Sashe 120
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ya isa haka, ya isa haka nace, bazan ja akan duk wani hukunci da zaka yankewa 'yarka ba, amma Ina so kasani zanyi maka biyayya iya gwargwadon yina amatsayina na matarka saidai Ina roqonka kadaka aibatamun 'yata agabana, domin hakan zai iya jawo duk girmamawa da kimarka da nake gani su zube, idan kace zaka koreta agidanka bazan hanaka ba matuqar zata samu cikar burinta, idan kace indena kulata zan dena matuqar farinciki da kuma addu'a ta natare da ita, amma bazan iya yin shiruba matuqar zaka cutar da ita ta lafuzzan bakinka dake iya aibata mani ita nahar abada agabana domin yin hakan kuskurene kuma illoline masu yawa da zaka jawowa yarinyata, don ALLAH da girmansa kayi haquri kayafewa 'yarka idan zaka iya idam kuma bazaka iyaba Ina roqon ALLAH daya tsare mani ita kuma ya albarkaci rayuwarta yakare mani ita ga shiga dukkanin baqincikin duniya dana lahira, no bana ganin laifin yarinyata kokad'an domin kaine kad'orata akan wannan tarbiyar, don haka fushinka bazaisa na d'au fushi da itaba, saidai zanyi qoqarin dakatar da ita ga dukkanin abubuwan daka fad'a tare da bin umurninka akan wud'anda basu sab'awa ubangijina ba."
Tana gama fad'ar hakan tajuya ta shigewarta kitchen taci gaba da aikinta, wayyo Allah yau ina wuta Abba yakad'ata, tana jinsa yana bambaminsa da fad'ace fad'acensa tayi tamkar ma bata jiyosa ba, don izuwa yanzu yafara kaiwa qarshen haqurinta.
Su uncle h kuwa gaba sukasa batool da little sukayi masu fad'a sosai akan yanda suka tsanantawa kansu soyyayyar junansu dake nema tajefasu cikin mawuyacin hali har suna lurar dasu cewa idan sun kasa jurewa arabasu lokaci na zuwa da ALLAH zai d'auki ran d'aya yabar na d'aya, shikenan sai d'ayan ya kasa rayuwa saboda an d'auke ran d'ayansu? Yakamata su sassautawa ransu yanayin son da sukeyiwa juna izuwa tubalin rayuwa bisa qaddaruwar kyakkyawar qaddara ko akasinta akansu domin hakan shine zaisa su iya canye duk wata jarabawar da ALLAH zai yimasu, kallon batool uncle Hussain yayi had'e da cewa.
"ke kuma ina son kisani cewa kuskurene mai girma bijirewa zab'in iyaye matuqar mai nagartane, haka kaima Nuraddeen taya mai laifi aikata laifinsa shima kuskurene babba domin ALLAH ya haramta sab'awa iyaye."
Gaba d'ayansu banda hawaye babu abunda ke zuba ga idanuwansu saboda jin kalaman dake fitowa daga bakinsa, wani irin tsorone ya ziyarci zukatansu akan rashin sanin ko wane hukuncin zasu zartar masu lura da irin nasihohin da suke yimasu, sun tabbata duk abunda suka fad'a gaskiyane amma taya zukatansu zasu amince sukarb'i wannan gaskiyar dakeda matuqar d'aci azuciyoyinsu, suna wannan tunaninne sukaji uncle Hussain yaci gaba da cewa.
"Sai dai kuma shi fiyayyen halitta kuma annabin rahama yayi mana hani da muyiwa 'ya'yayenmu auren dole sannan yaqara mana da cewa idan wanda muka aminta da addininsa da d'abi'unsa to mu aurar masa dashi, idan mukaqi kuwa hakan zai jawo fitina da fasadi mai girma a doron qasa, bisa wud'annan hujjoji yasa muka zab'i mu aurar daku ga junanku, domin fifita umurnin manzon ALLAH s.a.w akan na yayanmu saboda kaucewa abunda ya tsoratar mana, badon haka ba wlh tallahi kunji na rantse maku koda rayukkanku nafita suna dawowa bazamu tab'a barin ki sab'awa mahifinki ba, bazamu tab'a bari kicutar da zuciyarsa ba saboda ra'ayinki domin muna sonsa fiye da soyayyar da kuke yiwa junanku, saidai son da mukeyiwa manzonmu yasa dole mu ajiye soyayyar da muke yimasa muyiwa ALLAH da mansonsa biyayya."
Kallon little yayi idanuwansa cikin nasa yace.
"Shin ko kashirya kanada muhalli mu aurar maka da batool."
Tun kafin yarufe baki little yashiga kad'a masa kai had'e da cewa.
"Eh uncle."
"Yaushe?"
"Yau..." Little yabashi amsa tamkar anqwato muryar tasa da qarfi tafito, hakan yasa su uncle h sakin murmushin da Basu tashi yiba, ba ko shakka yamatuqar basu dariyar da Saida uncle Hassan yakasa tsaida murmushin nasa yakoma dariya, yana dariyar yace.
"Anya malan Nuraddeen kashirya ayau d'innan? Halama so kake mu d'aura maku aure kawai kawuce da matarka?.
Murmushi ya shigayi yana sosa qeyar kansa saboda wata kunya da yaji ta lullub'esa, baima san ya akayi ya furta hakan ba sai yanzu da uncle ya tambayesa, murmushin itama tayi kanta na duqe qasa tana kallonsa.
Dariya irinta manya uncle Hassan yayi don yana kalle dasu kafin yace.
"To kayi haquri, bazamu d'aura maku aure ayanxu ba domin kada ka d'auka cewa 'yarmu batada gata, batool da kake gani 'yar gatace gaba da baya fiye da yanda kake tsammani saboda haka yanzu kahuta kaci abinci sai kawuce gida, in Sha ALLAH da kanmu zamu nemi iyayenka tunda ka shirya nan da sati biyu sai a d'aura aure idan ALLAH ya yardar mana."
Wani irin murmushi yasaki, lokaci d'aya suka d'ago kai shida batool suna kallon juna tare da yin hamdala acikin zuciyoyinsu, babu ko shakka ayanzu sunada yaqinin cewa sunfara tako matakin nasara nafarko wajen cika burinsu, murmushin itama tayi sannan tamaida kanta qasa, haka su uncle suka cigaba da fira dasu wacce rabinta kusan duk nasihohine masu ratsa zuciya akan auratayya suka yimasu, kafin uncle Hussain yace batool tashiga cikin gida takawo ma little abinci da ruwa, sosai shikam little yasaki jikinsa dasu uncle h sukasha firarsu har tadawo d'auke da tray abinci wanda tanan suka sake fahimtar wani Abu akansa tare da yabawa nagartarsa da Kuma tarbiyarsa.
Tana shigowa su uncle h suka fita sukabar falon yarage daga ita sai shi, Saida tafara zuba masa ruwa a cup yasha sannan tazuba masa abincin a plate ta tura masa agabansa tare da komawa gefe tayi zaune tana kallonsa, tankwashe qafafuwansa yayi tamkar mai shirin d'aukar karatu tare da matsowa da abincin kusa dashi yafaraci, Saida yayi kusan cokali uku tukuna ya d'ago kansa had'e da kallonta yace.
"Gimbiya ke bazakici abincin bane?"
Girgiza masa kai tayi tana kallonsa alamun taqoshi sai shima yature plate d'in dake gabansa had'e da cewa.
"Shikenan Nima naqoshi."
Yafad'a had'e da qoqarin miqewa daga inda yake, da sauri tasauko daga kan kujera tana fad'in
"A'a'ah...don ALLAH kazauna zanci Nima."
"Kin tabbata?"
"ALLAH zanci, kaidai kawai ka zauna kaci naka."
Ta sake turo masa plate d'in abincin agabansa,"
Qinci yayi har saida yaga tazuba nata a plate ta soma ci sannan yayi murmushi had'e da d'aukar cokali yaci gaba dacin nasa,
Bai bar gidan ba sai bayan sallar magrib sannan yayi masu sallama yanufi gidan baba balarabe don bazai iya komawa borno ba alokacin.
Su uncle h kuwa tuni suka kira dady suka sanar dashi zance auren wanda suka ajiye nan da sati biyu, yayi matuqar farinciki dajin dad'i kafin yace yana son subashi dama ya tuntub'i su baba balarabe da baffa idan sun amince da lokacin harma da mahaifiyar yaron kuma sun amince masa da hakan inda sukace yabari da kansu zasu kira baffa su sanar dashi, hakan da sukayi yasashi qarajin dad'i ganin sun martaba wanda shine matsayin mahaifin yaron ayanzu don haka shi sai yakira baba balarabe da Rashida ya sanar dasu komai, ita dai Rashida tasan abunda yafaru tsakaninta da mahaifin batool don haka zuciyarta tashiga kokwanto cewa daqyar idan har da amincewarsa za'ayi wannan auren azahiri kuwa amsawa dady tayi da ALLAH yasa hakan shiyafi zama alkhairi, baba balarabe ma yayi farinciki sosai had'e da addu'ar ALLAH yasanya alkhairi, baffa kuwa amaimakon farinciki damuwace ta sake bijiro masa na ganin jikan nasa zaiyi aure ammababu mahaifinsa alhalin yana raye bai mutu ba.
Washe gari dady yasa Dr yagyara don yana fama da zazzab'i shi bazai iya tafiya ya bashi dubu d'ari yace yaje can kano yasami su baba balarabe da baffa ayanka masu sadaki su biya kafin lokaci yayi,
Bayan Dr yaje ya dawo yamiqawa dady kud'insa had'e da cewa.
"Dady gashi su baffa sunce ayi maka godiya sosai sunayi maka ya jiki da addu'ar ALLAH yabaka lafiya, sunce agaisheki sosai."
"Madalla duk dai kasamesu lafiya ko?"
"Alhamdulillah, kowa lafiya,"
"To ya akayi ka dawomun da kud'in?"
"Eh to, lokacin da aka yanka mana sadaki dubu saba'in ina qoqarin ciro kud'in sai shi kakan little wato baffa yaciro kud'in ya bayar, kaga kuma bazai yuyu nagardan tamasa anan ba saboda yanada haqqi akan jikansa fiye damu,."
"Eh to balaifi hakan ma yayi, haka ake son mutum yakasance mai tsayawa da kuma jajircewa ga dukkanin al-amurran ahalinsa, ubangiji ALLAH yafaranta zuciyar wannan bawan ALLAH bisa nuna godiyarsa agaresa ya maido masa da d'ansa agaresa ko zai samu farinciki."
"Amin dady, wlh dattijon nan kam mutumne, yanada matuqar qana'a da kuma zuciyar yi duk kuwa da qaramcin yalwatuwar da take da ita."
"Sosai kuwa, kaga sanin little jininsa ne kuma babu wanda yake Dole agaresa kamar shi yasa bai tsaya jiran kowa ba yayi abunda yakamata, kaga yanzu sai kaje da wud'annan kud'in kakira little idan akwai wani Abu ahannunsa ka karb'a abawa ita Fatima taje tahad'o masa lefe da sauran abubuwan daya kamata, sannan Ina son gobe kuje kaida d'an uwanka da alhaji sabiu, aminina ayankawa d'an uwanku shakur sadaki shima, idan son samune ma kuroqa amadadina akan abarshi shima nan da sati biyu saboda Ina son ayishi lokaci d'aya dana little, zan kira shi alhaji sabiun in fad'a masa inyaso sai kuje ku samesa can gidansa kutafi, shima shakur d'in ka lalubesa kaji idan akwai wani abun ahannunsa sai akarb'a ahad'o masu lefen atare don bazai yuyuba ace komai yimasu za'ayi kar akashe masu zuciya."
"To dady, Nima zanbasu dubu d'ari shida, faruk kuma yabasu hud'u sai ahad'a da abunda aka samu ahannunsu aje ahad'o lefen."
"Masha ALLAH Dr, ALLAH yayi maka albarka, haka ake son babba akoda yaushe ya zamana dashi naqasanshi zasuyi koyi, ALLAH yaqara had'a mani kawunanku baki d'aya yakareku daga sharrin maqiya."
"Amin dady, bari intafi"
Dr yafad'a had'e da miqewa yana maijin dad'in addu'o'in daya yimasa,
Tana gama fad'ar hakan tajuya ta shigewarta kitchen taci gaba da aikinta, wayyo Allah yau ina wuta Abba yakad'ata, tana jinsa yana bambaminsa da fad'ace fad'acensa tayi tamkar ma bata jiyosa ba, don izuwa yanzu yafara kaiwa qarshen haqurinta.
Su uncle h kuwa gaba sukasa batool da little sukayi masu fad'a sosai akan yanda suka tsanantawa kansu soyyayyar junansu dake nema tajefasu cikin mawuyacin hali har suna lurar dasu cewa idan sun kasa jurewa arabasu lokaci na zuwa da ALLAH zai d'auki ran d'aya yabar na d'aya, shikenan sai d'ayan ya kasa rayuwa saboda an d'auke ran d'ayansu? Yakamata su sassautawa ransu yanayin son da sukeyiwa juna izuwa tubalin rayuwa bisa qaddaruwar kyakkyawar qaddara ko akasinta akansu domin hakan shine zaisa su iya canye duk wata jarabawar da ALLAH zai yimasu, kallon batool uncle Hussain yayi had'e da cewa.
"ke kuma ina son kisani cewa kuskurene mai girma bijirewa zab'in iyaye matuqar mai nagartane, haka kaima Nuraddeen taya mai laifi aikata laifinsa shima kuskurene babba domin ALLAH ya haramta sab'awa iyaye."
Gaba d'ayansu banda hawaye babu abunda ke zuba ga idanuwansu saboda jin kalaman dake fitowa daga bakinsa, wani irin tsorone ya ziyarci zukatansu akan rashin sanin ko wane hukuncin zasu zartar masu lura da irin nasihohin da suke yimasu, sun tabbata duk abunda suka fad'a gaskiyane amma taya zukatansu zasu amince sukarb'i wannan gaskiyar dakeda matuqar d'aci azuciyoyinsu, suna wannan tunaninne sukaji uncle Hussain yaci gaba da cewa.
"Sai dai kuma shi fiyayyen halitta kuma annabin rahama yayi mana hani da muyiwa 'ya'yayenmu auren dole sannan yaqara mana da cewa idan wanda muka aminta da addininsa da d'abi'unsa to mu aurar masa dashi, idan mukaqi kuwa hakan zai jawo fitina da fasadi mai girma a doron qasa, bisa wud'annan hujjoji yasa muka zab'i mu aurar daku ga junanku, domin fifita umurnin manzon ALLAH s.a.w akan na yayanmu saboda kaucewa abunda ya tsoratar mana, badon haka ba wlh tallahi kunji na rantse maku koda rayukkanku nafita suna dawowa bazamu tab'a barin ki sab'awa mahifinki ba, bazamu tab'a bari kicutar da zuciyarsa ba saboda ra'ayinki domin muna sonsa fiye da soyayyar da kuke yiwa junanku, saidai son da mukeyiwa manzonmu yasa dole mu ajiye soyayyar da muke yimasa muyiwa ALLAH da mansonsa biyayya."
Kallon little yayi idanuwansa cikin nasa yace.
"Shin ko kashirya kanada muhalli mu aurar maka da batool."
Tun kafin yarufe baki little yashiga kad'a masa kai had'e da cewa.
"Eh uncle."
"Yaushe?"
"Yau..." Little yabashi amsa tamkar anqwato muryar tasa da qarfi tafito, hakan yasa su uncle h sakin murmushin da Basu tashi yiba, ba ko shakka yamatuqar basu dariyar da Saida uncle Hassan yakasa tsaida murmushin nasa yakoma dariya, yana dariyar yace.
"Anya malan Nuraddeen kashirya ayau d'innan? Halama so kake mu d'aura maku aure kawai kawuce da matarka?.
Murmushi ya shigayi yana sosa qeyar kansa saboda wata kunya da yaji ta lullub'esa, baima san ya akayi ya furta hakan ba sai yanzu da uncle ya tambayesa, murmushin itama tayi kanta na duqe qasa tana kallonsa.
Dariya irinta manya uncle Hassan yayi don yana kalle dasu kafin yace.
"To kayi haquri, bazamu d'aura maku aure ayanxu ba domin kada ka d'auka cewa 'yarmu batada gata, batool da kake gani 'yar gatace gaba da baya fiye da yanda kake tsammani saboda haka yanzu kahuta kaci abinci sai kawuce gida, in Sha ALLAH da kanmu zamu nemi iyayenka tunda ka shirya nan da sati biyu sai a d'aura aure idan ALLAH ya yardar mana."
Wani irin murmushi yasaki, lokaci d'aya suka d'ago kai shida batool suna kallon juna tare da yin hamdala acikin zuciyoyinsu, babu ko shakka ayanzu sunada yaqinin cewa sunfara tako matakin nasara nafarko wajen cika burinsu, murmushin itama tayi sannan tamaida kanta qasa, haka su uncle suka cigaba da fira dasu wacce rabinta kusan duk nasihohine masu ratsa zuciya akan auratayya suka yimasu, kafin uncle Hussain yace batool tashiga cikin gida takawo ma little abinci da ruwa, sosai shikam little yasaki jikinsa dasu uncle h sukasha firarsu har tadawo d'auke da tray abinci wanda tanan suka sake fahimtar wani Abu akansa tare da yabawa nagartarsa da Kuma tarbiyarsa.
Tana shigowa su uncle h suka fita sukabar falon yarage daga ita sai shi, Saida tafara zuba masa ruwa a cup yasha sannan tazuba masa abincin a plate ta tura masa agabansa tare da komawa gefe tayi zaune tana kallonsa, tankwashe qafafuwansa yayi tamkar mai shirin d'aukar karatu tare da matsowa da abincin kusa dashi yafaraci, Saida yayi kusan cokali uku tukuna ya d'ago kansa had'e da kallonta yace.
"Gimbiya ke bazakici abincin bane?"
Girgiza masa kai tayi tana kallonsa alamun taqoshi sai shima yature plate d'in dake gabansa had'e da cewa.
"Shikenan Nima naqoshi."
Yafad'a had'e da qoqarin miqewa daga inda yake, da sauri tasauko daga kan kujera tana fad'in
"A'a'ah...don ALLAH kazauna zanci Nima."
"Kin tabbata?"
"ALLAH zanci, kaidai kawai ka zauna kaci naka."
Ta sake turo masa plate d'in abincin agabansa,"
Qinci yayi har saida yaga tazuba nata a plate ta soma ci sannan yayi murmushi had'e da d'aukar cokali yaci gaba dacin nasa,
Bai bar gidan ba sai bayan sallar magrib sannan yayi masu sallama yanufi gidan baba balarabe don bazai iya komawa borno ba alokacin.
Su uncle h kuwa tuni suka kira dady suka sanar dashi zance auren wanda suka ajiye nan da sati biyu, yayi matuqar farinciki dajin dad'i kafin yace yana son subashi dama ya tuntub'i su baba balarabe da baffa idan sun amince da lokacin harma da mahaifiyar yaron kuma sun amince masa da hakan inda sukace yabari da kansu zasu kira baffa su sanar dashi, hakan da sukayi yasashi qarajin dad'i ganin sun martaba wanda shine matsayin mahaifin yaron ayanzu don haka shi sai yakira baba balarabe da Rashida ya sanar dasu komai, ita dai Rashida tasan abunda yafaru tsakaninta da mahaifin batool don haka zuciyarta tashiga kokwanto cewa daqyar idan har da amincewarsa za'ayi wannan auren azahiri kuwa amsawa dady tayi da ALLAH yasa hakan shiyafi zama alkhairi, baba balarabe ma yayi farinciki sosai had'e da addu'ar ALLAH yasanya alkhairi, baffa kuwa amaimakon farinciki damuwace ta sake bijiro masa na ganin jikan nasa zaiyi aure ammababu mahaifinsa alhalin yana raye bai mutu ba.
Washe gari dady yasa Dr yagyara don yana fama da zazzab'i shi bazai iya tafiya ya bashi dubu d'ari yace yaje can kano yasami su baba balarabe da baffa ayanka masu sadaki su biya kafin lokaci yayi,
Bayan Dr yaje ya dawo yamiqawa dady kud'insa had'e da cewa.
"Dady gashi su baffa sunce ayi maka godiya sosai sunayi maka ya jiki da addu'ar ALLAH yabaka lafiya, sunce agaisheki sosai."
"Madalla duk dai kasamesu lafiya ko?"
"Alhamdulillah, kowa lafiya,"
"To ya akayi ka dawomun da kud'in?"
"Eh to, lokacin da aka yanka mana sadaki dubu saba'in ina qoqarin ciro kud'in sai shi kakan little wato baffa yaciro kud'in ya bayar, kaga kuma bazai yuyu nagardan tamasa anan ba saboda yanada haqqi akan jikansa fiye damu,."
"Eh to balaifi hakan ma yayi, haka ake son mutum yakasance mai tsayawa da kuma jajircewa ga dukkanin al-amurran ahalinsa, ubangiji ALLAH yafaranta zuciyar wannan bawan ALLAH bisa nuna godiyarsa agaresa ya maido masa da d'ansa agaresa ko zai samu farinciki."
"Amin dady, wlh dattijon nan kam mutumne, yanada matuqar qana'a da kuma zuciyar yi duk kuwa da qaramcin yalwatuwar da take da ita."
"Sosai kuwa, kaga sanin little jininsa ne kuma babu wanda yake Dole agaresa kamar shi yasa bai tsaya jiran kowa ba yayi abunda yakamata, kaga yanzu sai kaje da wud'annan kud'in kakira little idan akwai wani Abu ahannunsa ka karb'a abawa ita Fatima taje tahad'o masa lefe da sauran abubuwan daya kamata, sannan Ina son gobe kuje kaida d'an uwanka da alhaji sabiu, aminina ayankawa d'an uwanku shakur sadaki shima, idan son samune ma kuroqa amadadina akan abarshi shima nan da sati biyu saboda Ina son ayishi lokaci d'aya dana little, zan kira shi alhaji sabiun in fad'a masa inyaso sai kuje ku samesa can gidansa kutafi, shima shakur d'in ka lalubesa kaji idan akwai wani abun ahannunsa sai akarb'a ahad'o masu lefen atare don bazai yuyuba ace komai yimasu za'ayi kar akashe masu zuciya."
"To dady, Nima zanbasu dubu d'ari shida, faruk kuma yabasu hud'u sai ahad'a da abunda aka samu ahannunsu aje ahad'o lefen."
"Masha ALLAH Dr, ALLAH yayi maka albarka, haka ake son babba akoda yaushe ya zamana dashi naqasanshi zasuyi koyi, ALLAH yaqara had'a mani kawunanku baki d'aya yakareku daga sharrin maqiya."
"Amin dady, bari intafi"
Dr yafad'a had'e da miqewa yana maijin dad'in addu'o'in daya yimasa,