Sashe 86
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"A'a hajia dakata, kibarshi muga irin sakayyar da ALLAH keyiwa bayinsa wud'anda suka cutar da wasu bayin nasa, wannan matar da kuke gani ba kowa bace face surukar Rashida data nemi salwantar da rayuwarta data d'anta saboda son zuciya, ya ALLAH Ina godiya agareka da keke gaggauta yin wani hisabi tunduniya saboda sauran bayinka su wa'aztu."
Wata irin zabura baba yayi had'e da miqewa tsaye yana sallallami yana kallon Rashida don tabbatar da abunda yayar tasu kefad'a, jinjina kai Rashida ta shigayi tana kallonsa itama had'e da cewa.
"Baba innar mu ce, meye yasameta haka!?" Tana kuka.
"Anya Rashida itace?, Innarku fa kikace mahaifiyar mijinki Nuraddeen? don ALLAH ki kalla da kyau kada kitayar mana da hankali."
"Wlh baba itace, bazan tab'a mantawa d fuskarta ba, innalillahi wa'inna ilaihirrajiuun, nashiga uku umma Ina ya nura yatafi haka yabar Inna acikin wannan halin?, wayyo ni ALLAH baba, meye yasami Inna haka."
Duk wanda ke falon binta yayi da kallo cike da mamakin lafuzzan dake fitowa daga bakinta, musamman Yaya Maryam data soma hasala ganin kukan da takeyi, cikin b'acin rai ta katsa mata tsawa had'e d cewa.
"Kirufa mana baki ko inzo intakaki awurin, munji mungani itace, sai akayi me kuma da zaki azawa mutane kuka?"
"Haba gwaggo! Haba gwaggo, uwar mijina face!, Surukata kakar d'an dana haifa, taya bazanyi kuka ba tana cikin wannan yanayi, gwaggo kidubi fa yanda takoma, dubi irin wahalar da take sha, don me baza'a tausaya mata tunda rayuwace itama."
"Rashida fita d'akinnan kafin na sab'a maki, gwaggon taki ke fad'a kema kina fad'a?" Baffa yafad'a ransa a b'ace.
"A'a bashar, ba dakai takeyi ba don haka kabarni da ita."
Shiru baba yayi had'e da komawa yasamu waje ya zauna jikinsa a mace, haqiqa ubangiji Mai jujjuya al'amurransa ne aduk lokacin da yaso, yau gashi 'yarsu da akaso ajefa cikin wani hali a haukatar masu da ita ALLAH yakareta ita kuma wacce taso hakan agareta ALLAH yajuyar da al-amarin akanta dama haka rayuwa take _(aljaza'u min jinsil amala)_ sakayya nazuwa daidai da irin abunda ka aikata.
Muryar matar baba balarabe hajia Aisha yajiyo tana fad'ar.
"Banda abunki Rashida meye na kuka awannan al-amarin? abunda ta aikatane ya koma mata, to tawane dalilin za'a tausaya mata, kiduba adadin mutanen data jefa cikin wani hali fiye da shekara d'aya, su kwana cikin qunci da baqincikin rayuwa duk ta dalilinta, ke kanki da mahaifanki harma damu duka sai yau ALLAH ya yaye mana d'inbin damuwar dake dasqare acikin zukatanmu, taya za'ayi ALLAH yabarta da wud'annan haqqoqa data d'aukarwa kanta batare da anbima bima masu sub?, Ai addu'armu d'aya itace ALLAH yakaremu da son zuciya irin nata."
"Kar kice hajia mama," da yake haka suke kiranta.
"Dukkaninmu bayi muke ga ALLAH, kuma babu wanda yawuce ajarrabi rayuwarsa da khairan ko kuma akasin haka kuma bawai don namanta da abunda tayi manine ba nake tausayin wannan halin da take ciki, kawai ina tausaya matane saboda darajar haihuwa da tayiwa mijina koba komai ma ai baza'a tab'a canjawa tuwo suna ba, matsayinta na kakar jininku baza'a tab'a kankaresa ba, kuma idan kun duba itama rayuwace kamar mu, wlh hajia mama indai akan abunda ta aikata agareni ALLAH ke azabtar da ita haka nayafe mata duniya da lahira."
Bud'e baki Yaya Maryam tayi da niyar yin magana maigidanta alhaji ubale yayi saurin dakatar da ita.
"Haba Maryam, don me zakiyi qoqarin tirsasata bijirewa kyakkyawar zuciyarta, wlh bana tantama akan yarinyar nan bazata tab'a walaqantaba duniya da lahira saboda akowane irin yanayi dake samunta arayuwa takan kasance mai tsarkakakkiyar zuciya da kuma haquri, ni inaga ku k'yaleta, tanda ikon yafewa duk wanda taga dama, tazubar da hawayenta aduk lokacin da take so kuma ta tausayawa duk wanda taga yadace domin ita take da iko akan zuciyarta, kamata yayi kuyi alfaharin samunta a matsayin 'ya tagari ba kuyi qoqarin chanzata izuwa kangarariyar 'yaba."
Saida Yaya Maryam tawatsa mata wata iwar harara tukuna sannan tace.
"To ai shikenan saita shirya muwuce mukaita wajenta tazauna tayi jinyarta, inaga haka shiyafi kuma shi zatayi tanunawa duniya kyawon zuciyarta da kuma tausayinta."
Murmushi dady da tund'azu ya mayar da hankalinsa ga tv yana mamakin irin yanayin da yaya hawwa take ciki kuma har ahalinta suka tsaya b'ata lokacinsu wajen zuwa asibiti, duk wanda yakalleta da abubuwan da takeyi yasan ba komai ke damunta ba illa matsalar jinnu ce, duk abubuwan da suke fad'a yana jinsu kawai yayi shirune saboda atunaninsa ba huruminsa bane, amma yanzu kalaman Yaya Maryam dake nuni da yanda ranta yab'aci su suka sakashi murmusawa har yake tunanin yakamata yace wani abu awannan gab'ar, musamman idan yayi la'akari da cewa akwai rashin cikakkiyar wayewa atattare dasu wanda yasa har suka iya irin wannan musayar bakin a inda bai kamata ba, kamata yayi ace sun ajiye wannan matsalar a tsakaninsu idan sun koma gida domin sirrin suce amma yanayin qaramcin wayewa dake tattare dasu yasa sun kasa fahimtar hakan.
Saida yayi gyaran murya sannan yafara basu haquri akan su ajiye wannan matsalar daga baya saisu zauna su tattauna akanta domin hakan shine sirri agaresu sannan yayi masu nasiha sosai sannan ya sake tayasu farincikin had'uwa da junansu da sukayi.
Sai alokacin baba balarabe da duk jikinsa yagama sanyi yayi ajiyar zuciya tare da sake miqa godiyarsu agaresu shida d'ansa bisa taimakon da sukayiwa 'yarsu da d'an uwansu da kuma matarsa.
Saida akayi sallar la'asar sannan su baba balarabe suka kama hanyar komawa, sunso a haukarsu su koma dasu umma da baba amma sai Dr ya roqesu subari idan an kwana biyu sun shirya tsaf sai yawuce dasu tunda wurin aikin sane,
Haka suka tafi cike d'inbin alkhairin da dady da ammie sukayi masu suna masu yabawa nagarta irin tasu, haka Dr nura shima ba'a barshi abaya ba don yayi masu alkhairi sosai harda suturu ya siya masu da sauran kayayyakin da zasuyi tsaraba dasu, saida yarakasu har suka fita gari sannan yajuyo ya koma can gida suka shiga tattaunawa da dady akan qudurinsa na mayar da Rashida makaranta da yayi gashi kuma yanzu da alama iyayenta bazasu barta anan ba idan suka tashi komawa.
Murmushi dady yayi had'e da cewa.
"Haba nura, ai kayi wauta, taya daga baka amanar yarinya zaka d'auko zance maida ita makaranta bayan kasan akowane lokaci zata iya komawa hannun iyayenta, bayan haka karka manta yarinyar nan tanada aure bai kamata ace kai tsaye kana zartar da abubuwa akanta ba, don haka ka ajiye maganar komawarta makaranta, iya taimakon daya kamata kayi kayi basai kashiga hurumin da ba naka ba kaji ko."
"Eh dady." Yafad'a yana mai yaba hangen nesa irin na mahaifinsa, sai yanzu yafahimci gaba d'aya shirmene yaso tabkawa, nan suka cigaba da tattaunawa akan sauran alamurran dake gabansu kafin akira sallar magrib suwuce masallaci, bayan anyi sallar isha'i yashigo part d'in na ammie Fatima na kwance ta tattake da bargo ita kuma ammie na zaune tana karatun alqur'ani bayan tagama sallah, gaisheta yayi had'e da yimata seda safe sannan yace Fatima tafito suje gida.
Cikin qarfin hali tamiqe had'e da yima ammie saida safe itama sannan tabi bayansa, sashensu umma suka nufa tana biye dashi,
"Sweety don ALLAH kabarni anan zan kwana, gaba d'aya banajin qarfin jikina."
Juyowa yayi had'e da d'an dawowa baya yariqo hannunta.
"Kiyi haquri Fatima bazan iya bacci acikin gidan canba idan har bakya nan kuma kinga ammie bazata barni na kwanar mata ad'aki ba da sai inyi kwanciyata anan nima.
Cikin qarfin hali tayi murmushi had'e da cewa.
"Haba dr! Ai kaima kasan kayi girma da kwanar mata d'aki."
"Ok, to kinga sai kiyi haquri kawai muje gida gaba d'aya tunda nayi girma."
Da haka suka iso sashen dasu umma suke sukayi sallama abakin qofa kafin umma tabasu izinin shigowa, kwance suka isko Rashida bisa qafafuwan umma shi kuma little nagefe yana bacci sai faman firarsu sukeyi hankali kwance, suna shiga ta tashi zaune tare da matsawa jikin umma ta d'ora kanta saman kafad'arta, sau d'aya Dr yakalleta ya d'auke kai had'e da gaisheda umma yana tab'o little dake bacci.
"Takwara yau har anyi bacci dawuri ahaka!"
"Aikuwa kaganshi nan inba ALLAH yatsare muba sai tsakar dare yatashi ya hanamu bacci da shegen kukannan nasa." I'm tafad'a tana qoqarin zame kafad'arta daga kan da Rashida ta aza mata,
"Maman boy kitashi muje ko." Fatima tafad'a tana zolayar Rashi don tasan babu yanda za'ayi tabisu.
Shiru tayi batare data amsa ba Dr. Yamiqe yana yima umma Saida safe,
"Rashida tashi kuke ko?"
Yanda Dr. Nura yaga ta shagwab'e fuska kamar zatayi kuka yasa yayi 'yar dariya had'e da cewa, "Kai maman boy saki fuskarki da wasa Fatima keyi, dama nazo muyi saida safe kuma muga yaronmu don nasan yau babu mai cewa ya rabaki da umman nan taki yasan ko waye ya aikesa."
Dariya duk suka sannan suka wuce bayan itama tayi masu seda safe.
Kusan ranar rashida da ummanta zaune suka kwana shikuwa baba masallacin dake cikin gidan yayi tafiyarsa ya kwanta bayan sun gama firar dashi kusan qarfe d'aya na dare.
_kuyi haqnayi manage ne nayi maku typing, sai ahankali wlh yikawai nayi, don ALLAH Ina baran addu'arku kada kumanta dani😰🙏🏻_
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___64💎
Cikin daren Yaya Maryam takira aunty marwiyya tasanar da ita zancen tafiyar zuwa borno tace.
"Bazata samu dama ba saboda itama mai gidanta bayajin dad'i, Amma don ALLAH idan sunje su gaishesu sosai."
Kasancewar son sukeyi suje ranar sudawo yasa tunda sassafe suka shirya, aron mota baba balarabe ya samo masu su hud'u, dashi da alhaji ubale mijin Yaya Maryam, sai ita da kuma matar baba balarabe guda wato uwar gidansa sukasa mai sannan suka d'auki hanyar zuwa borno...
Wata irin zabura baba yayi had'e da miqewa tsaye yana sallallami yana kallon Rashida don tabbatar da abunda yayar tasu kefad'a, jinjina kai Rashida ta shigayi tana kallonsa itama had'e da cewa.
"Baba innar mu ce, meye yasameta haka!?" Tana kuka.
"Anya Rashida itace?, Innarku fa kikace mahaifiyar mijinki Nuraddeen? don ALLAH ki kalla da kyau kada kitayar mana da hankali."
"Wlh baba itace, bazan tab'a mantawa d fuskarta ba, innalillahi wa'inna ilaihirrajiuun, nashiga uku umma Ina ya nura yatafi haka yabar Inna acikin wannan halin?, wayyo ni ALLAH baba, meye yasami Inna haka."
Duk wanda ke falon binta yayi da kallo cike da mamakin lafuzzan dake fitowa daga bakinta, musamman Yaya Maryam data soma hasala ganin kukan da takeyi, cikin b'acin rai ta katsa mata tsawa had'e d cewa.
"Kirufa mana baki ko inzo intakaki awurin, munji mungani itace, sai akayi me kuma da zaki azawa mutane kuka?"
"Haba gwaggo! Haba gwaggo, uwar mijina face!, Surukata kakar d'an dana haifa, taya bazanyi kuka ba tana cikin wannan yanayi, gwaggo kidubi fa yanda takoma, dubi irin wahalar da take sha, don me baza'a tausaya mata tunda rayuwace itama."
"Rashida fita d'akinnan kafin na sab'a maki, gwaggon taki ke fad'a kema kina fad'a?" Baffa yafad'a ransa a b'ace.
"A'a bashar, ba dakai takeyi ba don haka kabarni da ita."
Shiru baba yayi had'e da komawa yasamu waje ya zauna jikinsa a mace, haqiqa ubangiji Mai jujjuya al'amurransa ne aduk lokacin da yaso, yau gashi 'yarsu da akaso ajefa cikin wani hali a haukatar masu da ita ALLAH yakareta ita kuma wacce taso hakan agareta ALLAH yajuyar da al-amarin akanta dama haka rayuwa take _(aljaza'u min jinsil amala)_ sakayya nazuwa daidai da irin abunda ka aikata.
Muryar matar baba balarabe hajia Aisha yajiyo tana fad'ar.
"Banda abunki Rashida meye na kuka awannan al-amarin? abunda ta aikatane ya koma mata, to tawane dalilin za'a tausaya mata, kiduba adadin mutanen data jefa cikin wani hali fiye da shekara d'aya, su kwana cikin qunci da baqincikin rayuwa duk ta dalilinta, ke kanki da mahaifanki harma damu duka sai yau ALLAH ya yaye mana d'inbin damuwar dake dasqare acikin zukatanmu, taya za'ayi ALLAH yabarta da wud'annan haqqoqa data d'aukarwa kanta batare da anbima bima masu sub?, Ai addu'armu d'aya itace ALLAH yakaremu da son zuciya irin nata."
"Kar kice hajia mama," da yake haka suke kiranta.
"Dukkaninmu bayi muke ga ALLAH, kuma babu wanda yawuce ajarrabi rayuwarsa da khairan ko kuma akasin haka kuma bawai don namanta da abunda tayi manine ba nake tausayin wannan halin da take ciki, kawai ina tausaya matane saboda darajar haihuwa da tayiwa mijina koba komai ma ai baza'a tab'a canjawa tuwo suna ba, matsayinta na kakar jininku baza'a tab'a kankaresa ba, kuma idan kun duba itama rayuwace kamar mu, wlh hajia mama indai akan abunda ta aikata agareni ALLAH ke azabtar da ita haka nayafe mata duniya da lahira."
Bud'e baki Yaya Maryam tayi da niyar yin magana maigidanta alhaji ubale yayi saurin dakatar da ita.
"Haba Maryam, don me zakiyi qoqarin tirsasata bijirewa kyakkyawar zuciyarta, wlh bana tantama akan yarinyar nan bazata tab'a walaqantaba duniya da lahira saboda akowane irin yanayi dake samunta arayuwa takan kasance mai tsarkakakkiyar zuciya da kuma haquri, ni inaga ku k'yaleta, tanda ikon yafewa duk wanda taga dama, tazubar da hawayenta aduk lokacin da take so kuma ta tausayawa duk wanda taga yadace domin ita take da iko akan zuciyarta, kamata yayi kuyi alfaharin samunta a matsayin 'ya tagari ba kuyi qoqarin chanzata izuwa kangarariyar 'yaba."
Saida Yaya Maryam tawatsa mata wata iwar harara tukuna sannan tace.
"To ai shikenan saita shirya muwuce mukaita wajenta tazauna tayi jinyarta, inaga haka shiyafi kuma shi zatayi tanunawa duniya kyawon zuciyarta da kuma tausayinta."
Murmushi dady da tund'azu ya mayar da hankalinsa ga tv yana mamakin irin yanayin da yaya hawwa take ciki kuma har ahalinta suka tsaya b'ata lokacinsu wajen zuwa asibiti, duk wanda yakalleta da abubuwan da takeyi yasan ba komai ke damunta ba illa matsalar jinnu ce, duk abubuwan da suke fad'a yana jinsu kawai yayi shirune saboda atunaninsa ba huruminsa bane, amma yanzu kalaman Yaya Maryam dake nuni da yanda ranta yab'aci su suka sakashi murmusawa har yake tunanin yakamata yace wani abu awannan gab'ar, musamman idan yayi la'akari da cewa akwai rashin cikakkiyar wayewa atattare dasu wanda yasa har suka iya irin wannan musayar bakin a inda bai kamata ba, kamata yayi ace sun ajiye wannan matsalar a tsakaninsu idan sun koma gida domin sirrin suce amma yanayin qaramcin wayewa dake tattare dasu yasa sun kasa fahimtar hakan.
Saida yayi gyaran murya sannan yafara basu haquri akan su ajiye wannan matsalar daga baya saisu zauna su tattauna akanta domin hakan shine sirri agaresu sannan yayi masu nasiha sosai sannan ya sake tayasu farincikin had'uwa da junansu da sukayi.
Sai alokacin baba balarabe da duk jikinsa yagama sanyi yayi ajiyar zuciya tare da sake miqa godiyarsu agaresu shida d'ansa bisa taimakon da sukayiwa 'yarsu da d'an uwansu da kuma matarsa.
Saida akayi sallar la'asar sannan su baba balarabe suka kama hanyar komawa, sunso a haukarsu su koma dasu umma da baba amma sai Dr ya roqesu subari idan an kwana biyu sun shirya tsaf sai yawuce dasu tunda wurin aikin sane,
Haka suka tafi cike d'inbin alkhairin da dady da ammie sukayi masu suna masu yabawa nagarta irin tasu, haka Dr nura shima ba'a barshi abaya ba don yayi masu alkhairi sosai harda suturu ya siya masu da sauran kayayyakin da zasuyi tsaraba dasu, saida yarakasu har suka fita gari sannan yajuyo ya koma can gida suka shiga tattaunawa da dady akan qudurinsa na mayar da Rashida makaranta da yayi gashi kuma yanzu da alama iyayenta bazasu barta anan ba idan suka tashi komawa.
Murmushi dady yayi had'e da cewa.
"Haba nura, ai kayi wauta, taya daga baka amanar yarinya zaka d'auko zance maida ita makaranta bayan kasan akowane lokaci zata iya komawa hannun iyayenta, bayan haka karka manta yarinyar nan tanada aure bai kamata ace kai tsaye kana zartar da abubuwa akanta ba, don haka ka ajiye maganar komawarta makaranta, iya taimakon daya kamata kayi kayi basai kashiga hurumin da ba naka ba kaji ko."
"Eh dady." Yafad'a yana mai yaba hangen nesa irin na mahaifinsa, sai yanzu yafahimci gaba d'aya shirmene yaso tabkawa, nan suka cigaba da tattaunawa akan sauran alamurran dake gabansu kafin akira sallar magrib suwuce masallaci, bayan anyi sallar isha'i yashigo part d'in na ammie Fatima na kwance ta tattake da bargo ita kuma ammie na zaune tana karatun alqur'ani bayan tagama sallah, gaisheta yayi had'e da yimata seda safe sannan yace Fatima tafito suje gida.
Cikin qarfin hali tamiqe had'e da yima ammie saida safe itama sannan tabi bayansa, sashensu umma suka nufa tana biye dashi,
"Sweety don ALLAH kabarni anan zan kwana, gaba d'aya banajin qarfin jikina."
Juyowa yayi had'e da d'an dawowa baya yariqo hannunta.
"Kiyi haquri Fatima bazan iya bacci acikin gidan canba idan har bakya nan kuma kinga ammie bazata barni na kwanar mata ad'aki ba da sai inyi kwanciyata anan nima.
Cikin qarfin hali tayi murmushi had'e da cewa.
"Haba dr! Ai kaima kasan kayi girma da kwanar mata d'aki."
"Ok, to kinga sai kiyi haquri kawai muje gida gaba d'aya tunda nayi girma."
Da haka suka iso sashen dasu umma suke sukayi sallama abakin qofa kafin umma tabasu izinin shigowa, kwance suka isko Rashida bisa qafafuwan umma shi kuma little nagefe yana bacci sai faman firarsu sukeyi hankali kwance, suna shiga ta tashi zaune tare da matsawa jikin umma ta d'ora kanta saman kafad'arta, sau d'aya Dr yakalleta ya d'auke kai had'e da gaisheda umma yana tab'o little dake bacci.
"Takwara yau har anyi bacci dawuri ahaka!"
"Aikuwa kaganshi nan inba ALLAH yatsare muba sai tsakar dare yatashi ya hanamu bacci da shegen kukannan nasa." I'm tafad'a tana qoqarin zame kafad'arta daga kan da Rashida ta aza mata,
"Maman boy kitashi muje ko." Fatima tafad'a tana zolayar Rashi don tasan babu yanda za'ayi tabisu.
Shiru tayi batare data amsa ba Dr. Yamiqe yana yima umma Saida safe,
"Rashida tashi kuke ko?"
Yanda Dr. Nura yaga ta shagwab'e fuska kamar zatayi kuka yasa yayi 'yar dariya had'e da cewa, "Kai maman boy saki fuskarki da wasa Fatima keyi, dama nazo muyi saida safe kuma muga yaronmu don nasan yau babu mai cewa ya rabaki da umman nan taki yasan ko waye ya aikesa."
Dariya duk suka sannan suka wuce bayan itama tayi masu seda safe.
Kusan ranar rashida da ummanta zaune suka kwana shikuwa baba masallacin dake cikin gidan yayi tafiyarsa ya kwanta bayan sun gama firar dashi kusan qarfe d'aya na dare.
_kuyi haqnayi manage ne nayi maku typing, sai ahankali wlh yikawai nayi, don ALLAH Ina baran addu'arku kada kumanta dani😰🙏🏻_
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___64💎
Cikin daren Yaya Maryam takira aunty marwiyya tasanar da ita zancen tafiyar zuwa borno tace.
"Bazata samu dama ba saboda itama mai gidanta bayajin dad'i, Amma don ALLAH idan sunje su gaishesu sosai."
Kasancewar son sukeyi suje ranar sudawo yasa tunda sassafe suka shirya, aron mota baba balarabe ya samo masu su hud'u, dashi da alhaji ubale mijin Yaya Maryam, sai ita da kuma matar baba balarabe guda wato uwar gidansa sukasa mai sannan suka d'auki hanyar zuwa borno...