sarki baiwar ALLAH, ALLAH yasa adace, yarinyar nabani tausayi sosai, tanada matauqar juriya da haquri wlh, badon haka ba idan irin 'yan matan nan namu na zamani ne da yanxu tabi ta tayar maka da hankali dama kanta ga abunda Babu mai iya baku sai ALLAH, kuci gaba da haquri, in Sha ALLAH lokaci nazuwa da ijaba zata sauka, muna nan muna yimaku addu'a,"