Sashe 5
Sannu Sannu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hannu yabasu suka gaisa kafin yace, "kune iyayen bayin ALLAHn da mukazo dasu?." Cikin rawar murya Abba ya amsa masa da "eh bawan ALLAH mune, Ina zamu ganesu ne, suna ina?." Shiru mutumen yayi kafin ya d'an nisa fuskarsa cike da damuwa yace, "likitoci nakan duba su amma suna buqatar addu'ah sosai, shi namijin sun wuce da shi ICU (internatal care unit) ita kuma macen suntafi da ita gyni emergency." Shiru yayi tare da ciro gilashin idanuwansa yasa gefen babbar rigarsa ya goge k'wallan da suka zubo masa sannan yaci gaba da cewa, "dukkaninsu suna cikin wani mawuyacin halin da addu'armu kawai suke buqata, amma har yanzu ina kallon yanayin da naga baiwar ALLAHn nan aciki kafin suwuce da ita, abun gwanin ban tausayi yanda abun dake cikinta ke faman motsi Yana neman taimako yayin da ita d'in takasa d'aga ko d'an yatsanta da zaya iya bashi koda k'warin guiwa ne na second d'aya, Ina addu'a ubangiji yadubi karamci da tausayi irin na uwa alokacin da rauni yasa takasa bawa d'an dake cikinta taimako da yakawo masu tallafi da kuma agajinsa domin ceto duka rayuwarsu."
Wani irin jirine ya d'ibi su uncle hussain jin yanayin da 'yar d'an uwan nasu ke ciki daya sasu ja da baya tare da fad'awa zaune saman kujerun dake bayansu saboda tsananin tashin hankali suna furta kalmar, "innalillahi wainna ilaihirrajiun." dama shi Abba tunda sukazo suka samu suka lallab'asa ya zauna saboda bawata lafiyar qafafune keda shiba balle yajuri iya tsayuwa na tsawon lokaci, lokacin da yaji wannan labarin sai kawai ya sake fashewa da wani sabon kukan da dama tun d'azu yake yin abunsa saboda rashin sanin awane hali gudan jinin tasa take ciki, kalmar shahadar shima ya Fara maimaitawa had'e da cewa, "Amantu billahi, qadarallahu wama sha'a fa'ala." cikin tausayawa mutumen ke kallonsu kafin yace, "hak'uri zakuyi tare da addu'a kuma kusamu ku matsa inda suke nasan gab ake da anemi 'yan uwansu, ni ina kan hanya tane ta zuwana garin minna, dama tsammanin jiran isowarku anan kamar yanda d'an uwana ya sanar mun awaya shine dalilin daya tsaidani anan saboda nasan kuna isowa dole direct nan (emergency) zaku zo, don haka ni zan wuce, ga wud'annan takardun acikin aljihun namijin aka tsincesu" yaqarasa maganar tare da miqawa Uncle Hassan takardun, har zai tafi saiga wani Dr da shine suka karb'i case d'in anan emergency ya iso wajen had'e da kallonsa yace
"Ahhhh, ranka ya dad'e baka wuce bane?"
"Eh Dr sadeeq Amma yanzunnan zan tafi in Sha ALLAH, wud'annan sune patient relatives na mutanen da muka kawo" yabashi amsa tare da nuna masa su Abba dake zaune kamar ruwa yacisu.
"Masha Allah, ranka ya dad'e to ALLAH ya kiyaye ya kuma saka da alkhairi"
"Amin ya rabbhi" yafad'a tare da bashi hannu sukayi musa baha, kallon su uncle h yayi tare da cewa "duk wani abu daya kamata wannan Dr zai taimaka maku insha ALLAH, aminina ne sosai don haka ku kwantar da hankalinku, pls Dr you should consider..." har lokacin suna riqe da hannuwan juna.
"I will in sha ALLAH" yabashi amsa sannan suka yimasa godiya ya wuce, Dr yace sutashi yayi masu jagora zuwa can ICU d'in sannan suje gyni emergency, juyowar da zasuyi wajen Abba sukaga wayam babu kowa a mazauninsa, hankalinsu tashe saboda sanin yanayin da yake ciki suka fara duddu basa acikin wajen basu ganesa ba, cikin tashin hankali suka yiwa Dr bayanin ko wayeshi da matsayinsa ga patient d'in yace, "karku damu, inaga yakasa jurewane yanufi can, kuzo mutafi can d'in."
A b'angaren Abba kuwa kamar yanda Dr yafad'a kasa jure zama awajen yayi hakan yasa yamiqe lokacin da suke magana ba tare da sun lura ba yakamo hanyar gyni emergency jikinsa na rawa sai faman had'a hanya yakeyi, babu abunda yake buqata alokacin irin yaga 'yarsa kuma yasan ko awane hali take ciki, kasancewar dole sai yafito tacikin emergency ward d'in zai iya isa gyani emergency dake can gefe dasu yasa shurahbil ya hangosa yana harhad'a hanya tare da neman fad'uwa, da gudu yafita cikin motar ba tare da ya tsaya kula yaran dake tare dashi ba yanufi inda yake, da sauri ya qarasa wajen tare dasa duka hannayensa biyu ya rungu mosa yana fad'in,
"Abba ina kuma zakaje haka kai kad'ai, Ina su uncle ne?." 'Dago kai yayi ya kallesa ba tare daya iya furta masa komai ba sai dai ya nuna masa gefen da gyni emergency take da yake ana iya hangota daga nan inda suke, jujjuyawa shurahbil yayi yana kallon ta gefe gefensu ko zai hango su uncle h amma ko alamarsu babu, hakan yasa yariqasa suka nufi wajen, sukuwa 'yan biyun ganin yabar gambun motar abud'e yasa suka fito suma suna 'yan dube dube ta gefen, dai dai lokacin mutumen daya biyo bayansu Abba da mota shima yayi parking motarsa wajen tare da fitowa da sauri, cike da mamaki ya nufo wajensu tare da kamo hannun d'ayar yace,
"Ina zakuje ne?"
"Baba zamuje yabamu game." Tafad'a tana tsalle tsalle, tashi yayi ya leqa cikin motar yaga babu kowa aciki gashi kuma anbarta abud'e, gefe da gefe yakalla kuma baiga su uncle ba, hakan yasa ya rufe motar tare da ce masu, "to ina baban naku yaje?." hanyar da shurahbil yabi suka nuna masa. Kallonsu yayi yaga yanda suka jigata yace
"Zakuci abinci?"
"Eh zamuci dama yunwa mukeji" suka fad'a atare
"To kuzo muje" yafad'a tare da riqo hannuwansu, d'ayar ce ta wafce hannunta had'e da cewa, "ni bazan jeba." Itama d'ayar ta wafce hannunta had'e da cewa "nima bazan jeba" haddasu maqale kafad'a, tsaye yayi yana kallon su cike da burgewa kafin yace,
"To zaku zauna anan inje inkawo maku abinci?."
"Mu baba zamu bi."
"Haba yaran baba ai bakusan inda zaku ganesa ba tunda yayi nisa, ku zauna anan karkuje ko ina bari naje nakawo maku abinci kuci kunji ko?"
"A'a sai dai ka kaimu wajen dady da ummie zasu bamu abinci muci ko hassana!" d'ayar tafad'a tana kallon 'yar uwarta,
"Eh, ke ummie ke baki ni kuma dadynah take bani abaki ko"
Tsayawa yayi yana kallonsu cike da jin wani farinciki aransa wanda baisan dalilin saba, yanayin surutunsu na matuqar burgesa wanda yanzune ya gano wacce taqi karb'ar ruwa a hannunsa d'azu itace hassana kuma itace tafara cewa baza take ba, d'ayar kuma itace hussaina wacce ta d'an karce a gefen kuncinta na dama, wani irin tausayinsu ne yaji ya rufesa tunawo da halin da iyayen nasu keciki yayi tare da addu'ar ALLAH yatashe masu da kafad'unsu, juyawa bayansa yayi ya hango d'aya daga cikin security d'in asibitin yamik'e tare da isa wajensa yabashi hannu suka gaisa sannan yace
"Don ALLAH ko zaka iya kula mani da yaran can kafin inje indawo?."
Ganinsa babban mutum yasa yayi saurin cewa, "Babu damuwa Alhaji indai zasu zauna." Don yasan dole za'a shafa masa wani abun, komawa wajensu yayi yariqo hannunsu yace,
"Yawwa yaran baba, kuzauna anan kafin babanku yadawo zanje nakawo maku abinci kunji ko?." Da sauri yabar wajen yanufi wani waje da ake saida abinci cikin asibitin aransa yana addua'ar yana saqa wasu abubuwa.
Cikin mintuna biyar yaje ya siyo abincin ya dawo ya taddasu tare da security d'in sai faman surutu suke yimasa tamkar sun sanshi, murmushi yayi sannan ya bud'e bayan motarsa ya d'auko wata carpet mai girma ya shinfid'a cikin inuwar tare da aje abincin hannunsa sannan ya jawosu ya zaunar dasu ya bud'e masu abincin ya tura masu a gabansu, d'aya daga cikin take away d'in da yayo ya sake d'auka ya miqawa security d'in dama donsa ya siya tare da gorar ruwa d'aya da kuma lemu yanata godiya.
Kallonsa sukeyi sana kallon abincin batare da kowacensu tasa hannu ba yace, "kuci mana." Girgiza masa kai sukayi alamun bazasu ciba yace
"Meyasa" atare sukace "dady yake bani idan zanci" itama d'ayar tace, "ummie take bani abaki." Shiru yayi kafin yajawo gorar ruwan d'aya ya wanke hannunsa tare da d'ibar abincin yafara basu abaki ahankali, idan yaba wannan yaba wannan yana jin wani irin farinciki ya mamaye masa zuciya.
Shurahbil kuwa suna isa gyani emergency sukaga wasu nurses aguje sun wuce da oxygen cikin theater room d'in dake laqe da wajen, bayan kamar mintuna bayar suka wasu sun sake wucewa da wani aguje, tsaye sukayi tare da rashin sanin abunyi data inda zasu fara, sunyi minti uku a tsaye kafin suga wata docter tafito daga cikin wani office dake kallon d'akin theater d'in da sauri shurahbil ya tareta had'e da cewa,
"Assalamu alaikum, don ALLAH Dr ko nanne aka kawo wata patient da suka samu accident mai juna biyu?" Don kallo d'aya zakayiwa matar katabbatar da cewa ita d'in cikakkiyar likita ce,
"Eh nanne, yanzu haka ita aka gama yiwa tiyata, ko kune relatives nata?." Ta tambayesa atak'aice
"Eh mune Dr yafad'a tare da gyara tsayuwarsa da alama yana son jin qarin bayanine daga bakinta, amma ga mamakinsa sai yaga tawuce cikin d'akin ba tare data sake cewa komai ba,
Dr sadeeq kuwa koda sukaje ICU d'in yashiga d'akin da ake duba Abu sumayya ya tarar ana k'ok'arin gyarasa saboda mai kowa mai komai ya amshi abunsa wato dai ALLAH yayi masa rasuwa, rufe idanuwa yayi cikin jimami tare da girgiza kai sannan yanufi wajen wani dr dake tsaye akan gawarsa yana qoqarin had'a bayanan tabbatar da mutuwarsa bayan dogon bincike da suka gudanar akanta, kallonsa yayi yace
"Ahh..Dr sadeeq kadawo? Kadai ga yanda ALLAH yayi ikonsa akan wannan bawa nasa ko, ya samu internal injury ne cikin k'wak'walwarsa haka kuma zuciyarsa tabuga a sanadiyar tsoro da kuma fargabar daya ziyarcesa a lokaci d'aya Kuma sai akaci sa'a yana d'auke da hawan jini wanda shine ya qara tasiri wajen bugawar zuciyar tasa har tafashe" girgiza kai Dr sadeeq yayi had'e da cewa,
"ALLAH sarki, ALLAH yajiqansa yayi Masa rahama, dama relatives d'insa ne suka iso"
"Ok zaka iya sanar dasu."
"Nooo..bazan iya ba Dr naseer i feel their pain."
"Ba damuwa, bari naqarasa had'e bayanan sai naje na sanar dasu, hak'uri zasuyi don dukkaninmu ita muke jira"
Wani irin jirine ya d'ibi su uncle hussain jin yanayin da 'yar d'an uwan nasu ke ciki daya sasu ja da baya tare da fad'awa zaune saman kujerun dake bayansu saboda tsananin tashin hankali suna furta kalmar, "innalillahi wainna ilaihirrajiun." dama shi Abba tunda sukazo suka samu suka lallab'asa ya zauna saboda bawata lafiyar qafafune keda shiba balle yajuri iya tsayuwa na tsawon lokaci, lokacin da yaji wannan labarin sai kawai ya sake fashewa da wani sabon kukan da dama tun d'azu yake yin abunsa saboda rashin sanin awane hali gudan jinin tasa take ciki, kalmar shahadar shima ya Fara maimaitawa had'e da cewa, "Amantu billahi, qadarallahu wama sha'a fa'ala." cikin tausayawa mutumen ke kallonsu kafin yace, "hak'uri zakuyi tare da addu'a kuma kusamu ku matsa inda suke nasan gab ake da anemi 'yan uwansu, ni ina kan hanya tane ta zuwana garin minna, dama tsammanin jiran isowarku anan kamar yanda d'an uwana ya sanar mun awaya shine dalilin daya tsaidani anan saboda nasan kuna isowa dole direct nan (emergency) zaku zo, don haka ni zan wuce, ga wud'annan takardun acikin aljihun namijin aka tsincesu" yaqarasa maganar tare da miqawa Uncle Hassan takardun, har zai tafi saiga wani Dr da shine suka karb'i case d'in anan emergency ya iso wajen had'e da kallonsa yace
"Ahhhh, ranka ya dad'e baka wuce bane?"
"Eh Dr sadeeq Amma yanzunnan zan tafi in Sha ALLAH, wud'annan sune patient relatives na mutanen da muka kawo" yabashi amsa tare da nuna masa su Abba dake zaune kamar ruwa yacisu.
"Masha Allah, ranka ya dad'e to ALLAH ya kiyaye ya kuma saka da alkhairi"
"Amin ya rabbhi" yafad'a tare da bashi hannu sukayi musa baha, kallon su uncle h yayi tare da cewa "duk wani abu daya kamata wannan Dr zai taimaka maku insha ALLAH, aminina ne sosai don haka ku kwantar da hankalinku, pls Dr you should consider..." har lokacin suna riqe da hannuwan juna.
"I will in sha ALLAH" yabashi amsa sannan suka yimasa godiya ya wuce, Dr yace sutashi yayi masu jagora zuwa can ICU d'in sannan suje gyni emergency, juyowar da zasuyi wajen Abba sukaga wayam babu kowa a mazauninsa, hankalinsu tashe saboda sanin yanayin da yake ciki suka fara duddu basa acikin wajen basu ganesa ba, cikin tashin hankali suka yiwa Dr bayanin ko wayeshi da matsayinsa ga patient d'in yace, "karku damu, inaga yakasa jurewane yanufi can, kuzo mutafi can d'in."
A b'angaren Abba kuwa kamar yanda Dr yafad'a kasa jure zama awajen yayi hakan yasa yamiqe lokacin da suke magana ba tare da sun lura ba yakamo hanyar gyni emergency jikinsa na rawa sai faman had'a hanya yakeyi, babu abunda yake buqata alokacin irin yaga 'yarsa kuma yasan ko awane hali take ciki, kasancewar dole sai yafito tacikin emergency ward d'in zai iya isa gyani emergency dake can gefe dasu yasa shurahbil ya hangosa yana harhad'a hanya tare da neman fad'uwa, da gudu yafita cikin motar ba tare da ya tsaya kula yaran dake tare dashi ba yanufi inda yake, da sauri ya qarasa wajen tare dasa duka hannayensa biyu ya rungu mosa yana fad'in,
"Abba ina kuma zakaje haka kai kad'ai, Ina su uncle ne?." 'Dago kai yayi ya kallesa ba tare daya iya furta masa komai ba sai dai ya nuna masa gefen da gyni emergency take da yake ana iya hangota daga nan inda suke, jujjuyawa shurahbil yayi yana kallon ta gefe gefensu ko zai hango su uncle h amma ko alamarsu babu, hakan yasa yariqasa suka nufi wajen, sukuwa 'yan biyun ganin yabar gambun motar abud'e yasa suka fito suma suna 'yan dube dube ta gefen, dai dai lokacin mutumen daya biyo bayansu Abba da mota shima yayi parking motarsa wajen tare da fitowa da sauri, cike da mamaki ya nufo wajensu tare da kamo hannun d'ayar yace,
"Ina zakuje ne?"
"Baba zamuje yabamu game." Tafad'a tana tsalle tsalle, tashi yayi ya leqa cikin motar yaga babu kowa aciki gashi kuma anbarta abud'e, gefe da gefe yakalla kuma baiga su uncle ba, hakan yasa ya rufe motar tare da ce masu, "to ina baban naku yaje?." hanyar da shurahbil yabi suka nuna masa. Kallonsu yayi yaga yanda suka jigata yace
"Zakuci abinci?"
"Eh zamuci dama yunwa mukeji" suka fad'a atare
"To kuzo muje" yafad'a tare da riqo hannuwansu, d'ayar ce ta wafce hannunta had'e da cewa, "ni bazan jeba." Itama d'ayar ta wafce hannunta had'e da cewa "nima bazan jeba" haddasu maqale kafad'a, tsaye yayi yana kallon su cike da burgewa kafin yace,
"To zaku zauna anan inje inkawo maku abinci?."
"Mu baba zamu bi."
"Haba yaran baba ai bakusan inda zaku ganesa ba tunda yayi nisa, ku zauna anan karkuje ko ina bari naje nakawo maku abinci kuci kunji ko?"
"A'a sai dai ka kaimu wajen dady da ummie zasu bamu abinci muci ko hassana!" d'ayar tafad'a tana kallon 'yar uwarta,
"Eh, ke ummie ke baki ni kuma dadynah take bani abaki ko"
Tsayawa yayi yana kallonsu cike da jin wani farinciki aransa wanda baisan dalilin saba, yanayin surutunsu na matuqar burgesa wanda yanzune ya gano wacce taqi karb'ar ruwa a hannunsa d'azu itace hassana kuma itace tafara cewa baza take ba, d'ayar kuma itace hussaina wacce ta d'an karce a gefen kuncinta na dama, wani irin tausayinsu ne yaji ya rufesa tunawo da halin da iyayen nasu keciki yayi tare da addu'ar ALLAH yatashe masu da kafad'unsu, juyawa bayansa yayi ya hango d'aya daga cikin security d'in asibitin yamik'e tare da isa wajensa yabashi hannu suka gaisa sannan yace
"Don ALLAH ko zaka iya kula mani da yaran can kafin inje indawo?."
Ganinsa babban mutum yasa yayi saurin cewa, "Babu damuwa Alhaji indai zasu zauna." Don yasan dole za'a shafa masa wani abun, komawa wajensu yayi yariqo hannunsu yace,
"Yawwa yaran baba, kuzauna anan kafin babanku yadawo zanje nakawo maku abinci kunji ko?." Da sauri yabar wajen yanufi wani waje da ake saida abinci cikin asibitin aransa yana addua'ar yana saqa wasu abubuwa.
Cikin mintuna biyar yaje ya siyo abincin ya dawo ya taddasu tare da security d'in sai faman surutu suke yimasa tamkar sun sanshi, murmushi yayi sannan ya bud'e bayan motarsa ya d'auko wata carpet mai girma ya shinfid'a cikin inuwar tare da aje abincin hannunsa sannan ya jawosu ya zaunar dasu ya bud'e masu abincin ya tura masu a gabansu, d'aya daga cikin take away d'in da yayo ya sake d'auka ya miqawa security d'in dama donsa ya siya tare da gorar ruwa d'aya da kuma lemu yanata godiya.
Kallonsa sukeyi sana kallon abincin batare da kowacensu tasa hannu ba yace, "kuci mana." Girgiza masa kai sukayi alamun bazasu ciba yace
"Meyasa" atare sukace "dady yake bani idan zanci" itama d'ayar tace, "ummie take bani abaki." Shiru yayi kafin yajawo gorar ruwan d'aya ya wanke hannunsa tare da d'ibar abincin yafara basu abaki ahankali, idan yaba wannan yaba wannan yana jin wani irin farinciki ya mamaye masa zuciya.
Shurahbil kuwa suna isa gyani emergency sukaga wasu nurses aguje sun wuce da oxygen cikin theater room d'in dake laqe da wajen, bayan kamar mintuna bayar suka wasu sun sake wucewa da wani aguje, tsaye sukayi tare da rashin sanin abunyi data inda zasu fara, sunyi minti uku a tsaye kafin suga wata docter tafito daga cikin wani office dake kallon d'akin theater d'in da sauri shurahbil ya tareta had'e da cewa,
"Assalamu alaikum, don ALLAH Dr ko nanne aka kawo wata patient da suka samu accident mai juna biyu?" Don kallo d'aya zakayiwa matar katabbatar da cewa ita d'in cikakkiyar likita ce,
"Eh nanne, yanzu haka ita aka gama yiwa tiyata, ko kune relatives nata?." Ta tambayesa atak'aice
"Eh mune Dr yafad'a tare da gyara tsayuwarsa da alama yana son jin qarin bayanine daga bakinta, amma ga mamakinsa sai yaga tawuce cikin d'akin ba tare data sake cewa komai ba,
Dr sadeeq kuwa koda sukaje ICU d'in yashiga d'akin da ake duba Abu sumayya ya tarar ana k'ok'arin gyarasa saboda mai kowa mai komai ya amshi abunsa wato dai ALLAH yayi masa rasuwa, rufe idanuwa yayi cikin jimami tare da girgiza kai sannan yanufi wajen wani dr dake tsaye akan gawarsa yana qoqarin had'a bayanan tabbatar da mutuwarsa bayan dogon bincike da suka gudanar akanta, kallonsa yayi yace
"Ahh..Dr sadeeq kadawo? Kadai ga yanda ALLAH yayi ikonsa akan wannan bawa nasa ko, ya samu internal injury ne cikin k'wak'walwarsa haka kuma zuciyarsa tabuga a sanadiyar tsoro da kuma fargabar daya ziyarcesa a lokaci d'aya Kuma sai akaci sa'a yana d'auke da hawan jini wanda shine ya qara tasiri wajen bugawar zuciyar tasa har tafashe" girgiza kai Dr sadeeq yayi had'e da cewa,
"ALLAH sarki, ALLAH yajiqansa yayi Masa rahama, dama relatives d'insa ne suka iso"
"Ok zaka iya sanar dasu."
"Nooo..bazan iya ba Dr naseer i feel their pain."
"Ba damuwa, bari naqarasa had'e bayanan sai naje na sanar dasu, hak'uri zasuyi don dukkaninmu ita muke jira"