Sashe 144
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ya ubangiji kaine ka halicci bayinka kuma kai kake da iko akansu, ba'a shiga tsakaninka da bawanka akan duk hukuncin daka zartar akansa amma kai mai yafiyane tsakaninka dasu, rahamarka wadatacciya ce ga dukkanin wanda kaso sannan gafararka mai yawace ga bayinka, bamusan tsakaninka da wannan baiwar taka ba amma ALLAH kasheda duk abunda ke tsakaninmu muda ita musamman ni da nake da ikon kaina ALLAH nayafe mata duniya da lahira, ALLAH na yafe mata duniya da lahira ALLAH nayafe mata duniya da lahira Ina roqon kaima daka yafemata ya ubangijin sammai da qassai badon halinmu ba."
Yana gama fad'ar hakan yabada umurnin a rufeta haka dashi saboda basuda ikon hana abunda ALLAH ya tsaro, haka sunaji suna gani aka ida kakkad'a itace da ganyayyakin da za'a saka don babu Wanda zai iya shiga yajerasu yanda akeyi sannan aka ida tura qasa aka binneta sannan sauran mutanen suka watse kowa nafad'in albarkacin bakinsa akanta.
Baffa da baffa Usman sunjima bakin kabarin nata suna kuka tare da yimata addu'a sosai kafin sutafi,
Gari kam ko Ina ya d'auka irin yanayin mutuwar da Inna ruqayya tayi da abunda aka tarar kabarinta, wasu su tausaya mata, wasu suce haqqin baffane da suka d'auka da mijinta wasu suce haqqin jama'ane da tayita zalunta wasu kuma suce haqqin mijinta, koma dai meye musulmi bazai fidda rai ga rahamar ALLAH ba ana yimata addu'ar ALLAH ya gafarta mata.
Baffa Ali ma daya farka ka sanar dashi cewa yayi hukuncin da yadace kenan da ita tunda taqi ALLAH bayan gaskiya ta bayyana agareta, bazaice komai ba sai masu irin halinta su d'auki darasi tun kafin lokaci ya qure masu kuma su tubarwa ALLAH, kana ganin yanayin da take magana kasan cike take da baqinciki da kuma takaicinta, Saida su baffa sukayi da gaske suna bashi haquri ya yafe mata kuma ya nema mata gafarar ALLAH sannan yana kuka yace.
"Shikenan, nayafe mata a matsayina na mijinta Ina roqon dani da ita duka ALLAH kayafe mana, ALLAH ya sassauta mata ya lullub'eta da rahamarsa."
Kwanansa d'aya a asibitin aka sallamesa suka koma gida, alokacinne yayi kuka sosai don ya tabbata mai rabawa tariga tarabashi da ita musamman daya shiga d'akin sai yaji gaba d'aya kewarta takamasa dama mata da miji sai ALLAH, aranar kam baiyi bacci ba kwana yayi yana roqa mata gafarar ALLAH da kuma rahamarsa duk kuwa da rad'ad'in qurajen dake jikinsa dake damunsa.
••• ••• •••
Dr Nuraddeen kuwa kusan awarsu d'aya a filin jirgin kafin ya samu yaji ankira matafiya 'yan qasar tasa wato nageria, cike da farinciki ya isa bakin matattakalar jirgin yana d'agawa abokin nasa d'an qasar Thailand hannu don tunda ya kawosa cewa yayi bazai tafi ba sai yaga tashinsa.
Dama kai tsaye jirgin daya shiga kano zai sauka sai gashi gashi anyi sanarwa cikin jirgin cewa anaba dukkanin passinjojin ciki haquri saboda an samu matsala jirgin bazai iya qarasawa ba acan sanadiyar hazo da iska da suka yiwa sararin samaniya qawanya don haka ana bada haquri jirgin bazai iya sauka acan ba saidai a jahar borno, ko kad'an hakan beyi masa dad'i ba gashi da alama sai dare zasu sauka kuma babu wanda ya sani acan jahar balle yakwana awajensa kafin safe, tsaki yaja tare da aza kansa saman sit d'in jirgin da yake zaune yana furzar da wani iska ta bakinsa dake bayyanar da yanayin damuwar daya shiga.
Haka kuwa akayi jirgin nasu bai sauka ba sai misalin qarfe goma da rabi na dare ya fito agajiye had'e da ware hannuwansa yana shaqar iskan qasarsa, a hankali yace.
"Alhamdulillah, home sweet home!" Yanajin wani farinciki azuciyarsa alokaci d'aya kuma yanaji tana buga masa da sauri da sauri.
••• ••• •••
Rashida kuwa kusan yini tayi tana tunani had'e da kai da kawowa akan hukuncin da zuciyarta ke qoqarin yankewa, daga qarshe dai ta amince da little ya d'auki batool gobe yakaita taga mahaifinta saboda ba'asan halin ta rayuwa ba, kada suzo wani abun yafaru daga baya yayita damun zukatansu aqoqarinsu na ganin sun tirsasa zuciyarta akan abunda batada natsuwa dashi.
'Dauko wayarta tayi takira little tace yazo shida batool tana son ganinsu, cikin mintunan da basu fiye ashirin ba sai gasu sun iso kowanensu cikin yanayin da Bata so ba,
Murmushi tayi had'e da yimasu nasiha sosai akan yadda da dukkanin qaddarowar da ALLAH ya tsarowa bawansa sannan taroqi little daya yafemata akan hukuncin data yimasa na batason yayi mata maganar mahaifinsa da duk wani abun daya shafesa, tana hawaye ta kalli Batool tace.
"'yatah nafahimci damuwarki da kuma yanda kikeji a zuciyarki akan mahaifinki sanadiyar hakan yasa nima nafahimci irin jarumtar da d'ana yayi wajen yimani biyayya wacce natabbata idan kece bazaki iyaba saboda ke yarinya ce da bakisan ya ake b'oye zafi, rad'ad'i da kuma damuwa arai ba, sau da yawa nakanyi mamakin irin tsattsauran ra'ayin da kike dashi da kuma kafiya wanda yau sune suka lurar dani adalcin daya kamata nayiwa d'ana arayuwa, nagode maki sosai ALLAH yayi maki albarka ya kuma saukeki lafiya, ki kwantar da hankalinki in Sha ALLAH gobe zakije kiga mahaifinki"
"Kai kuma little Ina so yau kasani a matsayina na mahaifiyarka na amince maka uma na baka dama idan kukaje kacewa baba balarabe nace yakaika wajen dangin mahaifinka, kaje garesu na tabbata zaka rage damuwar da kakeji a zuciyarka kuma idan kundawo kanada zab'i kaje qasar malesia kanemo mahaifinka idan kanada ra'ayi idan kuma bakada nadai had'aka da danginsa kuma natabbata zasu rage maka kewarsa sosai. Suna can awani qauye da ake kira bebeji koda baba balarabe bazai samu damar kaika wajensu ba saboda yayarsa data hana tuntuni to kai kaje da kanka, idan kaje katambaya gidan marigayi aliyu gadanga, kakanka malan Idris Aliyu da 'yan uwansa naciki sai kace akaika wajensa kayi masa bayani, na tabbata zai ganeka sosai don bazai tab'a mantawa da fuskata ba, kuma kayi qoqarin had'ani dashi awaya kafin kadawo."
Atare shida Batool suka rungumeta cikin jin dad'i suna godiya musamman little dake jin tamkar ya tashi sama don jin dad'i, duk dako yasan cewa yadad'e da saninsu amma amincewar da mahaifiyarsa tayi yaje da izininta ya bayyana agaresu shiya yimasa dad'in daya tabbata akwai nasara biye a bayan hakan, batool ma harda qwallan farinciki tayi amma tad'au alwashin bazata bari asan da zuwan nata ba sai sun bar garin don kar Abba yahana.
Sun jima suna fira kafin suyi sallama da ita lokacin qarfe goma daidai na dare, dama tunda rana tayiwa su Dr bayanin komai wanda sud'inma suka qara qarfafa mata zuciyarta harta amince, hakama dady da umma takirasu ta sanar dasu, umma dai bata so hakan ba aranta amma jin dady ya qarfafawa Rashidar cewa taba little d'in dama yahad'u da dangin mahaifin nasa tunda dama shi yariga da yasan komai yasa tahaqura tace ALLAH yasa hakan shi yafi zama alkhairi,
Saida suka biya wajen Dr da fatima sukayi masu sallama suka yimasu fatan alkhairi sannan suka tafi gidan dady nanma albarka sukayita saka masu hadda ammi da hajia nafeesa sannan suka kama hanyar zuwa gida zuciyoyinsu cike fal da farinciki,
A daidai kan hanyarsu da zata kaisu gida idan sunyi yuton ta d'ayan titin sukaga mutum tsaye abakin titi da mita gefensa anbud'e gabanta da alama ta lalacene ana yimasu hannu, har zasu wuce sai kuma little ya tsaya mutumen ya d'an leqo ta gefensa had'e da cewa.
"Don ALLAH ko zaka taimaka ka ajiye wani bawan ALLAH d'aya daga cikin hotels d'in dake kan hanyar nan? Babban mutumne na d'auko daga airport yace yau yafara shigowa garinnan sai kuma taxi d'ina ta lalace."
Kallon batool yayi sannan yace.
"Ahh gaskiya da matsala, kace fa baqone agarinnan? kar fa muzo daga taimako kasaka mu a matsala."
"Haba bawan ALLAH, ALLAH dai yatsare, in Sha ALLAH babu abunda zai faru, nayarda da mutumen wlh sosai."
"Shikenan kace yazo, mudai da zuciya d'aya zamuyi."
Da gudu mutumen yaje yakira Dr Nuraddeen dake zaune cikin motar har baccin gajiya ya soma d'aukarsa, ya riqo masa jikkarsa har suka iso wajen motar su little ya bud'e masa baya ya shiga, kud'i Dr Nuraddeen yaciro aljihunsa da baisan ko nawa bane ya miqama drivern taxin cikin muryarsa mai sanyi yace.
"Gashi bawan ALLAH, nagode ALLAH yasaka da alkhairi,"
Baki bud'e drivern yasa hannu ya karb'a yana yimasa godiya tare da leqa inda little yake shima yayi masa godiyar yana cewa.
"Don ALLAH kuyi haquri ku saukesa ko hotel d'in can tacan gaba."
"Bakomai in Sha ALLAH"
Little yafad'a tare da Jan motar yabar wajen yana fad'in.
"Barka da isowa yallab'ai, awace hotel kakeso mukaika, mai sauqin kud'i ko mai tsada?"
"Duk wacce tasamu Alhamdulillah."
Dr Nuraddeen yafad'a yanajin wani irin fad'uwar gaba a tattare dashi haka shima little Saida gabansa yayi mugun fad'uwa da yaji muryarsa.
Batool ma kasa haquri tayi Saida tajuyo da qarfi tana kallon sit d'in na baya saboda yanda taji kamanceceniyar muryar tasu duk data Dr Nuraddeen tafi kauri amma da yake duhu ya mamaye motar bata iya ganin fuskar mutumenba saidai ta juya cike da mamaki aranta....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___101💎
A bakin wata katafariyar hotel naga little ya tsaida motarsa had'e dayin horn da sauri mai gadin dake zaune saman wata kujera a bakin gate d'in yana magana da wane dake tsaye gefensa ya ruga ya bud'e suka shiga, Saida ya daidaita tsayuwar motar tasa ya kashe sannan cikin girmamawa yace.
"Alhamdulillah maigida mun iso, Ina fatan kuma zatayi maka?"
Saida yayi Dr Nuraddeen yayi murmushi sannan yace.
"To masha ALLAH, zatayi da yardar ALLAH." Yafad'a tare da bud'e gambun qofar gefen nasa yafito had'e da jawo jikkarsa dake ajiye ya sagala a kafad'a ba tare daya damu da nauyin da take da shiba sannan ya rufe qofar yazo daidai saiti glass d'in qofar da little ke zaune had'e da miqa masa hannu, yana fad'in.
"Madallah fa, nagode sosai ALLAH yasaka da alkhairi kuma yayi albarka."
Yana gama fad'ar hakan yabada umurnin a rufeta haka dashi saboda basuda ikon hana abunda ALLAH ya tsaro, haka sunaji suna gani aka ida kakkad'a itace da ganyayyakin da za'a saka don babu Wanda zai iya shiga yajerasu yanda akeyi sannan aka ida tura qasa aka binneta sannan sauran mutanen suka watse kowa nafad'in albarkacin bakinsa akanta.
Baffa da baffa Usman sunjima bakin kabarin nata suna kuka tare da yimata addu'a sosai kafin sutafi,
Gari kam ko Ina ya d'auka irin yanayin mutuwar da Inna ruqayya tayi da abunda aka tarar kabarinta, wasu su tausaya mata, wasu suce haqqin baffane da suka d'auka da mijinta wasu suce haqqin jama'ane da tayita zalunta wasu kuma suce haqqin mijinta, koma dai meye musulmi bazai fidda rai ga rahamar ALLAH ba ana yimata addu'ar ALLAH ya gafarta mata.
Baffa Ali ma daya farka ka sanar dashi cewa yayi hukuncin da yadace kenan da ita tunda taqi ALLAH bayan gaskiya ta bayyana agareta, bazaice komai ba sai masu irin halinta su d'auki darasi tun kafin lokaci ya qure masu kuma su tubarwa ALLAH, kana ganin yanayin da take magana kasan cike take da baqinciki da kuma takaicinta, Saida su baffa sukayi da gaske suna bashi haquri ya yafe mata kuma ya nema mata gafarar ALLAH sannan yana kuka yace.
"Shikenan, nayafe mata a matsayina na mijinta Ina roqon dani da ita duka ALLAH kayafe mana, ALLAH ya sassauta mata ya lullub'eta da rahamarsa."
Kwanansa d'aya a asibitin aka sallamesa suka koma gida, alokacinne yayi kuka sosai don ya tabbata mai rabawa tariga tarabashi da ita musamman daya shiga d'akin sai yaji gaba d'aya kewarta takamasa dama mata da miji sai ALLAH, aranar kam baiyi bacci ba kwana yayi yana roqa mata gafarar ALLAH da kuma rahamarsa duk kuwa da rad'ad'in qurajen dake jikinsa dake damunsa.
••• ••• •••
Dr Nuraddeen kuwa kusan awarsu d'aya a filin jirgin kafin ya samu yaji ankira matafiya 'yan qasar tasa wato nageria, cike da farinciki ya isa bakin matattakalar jirgin yana d'agawa abokin nasa d'an qasar Thailand hannu don tunda ya kawosa cewa yayi bazai tafi ba sai yaga tashinsa.
Dama kai tsaye jirgin daya shiga kano zai sauka sai gashi gashi anyi sanarwa cikin jirgin cewa anaba dukkanin passinjojin ciki haquri saboda an samu matsala jirgin bazai iya qarasawa ba acan sanadiyar hazo da iska da suka yiwa sararin samaniya qawanya don haka ana bada haquri jirgin bazai iya sauka acan ba saidai a jahar borno, ko kad'an hakan beyi masa dad'i ba gashi da alama sai dare zasu sauka kuma babu wanda ya sani acan jahar balle yakwana awajensa kafin safe, tsaki yaja tare da aza kansa saman sit d'in jirgin da yake zaune yana furzar da wani iska ta bakinsa dake bayyanar da yanayin damuwar daya shiga.
Haka kuwa akayi jirgin nasu bai sauka ba sai misalin qarfe goma da rabi na dare ya fito agajiye had'e da ware hannuwansa yana shaqar iskan qasarsa, a hankali yace.
"Alhamdulillah, home sweet home!" Yanajin wani farinciki azuciyarsa alokaci d'aya kuma yanaji tana buga masa da sauri da sauri.
••• ••• •••
Rashida kuwa kusan yini tayi tana tunani had'e da kai da kawowa akan hukuncin da zuciyarta ke qoqarin yankewa, daga qarshe dai ta amince da little ya d'auki batool gobe yakaita taga mahaifinta saboda ba'asan halin ta rayuwa ba, kada suzo wani abun yafaru daga baya yayita damun zukatansu aqoqarinsu na ganin sun tirsasa zuciyarta akan abunda batada natsuwa dashi.
'Dauko wayarta tayi takira little tace yazo shida batool tana son ganinsu, cikin mintunan da basu fiye ashirin ba sai gasu sun iso kowanensu cikin yanayin da Bata so ba,
Murmushi tayi had'e da yimasu nasiha sosai akan yadda da dukkanin qaddarowar da ALLAH ya tsarowa bawansa sannan taroqi little daya yafemata akan hukuncin data yimasa na batason yayi mata maganar mahaifinsa da duk wani abun daya shafesa, tana hawaye ta kalli Batool tace.
"'yatah nafahimci damuwarki da kuma yanda kikeji a zuciyarki akan mahaifinki sanadiyar hakan yasa nima nafahimci irin jarumtar da d'ana yayi wajen yimani biyayya wacce natabbata idan kece bazaki iyaba saboda ke yarinya ce da bakisan ya ake b'oye zafi, rad'ad'i da kuma damuwa arai ba, sau da yawa nakanyi mamakin irin tsattsauran ra'ayin da kike dashi da kuma kafiya wanda yau sune suka lurar dani adalcin daya kamata nayiwa d'ana arayuwa, nagode maki sosai ALLAH yayi maki albarka ya kuma saukeki lafiya, ki kwantar da hankalinki in Sha ALLAH gobe zakije kiga mahaifinki"
"Kai kuma little Ina so yau kasani a matsayina na mahaifiyarka na amince maka uma na baka dama idan kukaje kacewa baba balarabe nace yakaika wajen dangin mahaifinka, kaje garesu na tabbata zaka rage damuwar da kakeji a zuciyarka kuma idan kundawo kanada zab'i kaje qasar malesia kanemo mahaifinka idan kanada ra'ayi idan kuma bakada nadai had'aka da danginsa kuma natabbata zasu rage maka kewarsa sosai. Suna can awani qauye da ake kira bebeji koda baba balarabe bazai samu damar kaika wajensu ba saboda yayarsa data hana tuntuni to kai kaje da kanka, idan kaje katambaya gidan marigayi aliyu gadanga, kakanka malan Idris Aliyu da 'yan uwansa naciki sai kace akaika wajensa kayi masa bayani, na tabbata zai ganeka sosai don bazai tab'a mantawa da fuskata ba, kuma kayi qoqarin had'ani dashi awaya kafin kadawo."
Atare shida Batool suka rungumeta cikin jin dad'i suna godiya musamman little dake jin tamkar ya tashi sama don jin dad'i, duk dako yasan cewa yadad'e da saninsu amma amincewar da mahaifiyarsa tayi yaje da izininta ya bayyana agaresu shiya yimasa dad'in daya tabbata akwai nasara biye a bayan hakan, batool ma harda qwallan farinciki tayi amma tad'au alwashin bazata bari asan da zuwan nata ba sai sun bar garin don kar Abba yahana.
Sun jima suna fira kafin suyi sallama da ita lokacin qarfe goma daidai na dare, dama tunda rana tayiwa su Dr bayanin komai wanda sud'inma suka qara qarfafa mata zuciyarta harta amince, hakama dady da umma takirasu ta sanar dasu, umma dai bata so hakan ba aranta amma jin dady ya qarfafawa Rashidar cewa taba little d'in dama yahad'u da dangin mahaifin nasa tunda dama shi yariga da yasan komai yasa tahaqura tace ALLAH yasa hakan shi yafi zama alkhairi,
Saida suka biya wajen Dr da fatima sukayi masu sallama suka yimasu fatan alkhairi sannan suka tafi gidan dady nanma albarka sukayita saka masu hadda ammi da hajia nafeesa sannan suka kama hanyar zuwa gida zuciyoyinsu cike fal da farinciki,
A daidai kan hanyarsu da zata kaisu gida idan sunyi yuton ta d'ayan titin sukaga mutum tsaye abakin titi da mita gefensa anbud'e gabanta da alama ta lalacene ana yimasu hannu, har zasu wuce sai kuma little ya tsaya mutumen ya d'an leqo ta gefensa had'e da cewa.
"Don ALLAH ko zaka taimaka ka ajiye wani bawan ALLAH d'aya daga cikin hotels d'in dake kan hanyar nan? Babban mutumne na d'auko daga airport yace yau yafara shigowa garinnan sai kuma taxi d'ina ta lalace."
Kallon batool yayi sannan yace.
"Ahh gaskiya da matsala, kace fa baqone agarinnan? kar fa muzo daga taimako kasaka mu a matsala."
"Haba bawan ALLAH, ALLAH dai yatsare, in Sha ALLAH babu abunda zai faru, nayarda da mutumen wlh sosai."
"Shikenan kace yazo, mudai da zuciya d'aya zamuyi."
Da gudu mutumen yaje yakira Dr Nuraddeen dake zaune cikin motar har baccin gajiya ya soma d'aukarsa, ya riqo masa jikkarsa har suka iso wajen motar su little ya bud'e masa baya ya shiga, kud'i Dr Nuraddeen yaciro aljihunsa da baisan ko nawa bane ya miqama drivern taxin cikin muryarsa mai sanyi yace.
"Gashi bawan ALLAH, nagode ALLAH yasaka da alkhairi,"
Baki bud'e drivern yasa hannu ya karb'a yana yimasa godiya tare da leqa inda little yake shima yayi masa godiyar yana cewa.
"Don ALLAH kuyi haquri ku saukesa ko hotel d'in can tacan gaba."
"Bakomai in Sha ALLAH"
Little yafad'a tare da Jan motar yabar wajen yana fad'in.
"Barka da isowa yallab'ai, awace hotel kakeso mukaika, mai sauqin kud'i ko mai tsada?"
"Duk wacce tasamu Alhamdulillah."
Dr Nuraddeen yafad'a yanajin wani irin fad'uwar gaba a tattare dashi haka shima little Saida gabansa yayi mugun fad'uwa da yaji muryarsa.
Batool ma kasa haquri tayi Saida tajuyo da qarfi tana kallon sit d'in na baya saboda yanda taji kamanceceniyar muryar tasu duk data Dr Nuraddeen tafi kauri amma da yake duhu ya mamaye motar bata iya ganin fuskar mutumenba saidai ta juya cike da mamaki aranta....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Page___101💎
A bakin wata katafariyar hotel naga little ya tsaida motarsa had'e dayin horn da sauri mai gadin dake zaune saman wata kujera a bakin gate d'in yana magana da wane dake tsaye gefensa ya ruga ya bud'e suka shiga, Saida ya daidaita tsayuwar motar tasa ya kashe sannan cikin girmamawa yace.
"Alhamdulillah maigida mun iso, Ina fatan kuma zatayi maka?"
Saida yayi Dr Nuraddeen yayi murmushi sannan yace.
"To masha ALLAH, zatayi da yardar ALLAH." Yafad'a tare da bud'e gambun qofar gefen nasa yafito had'e da jawo jikkarsa dake ajiye ya sagala a kafad'a ba tare daya damu da nauyin da take da shiba sannan ya rufe qofar yazo daidai saiti glass d'in qofar da little ke zaune had'e da miqa masa hannu, yana fad'in.
"Madallah fa, nagode sosai ALLAH yasaka da alkhairi kuma yayi albarka."