← Book details Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 131 OF 160

Sashe 131

Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ganin haka yasa umma tayi kwad'ayin yin haka koba komai ai dady ya kyautata masu baici ace ta wofantar da nashi ba tana nuna banbanci don itama takan sayi abubuwa wani lokacin tace akaiwa su Fatima da matar faruk wace yarinyarsu ma ta farin mai sunan ammie ana kiranta Islam tana hannun umma tun lokacin da za'a yayeta takarb'eta shikenan sai suka barta nan basu amsheta ba, gaba d'aya kulawarta tadawo tsakankanin ita da kuma ammien, hakan yasa ranar umma tasa ayo mata odar turarukkan wuta da khumra's masu qamshi acan kano wajen wata hamshaqiyar dilan kayan qamshi masu qamshin gaske dake saidasu bisa sassauqan farashi mai suna nana hafsat (miss xoxo) wacce anfi sanin sana'ar tata da sunan da takeyi mata laqani da *YERWA INCENSE* kayanta kam akwai kyau sosai don idan kagane amfani dasu to tabbas qamshi ya aureka duk inda kaje kaida 'ya'yanka, miji kuwa ba zancen zaman fira awaje saboda mararin yadawo gida ya shaqi wannan dadda'an qamshi dake kwantar da hankali da kuma natsuwar zuciya, ( _hajia wannan ba qanzon kurege bane, sai kin gwada zaki iya tabbatarwa, don haka idan kina son hana mijinki fira awaje saboda daddad'an qamshin da kikeyi keda 'ya'yanki da gidanki to kinemi YERWA INCENSE akan lambarsu ta talfo kamar haka👉 +234 809 521 5215 na tabbata zaki Sha mamaki kuma ki gode mani_ ) son da umma keyiwa kayan qamshinta yasa tasa aka kawo mata bokitayyen turarukkan da kwalaben khumra's d'in don ta rabawa sarakanan nasu, bayan ta kakkasa masu taba shahida ta d'auka taje ta kaimasu sai ta tuna da bata bada na imaan ba wato matar Shakur, da sauri tabi bayan shahida dahar takai bakin gate tana qwala mata kira riqe da bokitin turaren wutar d'aya da kuma kwalaben khumra's guda biyu a leda, muryarta da hajia nafeesa tajiyo yasata fitowa ta zauna akan d'aya daga cikin kujerun dake gefe wajen motocin Abba da alama baqi yayi suka tafi ta zauna tana lallatsar wayarta saboda tsabar gulma.

Batare da umma ta damu da ita ba tunda tariga tayi niya tamiqawa Shahida ledar tana fad'in.

"Ungo wannan mantawa nayi idan kin shiga kin bawa maman islam nata saiki biya ki kaiwa imaan wannan, kice muna gaishesu sosai..."

Ai bata rufe baki ba taji anbuge ledar da qarfi tafad'i qasa, da sauri ta d'ago kai sukayi ido biyu da hajia nafeesa sai wani faman huci takeyi sai kace wacce akayiwa laifi, bata tankata ba ta duqa zata d'auki ledar wacce ga alama kwalaben dake ciki sun mutu tasa qafa ta sake murza ledar bokin turaren ya fashe sannan tashurasu gefe tana fad'in.

"Ho iyayen munafucci da asiri, wane mugun abunne za'a d'auka akaiwa matar d'ana don arabani da ita, meye alaqarki da ita ko ina ruwanki da ita da zaki d'auki abu kice akai mata ban da baqin sheri dake zuciyarki da kuma iyayi.!"

Duk wannan abu dake faruwa ashe agaban idanuwan Abba ne lokacin yafito daga part d'in ammie zai shiga na ita hajia nafeesar ya d'auko wasu takardu ya hango abunda hajia nafeesar tayi, ran umma ya 'baci sosai amma saita qyaleta saboda bata buqatar tanka mata har tazamo silar jawo wata fitina agidan tadalilinta, inda ta shura kayan umma taje tasa hannu zata d'auke sauran don wasu duk sun d'an watse musamman turaren wuta sai taga anrigata, d'ago kan da zatayi sai sukayi ido biyu da dady, lumshe idanuwansa yayi sannan yabud'e yana murmushi had'e da cewa.

"Amaryata wannan wane irin turaren wutane mai qamshi da kuma sanyaya zuciya haka?" Saida ya d'an lakuto damshin ruwan khumrar dake jikin ledar ya sake sunsunawa had'e da rufe idanuwa sannan yaci gaba da cewa "kai! Masha ALLAH, wannan qamshin khumra haka sai kace an tattara qamshin turaren duniya aciki, fad'amun a Ina aka sayeshi kuma nawa nima in siya don na burgeku." Yafad'ai hakan da gangan yana kallon gefen da hajia nafeesa ke tsaye kamar an dasa ta da gefen ijiya.

Yanda yayi maganar yasa umma sakin murmushin da seda haqoranta suka bayyana suka miqe tsaye tare yana riqe da ledar sai qara shin shina yakeyi, Shahida kuwa sai faman toshe dariyar dake son fito mata takeyi aranta tana fad'in wannan tsohon akwai gwamawa mutun takaici, can tajiyo muryarsa yana kiran sunanta da sauri ta qarasa had'e da cewa.

"Na gaisheka tsoho mai ran qarfe, kayi naka kayi ta raggo ka dad'e kayi shekaru adadin yawan gashin rago,"

Dariya yayi had'e dasa hannu aljihu ya qirgo dubo goma ya miqawa umma yana fad'in,

"Ungo wannan asake kawo wasu sai akai mata, ke kuma Shahida ungo wannan ledar kikaiwa imaan d'in kice tayi haquri sun fashe tayi amfani dasu za'a sake kawo mata wasu." Yaqare maganar had'e da miqawa Shahida ledar ta amsa tawuce tana kallon hajia nafeesa da tayi fam tana dariya.

"A'a alhaji kabarshi akwai wasu zan sake bayarwa akai mata, basai ka wahalda kanka da kashe kud'in kaba." taqare maganar tana qoqarin saka mashi kud'in a aljihu, riqe hannunta yayi had'e da cewa

"Maman Rashida kibarsu kije kiyi yanda nace kawai ai hakan shine adalci."

Kafin yarufe baki hajia nafeesa tayo kukan kura kan umma ya zura mata idanuwa yana kallo yaga mezata aikata shima ya aikata mata irinsa sai yaga taja burki ganin kallon da yake yimata tafara zuba ruwan masifa inda take shiga ba nan take fita ba harda fad'in.

"Indai zalunci abunyine yaje yaci gaba dayi, akan tsohuwar mace yabi duk ya susuce ko tsufansa baya gani don kunya Bata ishesa ba agaban jikoki, to wlh in su anbasu sun canye anayin yanda akeso dasu ita ba'a isa ba, munafuccine banxa da wofi ai wannan kinimbibine za'ayi mata."

Cin mutunci kam dashi har umma tayi masu sai wanda tamance saboda zafin kishin abunda yayi mata, gaba d'aya idanuwanta sun rufe ta manta cewa yayi mata jan kunne akan karta sake takoma d'auko masa wata fitina agida baya buqatar haka sai gashi abun yauma takansa ya qare, Saida tayi mai isarta tagama sannan yacema umma tawuce part d'inta ita kuma yace daga nan karta kuru taqara taku d'aya cikin gidansa ta tafi gidansu sai yanemeta.

Wata irin gud'a ta ski had'e da cewa.

"Tafi nono fari, don ko yanzu nafita gidanka bazan rasa mai so ba, don haka takarda ta yakamata kabani ba kace intafi gidanmu ba, kana tunanin wai zaiji baqin cikine don kace intafi gidanmu?, to wlh ko d'aya don ko yanzu kasuwa tawatse d'an koli mai rabonci yaci."

Cikin yaranta ta qwalawa kira tace a d'auko mata mayafinta da takalmi dama wayarta na hannunta, ana kawo mata tasa had'e da cewa.

"To Ina jiran takarda ta mijin tsohuwar..."

Bata qarasa ba ya daka mata tsawa had'e da nuna mata gate yace tafita baya son ganinta...

*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎

_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*

_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋

_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞

*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖

*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️

Page___94💎

Batare data damuba tasa qafa taficewarta daga gidan, waje yanema ya zauna d'aya daga cikin kujerun dake wajen ya dafe kai, gaba d'aya yarasa wace irin rayuwace ga hajia nafeesa wacce batada lissafi da kuma sanin yakamata, ko kad'an bata gajiya da fitina arayuwarta duk kuwa yanda za'a jamata kunne, yana iya qoqarinsa wajen ganin yayi haquri da halayyarta har zuwa lokacin da zata canza amma hakan ya cutara har saida taqure haqurinsa tasa ya aikata abunda bai tab'a aikatawa tun qurciyarsa sai yanzu da manyanci ya kamasa.

Haka ya qarashi tunane tunanensa har yagaji yamiqe yakoma cikin gida yana mai Shan alwashi akan cewa koda zai amince tadawo masa gida saita gane gaba d'aya kurakuran data dad'e tana aikatawa tukuna,

Kimanin watanni takwas kenan da aurensu su little kuma adadin watannin cikin batool, zaune take tamimmiqe qafafuwanta tana faman yatsinar fuska saboda nauyin da cikin yayi mata, gaba d'aya duniyar tayi mata zafi ji take kamar ta fasa ihu, kallon little tayi dake mammatsa mata qafafuwanta alokaci d'aya kuma yana d'ibar wainar fulawa ga cokali yana bata abaki tace.

"Abu sumayya, agaskiya 'ya'yaye na d'auke da haqqin iyayensu sosai, sai yanzu nake jin tsananin rad'ad'in rashin kyautawar da nayi abbana azuciya akan kafiyar dana yimasa, da nabi komai ahankali da yanzu abbana bai haramta mani kusantar saba, wayyo...ni wannan karauniyar ce da akeyimun cikin ciki bana so wlh, Awwshhhh...ya ALLAH kabiya iyayenmu da alkhairi wlh da wahala renon cikin nan sosai,

Tafad'a had'e da d'an muskutawa tana qoqarin jinginawa a jikin kujera, cike da tausayinta ya d'anyi murmushi had'e da cewa.

"Ayya!, Yihaquri gimbiya, dama dole ai zakiji haka, kema ALLAH yabiyaki ya saukeki lafiya, idan summynmu tazo saina qwangare mata kai tunda ta wahalar mun da gimbiyata haka"

'Dan b'ata rai batool tayi tana turo baki gaba had'e da cewa.

"Karma kafara don bazan lamunta ba, yarinya 'yar gwal 'yar baiwa zaka dokanmun ita, ai kuwa da anjimu ko sumayya tah."

Taqare maganar tana shafar cikin nata tana murmushi, murmushin shima yayi mata tare da cewa.

"Kice akwai match agidannn don na lura sumy a partyn adawa zata zomun Kuma bazan yarda ba."

"Shikenan tunda kace haka, damankasan ita zatayi wining match d'in shiyasa kake adawa da ita, ni kama dena kiranta da sumy kana b'atawa yarinyata suna, sumayya take baiwar ALLAH."

"O'oh Anya gimbiya!, to shikenan nadena ranki shi dad'e ummu sumayya ALLAH ya saukeki lafiya."

Ta amsa da amin tana dariya.
Chapter 131 · 0% Book details