← Book details Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 123 OF 160

Sashe 123

Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ana kammalawa mutanen da aka tanada saboda su kula da jin dad'in baqin da suka halarci taron had'e da ci da shansu suka fara zagayawa da abintayye kala kala suna a'ajiyewa tare da gorunan ruwan sha masu sanyi da kwalayen lemuna kala kala, ga kaji da snacks suma sai abunda mutum kesonci zai zab'a yaci, _😅acan nahango mutanena su aunty fareeda da meamah dasu teemah gabs anbaje anata Jan gara, aunty fareeda kam sai tura kaji takeyi acikin jikka wai zata riqawasu arfatu, gani awaje an hanani shiga sai ta taga nake samun d'auko maku rahoto, nahadiyi yawu yafi a qirga amma babu wanda yakulani sai aunty maijidda data hangoni a jikin taga ta taso saye da hijab d'inta tundaga sama har qasa riqe da take away guda biyu duka naman kajine aciki ta miqomun tana fad'in, My billy ungo kirage zafi da wannan tunda sun hanaki shigowa, kece da naci komai sai kice sai kin d'au rahoto kin fad'awa mutane shiyasa suka saka maki idanuwa suka hanaki shigowa, ALLAH idan bakibi hattaraba ko motar kai amaryar ma baza'a bari kigani ba sai dai kawai kiji ance ta haihu nace, to aunty Maijidda taimakon da ruwa da lemun mana, ga samosa can da tsinken tsire guda hud'u ki had'omun dasu, dariya tayi had'e da d'aukomun tace, yo my Billy kice ke kinfima wud'anda suka samu shigowa murewa_

Saida kowa yaci yaqoshi hani'an mari'a sannan motocin suka sake kwashesu suka mayar dasu gida wasu kuma daga nan suka wuce gidajensu suna masu yiwa ango da amarya fatan alkhairi da kuma samun zaman lafiya da zuri'a masu albarka.

Batool nakomawa gida su uncle sukace aje agyarata yanzu za'a wuce da ita gidan mijinta, ai nan take jikinta yafara rawa hawaye suka soma zubo mata tashiga dube duben inda zataga mahaifinta ahankali tana kiran sunansa.

"Abba, abba, abbanah, momy Ina abbana?"

Tafad'a tana kallon matar mahaifin nata, dafata tayi sannan tace

"Ki kwantar da hankalinki kizo muje kigyara zan kaiki har inda yake kinji ko?"

Kamar wata samna batool tace.

"To.." tare da bin bayanta.

Bayan angyarota tana tashin qamshi tako Ina ajikinta mom takaita indasu uncle h suke tanzaunar da ita, hud'uba suka sake yimata kamar yanda iyaye keyiwa 'ya'yansu idan zasuyi aure sannan sukasa aka kira hajia mama ta sake yimata.

Cikin dakiya tace.

"Batool haqiqa yau kin samu cikar burinki duk da kin sab'awa mahifinki awani b'angare, Amma Ina roqon ALLAH kada yakamaki da wannan laifin ya yafe maki, Ina roqonki da kibi mijinki sau da qafa fiye da yanda nake yiwa mahifinki, ki girmama masa iyayensa fiye da yanda kike girmama naki, kishiga gidanki da niyar bautar aure ba kasuwanci ba, kaji tsoron ALLAH, kiji tsoron ALLAH, kiji tsoron ALLAH Kuma kiriqe ibada da kuma addininki, wannan shine nasihata agareki, du abunda kika yimani kuwa nayafe maki duniya da lahira, ALLAH yayi maki albarka yabaki zuri'a d'ayyaba yakareki da sharrin mutum dana aljani da kowace irin halitta, dafa kanta tayi had'e da karanto mata addu'a ta tofa mata sannan tabar d'akin da sauri saboda kukan dake neman kuccikke mata, batool kuwa tsananin kukan da takeyi ko fita sautinsa bayayi saidai sheshshekar da take famanyi kamar za'a cire ranta,

'Dagota uncle Hussain yayi had'e da riqo hannunta na dama uncle Hassan yariqota a gefen hagu suka nufi part d'in Abba inda d'akinsa yake, suna zuwa suka tarar da qofa kulle suka bubbuga yaqi bud'ewa, sunfi mintuna biyar suna magana amma bai tanka suba balle susa ran zai bud'e hakan yasa suka juyo da ita tana kuka tana waiwayen qofar d'akin had'e da kiran sunansa amma yaqi bud'ewa.

Ganin har zasubar part d'in bai bud'eba yasa ta kwace hannuwanta da gudu takoma bakin qofar d'akin tana kuka tana bubbugawa.

"Abbana don ALLAH kabud'e, Abbana, Abbana to kayimun magana ko zan samu albarkarka kaji Abbana, Abbana don ALLAH kabud'e na sake ganinka ko sau d'aya ne.."

Yana jinta yayi banza da ita harsu uncle h suka gaji suka dawo suka riqeta, wani irin kuka tafashe dashi had'e da cewa.

"Wayyo Abbana..za'a tafi dani don ALLAH kafito, abba, Abba.."

Ganin bazai tankata ba yasa taroqi su uncle subarta ko sau d'aya tayi magana dashi, bakin qofar takoma ta jingina tana fad'in.

"Abbana ina matuqar qaunarka, nasan cewa kana fushi dani bisa bijire maka da nayi amma don ALLAH ka yafemun, zan tafi cike da d'imbin kewarka azuciyata, ban sani ba zan dawo agareka ko kuwa rai zaiyi halinsa kafin nadawo gareka idan ka dena fushi dani, zan rayu cike da tsammanin cewa wata rana zaka waiwayeni da idanuwanka na rahama da kuma tausayina, Abba kacire damuwa akaina, natabbata cikin 'yan uwana da yawansu zasu share maka hawayen wannan halin dana saka, kayi haquri nakasa sarrafa zuciyata tafi qarfina akan abunda take so, Ina sonka abbana, Ina roqon ALLAH daya tabbatar da kai cikin amincinsa ya cika qirjinka da farincikinndan kasa sakaka aciki."

Tana rufe baki uncle Hussain yaja hannunta suka fita da ita kuka takeyi sosai kamar ranta zai fita har suka kai bakin motar da zata shiga, tana aza qafarta da sauri ta dawo da ita had'e da juyowa jin takun tafiyar da tasan ta mahaifinta kawai ce, shine yafito yana nufato inda suke fuskarnan tasa ba walwala aciki da gudu tanufi wajensa zata rungumesa yayi saurin dakatar da ita, tahanyar d'aga mata hannu, cak tsaya batare daya damu da wud'anda ke tsaye wajen ba yace.

"Nayafe maki Fatima Amma bisa sharad'i d'aya."

Da sauri ta d'aga masa kai tana qoqarin qarasowa inda yake ya sake dakatar da ita, alokacin su uncle h suma suka matso don sauraren me zaice suma ya dakatar dasu ta hanyar cewa.

"Ina buqatar yin magana da ita kad'aine ba daku ba, kunyi yanda kuke so naqyaleki, kun nuna isarku akanta na amince da hakan ayanzu kuma Ina so in nuna maku tawa isar akanta har ma daku gaba d'aya"

"Batool kije nayafe maki Amma bisa sharad'in karki sake tako qafarki anan gidan har sai lokacin dana barsa ko kuma raina ya rabu da gangar jikina, idan kuma kika kaucewa hakan to kitabbatar babuni babu ke kuma nafiddake a matsayin 'yata, Zaki iya had'uwa da duk wanda kike so ciki harda mahaifiyarki Amma ba'a cikin gidanan ba."

Yana gama fad'ar haka tajuya yanaci gaba da cewa.

"Wlh wlh duk Wanda yasa takarya wannan umurni nawa acikinku to yakarya dangantakar dake tsakanina da ita na uba da 'ya kunji nafad'a maku."

Bud'e da baki suke kallonsa don Basu tab'a tsammanin cewa zuciyarsa zata kasa lanqwasawa ba da kalaman da 'yarsa tayinmasa sai yanzu, asali ma da sukaga yafito sun zata ya saukone ashe wata baqar zuciyarce tasa taso, ai kan su juyo batool tazube awajen some sukayo kanta aguje.

Hajia mamace tafito tana hawaye riqe da cup da ruwa aciki ta yayyafa mata ta farfad'o, tana bud'e ido tafad'a jikin mahaifiyarta tana kuka, d'agata tayi tariqata takaita har cikin mota sannan tace.

"Batool indai ni nahaifeki Ina roqon kibi umurnin mahaifinki tunda yace hakan kad'aine zaisa ya yafe maki, kici gaba da addu'a nima zanyi maki ALLAH ya sassauta masa zafin rai, addu'a ta Kuma natare dake duk inda kika shiga in Sha ALLAH dakansa zai nemeki, b'acin rai yasa dole yayi haka Amma Ina roqon saukowarsa akoda yaushe, kidena kuka kinji ko Nima zanci gaba da rarrashinsa har zuwa lokacin da zai sauko."

Ta share mata hawaye sannan tanufi cikin gida itama tana share nata hawayen da suka jiqa mata fuska...

*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶‍♀️🚶🏻‍♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻‍♂️🚶‍♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎

_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*

_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋

_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞

*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖

*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️

Page___90💎

Ana fara kiraye kirayen sallar asuba little ya miqe daga kan gadon don dama baiyi bacci ba, tun faruwar abubuwan da suka wakana tsakaninsa da ita adaren jiya ya kasa rumtsa idanuwansa sai albarka yake samata, wani irin farinciki da nishad'i marar misaltuwa ya tsinci kansa aciki, tabbas batool alkhairice sosai agaresa domin adaren yau kad'ai ya gamsu da kasancewarta acikin rayuwarsa, kallon yanda take fidda lumfashinta hankali kwance tana barci yayi had'e dayin murmushi yana shafa fuskarta had'e da cewa.

"Waye yafi Abu sumayya samun mata 'yar baiwa kamarki, waye zai kaini sa'ar samun mace tagari a duniya? Gaba d'ayanki komai naki yiyi d'ari bisa d'ari bakida wata matsala, fatana ALLAH yabani ikon kulawa dake sosai ta yanda zanci gaba da alfaharin kasantuwata dake nahar abada."

A hankali tafara bud'e idanuwanta har suka sauka akan kyakkyawar fuskarsa, murmushi ya sakar mata itama ta mayar masa tare da d'ora hannunta akan nasa dake saman fuskarta.

"Lafiya Abu sumayya?"

"Ina fa lafiya nayiwa gimbiyata laifi!"

"Hmm! Ai duk abunda zakayiwa gimbiyarka bazakayi laifi awajenta ba matuqar kayi hakanne don kasamu farinciki."

"ALLAH gimbiya ta?"

"Sosai kuwa." Tafad'a had'e da rufe idanuwanta kamar mai shirin komawa bacci, jawo hannunta yayi ya sumbata sannan yace.

"Nagode sosai gimbiyata ALLAH yayi maki albarka, kin sakani acikin farinciki da bakina bazai iya misaltasa ba kuma komai zsn baki aduniya bazai iya biyan wannan daren alkhairin da kika tanadarmun ba, amma nayi maki alqawarin cewa matuqar muna tare araye zan bautawa soyayyarki har iya qarshen rayuwata, zan kula dake kuma nabaki gatar da bazan tab'a bari hawaye su kwaranya awud'annan kyawawan idanuwan naki ba, Ina sonki da qaunarki acikin zuciyata, rouhina dama dukkanin gangar jikina."

Wata irin ajiyar zuciya ta sauke tashiga bud'e idanuwanta ahankali tana kashe masa su had'e da cewa.

"Idan kayimun haka kagama mani komai Abu sumayya, ka biyani dukkanin dakon qaunarka da nakeyi azuciyata har kabiyoni bashi."

"To kid'auka hakanma tafaru matuqar ina raye, yanzu muje na taimaka maki kiyo wanka kafin a kirayi kiran sallah na biyu."

"Karka damu zan iya da kaina, kaje kafarayi karka rasa jam'i."
Chapter 123 · 0% Book details