Sashe 115
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin tausasa murya da girmamawa duk da kuwa dady ya girmesu yayi masu bayanin abunda ke tafe dasu cewa sunzo nemawa d'ansu ne izinin neman auren 'yar wajensu batool daya had'u da ita acan gidansa lokacin da taje hutu wajen matarsa hajia nafeesa, saboda bawani sanin dady sukayi sosai ba suna dai yimasa kallon sanine yasa sai alokacin suka gane cewa ashe shid'inne mijin hajia nafeesa 'yar qanwar tasu da suke qoqarin tunano inda suka san fuskarsa.
Bayan yagama yimasu bayani uncle Hassan ya sauke ajiyar zuciya had'e cewa.
"To masha ALLAH, kaga ashe kai surukin mune, munata faman laluben inda muka sanka duk ta dalilin rashin qarfafa zumunta, lokacin da kuka iso naso na ganeka amma a Ina shina manta tinda andad'e ba'a had'u ba, zumuncinne yanzu sai ahankali mutane bamu cika bashi muhimmanci ba."
'Dan russuna kai dady yayi had'e da cewa.
"Wlh kuwa, abubuwane da sukayi yawa gashi ba gari d'aya ba saidai ayita haquri."
"Eh da haka kuwa, ALLAH yayi taimako."
"Amin ya rabbi alhaji."
"To alhamdulillah munji abunda ketafe daku kuma munji dad'i da har ALLAH yasa d'anku yaso jininmu, kaga zumunci zai qara qarfafa idan ALLAH ya daidaita abun, saidai wani hanzari ba gudu ba, kinsan ita maganar aure anfiso ayita bisa kan gaskiya da gaskiya, ni da kuka gani tare da d'an uwana annan, qannene ga mahaifin ita wannan yarinya da d'anku keso, ita kuma matarka ya nuna dady, 'yace ga qanwarmu kasani uwa d'aya uba d'aya duk muke ba inki bawai, don haka bazamu b'oye maku gaskiya ba maganganu sun zo mana ko ince sunzo Kai tsaye ga kunnuwan mahaifin yarinyarnan cewa yaronku bayada asali wanda hakan yasa mahaifinta har yayi mata tsakani dashi bayan yasa anyi masa bincike acan garin antabbatar masa da cewa yaron nan bayada uba, kuyi haquri kada kuga nayi maku cin fuska, muna so musan sahihancin maganar ne don shi yayan namu yakafe akan bazata auresa ba sai gashi kuma yarinyar ta sanar damu zancen cewa zakuzo nema masa aurenta, hakan yasa mukayi tunanin zaunawa musaurareku don jin gaskiyar zancen."
Wani irin dimmmmm...baffa yajiya aransa duniyar ta shiga jujjuya masa saboda kalmar da yaji cewa wai jikan nasa shegene bayada uba, badon ALLAH yasa yana zaune bane to da Babu abunda zai hanasa fad'uwa adaidai wannan lokacin, wasu zafafan hawayene suka zubo masa a fuska da sauri yasa hannu yagoge yanajin wani qunci tare da takaicin d'ansa aransa.
Dady kuwa gabansa ne yafad'i jin kalmar da duk duniya mutum d'ayane yaji nayiwa little ita wato matarsa hajia nafeesa wacce baya tantama akan komeye yafaru itace ta assasashi.
Ganin duka yanayin da suka shiga yasa uncle Hussain jin badad'i aransa Amma ya za'ayi dolene suyi haka don susan yanda zasu kamo bakin zaren, cikin tausasa kalamansa yace.
"Ina nemawa d'an uwana dani kaina yafiyarku idan maganganunsa sun tab'a maku zuciya, har ga ALLAH ba muna nufin zamu yimaku walaqnci bane don kunzo neman alfarma wajenmu, a'a kuyiwa maganar kyakkyawar fahimta akan muna so kai tsaye mu binciki sanin kowaye yaronku tawajenku saboda munyarda daku, kuma Ina zaton ko a misulunce hakan ba laifi bane, idan bakwa buqatar hakan kuma to muna baku haquri tare da cewa kubamu d'an lokaci kafin muje muyi bince akai."
Da sauri baba balarabe yace.
"A'a babu buqatar hakan, asalima godiya yakamata muyi maku dakai tsaye kuka fuskancemu da wannan magana batare da kunje waje wurin neman sanin gaskiyarta ba, ni sunana malan balarabe qane ga mahaifin uwar yaron, Ina zaunene awani qauye da ake kira yarimawa, wannan kuma ya nuna baffa sunansa malan Idris Aliyu wato mahaifin baban yaron tare dashi kuma akwai qanensa malan Usman Aliyu, su kuma suna zaunene a qauyen bebeji, shi ya haifi uban wannan yaro da ake shegantawa ni kuma amatsayina na qanen mahaifin mahaifiyar yaron ni nabada aurenta a hannun wannan qanen mahaifin babansa bisa sadaki naira dubu hamsin, zaku iya zuwa atsakankanin wud'an nan qauyukka guda biyu kuyi bincike akan munda maganar alaqarmu don tabbatar da hakan."
A yanayin da yake yimasu bayani duk daqiqancin mutum dole yafahimci cewa yana fad'in gaskiyar zancene daga qarqashin zuciyarsa.
A hankali baffa ya d'ago kai tare da fara basu labarin dalilin da yasa aka jingina jikan nasa da cewa shegene, tun daga farko har zuwa qarshe batare daya b'oye masu gaskiya ko d'aya ba har yana zubar da qwallah, dady me ya d'ora masu cigaban labarin daga qarshe yakira Dr. yace yazo maza maza yana son ganinsa tare da bshi address d'in inda zai iskosu, ba'a jima ba saiga Dr ya iso dady yace ya sanar dasu kowaye little da mahaifiyarsa, kallonsu yayi d'aya bayan d'aya yace
"Meke faruwa dady?, Bazasu bashi auren tabane har sai an bayyana masu abunda yafaru akan mahaifiyarsa?, Ganinku bai isa ya gamsar dasu ko waye Nuraddeen d'inmu ba?, Idan ko hakane inaga babu buqatar hakan saboda babu yaddar da zata jawo auratayya a tsakani."
"Ya isa, kayi abunda nace maka." Dady yafad'a in a serious tone, ganin babu wasa a fuskarsa yasa yafara labarta masu halin daya tsinci mahaifiyar little har zuwa lokacin data had'u da iyayenta agidan mahaifinsa, anan dady yafad'a masu yanda akayi har yasan mahaifin Rashida wato kakan little, lamba da address d'in abokinsa da marigayi ke karb'ar takalmi awajensa Wanda nanne yahad'u da baba yabasu yace suje wajensa suqara yin bincike akai.
Gaba d'aya duk inda ilahirin jikin uncle Hassan da Hussain yake saida yayi sanyi, sosai kunya da dana sanin tambayoyi da kalaman da sukayi masu tarufesa, sun matuqar tausayawa rayuwar baffa tare da jinjinawa qarfin imaninsa haka sun girmamawa karamci irin na surukin nasu wato dady da d'ansa, da za'a samu irin wud'annan mutanen aduniya to tabbas za'a zauna lafiya cikin wadatuwa da ni'imar ALLAH.
Muryar baffa Usman suka jiyo yana fad'in.
"Little dake son yarinyarku ba shege bane kamar yanda kuka jiyo daga bakin qananun mutane dake yiwa alamari hawan qahura, su zauna akai suyi sharhin abunda basuda masaniya akai, mune iyayen babansa kuma da izininmu yaje karatu waje, qaddarawar ALLAH da kuma jarabtawa da wanzuwar alqalamin qaddara akan yaronsa tahanasa dawowa qasarsa zaku iya zuwa can ma'aikatar ilimi a b'angaren qananan malamai dake da rauni data taimaka musu ku bincika don kutabbatar da hakan domin ita taturasu qasar, bamu fidda rai da dawowar mahaifinsa ba a kowane lokace kmar yanda bazamu dena cigaba da rayuwarmu ba har sai lokacin da ALLAH ya dakatar mana da ita, Kuma in Sha ALLAH kusa ko nesa zai dawo garemu don tabbatarwa da duniya cewa d'ansa ba shege bane da yardar ALLAH."
Cikin sanyinyin murya uncle Hussain yace.
"Kuyi haquri, kuyi haquri, shikad'ai zamuce, damu bawai mu muka sheganta yaronku bane, kawai munfad'i abunda mukajine daga bakin wasu, amma yanzu mun gamsu da bayaninku d'ari bisa d'ari, dama haka ubangiji yace,
" _yaa ayyuhallazina amanu injaa akum fasiqun binaba'in fatabayyanu antusibu qauman bijahalatin fatusbihu ala maa fa'altum nadimuun_" ma'ana
" _yaku wud'anda kukayi imani!, Idan fasik'i yazo maku da wani babban labari, to, kunemi bayani, domin kada kucuci wasu mutane acikin jahilci, saboda haka ku wayi gari akan abin da kuka aikata kuna masu nadama_,
Shiyasa dashi yayan namu yayi nasa binciken mukaga yadace mu tuntub'eku da maganar kamar yanda ALLAH ya umurta don kaucewa aikata abunda zamuzo muyi nadama akai kuma alhamdulillah bamu d'auki wani matakiba koyin abunda zaisa muyi nadamar abunda muka aikata, don haka a matsayinmu na iyayen batool mun ba Nuraddeen dama yaci gaba da nemanta har zuwa lokacin da zamu sake waiwayarku akan batun aurensu,"
Cike da farinciki baffa ya d'aga hannu sama yayiwa ALLAH godiya sannan suka had'a baki shida dady dake murmushi sukace.
"Bakomai mungode, mungode sosai ALLAH yatabbatar da alkhairi."
Nan suka shiga musabahar hannaye kowanensu fuskarsa na nuna jin dad'in yanda abun yakasance, suna qoqarin tafiya aka kira sallar magrib, don haka uncle Hassan yaroqesu akan subari sai sunyi sallah sunci abinci sannan sutafi, haka kuwa akayi anan saman dardumar baba balarabe ya jasu limanci sukayi sallah sannan sukaci abincin, cikin qanqanen lokaci suka saba da juna har sukayi musayar lambobi sannan suka wuce cikin yaba nagartar juna da fahimta.
Suna wucewa Abba na isowa wajen kamar zai tashi sama, kallo d'aya sukayi masa dariya ta soma kuccikke masu da sauri suka gintse,
"Nagode da maidani d'an iska da kukayi a matsayina na yayanku, wato ni Ina can zaune ina jiran isowarsu ashe ku har kunyi mani yanda kuke so sai dai cikin anguwa atareni ana tambayar halama yau baqi nayi?, Yau kun nuna mani cewa ba bakin komai nake ba agareku kuma ban isa gareku ba." Sannan yajuya yanufi cikin gida, ayanda yayi maganar yasasu jin cewa kamar basu kyauta masa ba don haka suka bi bayansa suna bashi haquri,
Kusan sati ya d'auka yana fushinda kowa agidan, hatta abincin gidan bayaci, haka kuma baya wuni agida bacci kad'ai ke dawo dashi gidan shima safiya nawayewa zai tafiyarsa, sun matuqar damuwa da hakan ganin yanda gaba d'aya gidan yakoma ba dad'i suka dinga binsa suna bashi haquri, saida suka had'a gaba d'aya gidan har matansu da yaransu sukayita bashi haquri sannan suka samu daqyar ya hanqura saidai yatabbatar masu cewa ya haqura kad'aine bisa laifin da suka yimasa amma akan zancen auren batool da wannan yaron har yanzu yana nan kan bakansa.
Qoqarin fahimtar dashi da yimasa bayani sukayi amma sai yaqara birkice masu akan wai shi be yadda iyayensa bane saboda anfad'a masa cewa had'in bakine akayi da mijin hajia nafeesa aka d'auko hayar mutanen da sukazo a matsayin iyayensa.
"Ya ALLAH! Yaya wa Kuma ya sanar dakai haka?, wlh qaryane yaya, mahaifinsa na qasar waje sun riqesa daya gama karatu, don ALLAH Yaya ka tausayawa yaran nan tunda suna son junansu"
Uncle Hassan daya tsani tashin hankali yafad'i hakan cike da damuwa, shi dai hussain tsoron ALLAH ma yahanasa cewa uffan sai kallon yanda yayan nasa ke kumfar baki yakeyi....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️
Bayan yagama yimasu bayani uncle Hassan ya sauke ajiyar zuciya had'e cewa.
"To masha ALLAH, kaga ashe kai surukin mune, munata faman laluben inda muka sanka duk ta dalilin rashin qarfafa zumunta, lokacin da kuka iso naso na ganeka amma a Ina shina manta tinda andad'e ba'a had'u ba, zumuncinne yanzu sai ahankali mutane bamu cika bashi muhimmanci ba."
'Dan russuna kai dady yayi had'e da cewa.
"Wlh kuwa, abubuwane da sukayi yawa gashi ba gari d'aya ba saidai ayita haquri."
"Eh da haka kuwa, ALLAH yayi taimako."
"Amin ya rabbi alhaji."
"To alhamdulillah munji abunda ketafe daku kuma munji dad'i da har ALLAH yasa d'anku yaso jininmu, kaga zumunci zai qara qarfafa idan ALLAH ya daidaita abun, saidai wani hanzari ba gudu ba, kinsan ita maganar aure anfiso ayita bisa kan gaskiya da gaskiya, ni da kuka gani tare da d'an uwana annan, qannene ga mahaifin ita wannan yarinya da d'anku keso, ita kuma matarka ya nuna dady, 'yace ga qanwarmu kasani uwa d'aya uba d'aya duk muke ba inki bawai, don haka bazamu b'oye maku gaskiya ba maganganu sun zo mana ko ince sunzo Kai tsaye ga kunnuwan mahaifin yarinyarnan cewa yaronku bayada asali wanda hakan yasa mahaifinta har yayi mata tsakani dashi bayan yasa anyi masa bincike acan garin antabbatar masa da cewa yaron nan bayada uba, kuyi haquri kada kuga nayi maku cin fuska, muna so musan sahihancin maganar ne don shi yayan namu yakafe akan bazata auresa ba sai gashi kuma yarinyar ta sanar damu zancen cewa zakuzo nema masa aurenta, hakan yasa mukayi tunanin zaunawa musaurareku don jin gaskiyar zancen."
Wani irin dimmmmm...baffa yajiya aransa duniyar ta shiga jujjuya masa saboda kalmar da yaji cewa wai jikan nasa shegene bayada uba, badon ALLAH yasa yana zaune bane to da Babu abunda zai hanasa fad'uwa adaidai wannan lokacin, wasu zafafan hawayene suka zubo masa a fuska da sauri yasa hannu yagoge yanajin wani qunci tare da takaicin d'ansa aransa.
Dady kuwa gabansa ne yafad'i jin kalmar da duk duniya mutum d'ayane yaji nayiwa little ita wato matarsa hajia nafeesa wacce baya tantama akan komeye yafaru itace ta assasashi.
Ganin duka yanayin da suka shiga yasa uncle Hussain jin badad'i aransa Amma ya za'ayi dolene suyi haka don susan yanda zasu kamo bakin zaren, cikin tausasa kalamansa yace.
"Ina nemawa d'an uwana dani kaina yafiyarku idan maganganunsa sun tab'a maku zuciya, har ga ALLAH ba muna nufin zamu yimaku walaqnci bane don kunzo neman alfarma wajenmu, a'a kuyiwa maganar kyakkyawar fahimta akan muna so kai tsaye mu binciki sanin kowaye yaronku tawajenku saboda munyarda daku, kuma Ina zaton ko a misulunce hakan ba laifi bane, idan bakwa buqatar hakan kuma to muna baku haquri tare da cewa kubamu d'an lokaci kafin muje muyi bince akai."
Da sauri baba balarabe yace.
"A'a babu buqatar hakan, asalima godiya yakamata muyi maku dakai tsaye kuka fuskancemu da wannan magana batare da kunje waje wurin neman sanin gaskiyarta ba, ni sunana malan balarabe qane ga mahaifin uwar yaron, Ina zaunene awani qauye da ake kira yarimawa, wannan kuma ya nuna baffa sunansa malan Idris Aliyu wato mahaifin baban yaron tare dashi kuma akwai qanensa malan Usman Aliyu, su kuma suna zaunene a qauyen bebeji, shi ya haifi uban wannan yaro da ake shegantawa ni kuma amatsayina na qanen mahaifin mahaifiyar yaron ni nabada aurenta a hannun wannan qanen mahaifin babansa bisa sadaki naira dubu hamsin, zaku iya zuwa atsakankanin wud'an nan qauyukka guda biyu kuyi bincike akan munda maganar alaqarmu don tabbatar da hakan."
A yanayin da yake yimasu bayani duk daqiqancin mutum dole yafahimci cewa yana fad'in gaskiyar zancene daga qarqashin zuciyarsa.
A hankali baffa ya d'ago kai tare da fara basu labarin dalilin da yasa aka jingina jikan nasa da cewa shegene, tun daga farko har zuwa qarshe batare daya b'oye masu gaskiya ko d'aya ba har yana zubar da qwallah, dady me ya d'ora masu cigaban labarin daga qarshe yakira Dr. yace yazo maza maza yana son ganinsa tare da bshi address d'in inda zai iskosu, ba'a jima ba saiga Dr ya iso dady yace ya sanar dasu kowaye little da mahaifiyarsa, kallonsu yayi d'aya bayan d'aya yace
"Meke faruwa dady?, Bazasu bashi auren tabane har sai an bayyana masu abunda yafaru akan mahaifiyarsa?, Ganinku bai isa ya gamsar dasu ko waye Nuraddeen d'inmu ba?, Idan ko hakane inaga babu buqatar hakan saboda babu yaddar da zata jawo auratayya a tsakani."
"Ya isa, kayi abunda nace maka." Dady yafad'a in a serious tone, ganin babu wasa a fuskarsa yasa yafara labarta masu halin daya tsinci mahaifiyar little har zuwa lokacin data had'u da iyayenta agidan mahaifinsa, anan dady yafad'a masu yanda akayi har yasan mahaifin Rashida wato kakan little, lamba da address d'in abokinsa da marigayi ke karb'ar takalmi awajensa Wanda nanne yahad'u da baba yabasu yace suje wajensa suqara yin bincike akai.
Gaba d'aya duk inda ilahirin jikin uncle Hassan da Hussain yake saida yayi sanyi, sosai kunya da dana sanin tambayoyi da kalaman da sukayi masu tarufesa, sun matuqar tausayawa rayuwar baffa tare da jinjinawa qarfin imaninsa haka sun girmamawa karamci irin na surukin nasu wato dady da d'ansa, da za'a samu irin wud'annan mutanen aduniya to tabbas za'a zauna lafiya cikin wadatuwa da ni'imar ALLAH.
Muryar baffa Usman suka jiyo yana fad'in.
"Little dake son yarinyarku ba shege bane kamar yanda kuka jiyo daga bakin qananun mutane dake yiwa alamari hawan qahura, su zauna akai suyi sharhin abunda basuda masaniya akai, mune iyayen babansa kuma da izininmu yaje karatu waje, qaddarawar ALLAH da kuma jarabtawa da wanzuwar alqalamin qaddara akan yaronsa tahanasa dawowa qasarsa zaku iya zuwa can ma'aikatar ilimi a b'angaren qananan malamai dake da rauni data taimaka musu ku bincika don kutabbatar da hakan domin ita taturasu qasar, bamu fidda rai da dawowar mahaifinsa ba a kowane lokace kmar yanda bazamu dena cigaba da rayuwarmu ba har sai lokacin da ALLAH ya dakatar mana da ita, Kuma in Sha ALLAH kusa ko nesa zai dawo garemu don tabbatarwa da duniya cewa d'ansa ba shege bane da yardar ALLAH."
Cikin sanyinyin murya uncle Hussain yace.
"Kuyi haquri, kuyi haquri, shikad'ai zamuce, damu bawai mu muka sheganta yaronku bane, kawai munfad'i abunda mukajine daga bakin wasu, amma yanzu mun gamsu da bayaninku d'ari bisa d'ari, dama haka ubangiji yace,
" _yaa ayyuhallazina amanu injaa akum fasiqun binaba'in fatabayyanu antusibu qauman bijahalatin fatusbihu ala maa fa'altum nadimuun_" ma'ana
" _yaku wud'anda kukayi imani!, Idan fasik'i yazo maku da wani babban labari, to, kunemi bayani, domin kada kucuci wasu mutane acikin jahilci, saboda haka ku wayi gari akan abin da kuka aikata kuna masu nadama_,
Shiyasa dashi yayan namu yayi nasa binciken mukaga yadace mu tuntub'eku da maganar kamar yanda ALLAH ya umurta don kaucewa aikata abunda zamuzo muyi nadama akai kuma alhamdulillah bamu d'auki wani matakiba koyin abunda zaisa muyi nadamar abunda muka aikata, don haka a matsayinmu na iyayen batool mun ba Nuraddeen dama yaci gaba da nemanta har zuwa lokacin da zamu sake waiwayarku akan batun aurensu,"
Cike da farinciki baffa ya d'aga hannu sama yayiwa ALLAH godiya sannan suka had'a baki shida dady dake murmushi sukace.
"Bakomai mungode, mungode sosai ALLAH yatabbatar da alkhairi."
Nan suka shiga musabahar hannaye kowanensu fuskarsa na nuna jin dad'in yanda abun yakasance, suna qoqarin tafiya aka kira sallar magrib, don haka uncle Hassan yaroqesu akan subari sai sunyi sallah sunci abinci sannan sutafi, haka kuwa akayi anan saman dardumar baba balarabe ya jasu limanci sukayi sallah sannan sukaci abincin, cikin qanqanen lokaci suka saba da juna har sukayi musayar lambobi sannan suka wuce cikin yaba nagartar juna da fahimta.
Suna wucewa Abba na isowa wajen kamar zai tashi sama, kallo d'aya sukayi masa dariya ta soma kuccikke masu da sauri suka gintse,
"Nagode da maidani d'an iska da kukayi a matsayina na yayanku, wato ni Ina can zaune ina jiran isowarsu ashe ku har kunyi mani yanda kuke so sai dai cikin anguwa atareni ana tambayar halama yau baqi nayi?, Yau kun nuna mani cewa ba bakin komai nake ba agareku kuma ban isa gareku ba." Sannan yajuya yanufi cikin gida, ayanda yayi maganar yasasu jin cewa kamar basu kyauta masa ba don haka suka bi bayansa suna bashi haquri,
Kusan sati ya d'auka yana fushinda kowa agidan, hatta abincin gidan bayaci, haka kuma baya wuni agida bacci kad'ai ke dawo dashi gidan shima safiya nawayewa zai tafiyarsa, sun matuqar damuwa da hakan ganin yanda gaba d'aya gidan yakoma ba dad'i suka dinga binsa suna bashi haquri, saida suka had'a gaba d'aya gidan har matansu da yaransu sukayita bashi haquri sannan suka samu daqyar ya hanqura saidai yatabbatar masu cewa ya haqura kad'aine bisa laifin da suka yimasa amma akan zancen auren batool da wannan yaron har yanzu yana nan kan bakansa.
Qoqarin fahimtar dashi da yimasa bayani sukayi amma sai yaqara birkice masu akan wai shi be yadda iyayensa bane saboda anfad'a masa cewa had'in bakine akayi da mijin hajia nafeesa aka d'auko hayar mutanen da sukazo a matsayin iyayensa.
"Ya ALLAH! Yaya wa Kuma ya sanar dakai haka?, wlh qaryane yaya, mahaifinsa na qasar waje sun riqesa daya gama karatu, don ALLAH Yaya ka tausayawa yaran nan tunda suna son junansu"
Uncle Hassan daya tsani tashin hankali yafad'i hakan cike da damuwa, shi dai hussain tsoron ALLAH ma yahanasa cewa uffan sai kallon yanda yayan nasa ke kumfar baki yakeyi....
*ALLAH KAJIK'AN IYAYENMU*👏😭
[11/14, 22:52] Billy S Fari: 🚶♀️🚶🏻♂️ *SANNU SANNU*🚶🏻♂️🚶♀️
💎 _Bata hana zuwa..._💎
_WRITTING BY:_ *BILLY S FARI💎*
_DEDICATED TO:_ *BLOOD SISTER'S (AMZAHFAZ)*💋
_BESTOWED TO:_ *ZAINAB AL-AMIN (MOM NA'EEM)* AND *AMINA UBA AYUBA (OUM ASHFAQ)*💞
*DOMIN FARINCIKINKI SISTER SADIYA ZANGO (MIEMAH)*💖
*FATAN ALKHAIRI AGAREKU MOMMAH ME NANA HAFSAT (MISS XOXO) AND MAMANA HAFSAT RANO(OUM AFFAN)*❤️